a fili tana kallon kofar shigowa ɗakin, zuciya na ce mata ta fita tayi masa rashin mutumci shida baƙin sa wata zuciyar kuma na hana ta zuwa.
Akan idon ta yayi sallama ya shigo ɗakin, ta kafe shi da ido, kansa a ƙasa ya kasa kallon ta, da kyar ya iya ce mata "Ki fito ku gaisa da Sale." Yana gama fadar haka ya juya da sauri ya fice daga ɗakin.
Zuciya nata ingiza Safiya karta fita dan wallahi ganin abun take kamar a mafarki, gani take kamar ba da gaske ba ne, Abdullahin ta data sani ko duniya ce ta taru tace mata zai yi mata haka bazata taɓa yarda ba. Amma bari ta fita daga iya gudun ruwan su.
Hijabin Sallar ta tasa ta fito cikin gidan dai-dai lokacin kuma matan da suka rako Nana suka fito zasu tafi dattijuwar ɗazu ta sake ce mata "yarinya kiyi haƙuri kinji? Allah ya baku zaman lafiya."
Sauran matan suka amsa da Amin Dije ta raka su har wajen motar data kawo su saida motar su ta tafi sannan ta dawo cikin gida.
"Safiya ƙaraso nan magana zamuyi."
Sale ya faɗa yana fuskantar ta.
Akwai mutumta juna sosai tsakanin ta da Sale dan mutum ne shi ba abokin yarwa ba.
Kan taburmar da suke ta isa ta zauna daga gefe kamar wacce ta zauna akan ƙaya, sale yace "Safiya sai kuma kika ga Nana ta dawo ko?" Bai jira cewar taba yaci gaba da cewa
"Wallahi Safiya abun ne yazo haka katsam babu shiri, ni shaida ne Mai Kano bai san da maganar ba, umarnin iyayen sa ne babu yadda zai yi dole yayi musu biyayya, kiyi haƙuri Safiya nasan ba'a kyauta miki ba amma kiyi haƙuri haka Allah ya tsara."
Bata san lokacin da ta dago ta yiwa Sale wani mugun kallo ba dan ita tama rasa taƙamaiman abinda yake son cewa.
Basu ji isowar Dije wajen ba saiji sukayi tace
"Au saboda ka dawo da tsohuwar matar ka uwar ƴaƴan ka shine ka dakko Sale yake bata haƙuri Mai Kano? To saɓo kayi daka dawo da Nana ko wani mugun abu? da kake bata haƙuri haka sai kace wata uwarka."
Safiya a mamakan ce ta ɗaga kai tana kallon Dije dan ita tsawan zaman ta da Mai Kano bata san wannan fuskar ta Dije ba, "to dama haka take ko kuwa duk acikin shirin ci mata mutumcin ne ta canja hali?"
Safiya ta tambayi kanta, sai kuma ta miƙe tsam Sale na mata magana tayi ɗaki ta barsu anan.
Mai Kano ji yake kamar ya haƙa rami ya bunne kanshi a ciki tsabar kunyar Safiya data rufe sa.
Idon Safiya ya bushe sai baƙin ciki dake cin zuciyar ta, Husna data fara bacci ta tasa tasa ta cire uniform ɗin ta tace taje tayi Alwala tazo tayi sallar Magarba, bata tambaye ta Baffa ba dan tasan yana rakota gida yake komawa sai anyi sallar isha'i yake dawowa gida saboda suna zaman hadda a masallaci.
Tunda ta shige ɗaki bata sake fitowa ba Mai Kano yazo kanta yayi mata maganar duniya amma ko kallan inda yake batayi ba, da safe su Baffa na tafiya makaranta ta shirya ta kulle ɗakinta ta fice daga gidan.
Mai Kano sai fitowa yayi yaga ɗakin ta a kulle. Yayi shiru kawai yana kallon ɗakin, dama yasan za'ayi haka dan shirun Safiya yasan babu alkairi a cikin sa gwanda ma tayi faɗan yasan komai ya wuce amma sauda dama in tayi shiru irin wannan to abun baya kyau.
Lokacin da Safiya taje gidan su da labarin abunda ya faru buɗar bakin Momma sai cewa tayi "haƙuri zakiyi ki koma ɗakin ki dama maza suna haka Safiya, wannan ai ba komai bane a shafukan halin ɗan Namiji."
