son haya niya anan." Gum Nana ta rufe bakin ta da tafin hannu.
Ba'a jima ba aka kawo File ɗin Nana da ƙyar ta iya saka hannu a inda aka nuna mata saboda rawar da jikin ta keyi, a tsume Asp Zawaciki ya sake karanta mata abin da file ɗin ya ƙunsa da abinda ta sawa hannu bakin ta na rawa tace ta amince.
"Bazan ma sake ba in sha Allahu." Nana ta faɗa tana sharce zufa.
Da kin taimaki kanki." Zawaciki yayi maganar sai kuma ya maida hankalin sa kan Mai Kano. Saida suka yi magana sosai sanna ya sallame su.
Suna fitowa daga office ɗin Nana tayi ido biyu da wata mata da batafi shekarun taba ƴan sanda biyu sun taso ƙeyarta hannunta cikin handcup tayi firi....firi tana rusa kuka da magiya bakin ta yaƙi mutuwa fadi take.
"Dan Allah karku maida ni cikin wajen nan, wallahi tsautsayi ne bada gangan na jeho ta daga saman bene ba, ita ce ta fara tsokana ta, wayyooooo Allah jama'a ku taimake ni zasu kashe ni, na shiga uku." Haka matar nan take kurma ihu tana tsalle tana dara kamar doki babu mai bi takan ta bare ya saurare ta, to wajene da kowa ta kanshi yake, ƴan Sandan da suka rakota ɗaya a cikin su ya falla mata mari tare da faɗin.
"Keep quiet. a zafafe.
Wannan abu da Nana ta gani ya sake firgita ta har suka zo gida jikin ta rawa yake.
Suna zuwa gida kuma zazzaɓi mai zafi ya rufe ta saboda firgita da tayi, tun Mai Kano yana mata dariya a ɓoye tare da faɗin "Allah ya ƙara." harta koma bashi tausayi, dan sosai cikin ta ya saki ta rinƙa gudawa, daga karshe dai dole saida aka kira Aunty Nurse tazo tasa mata ruwa da allura.
*****Yau Husna ke cika sati biyu a gidan Kakanin ta tuni ta warke tayi fes da ita, kusan kullum sai sunyi waya da Maman ta, haka Babanta na zuwa dubata kullum, duk ciwukan jikin ta sun warke sai tabbunan da ko zasu ɓace dole sai a hankali.
Gaba ɗaya yanayin Husna ya canja yanzu bata da walwala da sakewa kamar da, dawowar yayan ta Baffa cema tasa taɗan ware.
Lokacin da Baffa ya samu labarin Maman su da Baban su sun rabu kuka ya saka duk da bawai an bashi labarin asalin abinda ya faru bane, amma shiba yaro bane yanzu yasan mai saki yake nufi dan gaf yake da gama secondary gashi yaro ne ma ilimin addini da nutsuwa, wannan yasa ya fahimci abinda ke faruwa har ma fiya da yadda Momma dake masa bayani tayi zaton zai gane.
"Amma dai Husna ta dawo nan ke nan da zama ko Momma?" Baffa ya faɗi yana duban Momma bayan ya gama jin labarin rabuwar iyayen su.
"A'a zata koma amma bamu san lokacin da za su mai da ita ba sai abinda Kawun ku yace."
Baffa sai yaji zancen wani iri, yace "wanne irin zata koma kuma? Anan ma ai za'a iya riƙe ta, ku dan bakusan baƙin halin waccar Nanan ba ne, bata da kirki wallahi." Baffa yayi maganar ranshi a ɓace sai kuma ya fara faɗin "gaskiya ba zata koma ba, ni zan yiwa Baba magana nasan zai barta muci gaba da zama tare anan tunda mu tamu ƙaddarar ke nan."
Maganar Baffa ta ƙarshe tasa su Momma jin tausayin sa ya rufe su, sai kuma suka bisa da kallon kai yaro ne bazaka gane ba.
Wai a haka ma gwanda Husna dashi da har yau tsawan shekara goma sha bakwai da haihuwar shi ke nan amma ubansa ya juya masa baya yaƙi duban shi a matsayin ɗan cikin sa, danma ƴan uwansa masu zumunci ne sosai suka jashi cikin su, dan tun Baffa yana JS 2 Musa ya kaishi kasuwa, yanzu shekara uku ke nan da fara zuwan sa kwari duk ranar Jumma'a Asabar da Lahadi yake zuwa kasuwa.
