shi ya fara ƙoƙarin turawa cikin wandon jikin ta, Husna kuma jin abu na taɓa mata jiki yasa ta buɗe idon ta da sauri tana zare su a cikin duhun ɗakin dan bata son haske kwana biyu saboda idon ta shi yasa Babanta kanya fita yake kashe mata fitila.
Jikinta taja kefe tana ƙanƙame wa, Abba daya zare hannun sa daga jikin ta tun lokacin data tashi yayi luf kamar baya ɗakin.
Bayan wucewar wasu yan mintuna Abba ya ɗauka Husna ta koma bacci ya sake matsowa zai taɓa ta, ta cikin hasken window taga mutum na matsowa kusa da ita duk da bata gane waye ba amma tabbas taga mutum wannan yasa tana gani yana miko hannun zai taba ta buɗe baki zata kurma ihu ya rufe mata baki yana zare mata ido acikin duhun ɗakin yace.
"Shishiiiiiii!" ya faɗi yana hanata ihun da zatayi, ai tuni jiki ta ya fara rawa saboda tsoro.
A hankali kamar ɓarawon dake gudun a kama shi yace "kiyi shuri kar kiyi kuka babu abinda zan miki kinji." Ya faɗa yana sake matsowa kusa da ita.
Kar...kar..kar Husna ta ɗaga masa kai ta na rawar jiki.
Hannun shi ya zare daga bakin ta, yana binta da kallon jaraba ta cikin duhun ya fara hilatar ta da cewa.
"Ki saki jikin ki kinji? Wani abu zan nuna miki in kika yarda zan baki Naira Ashirin gobe da safe, kuma zan siya miki duk abinda kike so kinji?"
Husna daba gane abinda yake cewa take ba tsabar firgici da tsoro kawai sai ta sake daga masa kai kamar ƙadangaruwa.
Wandon jikin shi yaja ƙasa daiga jikin shi ya fito waje ya miƙa hannun zai jayowa hannun ta ya ɗora akai ta kurma uban ihun da saida ya rufe kunne saboda ƙara.
Kamar a cikin bacci Mai Kano yaji ihun Husna firgigit ya farka yana sake kasa kunne yaji ko itan ce.
"Dan ubanki ba nace karkiyi min ihu ba? Abba ya faɗa yana hawowa kan gadon gaba ɗaya ta sake ƙwala kiran.
"Babaaaaaaaa! Babaaaaa!! Babaaaaaaaa!!!" Ta kira sunan Baban ta ajere har sau uku, Mai Kano da kiran suka sauka akan kunnen sa radau zumbur ya miƙe tsaye ya fara laluman rigar shi, kan ya kai ga saka rigar ya kuma jiyo kamar muryar Husna nata cewa
"Ni dai ka kyale ni, nace maka bana so, wayyo Allah Babana, Yayaaaaa! Mamaaaaa" Ta ƙwala wa Baffa kira tana rusa kuka, ai Mai Kano saiya yarda rigar ya fito da gudu.
Abba takaicin abinda Husna tayi masa yasa ya kifa mata mari yana huci zai kuma yin kanta yaji kamar an buɗe kofar daki za'a fito wannan yasa ya fasa kai mata cafka ya dira ta windo yayi ɗakin sa da gudu dama kuma ta nan ya shigo, Mai Kano yaji dirar mutum amma baiga Abba ba lokacin da ya fito, saida ya zo ƙofar dakin ya tuna bai ɗakko kubar ɗakin ba Husna na kuka ragunan ɗakin na kuka dan suma sun tsorata da dirar da Abba yayi.
Jikin Mai Kano na rawa ya buɗe ɗakin yana haske ciki da fitila, can karshen katifar ya hango Husna a cure jikin ta na rawa.
"Husnah meya same ki? Ke Husnah keda waye?" Muryar Baban ta da taji ya sake sata kuka, da sauri ya riƙo ta yana girgiza ta dan gaba ɗaya ta tsorata, Nana da tun ihun ta na farko ta tashi tayi kamar tana bacci jin suturun Mai Kano yasa ta fito tayi ɗakin tana faɗin.
