Elhaji Abdullahi ne ya nemi a yi zaman nan, a sanina na gayyaci HAJIA da mahaifiyar TAUFEEK ne, me yasa taron nan ya taru har haka?"
HAJIA marwa ta dauke kai a ranta tana ayana' sai dai ku yi du abinda za'a yi a wajen nan sai an yi shi da mu!'
HAJIA baba ta ce" Barsu, barsu ai ba komai, su zauna , ina son du wani makiyin ya ringa gannin ci gabansa a gaban idannuwansa, ku sani in har dayarku ce ta hadasa fitina kun yi aikin banza, Magidanci sai ya jera hudu sai dai a yi abinda za'a yi"
Yumnah dake kwonce jikin adarta harara tamkar idannuwanta zasu fita daga jikinta, a ranta kuwa addu'a take yi Allah ya karbi HAJIA KOWAMA ya huta, dan bata tunanin in har HAJIA na kusa zata bari su rayu cikin Salama ita da mijinta
Mahaifin Yumnah ya fitar da iskar bakinsa, a tausashe sosai ya ce" A yi hakuri HAJIA, a yi hakuri, Ni dama na nemi zaman nan ne dan na bada hakuri, domin ban san iya girman abinda mahaifiyar Yaren nan ta aikata ba, sai dai kamar yadda kika sani wani lokacin mata kan yi gaban kansu su manta du wani girma da ALKHAIRI su aikata aiki irin na son zuciya, Aure babu inda zai je, wannan yarinya Allah ya kadarta matar Elhaji ce, babu mai raba auren nan sai in Allah ne ya hukunta, in banda son kai irin nata da ace Tata ce aka aura zata so a maishe mata ita karamar bazawara?....."
"Elhaji, Walahi, Walahi Walahi da a mata irin wannan auren gwara ace ba'a yi ba ka ji na rantse, nawa take ne Yumnar? Gata da yaron ciki, ba'a duba halin da take iya shiga ba shikennan sai ace an mata kishiya ko sanar mata ba'a yi ba?, To Walahi in saki take so a sakar min y'ata cen ya karata da uwar matan!" Mahaifiyar Yumnah ta fada tana fashewa da kuka tana duban mijinta, wanda ya yi mutuwar zaune harda dafe baki
Da mamaki ainun HAJIA ta ce" Ahaf, Allah dai ya sa ba irin yan iska ka auro ba Magidanci!"
Mahaifin Yumnah da mamakinta ya ce" Kennan du irin nasihar da na maki bata shiga kunnenki ba? Du irin rarashi da ban baki da nuna maki cewar hakan ba laifi bane tunda ba haramun aka aikata ba baki ji ba? Na nuna maki cewa ki guji janyowa yarki wulakancin namiji wani auren yake karawar ya kuma zane matar gidan a zauna babu abinda za'a yi baki yarda ba Kennan? Nan na fada maki in me kike takama da shi ke da y'arki ku ringa jin tsoron Allah a mu'amalarku ta yau da kullum baki fahimta ba Kennan?, In me kike takama da shi Akoy wace ta dama ki ta shanye, ke dinma da kike wannan ikirarin an fada maki tsoronki ya hannani karra aure? Bani da halin hakan ke kin san dalili da inada hakan da na karra , shine kike jinginuwa da wannan kina neman yiwa kanki mugun abu? Saki ko? Ba laifi, in sakin take so ya saketa ta tashi mu je, kema ki kwashi naki kayan ki barta a nan tunda nine ubanta ki tafi kema gida ki koyo hankali, Ni zaki mayar mutumen banza? Ni zaki wulakanta dan ina rarashinki? Bari ki ji in har Elhaji nada wata wace yake son karawa na rantse maki da Allah sai na yi gaya na tara jama'a kin dora abincin taron karin aurensa, da ke kika haife shi ai ba zaki ce haka ba, kuma da ke kika haifi KHausar din ba zaki ce a zaba ko ita ko matar gidan ba!, Ki kula in bakinki ya kuma budewa kika furtan shashanci a nan zaki gane shayi ruwa ne!"