Yasha haɗu wa da Alhaji Manu Kwabo (mahaifinsa) amma kallo ɗaya zaiyi masa ya ɗauke kai, gashi komai nasa irin na ubansa ne kamar su ɗaya, kai hatta tafiyar sa irin ta Baban shice, yan kasuwa suyi ta maganar amma shi ɗan Alhaji ne ko? Shi dai baya basu amsa haka su Musa basa cewa komai, indai ba wanda suka san labarin ba to kowa a kasuwar kallon ƙaramin kanin su suke wa Baffa wasu kuma suce irin ƴaƴan ƴan uwan Alhaji Manu ne da yake ɗakko wa ya riƙe.
Dama a rumfar su Musa yake inba hanya ce ta biyo dashi ta wajen rumfar Baban shiba basa haɗuwa, haka shima baya bi ta inda Alhajin ma zai gashi.
Randa Husna ta cika sati uku da barin gidan su Yaya Ja'afar da kan shi ya maida ita gidan Babanta, Mai Kano bai san za'a dawo da ita ba sai ganin su yayi da yake da safe ne yana gida.
Yaya Ja'afar baice masa komai ba ya miƙa masa ita da tarin tsarabar ta ya juya ya tafi ya barta tana kuka da ihun ita ba zata zauna ba, sai kuma ta fara kiran Yayanta dan lokacin da suka taho baya nan ya tafi makaranta.
Wannan dawowar da aka yi da Husna saida ya haddasa rigima tsakanin su Aunty Maimuna da yayun su Maza dan sosai suka haɗe kai suka ce baza'a maida ita ba, Baba Habu kuma yace sun yi kaɗan wannan yasa suka yiwa gidan yaji tsawan sati biyu ke nan babu wacce ta sake leƙa su Momma sai dai su kirasu a waya.
A gidan Alhaji Ƙadiri kuwa rigima ce ta tashi sabuwa bayan dawowar Baffa gida ya samu labarin an mai da Husna gidan su, nan fa yayi tsalle yace saiya je ya ɗakko ta, saida Abdussamad yayi masa kaca-kaca sannan ya haƙura, sai kuma ya fara haɗa kayan shi yana kuka yace shima gidan Yayan sa Musa zai koma da zama ba zai zauna a gidan Alhaji ba tunda suka maida Husna.
....... Mai Kano ya samu Malam Idrisa maƙocin sa suka yi magana dashi sosai akan Husna, yayi masa godiya tare da roƙon shi dan Allah suna kusa Umman Bishira ta taimaka masa ta rinƙa sa masa ido akan ta shima kuma duk abinda ya gani naba daidai ba dan Allah ya faɗa masa tunda shi ne a kusa da gida.
Malam Idrisa ya jinjina kai bayan ya gama jin duka bayanan maƙocin nasa yace.
"Karka damu Malam Mai Kano in sha Allahu komai zai wuce, Allah ya kara rufa mana asiri."
"Amin ya Allah."
A haka suka yi sallama kowa ya shige gidan sa.
Lokacin da Baban Bishira yake faɗa wa Umma yadda suka yi da Baban Husna sai tayi murmushi tace "Ai munyi waya da Safiya washegarin tafiyar Husna mantawa nayi ban faɗa maka ba, kasan munyi zanje duba jikin ta ko?"
"Eh anyi haka."
"To danaje ai ban same taba sai su Momma suke cemin ta koma gidan Babban wansu Lagos, to anan mukayi waya da ita ta roƙe ni dan Allah na taimaka nasa mata ido akan Husna."
Malam Idrisa yace "Allah sarki wannan bayin Allah sunga jarrabawa, wallahi duk bakiga Mai Kano ba ya rame."
"To Malam damuwa ai bata da daɗi."
Haka Umma da mijinta suka yi ta tattauna wa akan matsalolin rayuwa.
Wannan karon sosai Mai Kano yasa ido akan Husna ya koma dawowa gida da wuri kamar yadda ya saba, haka sosai Nana ke dannar zuciyar ta, saidai yadda Mai Kano ke kula da Husna fiya da da abin naci mata rai, dan yanzu ko fuska yaga ta canja ya rinƙa tambayar ta meya same ta me take so? Kome ya kawo kuwa da kanshi yake rabawa ya bata nata ya bawa Ni'ima nata sauran kuma ya miƙawa Nana ko taci kota zubar matsalar ta.
A wajen kwanciya ma an samu canji, yanzu tare suke kwanciya da Ni'ima, da farko Ni'ima taso ta hanata kwanciyar Nana ta rufe ta da faɗa.