"To lafiya kuma cikin daran nan?"
Bai bata amsa ba sai lallaɓa Husna da yake tayi magana amma ta kasa saboda ta riga ta tsorata da ƙyar ta buɗe baki tace
"Baba Ab....ab...ab...ba ne ya shigo kum.... kum.....kuma yace sa...sas....saiya.....ya...yank..." ta kasa ƙarasa maganar kawai sai gani yayi ta sume masa.
Nan da nan ran Mai Kano yayi mugun ɓaci kanshi yaji ya sara lokaci ɗaya tsabar ɓacin rai yama manta data suma ya tashi ya tafi ƙofar ɗakin Abba yana kiran sunan shi.
"Abba kai Abba! Abba kai fito nan kai Abba kana jina."
Abba najin Mai Kano yana kiran sa yayi masa banza dama yana shiga ɗakin yasa sakata kai daga karshe ma saiya saka kiɗa a cikin daren yadda duk abinda Mai Kano zai faɗa ba zai jishi ba.
Mai Kano ya dawo ɗakin ya tadda Nana ta zuba wa Husna ruwa ta farka tana mata magana amma taki sauraren ta, sai kuka take kamar ranta zai fita.
A ranar dole Mai Kano a ɗakin ya ƙarasa kwanan shi dan Husna ta riga ta firgice.
A zaune ya ƙarasa ganin wayewar gari, yana zaune yana lissafa yadda zasu kwashe da Abba da safe aka kira sallar farko, lokacin kuma ya samu Husna ta koma bacci amma ta riƙe hannunsa ƙam Nana ta leƙo ɗakin taga yana zaune har yanzu yadda ta fita ta barshi haka yake.
Saida aka fara kiran Sallah sannan ya zame hannun shi da dabara ya fito yayi Alwala yana duban ɗakin Abba dake buɗe da alama baya ciki.
Abinda Mai Kano bai sani ba kuma shi ne Abba tun komawar sa wajen Husna ba daɗe wa ya fito ya kama katanga ya haure yayi nasa waje.
Bayan an fito daga Masallaci Mai Kano ya samu Malam Malam yake faɗa masa abinda ya faru.
"Subhanallah wannan yaron na Sale baya jin magana Abdullahi, yadda kasan ba Sale ne ya haife shi ba." Malam Malam ya faɗi maganar bayan ya gama jin bayanin Mai Kano, sai kuma ya sake cewa.
"Karka damu bari a jima saimu sashi a gaba muyi masa faɗa in sha Allahu ba zai sake ba."
"To malam Allah ya kaimu jimawar nagode sosai Allah ya ƙara lafiya."
Mai Kano ya faɗa yana juyawa gida, Malam Malam kuma ya shige gidan sa yana sake juya rashin jin Abba a ransa.
Da safe sama da ƙasa a ka nemi Abba a unguwar nan aka sara duk inda akasan yana zama anje amma baya nan, wannan tasa dole Mai Kano ya shirya ya fita kasuwa suka barwa dare inya dawo sayi masa magana.
Husna kuwa ranar duk rashin tausayin Nana saida ta kyale ta da jarababban aiken ta dan sosai ta tashi da zazzaɓi da ciwon kai, danma saida Baban ta ya bata magani kanya fita yace inya dawo sai ya kaita Cemist.
Ranar a kwance ta wuni a ɗaki abinci ma Ni'ima ce ta miƙa mata, da ƙyar ta samu taci kaɗan shima tana gamawa tayi aman shi.
Ni'ima ta dubi Nana tana zama a gefan ta bayan ta gama kwashe aman da Husna tayi tace "wallahi Ma'u tausayi take bani Nana dubi duk yadda ta koma daga daren jiya zuwa yau? Allah bakiji jikin taba har yanzu zazzaɓin bai sauka ba."
Nana ta taɓe baki tana ci gaba da yin aikin gaban ta tace "shi yasa yau kika taɓe a wajen ta sai kace uwarki ce ta kwanta ciwo? To ai ba uban wani ne ya ɗora mata cutar ba."
