haske.
Maganar Husna ta dawo da shi daga tunanin daya shiga, tana masa murmushi take faɗin.
"Yaya ranar nan bakazo dandali ba nayi ta jiranka." Kamar yadda tasan ba zata samu amsar maganar ta daga gare shi ba hakan kuma baisa ta tsaya da maganar ba taci gaba da cewa.
"Yaya rashin lafiya fa nayi, kwana nan uku bani da lafiya, Aramma da Ramma sunata siyamin magani amma cuwon yaƙi warkewa saida matar Sunday tazo ta bani magani."
Sai kuma ta ɗanyi shiru tana jin ciwon Abinda Baba Lirwanu yayi mata yana taso mata, a hankali tace "Kuma bata karɓi kuɗi ba wai ni ƙawar tace, Yaya ai dai tana da kirki ko?"
Husna tayi maganar tana kallon sa, sai taga shima idanun sa har yanzu suna kanta, ganin idanunshi sun fito sosai fiya da randa mota ta kusa kade ta, sai ta ɓata fuska ta kumbura masa baki tace "Ni Yaya ka daina kallo na da idan ka tsoro yake bani."
Bai motsa daga yadda yake ba amma sai taga yaja Idanun sa luuuuu ya rufe su ruf, Husna ta saki Murmushi tsce "yaya Bahari ma yana da kirki saida ya zo ya duba ni kuma har kuɗi ya bani, amma Baba Lirwanu ya kwace kuɗin Ramma tana ta roƙon shi ya bari ta raka ni asibiti dashi amma ya hana ta."
Husna ta faɗa tana tuno abinda yayi mata ranar sai Idanun ta suka cika da hawaye kukan baƙin cikin da take ta dannewa tun randa abun ya faru taji ya taso mata lokaci ɗaya, tayi ƙoƙarin danne kukan amma saita kasa dan tsawan kwanakin nan tayi sune cikin kuncin zuciya da rashin daɗin rai muryar ta na rawa tace "Mamana tace min zalunci babu kyau duk wanda ya zalunci wani Allah saiya saka masa, Yayana yace cin kayan daba naka ba haramun ne ka ɗauka Allah baya son haka, amma shi Baba Lirwanu ya zalince ni kuma banyi masa komai ba." Husna tayi maganar kuka na kwace mata.
Ba zai iya fadin hali ko yanayin da zuciyar sa ke ciki ba amma tabbas ta tashi hankalin sa a gaba ɗaya gangar jiki da zuciyar sa yake jin wani irin mugun tashin hankali da kukan da take yi a gaban sa, ya zai yi ya hanata kukan ne kuma bai sani ba.
Husna kuwa mai makon bayan masallaci da take zuwa tayi kuka da suturun ta yau saita sashi a gaba tana kuka tana faɗin.
"Yaya banyi masa komai ba, haka kawai ya tsane ni kuma haka ya cewa Aramma yanzu shi zan rinƙa yiwa talla a kasuwa, Aramma yace sai dai ya rinƙa biyana ladan talla inba haka ba bazan masa talla ba, shi ne yace ya yarda zaina biyana hakkina amma wallahi yaya nasan ba zai rinƙa bani komai ba, nasan yanzu shike nan haka zanyi ta masa talla baya bani ladana."
Ta ɗanyi shiru tana share hawayen Idanun ta da suke ta zubowa sai kuma taci ga da magana.
"Ranar mafa Famfon cikin gari ne ya lalace gashi bani da lafiya inata ciwon kai da zazzaɓi shi yasa na kasa ɗebo ruwa da wuri amma shi ne Baba Lirwanu yayi ta zagina da marina yace wai ni munafuka ce dan karna ɗebo ruwan nace bani da lafiya." Husna na faɗin haka ta sake fashe masa da kuka fiye dana farko, dan abinda Baba Lirwanu tayi mata ranar dama yana danƙare a zuciyar ta inta tuno maganar binsa kasuwa talla sai taji kamar tayi ta kuka.
Yana zaune yana jinta da kallon ta sai kuma yaga tasa hannu tana share hawayen ta tace "babu komai nasan da Mamana da Yayana suna nan da bazan zo nan ba." Sai kuma kukan data tsaida ya dawo sabo.