Shi yake fada HAJIA na sakin murmushi harda mikewa, su Baba kuwa hakuri suke bashi harda Akilah, su HAJIA nawarah kuwa kawunnansu nema suke su fi karfin gangar jikinsu dan kunya da tsoron wannan lamari
Yana huci ya maida dubansa kan TAUFEEK ya ce" mun fi karfin mu zauna muna tambayarku daya bayan daya zata zauna ko a'a, gakanan gata in ta ce ka saketa na rokeka ka saketan ta zo gidan ta sameni ina jiranta, kuma ina neman alfarma Elhaji dan girman Allah yarinyar da aka aura masa ta tare gobe ko jibi, tunda ai ba wata bazawara bace bale ta kama zama a gidansu, dan Allah ka taimaka ta tare , itama mutun ce idan ya so in ta zo Yumnah ki hadiye zuciya ji mutu!"
Daga nan ya mike yana kade babbar rigarsa ya umarci Akilah da HAJIA su mike su tafi
Du yadda baba ya so dakatar da shi kiyawa ya yi a haka suka tafi suka barsu sai su ya su
Ajiyar zuciya Baba ya sauke yana kallon Yumnah dake duke yanzu a tausashe ya ce" Tashi daga duken nan y'ata ki je kusa da Mamanku tashi kin ji?"
Yumnah ta mike daga duken, maimakun ta je kusa da Mama sai ta je kusa da HAJIA ta zauna jikinta har rawa yake yi
Baba ya sauke numfashi ya ce" Allah ya sanyaya, a yi hakuri dai, in sha Allah ko menene ALKHAIRI ne, ku ku tashi ku je bangaren ku tunda an gama, Allah ya sawaka"
Jiki ba karfi su HAJIA suka tafi, aka bar su Mama da HAJIA baba, da Taufeek da baba da Yumnah
Baba ya mike shima yana fadin" Sai da safe bari in je inada aiyuka a gabana, ka sameni da sasafe in sha Allah in baka takardun gidajen nan"
"Kai d'an nan maganar tarewar fa?" HAJIA ta fada tana kallon Baba,
Baba ya dakata ya dan juyo yana rage tsayinsa kadan ya ce" eh in sha Allah zan yi kiran Malam din abinda yace sai a yi"
Mama kanta wasai take jin ranta, baba na ficewa ta mike tana gyara lafayarta ta dan rage tsayinta ta ce" Sai da safe HAJIA "
HAJIA ta ce" Allah ya tashemu lafiya, ki yi addu'a dai kafin ki KWONTA kuma ki rufe dakin da ky, wannan kiyayar fa ta fara bani tsoro kar a bi dare a kasheki in shiga uku, baiwar Allah dubeta Magidanci solo solo da ita tsaf fa ake iya zane maka uwa dan da wahala in tana da karfi"
Mama kam tafiyarta ta yi tana murmushi
TAUFEEK ya juyo ya zubawa HAJIA ido bayan Yumnah ta mike ta haye da gudu gudu tana sakin kuka hajiar ta wani bankare ta ce" Ji abu ana guduma basa juyawa, wai Magidanci haka kake shaΖar bakin ciki?"