Anyi dirama an kai ruwa rana saida su Baba Habu suka shiga cikin maganar sannan Safiya ta yarda ta koma gidan Mai Kano dan cewa tayi wallahi ta gama Auran sa, amma saboda dattako da riƙe alkawari irin na Ahlin Alhaji Ƙadiri suka danne ta ta koma, a ranar ne kuma tayi kukan rashin mahaifinta, dan gani take da yana raye bazai bar wannan cin fuskar da aka yi mata ba.
Rai babu daɗi Maman Sama ta mai da ta ɗakin ta bayan ta sake bata haƙuri dayi mata nasiha.
Nan fa aka fara saban zama, farkon zaman Safiya tana ta ganin lefin Mai Kano da baƙin sa sai a hankali kuma ta fara gane ko kaɗan bashi da lefi, sannan duk abunda yasan zataji babu daɗi ƙoƙari yake ya kiyaye sa, wannan yasa Dije ta sashi a gaba da masifa kala-kala ta hana su zaman lafiya, tunda ta dawo da Nana bata barsu sun sarara ba kwanciyar hankali kuwa tuni tayi musu nisa a gidan....
_*WRITING.....✍🏻*_
*_MUTUWAR AURE.....!_*
_(Ƙaddarar wasu ƴaƴan)_
*_Kanawa ne👌🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_BOOK 1_
*_FREE PAGES_*
________________
*_WHATSAPP GROUP👇🏻_*
https://chat.whatsapp.com/LaVfMaCQz1C2WcC7zGfSL3?mode=gi_t
https://wa.me/+2348064789370
_________________
_EPISODE 10_
Tun kwanaki biyu da suka wuce akayi hutun makarantar Boko Baffa ya shirya kayan sa yace gidan Yaya Musa zashi hutu.
Safiya taso ta hana sa zuwa sai kuma tayi tunanin gwanda ma ya tafi hutun tunda gidan nasu yanzu babu daɗi ba wani sakewa yake yi ba Husna tafi kowa mitar tafiyar sa.
Da yamma Baffa yayi sallama da Maman shi da Husna ya tafi.
Washegari da safe Safiya ta fito da risho lungun dakin ta ta ɗora musu suyar dankali tana zubawa ta koma ɗaki danta dakko cokakin juyawa, tana fitowa ta tsaya turus tana kallon kan risho da taga an kifa kaskon sunyar akan sa mai da dankalin sun zube akai wasu kuma a ƙasa.
In ranta yayi dubu ya ɓaci dan tasan ba zube wa yayi ba zubar dashi akayi da gangan, tana tsaye Mai Kano ya fito ya ganta riƙe da cokali tana kallon risho.
Yace "Wani abune ya faru? A'a subhanallahi zube wa yayi?" Ya faɗa sanda yayi ido biyu da rishon da take kallo, ranta a ɓace tace "Ya zube ko aka zubar min, wai Abdullahi mene ne matsala ta da yan gidan nan?." Safiya ta faɗa bacin ranta na fitowa fili.
"Nice nan na zubar, sannan matsalar ki damu shi ne ki fita kibar min gidan ɗana."
Dije ta faɗa tana fitowa tsakar gida ta tsaya.
Mai Kano yana jin abinda Dije tace ya dafe kanshi yana ambaton sunan Allah a ransa, sai kuma yayi wajen ta yabar Safiya a tsaye.
"Iya dan Allah kiyi haƙuri ki daina wannan maganar, bafa wani abu tace ba, nina tambayi meya faru shi yasa kikaji tayi magana." Yayi maganar da fatan zata yi shiru zancen ya mutu iya nan.
Kamar wanda ya zubawa wuta fetur Dije ta dube sa sheƙeƙe tace "to baka isa ba, Mai Kano, nace baka isa ba wallahi, yau ba gobe ba wannan mara mutumcin matar da kake Aure saita bar gidan nan, kaji dai na faɗa maka."
Hayaniya da ruwan bala'in da Dije ke surfawa shiya fito da Nana daga ɗakinta ta cuge a ƙofa tana kallon su ɗaya bayan ɗaya .
Mai Kano ya tsugunna a gaban Dije kansa a ƙasa kamar mai neman gafara, tunda ta fara zazzaga masa masifar da ya kasa kane dalilin yin ta, yake durkushe yana bata haƙuri, duk abinda Dije take masifa tana lissafa wa ita kanta tasan ba'a yisu ba, san zuciya ne kawai da tsagwaron kin gaskiya.
Koda yake faɗan nata yayi kama da wanda ke jiran kaɗan ya sauke abinda ke ransa, in banda haka shi baiga abinda Safiya tace na tashin hankalin da zaisa Dije tana wannan maganganun ba.
