basu mata renon faɗa mata abunda ba zai yiwu ba da sunan hillata ko yiwa yaro wayo, sam Safiya bata yarda da wasan yiwa yaro ƙarya ko cewa zanyi maka kaza ko zan siya maka kaza dan yaro yayi shiru ko kar yayi rigima ba, a'a ita kai tsaye takewa yaran ta magana in akwai abu akwai, in babu ta baka haƙuri.
Yakan tuna wasu lokutan da inzai tafi kasuwa Husna kan bashi sautukan "Baba ka siyo min kaza da kaza." Sako dai irin na yara ga Iyayen su, duk lokacin da ta faɗi wani abu da bazai yiwu ba kan ya bata amsa Safiya zata ce "Husnah Baban ki bashi da kuɗin siyan jirgin sama kiyi addu'a Allah ya kawo su." A lokacin sai dai yayi dariya yace "ke kuwa Safiyya ki barta mana yarinta ce fa, kuma wannan dogon bayanin naki shekarun ta ba zasu gane ba."
"Zata gane tunda tana da Allah, ƙwaƙwalwar Yaro bata rena magana yanzu saita koyi ƙarya da yaudara." Duk sanda suka yi haka da Safiya sai dai yayi dariya ya fice.
Bai fara gano ma'ana da amfanin yin haka ba saida Husna ta fara girma.
Wannan tunanin yasa ya dubi ta ya dafa kanta cike da soyayya ya ce "zan kaiki wani waje da ban amma ba wajen Yaya da su Momma ba kinji?"
Duk da Husna ba haka taso ba amma saita daga kai kana duban sa, ita dai indai za'a bar nan ɗin to shike nan buƙatar ta ta biya.
_NI A'ISHA A ZUCIYA TA NACE "SHIKE NAN AMMA FA BA SHI KE NAN ƊIN BA ASMA'ULLAHI HUSNAH_.
Nana na zaune a ɗaki ta cika tayi fam Mai Kano ya shigo, kallo ɗaya yayi mata ya ɗauke kanshi ya fara shirin kwanciya.
"Baban Ma'u ban gane abinda kake nufi da kwana da kayi kana gadin Ma'u da sunan Sallah ba?"
Ba gaisuwar safe babu tambayar ya ya tashi kawai ta haushi da mita, akace wai sanin hali yafi sanin laya, bashi da lokacin fitina da ƙananun maganganun ta bacci yake son ragewa kansu tafi.
"Dan Allah bacci zan yi Nana karki samin ciwon kai, yi haƙuri kije waje inna tashi mayi maganar." Ya faɗi yana duban da da kyau, dan baya son ta sake masa wata magana kuma.
Ƙwafa tayi a ranta tana fitowa waje ta fara shara da hura wutar karin safe.
"Ai zaka tashin, dan wallahi bazan yarda da wannan sabon iya Shegen ba." Nana ke sharar tsakar gidan tana mita.
Bai tashi daga baccin ba sai goma saura, sosai yaji daɗin jikin sa nauyin da zuciyar shi tayi masa yaji ta ragu.
"Ina kwana Baba?" Ni'ima ta faɗa lokacin da ya fito tsakar gidan.
"Lafiya lau ƴar Iya." Ya amsa mata yana duban Husna dake juya kofin kokon dake gaban ta.
"Husnan Baba ko jikin ne har yanzu?" Ya tambaye ta, kai ta girgiza masa, ya sake tambayar ta tasha maginta na safe.
"Uhm." Ta amsa har yanzu kanta na ƙasa.
Yasan tasha ɗin tunda tace tasha dan bata da kin magani dama dai allura ce to nan fa ɗaya.
"A kaima ruwan wankan ne?" Nana ta tambaye shi, yace "A'a sai an ɗan jima." Ya bata amsar yana shigewa ɗakin da Husna ke kwana.