A kausashe ya ce" Ke dai ki ji tsoron Allah, kina waje maimakun ke baba in kika buda baki kika yi magana dan ki kashe wuta ne, a'a, kina buda baki dan ki asasata ne, tsufa kike yi kina masifa, ki tuba kar ki mutu a haka !, Kuma ki yarda ki bi Ni Saudiya ban san yaya zan jijigaki kafin na sake ki a zagaye ba, kuma da kike cewa zaki aura min mace hudu kika kuskura kika karan aure sai dai ki zauna da su , a tsaya ana min auren dole dan an ga bana cewa komai, to Mama kika haifa da mai kwanoni ba Ni ba, dilla tashi ki tafiyarki Ni in je in bata hakuri kin wani rikitata"
HAJIA ta yi zuru tamkar ta summa tana kallonsa ya mike yana harhada mata kayan turarenta
Wani haushi ya tukota ta ce" Kai dai munafiki ne, auren dole? Eh lalle munafiki ne kai, yanzu Magidanci Ni zaka Duba kace an maka auren dole? Khausarar nan in tana waje idannuwanka a kan murje bakin siririya yake, in ta mike ka wani yi KISKIRIM kana leke ko dan ina rufa maka asiri? Munafuki sai na karra maka auren , ana maka gata kana ki, kuma zan je in fadawa mai kwanoni cewar kace a zagaye zaka batar da Ni kuma ka min aure, Allah dai ya shiryeka , kuma in ka ba wancen abar hakuri sai na kaika kotu!"......ta karashe tana jan habar zani tana share yan kwallah ta fice cike da haushi, ita ba komai ya fi bakanta mata ba irin wai ya je ya ba wancen hakuri, du irin rashin da'ar da ta maka masu? Lalle
Bai nufi dakin Yumnah ba sai da ya je nasa ya yi wanka ya kimtsa kansa ya gama dukkan abinda yake sabo a gareshi sannan ya nufi dakin sai baza kanshi yake yi
Fitilar a kashe take, ama kuma har yanzu shashekar kuka take yi a saman gadonta a dukunkune
A hankali ya hau gadon bayan ya dafa ya ji daidai inda take kafin ya shige bargon a hankali ya shiga kokarin dago fuskarta a tausashe ya ce"
Kai ina , Ni fa Ni fa Daf nake da gamawa in fara *AZAL* IN SHA ALLAH ππππππ
[7/19, 3:17 PM] Maman Aslam: ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
*DA CIWO A ZUCIYATA*
ππππβ€βπ©Ήβ€βπ©Ήππππ
_MALLAKIN_
*SAJIDA NIJAR*
*FREE BOOK NE* 4οΈβ£8οΈβ£
*GARABASA, GARABASA, PROMOTION, PROMOTION DIN LITATAFAN MARUBUCIYAR A KAN FARASHI MAI SAUKI 1K, YAN NIJAR KUWA 1000 FRANCS CEFA*
1: Duk karyar kada
2: Yar mahaukaciya
3: Neman na kaina
4: Bani da zabi
5: Bak'a ce
6: Kutkale
7: Makauniya ce
8: Mage
9: Duk nisan jifa
10: Idan ka raina inda kake
11: Dutse
12: Alkalamin kadarata
13: Bani da zabi
14: Dakika Biyar
15:Wata kokowar
16: Aure yakin mata
17: Ni zan ladabi
18: Daga tafia daukar soja
*Dukansu a kan farashi mai sauki, zaka saka dubu guda ne domin promotion ne nake yi, ka tuntubeni kan layina kamar haka +227 93 81 16 18, Sajida Nijar*
Now
*Da CIWO A ZUCIYATA*
*Tallah, tallah, tallah*
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
_Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mata, nesa tazo kusa,Amarya ,Uwar gida,Ango da mai gida Har ma da yan mata da samari shin kuna sane da cewa HAJIYA FUSAM ta shirya tsaf domin gwangwaje ku da turarakunta masu dankaran kamshi? Tare Kayan gyaram jiki na musamman ,wanda daga nesa kamshin ki kadai ya wadatar ya isar da sakon zuwanki waje,gidan ki kuwa sai ya zam abun kwatance wajen kamshi, kar na cika ku da surutu bara in fara zayyano su_
Farar Humura
Bakar Humura
Humura special,
humura de bain
Humura epicΓ©
Lait de nuit
Parfums dΓ©sodorisant
Parfums rideau et dras
Lait de nuit
Alkam
Kulakcam
*WaΙannan kadan ne daga bangaren turaran ruwa*