"Na faɗa maka Mai Kano wallahi indai nice na haife ka yau saika saki wannan tsinanniyar arniyar mai baƙar ƙafa daka auro, wacce tunda ka Aure ta shekara goma sha biyu baka sake ajiye komai ba sai dai ka ƙare a gindin ta da ƴaƴan ta, gaka wahalalle, toba bawa na baifa miki ba, kinyi ƙarya wallahi sai naga bayan ki a gidan nan." Dije tayi maganar tana nuna ta da yatsa bakin ta na kumfa saboda masifa.
"Muguwa dangin jaraba, nifa dama shi yasa tun farkon kawo maganar Auran wannan mara cikakken musuluncin da kayi ba kaunar shi nake ba Aramma ne yafi ƙarfina amma da yaushe inaji ina gani kana cikakken Bahaushe zaka kwashi Beyerabiya? Shekarar ka goma sha huɗu da shigowa Birni neman kuɗi duk abokan ka da kuka fito nema tare sunyi gidajen kansu sun siyi gonaki sunada gidaje a kauye amma kai ka ƙare a gindin mace da ƴaƴan ta, saidai taci abinda take so tasa suturar da take so kai kullum kana tsaye kana nema ka kawo mata tayi yadda take so, har yanzu baka da komai sai a yawon haya ka ƙare, to wallahi tunda ita ba matar rufun asiri bace sai kun rabu, kai inma ƙaddarar rabon ce ta haɗa ku to daga yau na yanke ta, dama tunda tayi wannan abar ai bata sake haihuwa ba." Ta faɗa tana nuna Husna dake tsaye kusa da Maman ta, sai kuma taci gaba da faɗin.
"To ya isa haka ta fita taje can wani wajen ta shimfiɗa musu iko da baƙin halin ta amma ba a nan ba." Dije ta ƙarashe maganar bakin ta da babu haƙoran kirki fal da goro yayi ja duk ya furfurzo waje saboda masifa, a tsaya take akan shi har yanzu yana durkushe a gaban ta sai zufa yake saboda tashin hankali.
Tunda Dije ta fara ɗibar albarkar ta Safiya na tsaye a ƙofar ɗakin ta sanye da ƙaramin hijabin Sallah, Mai Kano dake durkushe kawai take kallo cike da tausayin sa, jira kawai take taga ikon Allah, dan halin masifar Dije har yau ganin sa take kamar a mafarki.
"Ka tashi ka sake ta yanzu a gabana basai anjima ba inba haka ba wallahi sai na ɗaga maka Nono." Dije ta sake faɗa tana gyara ɗaurin tsangalallan zaninta, da sauri Mai Kano ya dago yana kallon Dije idanunsa sunyi jawur a ransa yake maimaita kalmar "Innalillahi wa inna ilaihirraju'un, wannan wacce irin masifa ce.."
Fech fesch fesss....Dije ta fache majina sai kuma tasa hannun zani ta goge hanci, ƙananun idanunta da tsufa da masifa suka sake ƙanƙantar dasu ta ware akan Safiya tace "to wallahi ubanki Ƙadiri ma yayi kaɗan bare ke ƙaramar haki, wannan ƙafafun nawa da kike gani babu inda basu shiga ba, nasha gaban ki a biye biye, fes nake kallon ki tunda yaƙi sakin ki ta arziki zansa ya sake ki ta tsiya."
Tunda Dije ta fara zuba masifar ta Safiya bata ce mata ci kanki ba sai yanzu da ta ambaci ubanta, take taji ranta yakai ƙololowar ɓaci to dama ran nata a ɓace yake, meya rage nacin mutumci da wulaƙanci wanda Dije bata yi mata ba? Babu sai wanda ta manta, tunda Dije take ci mata mutumci ta zageta ta tsine mata albarka a gidan nan bata taɓa zuwa inda take jin ba zata raga mata ba sai yau dan haka a fusace cikin ɓacin rai da Hausar ta da kana jinta kasan yare ce ta furta.
"Wallahi bazan yarda kina zagin iyayena ba dan ina auran ɗan ki, Abdullahi ka sake ni dan Allah nima na huta da masifar Mamanka."
Cikin Mamakin kalaman Safiya ya ɗago kai ya kalle ta sai kuma ya taso da sauri yazo gaban yace "haba haba Safiyya ba halinki bane maida magana, kiyi hakuri zan lallaɓa Iya zata haƙura dan Allah karki sake yin magana kinji?"