"Hmmm Nana ke nan dan bakiga yadda take jin jiki bane?"
"Inna gani ma zan yaye mata cuwon ne? Ke dan Allah ni kin ishe ni da zancen banza, duk waya ja mata hakan inba jarababbiyar Kakar kuba, data barta wajen uwarta ai da kowa ya huta."
Ni'ima sai tayi shiru bata sake cewa komai ba saboda takaicin maganganun Nana....
_*WRITING.....✍🏻*_
*_MUTUWAR AURE.....!_*
_(Ƙaddarar wasu ƴaƴan)_
*_Kanawa ne👌🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_BOOK 1_
*_FREE PAGES_*
________________
*_WHATSAPP GROUP👇🏻_*
https://chat.whatsapp.com/LaVfMaCQz1C2WcC7zGfSL3?mode=gi_t
https://wa.me/+2348064789370
_________________
_EPISODE 14_
Wajen ƙarfe biyar na yamma gumi ya karyo wa Husna alamun zazzaɓin jikin ta ya sauka, a hankali ta yunƙura ta fito tsakar gidan, Nana kaɗai ta tarar a murhu, ruwa ta ɗiba a buta ta shiga ban ɗaki bata jima ba ta fito sai kuma ta samu waje a gefe ta zauna, wanka take so tayi amma tana tsoron ɗiban ruwa Nana ta balbale ta da masifa, daga karshe dai ta yanke shawarar zuwa ta ɗebo kamar yadda ta saba, ɗaki ta koma ta sako hijabin ta da wuyan ma ya ɗan buɗe kanta babu hula a haka ta ɗauki botiki ta fice daga gidan.
Duk abinda take Nana na kallon ta ta gefen ido amma tayi kamar bata san da tsuron ta a wajen ba harta fice daga gidan sannan ta raka bayanta da harara tana sakin tsaki tace "Aikin banza an barwa mutane wahala."
Husna na tafe tana gyara wuyan hijabin ta dake faduwa harta isa Famfo. Allah ya taimake ta babu layi, da yake yamma ce mutum biyu kawai ta tarar suna ɗiba tasa nata buga ruwan ma da dabara tayisa tana yi tana hutawa harta samu ta zuba rabin bokitin sai kuma ta tsaya jiran wanda zai taimaka ya ɗora mata.
Tun fitowar Husna daga gida Abba ya ganta akan indan shi ta wuce saidai ita kwata kwata bata kula da shiba harta ɗakko ruwan ta kamo hanyar gida.
Da ƙyar take takawa bokitin na yawo a kanta saboda rashin kwarin jiki, tadan gota digan Malam Malam kaɗan taji.
"Shuuuuuuu."
An zuba mata bulalar da saida ta zagaye cikin ta, tsabar gigicewa bata san tayi fatali da botikin kanta ba, tana juyowa suka haɗa ido da Abba dake tsaye a bayan ta riƙe da murtikekiyar igiyar dabai bainbayin Jaki yana huci Idanun nan nasa a juye kana gani kasan yasha wani abu, yace "Ke dan kut*****mar ubanki ni zaki yiwa ihu?"
"Tsuuuuuuuu" ya sake zubawa Husna duka da ƙarfi jikin ta na rawa ta fasa ihu ta kwasa da gudu, ya rufa mata baya, tana gudu nata kukan neman taimako shi kuma yana binta a baya yana duka kamar bawa da Ubangidan sa, haka Husna ta rinƙa gudun tsira tana kuka Abba yana binta a baya yana jibga suna zagaye layin, duk wanda yayi masa maganar ya daina dukan ta baya sauraren sa inka sake masa magana kuma ya dannama zagi, har ƙarfin Husna ya fara ƙare wa Abba bai dena binta yana duka ba, da taimakon Allah ta samu ta shige gida ya rufa mata baya Nana na zaune taga Husna ta shigo tana ihu rigar ta ta yage hijabin ta yayi nasa waje, kan tayi magana Abba ya shigo da gudu shima Allah ya taimaketa ta shige ɗakin Nana, zai rufa mata baya Nana ta tsaya a gaban sa, tace "Ina zaka kuma mara mutumci wallahi karka sake ka shigar min ɗaki." Nana ta faɗa tana babbake hanya.