Gagab, sandal flex, Durot, durus, sandal fleur, tafarce, farce, sandal bangui, sandal, hypotonic sandal, al'ut, coktail creation VIP, Gajiji, Mankaji, turaran wutar labule da cafet, Aba malan, boulettes
*Munada bangaren gyaran jiki kamar haka:*
mai mai saka santsin jiki, mai mai kanshi, Kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi santsi da laushi, kayan gyaran jiki mai saka fata ta yi fari, Sabulu mai saka fata ta yi haske, sabulu mai saka fata ta yi santsi, sabulu mai goge yanayin fata, mai wanda baya saka fari mai gyara fata
Sayen na gari mai da kudi gida,sai an gwada akan san na kwaraiππ
Hajiya Fusam na zaune a kasar Niger domin yin magana da ita kai tsaye tuntuΙi wannan number 97 82 44 94
*SECRET DE LA FEMME DU MANGA*
Gidan Kamshi, Sirrin Manyan Mataπππππ
A tausashe TAUFEEK yana kallon yadda gurbin idannuwanta suka yi rado rado fuskarta kuwa har wani hucin zafi take fitarwa ya talabeta sosai a jikinsa ya ce" ya dace zuwa yanzu ki yi hakuri da rigimar nan haka Yumnah, ya dace ki yi hakuri ki dauka haka Allah ya hukunta, kin ga ba ke kadai bace, saka abu a rai kin kusa min asara, bayan wannan fushin nan naki babu abinda baya saka ki, ya dace ki yi hakuri ki yi hakuri an bata maki ama Nima ki min uzuri ki kuma roki ALKHAIRIN dake tare da KHAUSAR a zamantakewarmu"
Yumnah ta lumshe idannuwanta wasu hawaye suka sake biyo wa saman kuncinta, a raunane ta ce" Ta yaya zan iya danar zuciyar tawa? Na rasa ta yaya, tun kafin ka aureni na san cewa ina cin alfarmarta ne, a yanzu da ka aureni ta zamo itama matarka na tabbata zan zamo ne tamkar bola a gidan mijina, ban taba jin kishin mutun da kin kasancewarsa a waje irinta ba, TAUFEEK bana so, bana so Taufeek"
A hankali ya sakata a jikinsa, hannunsa mai dauke da yalwantacen gashin hannu ya saka a hankali ya tare bayan keyarta, da dayan hannun kuwa ya ringa shafa bayanta a hankali idannuwansa a lumshe
Shashekar kukanta ne ya fara daidaituwa sakamakon jinta a jikin da take gannin darajarsa da girmansa fiye da kowani jiki duniya, kanshin jikin da duminsa na sakata barci koda bata yi niya ba, fafadan kirjin na saka tsigar jikinta tashi, a hankali kunnayenta suka ringaa jiyo mata dadadar iskar bakinsa mai dumi a kunnenta
A hankali ya juye da ita a cikin bargon ya zamo tana kasansa shi kuwa a sama
Idannuwanta da sukai shame shame da hawaye yake kallo, cen kasan zuciyarsa kuwa kokowa yake yi da tarin tunanin wace take kila wa kalar rayuwarsa, wace bata kallonsa a matsayin katon dake iya kai keyarta kas,
A hankali ya dan matsewa junnansu waje sosai , yana sinsinar wuyanta a tausashe cike da rarashi ya ce" Idan kika ga mace ta zama banza a gidanta, ita ta fara banzatar da kanta, ko a soyayata da ke ke ba banza bace da ban aureki ba, Yumnah, KHausar ta shigo rayuwarmu, Please kar ki ja, Bana so ki ja, bcz ni da kaina ban kwatanta ja ba, ki yi hakuri zan kasance mai KAMANTA adalci a tsakaninku ko dan gobena, I'm sorry wife "
Kwarai ake cewa, dadadan zance na sanyaya zuciya haka ne,
Yumnah na tare da tashin hankali da bakin cikin auren mijinta, sai dai irin yadda ya bata kulawa ya matukar saka ta ji yar Salama a zuciyyarta, ama tana kan bakanta, ba zata taba son KHausar ba, KHausar makiyaya take a duniyarta, kuma in sha Allah sai ta ci galaba a kanta, ba an aurawa mijinta ita ba, ta yi alkawarin sakata barin gidan nan da kaffafuwanta, in ta san wata bata san wata ba, ko ba komai ta rigayeta tashi tunda har ta rigayeta Sannin waye TAUFEEK a badini!