"Karki jamin masifar da bazan iya fita daga ciki taba, Ni'ima wannan yar da kike gani masifa ce a gidan nan."
Haka suke kwana tare saidai babu dama tayi juyi ta taɓa jikinta saita haure ta da ƙafa kota ɗaka mata duka, wannan yasa dole Husna ta koyi haɗe jikin ta waje ɗaya.
Satin farko Abdulgaffar ne yazo duba Husna ya same ta babu lefi duk da gyaran dai sai a hankali amma kuma babu ƙazanta a jikin ta, ya kawo mata su Popcorn biskit da yawa ya bata leda daban yace ta bawa su Bishira inji Maman ta, ai kuwa da gudunta ta shige gidan su Bishira ta kai musu Umma nata godiya. Abdulgaffar yaɗan jima da ita kanya tafi, tana shigowa gida da nata kuma ta ɗibi tsaraban da Kawun ta ya kawo mata ta bawa Ni'ima.
Da farko Ni'ima taso taƙi karɓa sai kuma ta amsa tana kallon Husna Nana ta taɓe baki.
Akace wai hali zanan dutse barin hali sai mutuwa, Nana ta gaji da kallon Husna tana yin abinda taga dama bata da damar hanawa, kullam inta ganta a sake zuciyar ta zafi take wannan yasa ta canja salon mugun ta.
Mai Kano na fita kasuwa to duk wani aiken gidan Husna ke yi saidai in tana makaranta wacce ita ma ta rasa yadda zatayi ta hanata zuwa ne amma ba'a son ranta take tafiya ba, wanke wanke da shara kuwa tun tana buja-buja yanzu harta fara iya wa.
Tsawa da mugun zagi tuni Nana ta dawo dasu akan sai dai duka tanayi ne a bayan idon Mai Kano, in yana gidan cikin sanyin rai zakaji tana yiwa Husna magana.
Wanka kuwa tuni yafi ƙarfin yinta kullum, dan kuru-kuru Nana take hana ta wanka tace zata yi mata wasan ruwa.
Umman Bishira tana ƙoƙari sosai wajen duba Husna dan yanzu kitso ma itake mata da yake ta iya, tana zuwa Boko da islamiyya saidai karatu da ƙoƙarin ta yaja baya sosai, homework kuwa duk wanda ta gane take yi wanda bata gane ba kuma ta barshi, to dama Yayanta ne ke koya mata homework da hadda yanzu kuma babu shi, Baban ta kuma bashi da cikakken lokacin yi mata duka wannan, Islamiyya ma yanzu ba koda yaushe take iya bada hadda ba tun ya Sayyadi yana dukanta akan bada hadda harya daina.
Watan daya wuce kuɗin hayar gidan su Husna ya ƙare, Mai Kano yaje biyan kuɗi mai gidan yace ya bashi notice gidan zai siyar....
Tun daga lokacin yake neman gidan da zasu kama amma har yanzu da suke gab da cinye notice din ba'a samu gida ba.
"Na faɗa maka ka koma gidana muci gaba da zaman mu tare amma kaƙi, kaga yanzu ni ba mata gare ni ba zaman kaɗaici dama ya ishe ni, Amma Mai Kano in kana kusa ai kaga zan najin daɗi ko? Kuma ma kace min cikin shekarar nan kake son fara naka ginin kaga shi kenan kana kusa kana ganin abinda ake yi zaifi maka sauƙi ma" Sale ya sake maimaita wa Mai Kano Ƙudirin sa nasan ya koma gidan sa da zama bayan ya gama jin ƙorafin shi akan neman gida da yake tayi bai samu ba.
"Shike nan zanyi tunani in komawar cance tafi saimu dawo, amma kaima Sale ya kamata kayi aure zuwa yanzu lokaci ya fara ja, gashi Maman su Abba ta doshi shekara da rasuwa."
"Hmmmm! In sha Allah zanyi amma babu Wani tunani da zakayi Malam kawai ku fara haɗa kayan ku daga yau."
Sale ya tari numfashin sa da sauri yana ɗan sakin murmushin jin daɗi.
"Ai shike nan tunda ka dage saimu koma ɗin."
Bayan Mai Kano ya dawo gida yaci abinci ya huta yake faɗa wa Nana ta fara haɗa kayan ta cikin satin nan zasu tashi, tace "A'a an samu gidan ne?" Kai ya girgiza mata.
"A'a Hotoro zamu koma gidan Aminina Sale can ƴandodo." Nana taji daɗin maganar dan tasan Sale sosai mutumin kirki ne.