Nana da taji abinda yake cewa Safiya cikin izgilanci da zuga ta karkace ta rangaɗa buɗa, sai kuma tace "Ah lallai Iya kin mori Haihuwa."
Dije kuwa tunda Mai Kano ya tashi daga durƙuson da yayi a gabanta ya tafi wajen Safiya ta bisa da kallo baki hangame tace "kan uban nan, Mai Kano daga gaban nawa ka tashi ka tafi lallashin kafurar Matar ka?"
Kafin yayi magana Safiya tace "wallayi kina ganin kafurci a dangin ki amma mu duka iyayen mu babu kafurai." Ta faɗa tana rushewa da kukan baƙin ciki, itama Husna dake gefan saita fashe da kuka ganin Mamanta nayi.
Dije kuwa najin abin da Safiya tace sai ta ɗora hannu aka ta rusa ihu kamar wacce aka yi wa mutuwa tana faɗin.
"Mai Kano yanzu har nayi lalacewar da matar ka zata zageni a gaban ka kuma ka tsaya kana kallon ta?"
Sai kuma tsangal tsangal tayi hanyar ɗakin data sauka ta fara tattara kayanta a bakko tana faɗin.
"Gwanda na tafi na bar maka gidan ka tunda Safiya ta fini na barka da duniya da Safiya."
Kan Mai Kano yayi masa dum ya tsaya ya rasa inda zai saka kanshi saboda tashin hankali. Ganin Dije ta fito riƙe da bakkon ta a hannu mayafinta a kafaɗa tana kuka yayi wajen ta da sauri yana cewa
"Iya dan Allah ki rufamin asiri karki jamin zagi da fushin Allah, yanzu in kika tafi me kike so mutane suce a kaina?"
"Ka kori Uwar data haifeka akan Kafurar Matar ka." Dije ta faɗa, kanta rufe baki Safiya ta sake cewa.
"saidai kece Kafura Wallahi."
Nana ta ware Idanu tace "wallahi Mai Kano kayi asara agaban ka Matar ka ke zagin mahaifiyar ka harta kirata Kafura kanaji kana gani, hmmm lallai ka shawu."
Baiibi takan maganar Nana ba yaci gaba da ƙoƙarin hana Dije tafiya.
Ran Safiya a mugun ɓace ta shige ɗakin ta Husna ta bita a baya, bata jima ba ta fito ta canja hijabi Husna dake kuka na biye da ita a baya suka fice daga gidan ko kallon inda Mai Kano yake bata yi ba.
Kamar ta hana Husna binta sai kuma tayi tunanin inta hanata binta gunwa zata koma, wajen Nana da babu alkairi a bakin ta ko wajen Dije da take ji kamar ta sasu a wuta ta ƙona ita da Husnan, hannuta ta kama sukabi ta bayan layi.
Safiya taso ta wuce Birget gidan su sai kuma tayi tunanin yau Sunan Yaya Kemi gwanda taje gidan sunan tasan yanzu duka ƴan uwanta suna can, itama tun jiya da yamma taso taje ta kwana Mai Kano ya hanata, daidai transformer Ali Babur suka sauka, tana riƙe da hannun Husna har digan Yaya Kemi tun daga relar gidan ta fara cin karo da yaran ƴan uwanta suna ganin ta suka fara gaishe ta bata amsa ba ta shige cikin gidan.
Tawakallatu da Aunty Mansura dasu ta fara cin karo a bakin Famfo suna wanke hanji, afujajan suka ganta ta shigo idanunta sunyi ja sun kunbura, gaban Aunty Tawakallatu ya faɗi ta tare ta da sauri tana cewa "Ke Safiya lafiya kuwa daga ina kike haka?"
Aunty Mansura ma sakin wanke naman tayi ta dauraye hannunta suka taru a kanta suna tambayar ta lafiya, maganar Aunty Mansura tasa Safiya fashewa da kuka ta rungume ta.
"Innalillahi wa inna ilaihirraju'un, Safiya daga ina kike haka? Meya faru? Ina Husna? Wani abu ne ya samu Abdullahi?"
Ba ƙaƙƙautawa Tawakallatu ta jero mata tambayoyin lokaci ɗaya, kukan Safiya da hayaniyar su Aunty Mansura ya jawo hankalin sauran mutanen suka fito da sauri, ganin abinda ke faruwa su Aunty Sakina da suka fito daga ɗakin Yaya Kemi suka zagaye Safiya dake kuka sosai suna tambayar ta lafiya, Yaya Kemi ce ta kula da Husna dake tsaye a gefe tana kuka ta kamo hannunta tace "A'a Mamana zo nan, Sakina kama ta muje ciki."