Da kyar ta samu barci, shi kuma ya mike ya koma dakinsa yana jin yannayinsa du a takure
A kan salaya ya kusan raba dare , yana fadawa Allah dukan damuwarsa
Sai da ya gama sannan ya KWONTA da layin KHausar a hannunsa
Yana so ya saka layin a wayarsa wani abu na hannashi, bai san me yasa yake so du wani abinda ya shige nata ya zamo nasa ne! Shi fa baya tunanin zai iya kawar da kai da wasu abubuwan, ama zai bi a hankali yadda komai zai zamo masa yadda yake so
Washe gari kusan karfe goma ya sauko
Yumnah ya samu a falo tana zaune da wayarta a hannunta
Amsa wayar take yi, gannin ya sauko ta yi salama da wace suke wayar ta ajiye a gefenta tana kallonsa tamkar ta daukeshi da idannuwanta dan ya mata kyau sosai
Zama ya yi gefenta kadan yana amsa gaisuwarta
Sai da ya dan nutsu ya fuskanceta, da yannayi na serious bayan ya ji jikinta da sauki ya ce" Yumnah, ina so na sake maki magana a kan kula da mutunta Mama da HAJIA, ban kamaki da wani laifin da zan tuhumeki ba, ama ina dan tsintar wasu yannayi naki da basa min a wajen mahaifiyata, ki kula, nan din ba wajen da za'a kawo wargi bane, ki mutuntata su Yumnah ko dan haihuwata da suka yi!"
Kai ta sada, muryarta a rarabe ta ce" Ka yi hakuri, ba abinda kake tunani bane, raina ne a bace"
Bai sake cewa komai ba sai mikewa da ya yi ya haura sama
Ajiyar zuciya ta sauke ta sake dauko wayarta ta dannawa mahaifiyarta kira, magana suke yi tunda safe kan maganar tarewar nan, lalle mahaifiyarta ta kwontar mata da hankali kan maganar, yanzu haka zata koma dakinta ne ta yi jiran sakon da za'a kawo mata, ta san cewa kamar yadda Mamanta ta fada maza basa son mace ruftata a bari ta taren sune zasu fitar da ita da nasu baiwar da Allah ya masu, ta kuma sake sanyaya mata zuciya cewar ta dakata ta gani ita dake dauke da cikinsa ta san ta gama shiga gaban du wata banza, danma babansu ya hannata fitowa da da kanta zata zo ta kawo mata dukkan abinda ta fada din
A bangaren HAJIA kuwa tunda safe ta fice a gidan ta tafi kasuwa da direba, sai kusan karfe daya na rana ta dawo a lokacin manyan motocin kampanin furniture sun karaso har biyu shake da kayan daki na kasa da kasa sunna ciki sunna nasu aikin ta wuce bangaren su Mama ta je ta zube kayan da sisiyo ta saka Mama a gaba du irin kunyar da take ji ta sakata karanta mata abubuwan ita kuma tana warewa daki daki kaya irin na gyaran mata masu inganci har suka gama ta kwashi abinta da nufin zuwa ta fara dafawa ta saka a frij , maman kuwa ta yi murmushi tana girgiza kai cike da kunyar lamarin nan na HAJIA , sai dai ba halin nunawa ta shirya ta yi ficewarta itama dan zata je ne ta daidaita harkar kunshin Khausar din da kitso da dilkar da za'a yi mata a gidan HAJIA FUSAM GIDAN KANSHI
Da gaske dai tarewar Khausar ta tabata dan Aba ya bada amanar ta tare din tunda har mijinta ya bukaci haka kamar yadda baba ya nuna