A cikin satin Kuma suka tashi Umman Bishira bata da labari tunda basa shiri da Nana saboda tace ita munafukar Safiya ce, sai da mota tazo ɗiban kaya sannan taji.
Umman Bishira taji babu daɗi sosai da tashin su dan sosai su Bishira suka saba da Husna, jikin Umma a sanyaye ta koma cikin gida tana tunanin koya rayuwa zatayi da Husna kuma nan gaba.
Da malam Idrisa ya dawo Umma ke faɗa masa tashin su Husna, tace "sosai nayi mamaki Malam tashi babu sallama sai ɗazu dana fita ana kwashe kayan Baban Husna ke yimin godiya a bakin shi naji ashe Hotoro zasu koma can inda suka fara zama."
"Eh wallahi kwanaki ya faɗa min zai tashi amma shaf na manta na faɗa miki, ai gidan abokin shi daya taɓa zama zasu koma." Umman Bishira tayi shiru tana juya Maganar sai kuma a hankali tace "to Allah ya basu zaman lafiya, ni wallahi Husna nake taji."
Malam Idrisa yace "Babu komai kiyi mata addu'a akwai Allah."
_*WRITING.....✍🏻*_
*_MUTUWAR AURE.....!_*
_(Ƙaddarar wasu ƴaƴan)_
*_Kanawa ne👌🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_BOOK 1_
*_FREE PAGES_*
________________
*_WHATSAPP GROUP👇🏻_*
https://chat.whatsapp.com/LaVfMaCQz1C2WcC7zGfSL3?mode=gi_t
https://wa.me/+2348064789370
_________________
_EPISODE 13_
A karo na biyu zama ya sake mai da Mai Kano da iyalinsa gidan Aminin sa Sale, tunda suka shigo farkon layin Mai Kano ya hangi sale tsaye a ƙofar gidan shi yana jiran iso war su.
"Maraba da Abokina lalle da dawowa kusa dani ɗan uwa." Bakin Sale a buɗe da fara'a yake faɗin kalaman lokacin da motar ta gama tsayawa suka yi hannu biyu da juna.
"Hhhhh yau dai ƙorafi ya ƙare gamu kusa ko?" Mai Kano ya faɗa yana dariyar jin daɗi.
Kanya bashi amsa Nana data ƙaraso wajen tace "ina wuni Baban Abba?"
"Sannun ku da zuwa uwargida, a'a wai Ni'ima ce ta sake girma haka kai masha Allah, Husnan Baba yada maƙale wa daga baya? zo nan mu gaisa, ko rigimar ce ta motsa?" Sale ya ƙarasa maganar yana kamo hannun Husna data tsaya a bayan Ni'ima, Nana ta kalle ta ta gefan ido, a ranta tace "Munafuka in batayi haka ba tasa a zage ni." Sai kuma tayin gaba.
"Ina wuni Baba Sale?" Ni'ima ta gaisheshi, ya amsa mata da fara'a, Husna ma tace "ina kwana Baba."
"A'a ina wuni dai Husnan Baba, ko kuma nace Ekaro dan nasan Safiya bata wasa da yarenta tun kina ƙarama ake miki Yarabanci zuwa yanzu kuwa ai tuni ya nuna a bakin ki." Sale yayi maganar cikin wasa da sakewa da yara kamar yadda yake a dabi'ar shi, ta wani bangaren kuma yana tuna zaman su na baya tare da Safiyar mace mai karamci da sanin ya kamata.
"Ai yadda kasanta haka ta rene su da Yarabanci da Turanci sosai suka nuna a bakin Husnah." Mai Kano ya faɗa yana ɗan jin wani abu na taso masa, Sale yayi murmushi zuciyar sa fal da tausayin Abokin nasa.
Cikin gidan suka shiga a tare, ginin gidan fuloti guda ne awun igiya babba, ɗakuna huɗu ne a gere uku manya sai ɗan ƙarami daga karshe wanda shi ne cikon na huɗun, banɗakin gidan babba ne ɗaki kuda sai Kitchen da Turken awakin shi daga tacan karshen gidan, tsakar gidan kanta katuwa ce, duka ɗakunan a gyare suke a sumince tsakar gidan ce dai babu suminti da alama za'a sha shara.
