Share this page
kuma tsakaninta da Elhaji karamin ai sun fi kusa , zasu daidaita kansu ne bi izinillah " Yanzun kam dago kai ya yi ya zubawa mahaifinsa ido, hakama du wani wanda ke wajen ama banda Mama wace ke murmushi itama ta diramar mijin nata da sarakuwarta Hajia ta yi murmushi gannin yannayin TAUFEEK, ta mike tana fadin" Ku karaso mu zauna a yi maganar abinda ya faru jiya, ke yaminah je sako hijab mana in Ni kin rainani kina yawo da rigar nan da hula a gabana Wadinnan din ai sirikanki ne harda uban mijinki ai da kunya ko?" Yumnah ta zubawa Hajia ido, idan har zata iya zuwa dakinta a irin wannan lokacin ai tana iya zuwa ko'ina ma Bata tunanin ko zata iya zuwa wani daki sako hijab maganar da baba ke yi ke neman sakata juwa, dan haka ba tare da ta je din ba ta karasa kusa da TAUFEEK ta zauna a saman kafet din kamar yadda ya yi sannan ta zubawa Baba ido wanda ke saman kujera , hakama su Hajia Dukansu a saman kujerar suke A nutse Baba ya ce" Assalamu alaikum wa rahamatulah, kamar yadda Hajia tace, haka ne, ina son sanar maku ku dukanku abinda ya faru jiya, alhamdulilah daurin auren da muka je da Magidanci aka daura shi , wannan din hukunci ne na Ubangiji, haka Allah ya so, da wannan nake dubanki Yumnah kan maganar, na san me mata ke daukan abokiyar zama, haka kuma ana iya fasarar cewa baki jima a gidanki ba hakan ta faru, ki Kadara cewa Allah ne ya hukunta haka a rayuwarki, dan kin ga Hajia gatanan da mahaifiyar mijinki rana daya na aure su, kowani bawa da irin kadararsa mijinki kansa bai san cewa san daura aurensa da KHAUSAR ba, ita dinma cikin firgicin abin take harda kukan bata so, to gaba daya dai hakuri za'a ba kowa da kuma fatan Allah ya sa KHAUSAR alkhairi ce a garemu baki daya, ban nemawa mijinki auren Khausar dan na ga gazawarki ta kowani fani ba, ban kuma yi haka dan wata mummunar manufa ba, Allah ne ya Kadara ita din matar mijinki ce , ina fatan zaku mana biyayya gaba dayanku ku zauna lafiya" Hajia ta saki wani murmushin gannin irin zazaro idannuwan su Hajia nawarah da ita din kanta Yumnar, Mama kuwa kanta a kasa dama bata dago ba, dan bata da ta cewa a taron da bayanin TAUFEEK kallon fuskar mahaifinsa yake yi tamkar ya ga bako a duniyarsa, Hajia ta gyara zamanta ta ce" To hakurinma da kake badawa Ni ban ga laifin da aka yi ba, aure fa aka ce, in ba'a yi ita aka aurota? Kawai dai batun kishiya ne ba dadi ama in ta yi duba da khausara ai dama kishiyarta ce ba yau ba sai ta ba kanta lafiya a zauna lafiya, magidanci kuwa Ni dama ina hango shi a mace hudu ne, dan in ka yi duba da auren nan sunna ce ta ma'aiki, jikana kuwa baya tsoron uban kowa bale ya ki jera hudu ana masa cenji cenjin tukunya yana rayuwa tamkar da Sarki wannan shine more rayuwa, itama Khausarar da take kukan bata son shi zan koma ne, na sameta , babu mai hannani wanka mata mari a kan magidanci!" TAUFEEK a hankali ya maida idannuwansa ya lumshe , daga zaunen da yake ya gama gane Yaren mahaifinsa da kuma kakarsa, ana nufin cewa auren da aka daurawa Khausar aminiyarsa a jiya da shi ne aka daura shi? Idannuwan nasa ya so budewa a hankali, sai dai da sauri ya bude su sakamakon faduwar Yumnah saman kansa rana jan numfashinta da dukkan karfinta