Abba ya wani juya kai yana kallon Nana da jajayen idanun sa, yace "Ke wallahi in baki matsamin a hanya ba saina haɗa dake."
"Inka fasa haɗawa dani baka haifu ba, kai nace maka inka fasa dukana shege kake ba ɗan halak ba. Kuma wallahi inka sake ka shigar min ɗaki saina sheka maka tafasasshen ruwan can nakan wuta inka isa kuma ka ture ni ka shiga ka gani."
Zuciyar Abba da abinda yasha suna faɗa masa ya ture Nana kawai ya shige Malam Malam ya shigo gidan yana kwala masa kira dawowar sa ke nan almajiran shi da ƴan unguwa suke faɗa masa abinda ke faruwa.
"Kai Abba kai Abba wannan wanne irin dabban cine? Kanada hankali kuwa?" Malam Malam ya faɗi a faɗace.
Duk iskancin Abba yana dagawa Malam Malam ƙafa saboda ba shiga harkar shi yake ba kuma Abokin Baban sa ne, amma da yake ƙwayace a kansa sai cewa Malam Malam.
"Wai harni wannan yarinyar zata yiwa ihu danna shiga ɗakin ta? To wallahi kinyi sa'a yau kin tsira amma da saina kusa turaki ƙiyama yadda ko kuɗi aka baki bazaki sake mun musu ba." Abba ya jero maganganun yana yin gaba da baya kamar zai kifa.
"Innalillahi wa inna ilaihirraju'un kai Abba babu kunya babu tsoron Allah kake faɗin wannan maganar? To zoka fita kabar gidan nan, in kuma kaƙi wallahi yanzu nan zansa garada su danne min kai na saka a mari." Malam Malam ya faɗa yana tattara malum malum ɗin sa. Abba yace "Eh.....ai zan fita, amma ke duk randa kika kuma yimin ihu wallahi saina..." Sai kuma bai ƙarasa maganar ba ya juya yana tangaɗi yayi waje.
Nana tace "Salamamme mara amfani haihuwar asara."
Ni'ima data ɓoye a bayan Malam Malam saboda tsoro da sauri ta matsa ya wuce, Malam Malam kuma ya rufa masa baya.
Ƴan unguwa kuwa abin nema ya samu tuni suka fara kus kus kowa da abunda yake faɗa, wanda abun ya faru a gaban idan su sai mai da zance suke.
..........Mai Kano na dawowa Malam Malam ya tare shi da zancen, faɗin ɓacin ran da ya shiga dajin wannan mugun zance ma bata baki ne, a zuciyarsa yace "dole abinda banaso shi zanyi."
Bai tsaya dogon zance da Malam Malam ba ya shige gida yana ayyana halin da zai iya samun Husna aciki.
Da sallama ya shiga gidan, Nana da Ni'ima suka amsa tare da yi masa sannu da zuwa.
"Yawwa Sannun ku." Ya faɗa yana rarraba ido a tsakar gidan, can kusa da ƙofar ɗakin Nana ya hango mutum kwance akan taburma yana rawar sanyi, ko ba'a faɗa masa ba yasan Husna ce dan ya hangi zanin atamfar ta data rufa dashi.
"Subhanallahi." yayi maganar yana ƙarasa wa kanta da sauri, ya yaye zanin yaga ta dunƙule waje ɗaya tana rawar sanyi haƙoran ta har haɗuwa suke saboda mugun bugun da zazzaɓi ya sake mata bayan dukan da tasha a hannun Abba.
"Husnah sannu kinji? Yi haƙuri tashi zauna mu gani, bari muyi Sallar Magarba saina kaiki ko nan Sir Sunusi ne, kai amma jikin naki yayi zafi da yawa." Mai Kano ke jero maganganun yana tashin ta zaune, amma saita kasa zama saboda zazzaɓi sai a jikin shi ya jingina ta.