Kayan sawarta ya gyara ya kwashe masu dattin ya zuba a jakar sama, saida ya gama haɗa kayan waje ɗaya sannan ya zuge ƙatuwar akwatin kayan nata, sauran na jakar kuma ya barsu a buɗe bai rufe ba, doguwar rigaa baƙa ƴar Saudi ya ciro mata wanda zata saka in zasu tafi sannan ya ciro mata sabon hijabin ta fari ɗan ƙarami mai kyau ma haɗin rigar ya ajiye akan katifar.
Waje ya fito yace "Husnah tashi kiyi wanka rana na sake yi." Yana faɗa mata haka ya ɗakko botiki da kanshi ya zuba mata ruwa, ruwan zafin da Nana ta ɗora masa na wanka ya ɗebo ya sirka mata ruwan sannan ya kai mata banɗaki yace "jeki kiyi wankan ina jiran ki maza."
Nana baƙin ciki ya sake kashe ta a zaune.
"Ai wallahi da nasan ita zaka bawa ruwan nan daban ɗora maka ba." Tayi maganar a ranta a fili kuma saita ɗan ja tsaki ƙasa ƙasa yadda ba zai jita ba.
Ni'ima ta dubi Baban nasu tace "Baba wani wajen zaku?"
Yace "eh ƴa Iya."
"Allah ya kiyaye hanya." Ni'ima ta fada, Nana ta harare ta dan ba haka taso tace ba taso ta tambaye shi inda za su dan tasan halin baƙin zurfin cikin sa inba shi ya gadamar kaji abuba to duk nacin ka baka isa ya faɗa maka ba.
Husna na fitowa daga banɗakin ya ce ta zauna ta sake wanke kafarta, sannan ya shiga shima yayi wanka.
Ƙarfe sha ɗaya mai kyau sun gama shirya wa, Nana nata bugun cikin shi taji inda zai kai Husna dan taga ya fito da duka kayan ta ya ɗaure katifarta amma sai yayi mata banza dan fes ya gane nufin ta.
"Koma inane ai maji daga baya." Nana ta faɗa a ranta, lokacin da suke ficewa daga gidan yana riƙe da hannun Husna.
Ɗan sahun daya ɗakko su na tsayawa a cikin tashar Yankaba inda ake hawan motar Gumal ƴan Union suka fara tambayar.
"Alhaji tafiya ne? Ina zaku je? Gumal ne ko Garki, Mai gatari, Malam madori ko Hadeja?"
"Gidan'ri zamu." Mai Kano ya basu amsa bayan ya sallami me mashin ɗin daya kawo su.
"Kai ɗan Small gana Gidan'ari sasu a motar Garki."
Kujerar baya ya biya kuɗin mutum uku aka ƙara mutum ɗaya suka zauna a wadace.
Basu jima ba motar ta cika suka tashi, kansu tafi sai da ya siya wa Husna lemon bawo suna fara tafiya ya rinƙa ɓare mata yana bata tana sha dan ya santa da aman mota sam bata son warin fetir.
Gidan'ari babu nisa titin Hadeja road wanda zai kaika Gezawa shizai kaika har garin babu kwana, dan tafiyar bata wuce awa ɗaya ba, kana zuwa Gezawa kayi rabin tafiyar, Gidan'ari ƙyauye ne amma a bakin titi yake kamar yadda Gezawa da Gabasawa suke a bakin titi, haka titin shizai kaika Doko, Garki Har zuwa Mai Gatari.
_To fa, ga rayuwa ta sake ɗauke Husna daga Birnin Kano zuwa garin su Mahaifin ta a cikin Jihar Jigawa, cikin wani ɗan ƙaramin ƙyauye da ake kira Gidan'ari._
_Shin koya rayuwar ta zata kasance a wannan gari?_
_Wacce irin rayuwa zata fuskanta a garin su maihaifin ta?_
_Me zata tarar?_
_Shin dangin mahaifi ta zasu karɓe ta hannu bibbiyu ko akasin haka?_
_*WRITING.....✍🏻*_
*_MUTUWAR AURE.....!_*
_(Ƙaddarar wasu ƴaƴan)_
*_Kanawa ne👌🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_BOOK 1_
*_FREE PAGES_*
________________
*_WHATSAPP GROUP👇🏻_*
https://chat.whatsapp.com/LaVfMaCQz1C2WcC7zGfSL3?mode=gi_t
https://wa.me/+2348064789370
_________________
_EPISODE 15_
A 2009
Husna ta shigo cikin garin su mahaifin ta da sunan zaman ɗan wani lokaci.