hannunta a damke da rigarsa tana kallonsa a hankali idannuwanta suke rufewa har ta rufe su ruf still tana jan numfashin nan da kyar tamkar wace zata bar duniya A rikice du suka mike, Bama kamar su Hajia Nawarah ba sunna Salalami , dama tunda Baba mai kwanoni ya fara bayanin nan suka kasance a kololuwar mamaki sunna binsa da kallo sai zubewar Yumnah ta saka su mikewa sunna neman daukaka abin fiye da misali Hajia ta rafka salatin itama tana gannin yadda su Hajia suka talafo Yumnah ama ta ki sakin rigar TAUFEEK, haka kuma numfashinta da gaske sama sama yake yi tamkar wace zata summe Da tarin al'ajabi Hajia ta ce" Wai summa ta yi? La ila ha ilalahu Muhammadu rasululahi sallalahu alaihi Wasallam, summa ta yi daga mata abokiyar zama ko me ?" A tausashe TAUFEEK ya kalli Hajiar kasa kasa ya ce" Ki daina ihun nan mana ki yi a hankali bakya gannin halin da take ciki?" Hajia ta yi tsuru tana kallon yada yake magana da wani yannayi na lisilama, sak kamar munafuki, in ba mantawa ta yi ba dazunma da tana bashi abinci ai magana ne ya kasa kuma ya kasa ci da kansa ko? Yaushe ya samu lafiyar talafar wannan tabaryar har yake son mata iya shege? Baba ne ya budi baki shima hankalin nasa a tashe ya ce" Alhamdulilah, mun fa dawo, sai fatan Allah ya bamu ikon yin typing lafiya, ya kuma bamu ikon farantawa junna *DUBUN GAISUWA DA FATAN ALKHAIRI ZUWA GAREKU YAN UWA DA AMINAN ARZIKI, SPCLY SAJIDA PALACE, MEMA ZAN CE? TA INA ZAN FARA? A INA ZAN SAUKE? ADDU'A ITACE TSAKANINA DA KU DA FATAN ALKHAIRI, KUN YI RAWAR GANI NA MAMAKI, KAMAR YADDA KUKA SABA KUN YI MIN ALKHAIRI FIYE DA TUNANINA, ALLAH YA SAKA DA MAFIFICIN ALKHAIRI, ALHAMDULILAH Y'ARKU NA GODIYA, ALLAH YA BIYA, WA'INDA SUKE TAMBAYANA DALILIN SHIRUNA DA YAWA KU YI HAKURI HAIHUWA NA YI SHI YASA, WA'INDA BAN AMSAWA BA KU GAFARCENI , WALAHI MSG DIN DA YAWA SOSAI FA, INA FATAN ALKHAIRIN ALLAH YA KAI MUKU A DUK INDA KUKE, KUN SHIRYA JIN ME ZAI FARU A RAYUWAR KHAUSARA YAR GIDAN ABA DA AMININTA DA KUMA ABOKIYAR ZAMANTA? ME ZAI FARU TSAKANIN MAMA DA ABOKANAN ZAMANTA? MU KAFTA PEOPLE๐Ÿ˜Œ๐Ÿ˜Œ๐Ÿ˜Œ* ๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’” *DA CIWO A ZUCIYATA* ๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’” _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4๏ธโƒฃ3๏ธโƒฃ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicรฉ Lait de nuit Parfums dรฉsodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waษ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษ“i wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ Baba ne ya budi baki shima hankalin nasa a tashe ya ce" Subahanallah, yaya kun ririketa kun gaza dagata, dagata TAUFEEK mu je asibiti dagata mu je" Mama dake tsaye tana jiran gannin su Hajia in kamata zasu yi su kamatan ama sai wani daukaka abin suke ne, Hajia baba kuwa dama hannayenta biyu a kirjinta banda harara babu abinda take makawa magidanci dan bata taษ“a tunanin zai samu karfin tare wannan matar ba shi da ba lafiyar kirki ne da shi ba? A nutse mama ta dan matso ta ce" Hajia dan gyara in gani" Hajiar ta dago ta dubi Mama, ta ga Maman sosai fuskarta a hade, abinda bata taษ“a gwadawa ba, kai abinda ya shafi magidancin nema Maman tana matukar nuna kara da