"Ai zazzaɓin ma ɗazu ne ya sake rufe ta bayan wancan sallamammen ya jibgeta amma ai bata wuni dashi ba, inka karɓo mata magani anan Cemist ɗin bakin hanya ma zata ji sauki, ba sai kayi wahalar zuwa asibiti ba dan ciwon nata ba mai yawa bane tsamin jikine kawai yasa ta sake narke wa, wannan kuwa dama ai dole tayi shi tunda ta daku." Nana ta faɗi maganar tana aje masa ruwan shan data kawo.
Caraf Ni'ima dake saurarensu tace "taɓ wallahi Baba Ma'u yau a kwance ta wuni da zazzaɓin nan."
"To ƙarya nayi ke nan? Ƴar me bakin maganar tsiya." Nana ta faɗa tana bankawa Ni'ima harara.
Takaicin Nana ya kama Mai Kano dama gashi ranshi a ɓace yake, ya fita da ɓacin ran abinda ya faru ya dawo ya tadda wani maimakon ta tayashi jimanta abinda ya faru shi ne zata sashi a gaba tana masa soki burutsu.
"Eh soki burutsu mana inba haka ba wani mara hankalin ne zai ga jikin Husnah yace wai ciwon ba wani mai zafi bane." Yayi maganar a ranshi, a fili kuma sai ya dubi Ni'ima yace "ƴar Iya zoki zauna kusa da ita naje masallaci na dawo."
"To."
Ni'ima ta amsa tana tasowa daga inda take zaune ta dawo kan taburmar da Husna ke kwance.
Idanun ta biyu amma zafin zazzaɓi ya hanata magana kukan ma saboda tsabar ciwon da kanta ke mata baya fitowa sai hawaye kawai kebin gefan fuskar ta.
Jingina ta yayi da jikin katanga amma ta kasa zama dole ya sake kwantar da ita ya tashi, hular shi da wayar sama anan ya bar su yayi Alwala ya fice dan har an tada Sallah.
Ana idar da sallar yayo gida ya samu Ni'ima na bata ruwa fuskar shi a sake ya kama Husna yasa Ni'ima ta dakko mata riga da hijabi yasa mata, Ni'ima tace "Baba zan biku." Sai da ya riƙo Husna zasu fita daga gidan sannan yace "A'a ƴar Iya kinga yanzu dare ne muma yanzu zamu dawo kinji?"
"To Baba Allah ya sawake."
Ta faɗi da tausaya wa, sai kuma sannan Nana tayi magana.
"Allah ya bata lafiya."
"Amin."
Ya amsa suna ficewa waje inda mai Adaidaita sahu ke jiran su dan daga masallaci ya taho dashi saboda yasan Husna bazata iya hawa bayan mashin ba.
Suna fita Nana tace wa ni'ima "Yar me shishshigin jaraba, banza mara kishin kanta kina zaune kina kallo ubanki na nunawa wata so amma kina tayashi dan asara."
Ni'ima tana jinta tayi mata banza sai baki data tura gaba.
_Sir Muhammadu Sunusi Hospital_
Mai Kano ya sha faɗa a wajen likitoci kansu karɓi Husna, yara ƙananan da ya haifi wasun su haka suka rinƙa yi masa faɗa amma haka ya rinƙa basu hakuri.
To ya ya iya da Ƙaddara yasan komai ya faru Allah ne ya jarrabe shi kuma Iya taja masa dan ita ce sila. Badan ƙaddara da bawa baya wuce ta da mai zai kawo faruwan hakan ma bare har yazo nan yara na shimfiɗa masa wulaƙanci.
"Malam ga wannan kaje ciki ka siyo mana wannan alluran yanzu, dan Allah karka ɓata lokaci." Wata Nurse ta faɗawa Mai Kano haka tana miƙo masa takardar da aka yi rubutu akai.
Bai ce mata komai ba ya karɓi takardar yabar wajen, Allah ya taimake shi bai samu layi a wajen siyan Allurar ba.