Wunin ranar Yumnah bata kuma fitowa ba, abinci kuwa dama rabonta da shi tun anaa gobe auren aminiyar mijinta, idan ta ji yinwa takan samawa kanta ne bata bi ta cikinsa, dan ta kula idan ta bashi ko a'a ba zai zauna da yinwa ba tunda kakarsa na gefe
A bangaren TAUFEEK kuwa sai dare ya dawo gidan, yauma shi dai ya samu Yumnah a bangarenta, gwargwadon iyawarsa ya kwatanta bata kulawa , ko dan abinda ke cikinta, sannan har ga Allah yana so ya bata darajar ta daidai misali, dan baya so ya shiga hakinta ko kadan, Khausar kuwa dama yau bai ganta a wajen aiki ba, bai kuma je gidan ba, dan ya dan tsinci cewar tana cen tana kuka, bashi da amsar bawa kansa sai girgiza kai da ya yi ya ci gaba da lamuransa, abu daya ne ya sani rikici ne Mai kwanoni da Malan muntari sun daurawa kansu, mai kuncewa fitar ransa ne daga gangar jikinsa, gwarama Yumnah da Khausar su ba kansu lafiya ko su yi, zai kasance mai raka du wani mai doguwar tafiya ne har su kai inda yake so bi'izinilah
A gidan su KHausar Hajia Fusam ce da kanta ta yiwa gidan dira tun a lokacin da Mama ta je mata da bukatarta suka yi magana irin ta manya suka kuma shirya cikin harka ta manya, da kanta ta dauki motarta bayan Maman ta mata kwatance ta kuma sanarwa Maman su KHausar din cewa za'a zo a shiga kimtsa Khausar din
Kaya ne ta je da su na kasa da kasa, ko da ta karasa su Rukaya ne suka tayata saka kayan cikin gidan Aba dan da yawansu
Du irin yadda Khausar ta rikice da bayanin wai kwana biyu kawai zata je gidan su TAUFEEK matsayin mata a wajen TAUFEEK sai da Mama ta mata magana daya da ta sakata sakarwa ta zubawa sarautar Allah ido
Hajia Fusam ta fara ne da hada hadin da zai goge kunshin da aka yiwa Khausar ta shafa mata aka bari na dan lokaci kankani aka wanke da ruwan dumi, sai kuma ta kawo hadin da ta yi dan dora Khausar din a kujera hadi na mamaki ta saka Khausar din mikewa ta shafeta da shi ama fir ta ki yarda har wasu sassan jikinta sai ita da kanta ta shafa irin su Mamanta da cinyoyinta da mazaunanta, ita dai Fusam ta bata damarta dan ko ba komai budurwa take mai kunya abinda dai ya tabatar shine ko'ina ya samu sannan ta haudata kujerar nan ta rufeta da rigar da ake rufewa aka bar fuskarta kadai a waje
Hayaki na ratsata har cije lebe take yi dan sosai yake ratsata, gefe guda kuwa Hajia Fusam na aikin hade haden gyaran fuska da lebe da kuma na raba rabar cinyoyi da mazaunai, hadi dai na mamaki , ga kuma hadin madara mai sanyi da ta sakawa zuma ta mata da magani mai kyau da inganci namu jikake na wajen Maman khair tana yi tana kafa mata tana sha har suka gama aka sauka aka nufi bayi dan wanke kwanin