Aramma dake sauraren bayanin da Mai Kano ke masa akan ɗan abokin shi ya girgiza kai yana ambaton sunan Allah.
"Ashsha gaskiya Sale yana cikin jarrabawa, Subhanallahi, Allah ya shiryi masa wannan Yaro, karka damu saita zauna a nan ɗin hankalin ka zaifi kwanciya gaskiya, in yaso inka gama ginin sai kazo ka ɗauke ta, Allah dai ya sake taimaka wa ya rufa muku asiri duniya da lahira." Aramma ya faɗi maganar yana jin tausayin Sale.
Dije dake gefan shi a zaune kuwa baki ta kama tace "kai amma wannan anyi shaiɗanin yaro mara ta ido, to Allah dai ya rabaku dashi lafiya dan irin waɗan nan yaran zama dasu sai ana kulawa, sam baiyi halin ubanshi ba, uwarsa ma ai mutuniyar kirki ce bakaga abun arzikin da take min ba innaje, kayya albasa batai halin ruwa ba."
"Kayya kayya Hadiza wannan wacce irin magana ce haka? Ina hanaki aibata ƴaƴan wasu ba kya ji ko? Kai da kake da ya'ya ga jikoki nan turmus wasu ma ba'a haife suba, wasu kuma saika mutu zasu zo duniya amma shine kike wannan magana haka mara daɗin ji akan ɗan wasu? Dije waya aike ki irin wannan zance? Kayiwa ɗan wani fatan Alkhairi Allah saiya gyara maka naka. Karna sake ji dan Allah." Aramma ya tari numfashin Dije da tsawatar wa akan abinda tace.
Aramma ya dubi Mai Kano yace "ai kace karshen watan nan zaka fara ginin ko?"
"Eh in sha Allahu haka nake fata, ko ɗaki biyu na samu na rufe kawai saimu koma."
"To hakan yayi Allah ya taimaka yasa Albarka, ke Asma'ullahi Husnah zomu gaisa mana kwana biyu baki biyo Babanki kunzo tare ganin tsohon angon naki ba." Aramma yayi magana yana kama hannun Husna dake zaune a kusa da Baban ta.
"Ina kwana?"
Aramma yayi dariya yace "ai kina shigowa muka gaisa ko dai harkin fara tsufa ne Husnatu." Da tsokana irin ta kaka da jika Aramma ke yiwa Husna magana, Dije kuwa taɓe baki tayi, dan tunda suka shigo Husna ta gaishe ta ta amsa sau ɗaya bata sake kallon inda take ba.
Mai Kano ya ware kayan sawar ta mai datti yace "wannan masu datti ne." Aramma ya dubi kayan yana Murmushi yace "Asma'ullahi dai ba zata iya wanki ba tunda ba renon mu, bace wannan riƙon shayi da Burodi ce bata da ƙarfi, saina bata tuwon gitti da miyar kuka tukunna zatayi ƙwari. Aramma ya faɗa yana Murmushi sai kuma yace "babu komai inaga sai a kaiwa uwarta Mariyatu ta wanke mata masu dattin ko?." Dije tayi caraf tace "yanzu wannan ƙatuwar budurwar ce za'a ce sai anyi mata wanki banda dai san ɓata yaro irin naka Aramma? Sa'ar Sajidan Mariya ce fa, yanzu meye Sajidan batayiwa kanta."
"Ke matsala ta dake rashin gane wa Hadiza in sa'anin juna ne yanayin tasowar su ai ba ɗaya bace, yaran Maraya (binni) kamar wannan basa wanki, kuma in kinyi haƙuri ma zaman nata anan duka duka na kwana nawa ne zata koma inda ta fito."
Mai Kano dai yana zaune yana jinsu haka Husna dake zaune a kusa da Aramma.