Cikin lokaci ƙanƙani suka yiwa Husna Allurai suka saka mata ƙarin ruwa tun ba'a daɗe da ɗaura mata ruwan ba bacci yayi awun gaba da ita, yana zaune a kusa da ita ledar farko ta ƙare aka saka mata ta biyu.
Gumi yaga ta fara yi alamun zazzaɓin ya sauka, hannu yasa yana share mata gumin sai kuma ya cire mata hijabin jikin ta da dabara yadda zata sha iska.
Sha biyu na dare baifi saura ƴan mintuna ba suka baro asibitin, lokacin kuma Husna da ƙafafun ta take takawa yana riƙe da hannun ta, Alhamdulillah jikin nata yayi sauki sosai dan yanzu bata jin ciwon kan haka babu zazzaɓi, sai sauran tsamin jiki da sai a hankali zata dena ji.
Suna fitowa ya samu mashin sai dai yasha tsada dan dare ya fara yi.Yana riƙe da ledar magungunan ta ita kuma tana zaune a gefan shi.
Tunda ta tashi daga bacci bata yi masa magana ba, har yanzu da suke hanyar komawa gida batace masa komai ba, duk abinda yace mata kuma saidai ta ɗaga masa kai alamar "eh." Ko "a'a
Shi bai san Husna da miskilanci ba amma ya fuskanci sauyin rayuwa yasa ta fara canjawa, abubuwa da yawa daya santa dasu duk yanzu babu.
Ya juyo ya kalli yadda ta kwantar da kanta ajikin mashin ɗin tana kallon hanya duk sai yaga ta canja masa kamar ba Husnan shi daya sani mai yawan cika shi da surutu da karaɗiba. Yarinyar da ko faɗa suka yi da yayanta yana zuwa shi take fara faɗawa amma dubi yadda yanayi yasa tayi masa shiru ko zancen dukan da Abba yayi mata bata yi masa ba.
Sosai yaji wani abu mara daɗi ya tsaya masa a wuya, har mai mashin ɗin ya kawo su kofar gida Mai Kano na lissafi da tunanin yadda zai inganta rayuwar ƴar shi dan ranshi baya masa daɗi inya ganta cikin damuwa da kaɗai ci.
"Anya banci amanar Safiya ba?" Ya tambayi kanshi yana sake duban Husna....!
.........Nana najin shigowar su ta fito tsakar gidan.
"Kun dawo?" Ta faɗi tana duban shi, kai ya gyaɗa mata, ta mele baki gefe sai kuma ta sake cewa.
"Allah ya sawaƙe."
"Amin." Ya amsa yana yin hanyar ɗaki da Husna.
Wajen kwanciyar ya sake gyara mata tana tsaye tana kallon shi tausayin kanta da mugun tsoron Abba zai sake dawowa ya kamata jikin ta har sai da ya ɗan fara rawa kuka na son kwace mata.
"Zoki kwanta kafin Allah ya kaimu gobe." Babanta ya faɗa yana kamo hannun ta tazo ta kwantan amma sai taɗan tirje taƙi zuwa ta kwanta, kanshi ya ɗaga ya kalle ta sai kuma yayi murmushi ya ja mata hanci yace "Babu fa inda zani yau tare zamu kwana."
Ya faɗa yana ɗan dariya kaɗan dan ba ƙaramin tsoro da firgicin ya hanga a cikin idanun taba, kai ta ɗago ta zuba masa ido cikin son tabbatar wa ya jinjina mata kai alamar "da gaske yake."
Matsowa tayi ta kwanta tana kallon shi, yace "ko zaki ƙarasa shan furar ki?"
"Um um." Ta faɗa a hankali muryarta bata wani fita sosai.
Ɗakin ya fude ya koma ɗaki ya ɗakko Sallaya ya shimfida a ƙofar ɗakin ta waje yadda zata rinƙa ganin sa, Alwala yaje ya dauro yazo zai tada Sallah Nana ta fito tana kallon shi da ɗan Mamaki, sai kuma tace "A'a yau kuma anan zakayi sallar Baban Ma'u?"
"Eh."