kauda kai, da dan mamaki ta matsa din ta bata waje Da kula sosai Maman ta ce" Sai an kaita asibiti ne? Numfashin nata nake gani sama sama Elhaji?" Shi da kansa ya yi mamakin wannan lamari na mama duda halin da yake ciki na rabuwar tunani da kuma matarsa mai dauke da dan tayin cikinsa dake kwonce saman jikinsa idannuwanta a rufe ruf tana kokowa da numfashinta, da kula ya ce" Yumnah, Yumnah hey......" Mama ta duka daf da su sosai , da kula ita dinma ta dafa bayan Yumnar a hankali tana dan shafa kanta ta ce" Daughter, Please calm down, kin san halin da kike ciki kar ki janyowa kanki wani ciwo a kan abinda ya riga ya faru, Please calm down...." Hajia Baba ta sake yin KISKIRIM tana bin kowa da kallo Baba dake tsaye ya bi Hajia Fatahiya da ido wace ta fita tana dana waya cike da basar da uban kowa, wayar Tata kuwa ba kowa take nema ba sai uwar Yumnah, domin tsabar bin salsala irin na kuturta bin dan aboki har numbar junna ne da su sunna zumunci irin nasu Baba ya ce" Ka dauketa mu je asibiti ba wata kama ce da ita ba?" Sai yanzu TAUFEEK ya sauke ajiyar zuciya , shi kokarinsa na gannin ta daina jan numfashinta ne, ama firr abu ya gagara , dan haka ya mike tsaye tsaf da ita a jikinsa tamkar ya dauki yar jaririya ya juya ya nufi hanyar fita da ita dan bin umarnin iyayensa cewar a sadata da asibiti Hajia ta rafka salati harda talabe haba, tana biye da su ta dan riko hannun baba ta ce" Ka san wa bilahilazi yaron cen dazu sai da na masa dan jagora na fitar da shi daga dakinsa na sauko shi kasa na bashi abinci, dan sak yace da Ni baya gani jinninsa ya hau, ka ga wannan abar ta suma ya dauketa, to ko dai Mayu suka rike shi kuma yanzu suka sake shi da na yi da gaske?" Baba mai kwanoni ya yi murmushi ya ce" Hajia ai saukin dai ya samu ne kawai, Allah dai ya tsare gaba" Har kusan babar motarsa suka karasa Mama ta bude bayan motar ta shiga ba tare da ta bada damar wata zata rakata ba ta masa alamar ya sako Yumnar Hajia ta zagaya gidan gaba ta bude ta shige tana fadin" Mika mata ita mu je, bayanin dan tayin nan ya fi komai tsaya min a rai mu je , sai mun dawo " Baba mai kwanoni ya yi murmushi bayan motar ta fice a gidan, watau sosai ya yi mamakin mahaifiyar TAUFEEK yau gannin idonsa itace ta yi gaba da lamarin yaronta, ya kuma ji dadi mai girman gaske, sai kuma TAUFEEK din dake hade girar sama da ta kasa na rashin kunya Sunna isawa asibitinsa kamar yadda dokar wajen take idan har aka kawo daya daga cikin dangin wani ma'aikacinsa, Wada suke da kusanci sosai kama daga mahaifiya, mahaifi, mata, ya'ya to ba za'a duba marar lafiyar da mutumen ba dan gudun rikicewa da sauransu , dokar kuma na kan kowa ne ba iya ma'aikatan ba, har shi mai wajen, dan haka sunna isawa aka dorata a kujerar tura marar lafiya aka shige da ita bangaren emrgency, shi kuwa ya zauna a office din doctern dake aiki a ranar a hankali ya jinginar da bayansa bayan doctern ya fitar masa da ruwan roba ya ajiye masa sannan ya fita da sauri ya tarda abokanan aikinsa dan bata taimakon gaggawa Cikin ikon Allah a lokaci kankanin aka samu aka daidaita bugawar zuciyarta sannan aka tsayar da zubar da jinin da ta fara , sai dai kukan da take yi sun gaza hannata shi, sun yi iya yinsu