"Kinga tama fasa zama a ɗakin ki dan naga alamar bazaku shirya ba, a matan gidan nan zan yi mata uwa da kaina saboda naga alamar bazaku daidai ta ba." Aramma ya faɗi yana ƙwala wa yaran cikin gida kira, basu jiyo shiba, ya dubi Husna yace "Asma'ullahi maza jeki cikin gida kice Ramma tazo injini."
"To." Ta amsa mishi tana miƙe wa ta fito waje, dan tasan duka matan gidan tunda suna zuwa da Maman ta.
Bata jima da fita ba sai gasu sun dawo tare da da Ramma, a ƙofar ɗakin Ramma tayi sallama, daga cikin ɗakin Aramma da Mai Kano suka amsa, sai kuma ta durƙusa tace "Aramma gani."
"Dama ƴace nayi miki gata nan Asma'ullahi zata zauna damu na ɗan wani lokaci."
Cikin girmamawa Ramma tace "to Aramma nagode." Ta faɗi da murnar ta dan bata da yaro ko ɗaya a gidan wajen shekarar ta guda ke nan da auran Lirwanu amma har yanzu Allah bai bata haihuwa ba, sannan tasan Maman Husna duk da baifi sau biyu ta taɓa ganin taba amma ita kanta ta shedi kirkin matar.
Aramma ya sake cewa "Yawwa ki duba cikin gida insu Iro na nan kice nace suzo su kawo miki kayan sawar ta."
Ramma ta amsa wa Aramm da "to." Ta miƙe ta koma cikin gida.
Dije kuwa saita taɓe baki tace "nima na huta gwanda ma daka haɗa su can su karata."
Aramma baibi takan zancen taba suka ci gaba da magana da Mai Kano.
Yara na fita da kayan Husna Lirwanu ya shigo ɗakin da Sallama.
"A'a harka dawo daga ɗan bagajen ke nan?" Dije ta faɗa, saida ya zauna a kusa da Mai Kano sannan yace "eh nadawo dama ƴan gaisuwa nakai ina kaisu kuma na juyo.Yaya Mai Kano sannu da zuwa?"
"Yawwa Sannun ya gida da iyali?"
"Lafiya Alhamdulillah a'a Ma'u yau tare kuke ke nan?"
Husna ta ɗan zamo ta rusuna kamar yadda ta saba tace "ina wuni." Yana cika baki da ruwan tsaki da kanwar daya gani a gaban Aramma ya amsa mata.
Aramma ya dube shi sai kuma ya girgiza kai ya mai da hankalinsa wajen Mai Kano yace "kaga wannan kanin naku sai kuna masa addu'a ni bansan ina Lirwanu ya kwaso halin shiba, kowa na neman yadda zai rufawa kanshi asiri amma banda shi gashi da mata da yara amma har yanzu hankalin nashi da saura."
"Wani abun ya kuma yi ko Aramma?" Mai Kano ya tambaya yana duban Aramma dan yasan halin Lirwanu da rashin sanin ya kamata.
"Hmmm! Ɗan mashin ɗin da Salisu ya haƙura yabar masa yana acaba dashi tunda yaƙi zuwa kasuwa ya nemi kuɗi, to shiya ɗauka ya siyar shekaran jiya."
Mai Kano ya buɗe baki yana duban Lirwanu da mamakin jin maganar yace "Kai to me kayi da kuɗin?"
Kan yayi magana Dije tace "kaji Mai Kano da wani zance yanzu magidanci kamar Lirwanu har a tambaye shi me yayi da kuɗi."
Aramma ya dube ta cikin takaicin zancen ta yace "da yake shi kadai ne me Iyali ko? Wai me yasa duk lokacin da Lirwanu yayi abu bakya bari ayi masa magana ne Hadiza? Yanzu bama wannan ba ki faɗa min me yake siya a gidan nan na hidimar Iyali wanda zai sa har ya dauki mashin ya siyar?"
"Sabulun wanka dana wanki mana Aramma ai kasan dai shi yake siyawa matan shi."