Shi ne kawai amsar daya bata, ta sake cewa "to bakaci abinci ba, ko a kawo ma nan?"
"A'a na koshi naci da safe in Allah yasa muna raye."
Yana dire maganar bai bata damar sake cewa komai ba ya tada Sallah.
Sororo Nana tayi tana duban sa, ta ɗan jima a tsaye tana tunani sai kuma ta koma ɗaki ta kwanta tana jiran shigowar sa.
Husna kuwa ganin Babanta na Sallah a ƙofar ɗakin yasa hankalin ta ya kwanta tsoron da take ji ya ragu, har bacci ya ɗauke ta tana ganin sa yana Sallah, sai dai tsoron data kwanta ta dashi yasa har cikin bacci take ɗan kiran sunan shi, wasu lokutan kuma saita farka ta kalli ƙofar ɗakin da sauri inta ganshi har yanzu yana wajen saita sake komawa baccin ta.
Nana tun tana jiran shigowar sa har ta gaji ta kwanta bacci ya ɗauke ta, bata farka ba sai wajen uku na dare da mamaki take kallon ɗakin taga baya ciki, tsakar gidan ta leƙo sai ta ganshi tsaye a ƙofar ɗakin yana Sallah har yanzu.
Shi kuwa Mai Kano kwana yayi yana gadin ƴar sa yana kuma kai kukan shi wajen Ubangiji, sosai yayi Sallah yayi doguwar sujuda in ya gaji yakan zauna yayi karatun Alkur'ani yayi wa Annabi SAW Salati yayi istigfari da hailala, kafin ya sake miƙe wa ya tada wata sallar, ranar kwana yayi yana Sallah da zikiri har asuba.
Saida aka kira sallah a masallaci sannan ya tashi ya duba Husna jin garin sanyin asuba ya sauka sai ya koma ɗaki ya ɗakko malum malum ɗin shi ya rufa mata sannan yayi Alwala ya fita zuwa masallaci dan bada jam'i.
Yaɗan jima bai shigo gidan ba saboda sun tsaya da malam Malam a waje, anan Mai Kano yake faɗa masa Abba ma bai kwana a gidan ba.
Lokacin da ya shigo gidan gari yaɗan fara haske, ɗakin Husna ya koma ya tashe ta tayi Sallah, bayan ta idar tace masa ina kwana, ya amsa mata da kulawa yana tambayar ta jiki tace da sauƙi.
Ya tashi zai fita dan so yake yaje ya ɗan kwanta kan a jima, har yasa kafar sa a waje yaji ta kirasa.
"Baba."
Ta kira sa da muryarta data sake sanyaya.
Juyowa yayi yaga yadda take kallon shi, sai kuma ya dawo kusa da ita ya zauna yana fuskantar ta yace "ya ya aka yi Husnan Baba?"
Kanta ta sauke ƙasa wahaye na taruwa a idanun ta, muryarta harta fara rawa tace "Baba dan Allah, dan Allah, Baba dan Allah ka kaini wajen Yayana dasu Maman Sama dan Allah Baba ka kaini can, ni bana son zaman nan can nake so." Ta ƙarasa maganar kuka na kwace mata.
Sosai maganar ta tayi melting heart ɗin sa, yasan abinda take tsoro kuma shi ma shi yake tsoro da gudu, tabbas kuma ko bata roƙa ba ta gama kwanan gidan nan daga yau dan ba zai yiwu ba yana ji yana gani a lalata masa ita ba, ko babu Safiya a duniya bama a gidan shiba, yana sane dai ba zai taɓa bari a wulakanta rayuwar ƴar suba.
"Baba zaka kaini ko?" Husna ta sake jefo masa tambayar tana riƙe hannun sa.
"In sha Allahu anjima zamu tafi daga nan kinji." Ya bata amsar yana ɗan sakar mata murmushi.
"Wajen yaya zaka kaini ko Baba?" Ta tsare shi da idanun ta da har yanzu basu koma daidai ba.
Basu rene ta da ƙarya da kwana kwana ba, haka
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 15 Chapter of 31