"Ku ɗauki wancan ɗakin na karshen gabas nasa an sake gyara shi, ga ɗakin su Khairiyya can (yaran shi) sai su Husna su ɗauka, ni kuma ina kusa da yarana, wannan ɗayan kuma na tsakanin mu raguna nake kulle wa a ciki da daddare saboda mutanen namu kasan Sallah ta matso yanzu sun matsa mana da sata, babu dama dabbar ka ta fita sai wani ikon Allah zata dawo gida, yanzu kuma abun nasu har gida suke haurowa cikin dare su kunce maka dabba, abun kuma kamar da tambaya (asiri ) suke zuwa har suzo su sace su fita baza ka sani ba kai ko motsin su bazaka jiba sai gari ya waye kaga wayam sun yashe ka." Sale ya faɗa da alhini.
Mai Kano yace "Subhanallah yanzu kuma haka suka zama a gidan ma kayan mutum bai tsira ba?"
"Ai kaidai bari lamarin mutanen nan namu sai dai Allah ya saka mana, kasan shekaran jiya aka shiga gidan Mamuda na nan gaban mu kaɗan wallahi raguna biyu suka kunce masa, kuma abinda zai baka mamaki gana ƴan gargajiyar unguwar nan a waje duk a titi suke kwana amma ko da wasa bazaka taɓa jin ance an sace musu dabba ba."
"Eh to ai kasan ba'a raba su da ƴan kange kange, gaskiya kayi dabara gwanda ka rinƙa kullewar, Allah ya sake shiga tsakanin mu dasu."
"Amin ya Allah." Sale ya faɗi.
Cikin ƙanƙanin lokaci aka gama shirya komai ɗakin su Husna Mai Kano da kansa ya shiga yasa musu katifa ya buga musu net (gidan sauro) saida suka tabbatar da komai yayi daidai sannan suka fice daga gidan zuwa masallaci dan gab ake da kiran sallar Magarba.
Suna tafe suna hira wanda kallo ɗaya zaka musu ka sheda cikakkun abokai ne.
"A'a Malam Abdullahi yau kaine a anguwar tamu?" Malam Malam ya faɗa yana duban su dai dai lokacin da suka iso ƙofar gidan shi.
Sale ne ya karɓe zance da cewa "wallahi shi ne gashi nan na sake nemo mana shi."
Mai Kano suka gaisa da Malam Malam ya tambaye shi almajirai yace "Alhamdulillah"
"To Allah ya taimaka." Mai Kano ya faɗa sunayin gaba.
Bayan sun dawo daga masallaci suna tsaye a ƙofar gida suna sake tattauna wa Mai Kano ya dubi Sale yace "wai ni kuwa ya wajen Abba? Yanzu komai yayi daidai ko?"
Sale ya girgiza kai fuskar shi har ta canja yanayi "lamarin Abba ai sai addu'a, Yaron nan ya zame min jarrabawa, ko kasan ya sake guduwa daga makarantar dana cema na canja masa?"
Mai Kano ya zare ido yace "ya sake guduwa kuma?"
"Eh, kwanan shi huɗu acan Malamin su ya kirani yace min basu ganshi ba, ban tashi hankali na wajen neman saba dan kasan wannan ba shi ne karon sa na farko yana gudun makaranta ba." Sale yayi furucin cikin rashin jin daɗi.
"Kayya amma ai daka neme sa a ƙalla dai kasan inda yake ko?"
"Mai Kano bazan neme saba, kaga in nayi wasa baƙin cikin Abba ne zai kashe ni nabi uwar shi kabari lokacina baiyi ba, dan haka duk ma inda yake yaje can ya karata daɗin abin Namiji ne shi ba mace ba, kuma rashin zaman Abba a kusa dani shi ne kwanciyar hankali na, kasan halin Abba bajin magana yake ba tunda uwarsu ta rasu komai ya sake kwaɓe wa, kullum cikin kawo min ƙarar sa ake, a unguwar nan ya hana yara sake wa, yaƙi Boko yaƙi Islamiyya yaƙi neman kuɗi to ya yake so nayi masa? Allah ya sani nayi iya nawa yaje duniya ce t......"
"Kai Sale."
Da sauri Mai Kano ya hana shi ƙarasa maganar ta hanyar kiran sunan sa da yayi.
"In rai ya ɓaci hankali fa baya tafiya kada ɓacin rai yasa kayi masa baki ya sake lalacewa, nasan komai akan Abba nasan kuma shi ne matsalar ka, amma kayi hakuri muci gaba dayi masa addu'a Allah ya dawo da shi kan hanya ya gane dai-dai, sannan dole ka kira yan uwa kaji koya je wani wajen."