Tana fitowa Fusam ta kama dirzarta da dilka, tamkar zata kwaye mata fata dan kuwa bata yi mata da sauki ba , sosai ta darjeta har tana yan hawaye , shima aka darwaye da ruwan dumi aka kuma hauda mata kurkum hadi mai madara sannan ta dawo fuskarta ta shafa mata hadin tumatur,....a wannan rana dai Khausar ta ga ikon Allah dan hadi kan hadi ake juye mata ga na sha a gefe sai da ta ji cikinta tamkar zai fashe, ga lebenta da aka samu da nasa hadin aka darje shi da bruch har sai da ya ringa wani irin MUSMUS a ido bale a tabawa , kafin ta kare da sakata a babar robar Mama ta wanki cikin rantsatsen turaren mata masu daraja, su turarukan nan kala uku ne, dama aikinsu ratsa jikin mace ne dan ba'a shiga da pant sai da ta shiga ya zauna ta rufa jikinta da zani sai dan zabura take yi saboda zafin ruwan da aka zuba turaran ciki
Tana zaune a cikin ruwan Fusam ta ajiye kujerar tsuguno a bayanta ta shiga gyara mata gashin kanta ta hanya shafa mata hadin lallen da ta hada shi da sinadaren gyaran gashi da kuma turaren gashi mai nutsatsen kanshi bayan ta rereda shi ta ringa fesa hadin danyar cita da kananfari da ta markada ta matse ruwa ruwan ta zuba a abin fesawa ta fefesa mata shi sosai sannan ta saka mata hular kan ta daure mata shi tam
Sai kusan magariba suka gama shirin yau, tana tsaye a kanta har ta dauro alwallah bayan ta kuma yin wanka da wani hadin ta zo ta tayata shafa man da ta hada mata mai karra laushi da santsin fata ta sakata a gaba ta ci dahuwar kazar amarya mai ridi da nonon rakumi ta kuma bata tsumi matsayin ruwa sannan ta zauna har suka yi sallar isha ta masu salama bayan ta tabatar mata gobe idan Allah ya kaimu zata dawo tun da duku duku duku mai kunshi da mai kitso , sannan ta tafi
Bayan tafiyarta sosai Khausar ta so tsundumuwa a tunani, sai dai wani irin kanshi da laushin shinfidar da aka yi mata ya luliyata a barci mai nauyin gaske, ko ba komai wannan dirza da ta sha da gasuwa da ruwan dumi sun isa su sakata barci koda bata yi niya ba
Mama kam ta kwana saman salaya
Tana neman alkhairin auren nan da kuma adu'ar Allah ya kade dukkan wata fitinar dake iya kunnowa, ya kawota da sauki, fatanta yarinyarta ta amshi aurenta ta kuma je ta yi biyayya a dakin mijinta, sun yi magana sosai a kan tarewar, Aba ya nuna damuwarsa na yana so ya yi mata kayan daki ama Baba mai kwanoni ya daureshi da jijiyoyin jikinsa ya hannashi maganar kayan dakin, duda haka tanadin da ya yi dan kayan dakin da garar sai ya zuba kaf a Gara , ya yi niya zai mata Gara ta mamaki, mamama ta yarda da haka, babu abinda ya gigitasu harda makota irin akwatunan da aka kawo, ta san aure wani lamari ne na Ubangiji, lalle Khausar ta yi goshi na mamaki, maganar akwatunnan Khausar har gidan su tsohon saurayinta ya kai, wace ta kai maganar kuma ita ta kawowa mama cewar mamansa na cewa auren jari aka yi, Maman kuwa ta bata amsar ai ba laifi bane, ba haramun bane !
Babar rana
Rana bata karya sai dai uwar diya ta ji kunya in ji yan magana
A dade ana yi kuma sai gaskiya
A yau ranar asabar ta kama babar ranar da ta zamto ranar tarewar Khausar a dakin mijinta, amini a gareta, abokinta bisa hukuncin ubangiji ba tare da shirinta ko yardar ta ba sai dan hakan shine a rubuce a kundun tarihinta, tsayin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 32 Chapter of 47