Baƙin cikin managar ta ma saiya hana Aramma sake cewa komai.
"wai sabulun wanka dana wanki." Dan Allah ji wani zancen banza.
Mai Kano ya gyara zama zai yi magana sai kuma ya cewa Husna "jeki cikin gida wajen su Indo kuyi wasa, bari nayi magana da Babanki kinji?"
Kai ta ɗaga masa ta fita daga ɗakin, shi kuma ya fuskanci ɗan uwan nashi ya fara masa faɗa da nasihar da in haddace wa ce ma ya kamata ace zuwa yanzu ya hadda ceta tsaf babu gyara saboda kusan duk sanda yazo garin saiya biya masa ita kanya tafi sai dai in basu haɗu ba.
....... Husna na fitowa ta gaida matan gidan, ta samu waje ta zauna a ƙasan unuwa, sauran matan sai tambayar ta suke tana daga masu kai, Indo ƴar gidan Salisu da suke kusan sa'ani duk da ta ɗan girme mata kaɗan ita ce tazo wajen ta tana mata surutu, ita ma bata wani kula taba sai kallo da take binta dashi.
A gaban ta su Zahara da sauran matan makota suka kafa gulma harda masu ƙarfin halin tambayar ta ko an dawo da ita nan da zama.
"Allah na tuba dama fa Nana bazata riƙe wa Yaya na Kano ƴa ba, a banza ma tana son nuna isa da ƙafafa bare yanzu tayi nesa da gida babu mai saka mata ido, ai sai abinda ta shuka." Zahara ta faɗa, Naja ma ta kama baki tace "yo Miji ne Allah ya wanke ya bata irin Yaya Mai Kano da indai yana dashi babu mugunta, ai kuwa yanzu zata fantama san ranta."
Gaje ta ɗago kai ta dube su baki a taɓe tace "hmmm ai nizan baku labarin Nana tunda munɗan zauna tare, bata da kirki ga baƙin cikin tsiya ta tsani taga Yaya Mai Kano ya yiwa wani abun arziki, yanzu bagashiba ta ɗauke tata yar ta turo ta kishiya ƙyauye."
Haka suka yi ta caccakar Nana daga baya kuma gulmar ta koma kan Dije duka Husna na zaune tana jinsu, Ramma bata wajen tana murhu dan ita ce da girki.
Ana kiran sallar la'asar Aramma suka fito daga ɗaki, Dije na biye dasu a baya, alwala suka yi, Husna ta tashi taje wajen Baban ta.
"Bari naje masallaci na dawo ko?" Ya faɗa yana duban ta, kai ta ɗaga masa.
Sun zo zasu fita yaga kayan dattin Husna da Ramma ta wanke ta shanya su akan danga, hakan yayi masa daɗi sosai, dama ɗazu Aramma ke sake faɗa masa halin kirki da nutsuwar Ramma.
Ya ɗanyi gaba da matan gidan ya kira Husna ta zo wajen shi, hannu yasa a aljihu ya ɗakko ƴan ɗari biyar biyar guda biyu ya miƙa mata.
"Ga wannan ki kaiwa sabuwar Maman taki kice kusai sabulu, in sha Allah zan bada sabulun ma a kawo muku sauri ne yasa na manta bamu siya ba."
Husna ta dub Babanta da son ƙarin bayani dan bata gane wace sabuwar Maman taba, murmushi yayi yace "gata can wacce tayi miki wanki, aikin gane ta ko?."
"Eh." ta faɗa tana karɓar Kuɗin, tace "Nagode Baba." Sannan ta juyo cikin gidan.
Duk abin da ke faruwa tsakanin Husna da Baban ta Dije na kallon su, duk da batajin me yake faɗa mata ba amma taga sanda ya bata kuɗi.
Husna ba munafunci dan bata san wani a abu wai a ɓoye abu ko a aike ka kaƙi bayar wa a gaban mutane ba, zuciyar ta ɗaya ta miƙa wa Ramma kudin tace "Gashi inji Babana yace kuɗin sabulu ne."