Babu karsashi a zancen Sale yace "hmmm! Amin."
........Sannu a hankali rayuwa ta fara tafiya gashi yau har su Husna sun cika kwanaki biyar da dawowa, Sale da Mai Kano tare suke cin abincin dare.
Husna har yanzu Babanta na kula da ita Nana tayi makircin tayi kwantar dakan amma Mai Kano yaƙi sake yarda da ita.
Wannan abun nashi kuma shi ke mata ciwo, kullum da baƙin cikin su take kwana take tashi babu in taga ya saka ta gaba yana jero mata tambayoyin "me kike so? Babu abinda ke damun ki ko?" Duk lokacin da ta gansu haka wani ƙullutun baƙin ciki ne yake ƙume mata zuciya.
Karma inta ganshi yana mata wanki ita kuma ta sashi a gaba tana masa surutu.
Kamar yadda ya saba yau ma da kansa ya shiga ɗakin su ya fara ware kayan dattin Husna yana fitowa dasu waje, tunda Nana taga haka tasan wanki zai yi mata.
"Ke Ni'ima kema ɗebo naki kayan Baban ku ya wanke miki ai ba ita kaɗai bace ƴar sa kema fa haihuwar ki akayi, yarinya ta zame mini kishiya dan masifa." Nana ta faɗa tana huci dan yau ji take komai za ayi saidai ayi wallahi amma ta gaji da wannan iskancin.
"Kema dai Nana nice Baban mu zaimim wanki saboda jin daɗi? Ita mafa kinsan dan ba zata iya bane yake mata ke kuma kince ba zakiyi mata wanki ba." Ni'ima ta faɗa mata haka kanta tsaye.
Nana tace "Allah ya tsare ni da yiwa ƴar kishiya wahala."
Sai kuma fuuuu tayi ɗakin ta, sai gata ta fito da zanin gado daidai Mai Kano da baisan me ake ba ya kwaso kayan wankin Husna ita kuma ta ɗebo wasu tana cewa "yawwa Baba kace zaka fara koya mini wanki ko?"
"Eh amma saikin ƙara girma." Ya bata amsa yana zube kayan a hanyar banɗaki.
"Ga wannan saika haɗa da shi ka wanke mana dan Wallahi bazan iya wanke wa ba." Nana ta fadi a gadarance tana aje zanin gadon a kusa da shi.
Bawai bazai iya wanke mata bane amma yadda tayi masa maganar ne baiyi masa ba dan shi ba danta bane, har ya buɗe baki zai yi mata magana sai kuma ya fasa saboda yara na wajen bai kamata yana kulata sunayin magana irin wannan a gaban suba, maimakon haka saiya kalli Husna yace "ɗakko wancan ƙaramin botikin kizo."
"To." Ta juya da sauri inda botin yake ta dakko.
Kujera yasa mata a gaban shi yace ta zauna, ruwa ya zuba da omo a botikin ya ware pant da bes ɗin ta ya bata.
"Ki fara wanke waƴan nan in naga sun fita saina sake baki ɗan kwali ki wanke in kuma basu fita ba shike nan Husnan Baba bazata iya wanki ba."
Ai kuwa cikin murna dajin daɗin itama yau zatayi wanki ta fara wanke kayan tana ta zuba masa surutu, yayin da hakan ya sake kona ran Nana dan duk abinda suke tana kallo kuma tana jinsu.
"Wai kai da Mijin ka baza kuyi hira ba, inya dawo hankalin shi nakan yarinya ƙara ma dan jaraba." Nana ta fadi a zuciyar ta tana sake sake.
"Baba na gama wanke wa kuma duba ka gani ai sun fita ko?" Husna ta faɗa tana nuna masa cikin botikin.
Ga mamakin shi sai yaga kayan sun wanku sai ɗan abinda baza'a rasa ba.
"Gaskiya Husnan Baba tayi ƙoƙari, inye shi ke nan ta fara iya wanki."
Ai kuwa daɗin maganar shi yasa ta kyalkyale da dariya sai kuma tace
"Yawwa Baba yaushe zaka kaini wajen Mama da Yaya?"
Shiru ya ɗanyi yana haɗa abinda zai ce mata dan tambaya ce da bata gajiya dayi masa ita.
"Kin tuna nace miki Mama bata nan tayi tafiya?"
"Eh." ta ɗaga kai.
"To bata dawo ba amma inta dawo zan kaiki."
"To wajen Yaya fa?"
Kanya bata amsa Allah ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 13 Chapter of 31