A tsakiyar falon Yaya Kemi suka zaunar da Safiya dake kuka kamar ranta zai fita, Aunty Momi data fito daga uwar ɗakin Yaya Kemi hannuta riƙe da jariri tayi turus gaban ta ya faɗi tana kallon ƴan uwanta da suka zagaye Safiya, Tawakallatu ta cire mata hijabi ganin tana zufa, Aunty Mansura ta ƙara gudun fanka Yaya Kemi ta zauna a gaban Safiya sauran ƙannen ta suka zagaye ta.
"yi hakuri Safiya ki faɗa mana maiya faru, duka hankalin mu ya tashi."
Safiya sai tayi kamar zata danne kukan ta amma inta tuno maganganun Dije sai baƙin ciki ya taso mata ta sake fashewa da kuka, ganin haka yasa hankalin su Yaya Kemi sake tashi, tabbas duk abinda yasa Safiya kuka irin wannan ba karami bane, sunsa Safiya tanada hakuri ga zurfin ciki, ita ce ƙarama a cikin su amma duk ta fisu haƙuri sanyin hali da rashin san fitina, jikin su a sanyaye suka fara rarrashin ta da ban haƙuri da kalaman kwantar da hankali, ganin hankalin ƴan uwanta ya tashi ta daina kukan sai haɗiyar zuciya, ruwa Aunty Mansura ta bata tasha ta ɗan nutsu Yaya Kemi ta cewa Aunty Momi.
"kai Husnah wajen su Maamah kice su lallashe ta su bata abinci dan bana jin sun karya, itama Safiyar Tawakallatu haɗa mata shayi ta karya."
Muryar Safiya a shaƙe tace "ku bari bazan iya shaba."
Maimakon su bari ɗin kamar yadda tace sai Aunty Mansura ta miƙe ta haɗa mata shayin Aunty Momi kuma ta kama hannun Husna suka fita. Wajen yaran Yaya Kemi takai ta tace su kula da ita, sannan ta koma bangaren Yaya Kemi.
Da ƙyar Safiya tasha rabin kofin shayi amai ya taso mata saida ta amayar da shayin da tasha tass sannan ta wanke bakin ta Tawakallatu na dafe da ita suka dawo falon Allah sarki Yaya Kemi duk isakar falon saida ta haɗa dayi mata fifita da muhuci.
Saida tadan sake samun nitsuwa sannan tana share hawayen daya zobo mata ta kalli yan uwanta murya a karye tace "Maman Abdullahi ta sani a gaba, wallahi tunda ta dawo da Nana bani da kwanciyar hankali, Maman shi ta hana ya kwana a ɗakina saboda nace bazan iya cin girkin matar shi ba, ta hana sa shiga wajena, tace inya sake shiga ɗaki na ko bayan idonta ne Allah ya isa bata yafe masa ba, in inason magana dashi sai dai na fito mu haɗu a cikin gida shima tana jin fitowa ta zata fito ta tsaya a wajen wai karya kwashe kuɗi ya bani nayi girki tunda nafi ƙarfin naci wanda Nana tayi, ta hana mana kwanciyar hankali duk abun nan da take bana kulata tunda inada komai na amfani ko Abdullahi bai bani kuɗi ba yasan zanci abinci amma duk da haka tasa ni a gaba safe dare da rana masifa take, ita lallai bata yarda ba dole shi yake bani kuɗi a ɓoye, Husna bata isa taje kusa da Baban taba saita kore ta sai dai Matar shi da Ni'ima, komai ya kawo inya bawa Husnah sai ta kwace ta rage tace yayi yawa ita ce ƙarama wai danme zai bata kai ɗaya da yayarta, Matar nan ta hanani zama lafiya kullum masifa babu dare babu rana amma haka na haƙura saboda tausayi Abdullahi yake bani, wallahi duk ya rame saboda damuwa.
Safiya tashare hawaye tace
"Yauda safe......ta kwashe labarin duk abinda ya faru ta faɗawa yan uwanta.
Aunty Mansura da tafi sauran saurin hawa da zuciya ta miƙe a fadace tace "ku tashi muje wallahi basu isaba."
Yaya Kemi ta kalli Aunty Mansura tace "kinga koma ki zauna muyi magana a nitse gidan nan da mutane kar kusa hankalin su ya dawo kanmu."