Baiwar Allah Ramma da hannu biyu ta karɓi kuɗin kamar shiya bata da kanshi tace "an gode."
Nan fa matan gidan suka fara mata tsiya da shewa.
"A lallai riƙo ya fara rana tab jaka biyar zuwait da marecen nan lallai Ramma yau shar dake."
Suna mata karaɗin tana murmushi Dije tazo kansu ta tsaya tana cunkushe fuska ta cewa Ramma.
"Bani kuɗin da Mai Kano yasa Ma'u ta kawo miki."
Gaje tayi caraf tace "Ah uwar Mari kuɗin Sabulu ne fa bakiga tayi mata wanki ba?"
"Ban gani ba nace ban gani ba ƴar me baki a sama, caraf harkin karɓe zancen kamar kena tambaya."
Zahara da kishi da bakin cikin kuɗin ke cinta arai tace "A'a ke ma Ramma dama ai ba duka zaki riƙe ba, na ɗauka dama bayar wa zakiyi Iya ta cire miki kuɗin sabulun ki sauran a kasawa yan gida."
Ramma bata ce komai ba ta ɗakko kuɗin zata bayar Naja ta rinƙa kifta mata ido ta rage amma, sai bata kula ba ta bawa Dije duka, ta kuwa sa hamnu ta amshe tana faɗin.
"Ah lallai keda saiki riƙe duka jaka biyar ɗin da sunan kuɗin Sabulu, saboda haɗa ma?" Ramma dai bata ce mata komai ba, Dije ta kun ce zanin ta ta ɗakko tsohuwar Jaka guda a cikin Kaja (yar jakar da tsaffi ke daurawa akan siket) ta miƙa wa Ramma tace "gashi kuɗin sabulun harda riba."
Gaje kamar ta hana Ramma karɓa amma babu dama, dan ita dama basa zaman daɗi da Dije saboda bata bar mata, duk wani iko da mulkin da Dije keyi a gidan bata wa Gaje dan ita ma da ɗuwawon ta take zaune a cikin gidan. Wannan yasa kullum Dije inta zauna saita zagi gaje tace sun yiwa Salisu asiri ita da Uwarta sai abinda suka ce masa. Duk sanda Dije ta faɗi haka Gaje saidai tayi murmushi ta manna mata hauka randa ƴan rigimar ke kanta kuma ta kulata suyi, amma duk da wannan Dije bata iya ɗaukar wani matakin arziki akan gaje saidai zagi da baƙaƙen maganganu.
Baiwar Allah Ramma kuwa hannu biyu tasa ta karɓi ɗari biyun harda godiya.
Magarba na kawo kai kowa ya koma kewayen shi, Ramma taja Husna suka shige wajen su ta nuna mata taburmar data shimfida ta zauna akai, tana kallon ko ina a lungun, bawai dan bata san gidan da mutanen gidan ba Zaman jiran shigowar Baban ta take tun dazu, dan tunda suka fita Sallar la'asar basu dawo gidan ba gashi har ana kiran sallar Magarba yanzu.
Yayin da Husna ke can zaune tana zaman jiran dawowa Babanta, shi kuwa tuni ya tsufa a Kano dan dama saida yayi sallama da Dije kanya fito daga gidan, suna idar da sallar la'asar ɗin kuwa bai jima a tashar ba ya hau mota ya dawo gida.
Da gangan kuma yayi haka, yaƙi komawa gidan ne saboda yasan muddin Husna zata ga tafiyar shi to sai tayi kuka tace ba zata zauna ba, wanda shi kuma haka ne baya so ya gani, wannan yasa ya sulale yayi tafiyar sa ba tare data sani ba.
Karfe shida a gida ta same shi, bayan ya huta Ni'ima ta dakko wata farar leda mai dan girma ta aje a gaban shi tace "Baba wannan kayan Ma'u ne, ɗazu baku jima da tafiya ba wani yazo a mota neman ta, nace masa kunyi tafiya shi ne yaban wannan yace na bata zakuyi waya dashi."