dan gannin ta daina kukan ama ta kiya, uwa uba tunda suka daidaita harkar bugawar zuciyarta ya zamto ko me aka zo za'a saka mata sai ta karanta a zaune cir a saman gadon take hakan ya sa ta ki a saka mata alurar barci, abinka da wace take da damar dakatar da su din ne, domin da wani ne gaskiya Bama zai tarki haka ba Docter Muktar ya dubi Nurse Halima da kula ya ce" Ina ga ki tabo docter, dan kar ya mana fadan cewa a kan me zamu saurari ra'ayinta kin san baya son wasa da irin haka" Nurse Halima ta fitar da numfashi tana cire safar hannunta ta ce" Ok docter" Fitowa ta yi da dan gaggawa dan karasawa office din docter Ahmad din dan ta isar da sakonsa, sai dai tana fitowar ta samu wajen dakatawar ya cika sosai, dan kuwa matan Elhaji mai kwanonin sun karaso su dukansu, haka kuma mahaifiyar Yumnar da yayarta wace ta zo gannin jikin mahaifinsu da ya yi yar jinya su dinma sun karaso din, sai dai yannayin mahaifiyar Yumnar sam ba alamun sassauci a fuskarta kamar yadda yannayinta yake Tunkarar Nurse Halima ta yi , fuskarta a hade hakama yannayinta ta ce" Nurse yaya jikin yarinyata? Ina fatan tana iya mikewa mu je gida?" Yayar Yumnah dake tsaye kusa da Hajia ta yi gagawar kallon mahaifiyar Tata, 'ya ALLAH' shine abinda ta ayana a cen kasan zuciyarta, shin yaya zata yi da wannan fitina ne? Ama a gaskiya wannan mata da ta kirayi mamansu ta ziga rikicin nan bata yi masu adalci ba, yanzu gashi tunda mahaifiyarsu ta zo ko gaisar da iyayen TAUFEEK din bata yi ba sai fizge fizge take yi har ta saka Hajia gaishe da ita cike da mamakinta, sai kuma ga wata Maganar? Nurse Halima da kula sosai ta ce" Sorry Hajia, matar Sir ce a ciki, jikinta da sauki sosai sai dai ba maganar tafiya da ita yanzu, ki dan yi hakuri zan je wajen sir din ne" Da sauri mahaifiyar Yumnah ta dan tareta ta ce" ki dan dakata, ina son shiga ganninta, du wani wanda zai ce wani abu a kanta bayana yake dan nice mahaifiyarta, ina bukatar a bani y'ata na cenza mata wata asibitin!" Da sauri yayar Yumnah ta matso ta ce" Mama, dan Allah ki yi hakuri ki zo ki zauna" Rai bace ta juyo tana daga hannunta kusa da ita ta ce" Ke Akilah walahi idan kika yarda kika kawon raini a wajen nan zan dauke fuskarki da mari, in ke baki san zafin Yumnah ba Ni na san ciwon abata idan ba zaki iya ganni ba kauce ki koma gida!" Wani tsadadan murmushi Hajia Fatahiya ta saki tana sake talabe jaririyarta, hakama Hajia Nuwairah ta dauke kanta tamkar basa wajen Hajia ta shiga rafka salati tana kallon mahaifiyar Yumnah, lokacin ne kuwa Nurse Halima ta wwucewarta dan ta kula abin na nema ya zama family isu Hajia ta ce" Ikon Allah, wai kamar wace kike yade yaden magana a wajen nan , Ni wama ya sanar maki da maganar nan ne? Mu bamu isa mu kula da ita bane sai an taso ki? Aure ne fa aka daurawa magidanci Bama shi ya je ya nemi auren ba shine zaki zo kamar kubunuwa kina magangannu kamar wace ke daf da kyatsa ashariya? Allah dai ya sa ba magidanci kike son fadawa magana ba , dan da wahala na iya kawar da kaina kowani shashasha ya wulakanta min jika, da kika ganni nan babu irin fadan da ban gani ba, ke karama ce, in zaki nemi kawo min raini a duniyar magidanci in dauke fuskarki da mari ba wani abu bane a