Jin labarin halin da Safiyya take ya ɓata ran su kowa ka kalli fuskarsa babu walwala ko kaɗan, babu abinda yafi ci musu rai irin yadda Dije ke zagin ubansu dake kwance a kabari da kiran su arna Kafurai, Shawara suka yanke, Tawakallatu Aunty, Momi da Aunty Sakina su raka Safiya gida ta dakko abunda take buƙata daga gidan sunan saisu wuce Birget gidan su dole Mai Kano yazo su Baba Habu su shiga maganar a yiwa Safiya tsakani da Nana da Maman sa. Wannan shawara ta Yaya Kemi tayiwa kowa dai-dai banda Aunty Mansura da taso suje suci ƙaniyar Nana da Dije daman ita akwaita da zafi ga faɗa, badan taso ba Yaya Kemi ta danne ta da faɗin.
"Ko babu komai Mansura saimu duba Abdullahi yana da kirki kuma duk munsan yadda yake son Safiya da kula da ita, duka Mazajen mu sunfi sa rufun asiri nesa ba kusa ba amma cikin mu babu wanda ya kai Safiya kwanciyar hankali da samun kulawar Miji, to kodan wannan muyi masa uzuri mu bari su Baba Habu su fara shiga cikin maganar komai zai yi daidai."
Wannan magana ta Yaya Kemi tasa duk jinkin su yayi sanyi dan duk sun sani sun kuma shaida Mai Kano na kaunar Safiya su kansu suna jinjina wa ƙoƙarin sa dan mutum ne mai wadatar zuci ga kirki da haƙuri, ko baka ganshi ba inya ganka saiya ma magana ya ma alheri inda yaro a hannuka baya rasa abinda zai basa koba yawa, haka baya gajiya da zuwa gaida iyayen su tun Alhajin su na raye, kuma har bayan mutuwar sa bai daina zuwa ba, duk lokacin da yaje gaida su Maman Sama baya rasa mezai kai musu dai-dai karfin sa, kai ko Mazajen su da suka dame shi a wadata da samu ba zasu nuna masa Alkhairi ba, baya gajiya Mazan su da matan su sun san haka sau da dama sukan ce "Safiya ke dai Allah ya dube ki yaga baƙin cikin da kika shaƙa a baya a gidan Alhaji Manu shi yasa ya wanke miki zuciya da miji irin Abdullahi, ko suce Allah ya baki Mijin marainiya." sun sha faɗa wa Safiya haka har basu san adadi ba, dan haka suke girmama shi.
Ƙaddara ta riga fata
..........Wannan komawa ta Safiya da ƴan uwanta gidan Mai Kano ita ce mafari silar faruwar komai.
Ita ce mabuɗin Ƙaddarar Husna
Ita ce dalilin wahala, mafarin shigar wani sabon lissafi cikin rayuwar Husna.
Wannan komawa ita ake kira da rashin sani wanda yafi dare duhu, tsautsayi wanda ba'a saka masa rana, tabbas da Safiya da ƴan uwanta sunsan da guzurin da zasu dawo daga gidan Mai Kano da basu jeba, da basu taka ƙafafun su a Rimin kebe ba.
Saidai masu iya magana sun ce "ita ƙaddar ta riga fata, haka bawa baya wuce ƙaddarar sa"
Wannan zanen ƙaddara ita ce ta faru da Rayuwar Safiya alokacin da ta saka ƙafafun ta a gidan Mijinta uban yarta Husna....
Da Sallama suka shiga gidan Aunty Sakina ce a gaba Safiya da Tawakallatu a baya, a tsakar gida suka tadda mutanen gidan Nana na zaune tana cin tuwo, Dije na kan taburma Mai Kano yana zaune a gefan ta.
Shi kaɗai ne ya amsa Sallamar jikin shi a sanyaye.
"A'a Baban Husnah kana nan ashe baka fita kasuwa ba." Aunty Momi ta faɗa.
"Um ina nan Aunty yanzu nake shirin fita, sannun ku da zuwa." ya faɗa yana kallon Safiya data wuce ɗakin ta.
Su Aunty Sakina kamar su wuce basu gaida Dije data haɗe rai kamar taga mutuwar ta ba sai kuma wata zuciyar ta tuna musu ko babu komai fa Uwar Abdullahi ce, Abdullahi kuma mutum ne harda ƙari dan haka taci darajar ɗanta da shima bai taɓa kin gaida nasu Iyayen ba.
Aunty
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 31