Mai Kano ya ɗanyi shiru yana tunanin to waye wannan, saida yaji Ni'ima ta sake cewa "Baba na sanshi fa in muka je gidan Alhajin Birget ina ganin shi, wani da Ma'u ke kira Abba."
Sai yanzu ya gane waye "oh Abdussamad ne." Ya faɗi yana duba ledar, kayan ciye ciye ne irin na yara. Ni'ima ya cewa ta ɗauki ledar duka kayan ciki ya zama nata, sai kuma ya ɗora da faɗa mata.
"Husnah bata nan na kaita Gidan'ari ki ɗauka duka ya zama naki." Ni'ima ta ɗauki ledar tana murna, yayin da Nana taji saukar maganar shi kamar yayyafin ruwan sanyi a cikin zuciyar ta.
"In Allah yaso ta tafi ke nan, can zata ƙare rayuwar ta." Nana ta faɗi haka a ƙasan zuciyar ta, tana shewa ranta fari tas.
A fili kuma sai ta murje taci gaba da uzurin dake gaban ta kamar bata san wainar da suke toyawa ba, tana jinshi suna hira da Ni'ima yanata bata labari, Nana tayi musu fakare kamar bata gidan.
*****Har bayan sallar isha'i Husna bataga Baban ta ya shigo ba, nan fa ta fara zare ido zatayi kuka, tuwon da Ramma taje ta sako mata a ƙofar Dije ma kasa ci tayi ta sashi a gaba tana juyawa.
Lirwanu ne ya shigo wajen nashi ya ganta a zaune tana juya tuwo Ramma na gefan ta tana irga sauran alewar da take siyar wa, taga ta nawa ce ta rage.
"Sannu da zuwa." Husna ta faɗa muryar ta na rawa.
"A'a Ma'u kina nan ashe?"
Ramma tace "ka ganta nan tana zaman jiran shigowar Yaya".
"Wanne yayan kuma? Badai Babanta ba ko? Dan shi yanzu ai ya daɗe da zuwa gida."
Ai Husna najin haka ta fasa kukan da take ta riƙe wa, duka sai suka tsaya suna kallon ta, kuka take bin hakki harda sheshsheka, tausayin ta ya kama Ramma ta fara lallashin ta amma fir taƙi yin shiru, Zahara ma tasa baki taƙi kula su, Lirwanu da haushin ta ya kule ya daka mata tsawa.
"Ke yimin shiru anan ko nabi ta kanki, ƙatuwa dake zaki samu gaba kina mana kukan iskanci dan ance ubanki ya tafi, to da sakaki zai yi a gaba yana kallo? Naji kin ƙara bude bakin ki anan saina tattaka ki."
Gum Husna ta rufe bakin ta da hannu amma kukan har yanzu take saidai ba sauti sai gurnanni.
Aramma da shigowar shi gidan ke nan yaji hargowar Lirwanu yace "to shi kuma wancan shida waye yake wannan faɗan?"
Dije ta ce "shida Ma'u mana, ina nan naji kukan ta nayi lungun nasu sai naji wai ashe kukan tafiyar uban take shi ne na fasa shiga na dawo."
"Yanzu Asma'ullahin Lirwanu yake wa wannan tsawar sai kace wata babba?" Aramma yayi maganar yana fasa zaman da zai yi ya fara ƙwala mata kira "Asma'ullahi! Asma'ullahi!!! Ke Indo kiramin ita a wajen Lirwanu, haka kawai yasa yarinya a gaba yana mata hargagi wannan ai saiya sake fitgita ta."
Indo ta tafi kiran Husna Indo na shiga lungun tace "Ma'u kizo inji Aramma." Husna ta miƙe zumbur tana haɗa hanya tabi bayan ta.
"Zo nan kusa dani ki zauna kinji mai sunan manya, yi haƙuri dena kukan haka." Aramma ke lallaɓa Husna lokacin da Indo ta rakota wajen shi.
Kusa da shi ɗin taje ta zauna amma sai kukan da Lirwanu ya hanata yi ɗazu ya kwace mata, ta kife kai a jikin gadon da Aramma ke
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 31