wajena! Ke yau ga salamamiya, an yiwa yar taki kishiya kuma ubanda ya kirayeki ko waye ya kuka da kansa, ai ji ji zaki yi dan ba abin a boye bane, yaro kuwa da kudinsa da lafiyarsa akoy wanda ya isa ya tsayar da shi a daya kwalin kwal ? Ai hudu cifff zai jera maki gani ya kauda idannuwansa!" Hankali tashe Akilah ta karasa tana kokarin riko hannun Hajia ta ce" Hajia, dan Allah ki yi hakuri, duka abin nan an samu rashin fahimta ne, irin yadda aka sanar da momynmu maganar auren da rashin lafiyarta ne ya tayar mana da hankali, ama ba maganar wulakanta TAUFEEK,, itama momy ba zata yi haka ba , an riga an zama daya ai du wata fitina ana fatan Allah ya tsare ta, aure kuwa ai nufi ne na Allah dan ya yi aure ai ba shine damuwar ba in dai mutuniyar kirki ce fatanmu Allah ya hada kansu ya bada zaman lafiya............" Magana Akilah ke yi da dukkan gaskiyarta, burinta ta katse fitinar da take gannin na kokarin Kunno masu a tsakaninsu, bayan ita fitina farkonta aka sani ba'a san karshenta ba, kuma ko ba komai a duniyar hausawa ake kuma musulmai, idan har aka yi duba da irin yannayinsa bata san lafiyarsa ba ama a tsarin dukiya da yannayin nasabarsa tara mace hudun da kakarsa ke ambata ba laifi bane, dama an umarta a yi idan za'a iya kula da su a fita hakinsu ne, a nan bata ga abin rikicin nan ba, abinda ba'a yiwa kanwarta adalci ba daya ne tak, shine aka yi ba'a sanar mata ba, dole ne a ji ba dadi, ama idan rai ya bace hankali ya tashi sai a yi shiru a yi ta ambaton sunnan Allah sai ka ga komai ya zo da sauki Tana rike da hannun Hajiar wace ta zuba mata ido tana kallonta alamun jikin Hajiar kamar ya fara yin sanyi jin kalaman Akilar suka ji an fizgo Akilar, basu yi wata wata ba suka ji dauke fuskar Akilar da zazafan marin da ya saka MAMAN TAUFEEK dago kanta daga wajen da take kallo tana jan carbinta irin na jikin yatsar nan fari kal mai yar kyalkyali a jikinsa ta sauke dubanta a kan su gaba dayansu, daidai lokacin ne kuma TAUFEEK ya karaso, ya dan samu tsaikon isowar ne sakamakon rigar aikinsa da nurse Halima ta je cen sama office dinsa ta dauko masa da takalmin aiki da Safar hannu da abin auna awon zuciya A nutse yake karasowa, idannuwansa a kansu baki dayansu, tun daga kan iyayensa har na matarsa A hankali ya sauke dubansa a kan Akilah, wace ta dafe fuskarta kanta a kasa tuni hawaye ya fara wanke mata fuska, a haife ko Akilah ya girma bale Yumnah, sai dai a yadda take mutuntashi yakan ce mata auntynmu , itama sai tace da shi yayanmu dan girmama junna Kai ya dauke ba tare da ya iya cewa kowa komai ba ya ratsa su, cike da kamala da yannayi irin na baban likita ya shige ciki, hakan ya sa gaba daya suka bi shi da kallo kowa na ayana abinda yake ayanawa a ransa dangane da dan uwansa a kan TAUFEEK din Yana shiga dakin ya karasa wajen allurar da docter Muktar ya haษ—a ya amsa a nutse ya karasa gaban gadon nata ya janyo kujerar dake gaban gadon ya zauna sannan ya zuba mata ido bayan ya dauki audugar da zai yi anfani da ita dan yi mata allurar tunda ba karin ruwa ta yarda aka jona mata ba Numfashi ta ringa ja tana kallonsa, kallo irin kamar ta ga wani maciyin amana, dubansa take yi kamar wace ta ga bakinta, tarin hawayen da ya cika gurbin idannuwanta kuwa na masa nuni da tashin hankalin dake saman harshenta, sai dai tarin firgicin da ya sameta, da irin yadda ya kasance mai tasiri a dukkan motsinta ya hannata iya budar baki bale har ta masa rikicin da take jin tana iya yi masa a kan maganar da ta gama yankewa kanta ko ita ko wace ake nufin an aurawa mijinta! A hankali ta budi bakinta gannin ya kama hannunta ya daura yar igiyar da zata bashi damar samun jijiyar da kyau sannan ya rike audugar a nutse ya goge bayan hannun nata, ita kuma ta budi baki ta ce" Yayanmu, dan Allah ka ce min ba zaka iya amsar auren nan ba, na san ba son ranka bane, kana da damar sakin............." "Yumnah" ya fada a hankali, cike da fitar da amon da ya fi kasarata, ya tsare idannuwanta da manyan idannuwansa, a dole ta sauke dubanta kan sajensa domin kallon ya matukar mata girma A nutse ya maida dubansa ya soketa da allurar ya kunce daurin ya zuba mata ruwan allurar sannan ya zage ya dane da audugar ya ajiye allurar a cikin dan kwanon da nurse ke rike da , shi kuwa yana rike da hannun nata a hankali yana dan murzawa yana kallon fuskarta mai zubar da hawaye har ya dauki mintinan da zasu kai sha biyar sannan ya mike yana gyarata gaba dayanta ya rufa mata abin rufa kadan sannan ya juya bayan ya daidaita mata ac ya fice a dakin yana cire safar hannunsa Yana fitowa ya ja ya tsaya gaban ahalinsa, a yadda ya shige ya barsu yanzun basa hayaniyar, sai dai kana ganninsu ka san kowa a dane yake, sai kuma ya fuskanci abinda ya hanna su hayaniyar vigil din dake tsaye su hudu ne kowane ya hade girar sama da ta kasa sun fada masu cewar du fa wanda ya masu hayaniya fitar da shi zasu yi Da kula ya ce" ๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’” *DA CIWO A ZUCIYATA* ๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”โคโ€๐Ÿฉนโคโ€๐Ÿฉน๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’”๐Ÿ’” _MALLAKIN_ *SAJIDA NIJAR* *FREE BOOK NE* 4๏ธโƒฃ4๏ธโƒฃ *GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA* 1: Duk karyar kada 2: Yar mahaukaciya 3: Neman na kaina 4: Bani da zabi 5: Bak'a ce 6: Kutkale 7: Makauniya ce 8: Mage 9: Duk nisan jifa 10: Idan ka raina inda kake 11: Dutse 12: Alkalamin kadarata 13: Bani da zabi 14: Dakika Biyar 15:Wata kokowar 16: Aure yakin mata 17: Ni zan ladabi 18: Daga tafia daukar soja *Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar* Now *Da CIWO A ZUCIYATA* *Tallah, tallah, tallah* *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* _Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_ Farar Humura Bakar Humura Humura special, humura de bain Humura epicรฉ Lait de nuit Parfums dรฉsodorisant Parfums rideau et dras Lait de nuit Alkam Kulakcam *Waษ—annan kadan ne daga bangaren turaran ruwa* Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes *Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:* mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwarai๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuษ“i wannan number 97 82 44 94 *SECRET DE LA FEMME DU MANGA* Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ๐Ÿ’ƒ Da kula sosai ya ce" Alhamdulilah ta samu barci, ku mu je a maida kowa gida dan basa yarda da yan

Chapter 29 of 47