Ta kife kai s saman cinyar ta tana kuka, yasa Sandar hannun sa ya ɗan daki ƙafar ta kaɗan yadda ba za taji ciwo ba, Husna ta ɗago tana duban sa sai taga idanun sa sunyi wani irin Blue kamar ba na mutane ba, bataji tsoron ganin idanunsa ba, shi kuma saiya cusa hannun sa a cikin tulin sumar kansa yana girgiza mata kai, lamarin daya bawa Husna mugun mamaki ke nan, ta tsaya tana kallon sa, ganin ya zuba mata ido yana juya kai saita saka bakin hijabinta ta share hawayen fuskarta.
Tana kallon sa har yanzu ya ɗan yi baya kaɗan sai kuma ya saka hannu a cikin burgujejen aljihun jallabiyar jikin shi ya ciro wata farar leda mai kyau ya miƙa mata, Husna ta kalle sa ta kalli ledar, sake bata yayi tana kallon fuskar shi ta karbi ledar sai taji da ɗan nauyi.
Tana buɗe wa taga wani Shortbread mai ɗan girba sai wata chaculate babba guda ɗaya da wasu sweet guda biyu Husna ta ɗago tana kallon sa sai kuma a hankali tace "yaya waya baka wannan?"
Kansa ya ɗauke ya maida gefe, Husna ta cika da mamaki ta kalli cikin ledar ta kalle sa.
"Yaya a ina ka samu wannan?" Wannan karon tana rufe baki taga ya juyo da sauri ya miƙa mata hannun sa alamar ta bashi abun sa, Husna ta kalle sa ta kalli hannun sa me zako-zakon farata daya miƙo mata saita maƙe masa kafaɗa a sakalce tana yin gefe ɗaya da ledar, yadda tayi abun kamar wata yar shekara biyu saiya koma jikin bishiyar ya jingina bayan sa tare da maida hannun sa.
Husna kuwa man kanta da lissafin ta bai faɗa mata komai ba tace "Yaya bani ka bawa ba?"
Kallon ta kawai yake amma babu amsa, itama kuma bata tsaya jiran amsar tasa da tasan ba zata samu ba ta buɗe biskit ɗin a gaban shi ta fara ci, shi kuwa saiya ci gaba da ƙare mata kallo har saida taci rabin biskit ɗin sannan yaga ta miƙo masa sauran tana masa murmushi tace "uhm! Yaya yana da daɗi ban taɓa cin irin saba, kaima kaci kaji."
Ga mamakin ta sai taga ya miƙa mata hannu, ta kalli hannun nashi da yayi wani baƙi baƙin da ya hana a gane asalin kalar fatar jikin shi, sai kuma ta ɗago ta kalle shi, Shortbread ɗin ya nuna mata da hannu tace "Za kaci?"
Shiru yayi mata yana duban ta, saita miƙa masa amma sai yaƙi karɓa saida tasa a ledar sannan ya karɓa ya fara ci tana kallon shi tana murmushi, duka ya cinye ya mai da mata sweetie ɗin da chaculate ɗin. Abin saiya yi mata daɗi, batayi tunanin komai ba ta ci gaba dayi masa hira zancen nata duk labarin Yayanta da Maman tane sai ƙanin ta da bata sani ba, har lokaci yaja ya miƙe tsaye ta tashi yauma tana gaba yana binta a baya saida yaga shigar ta gida sannan ya juya yabar wajen gaba-daya.
Kwanan Husna huɗu tana jinya ta warke gaba ɗaya ta fara fita kasuwa.
Yau jumma'a Garki za su tun safe Lirwanu ya tafi tare da faɗa mata inda zata same shi a kasuwar Husna duk ranta babu daɗi ta amsa masa.
Suna cikin motar Naira saiga Bahari ya zo wajen yana tsokanar ta.
"Lallai su Ma'u jiki ya warke har za'a koma filin daga?" Husna ta ɗan harare shi.
"Ɗan sa ido ne fa kai Bahari." Ta faɗa.
Yana tsaye a wajen Motar suna hira har motar ta cika suka tafi.
Ta samu Lirwanu a rumfar daya faɗa mata, harya sari buhun barkono biyu Husna ta aje farantin ta yana daura wa tana jerawa a farantin saida farantin ya cika ta ɗauka ta shiga cikin kasuwa.
Kafin kace meye wannan harta siyar ta sake zuwa ɗiban wani, haka ta rinƙa zuwa tana ɗauka yana ƙare wa har lokacin da suke siyan abincin rana suci yayi, ta faɗa wa Lirwanu ya bata kuɗin abinci sai ya dube ta fuska a haɗe yace "bakinci tuwo ba kan ki taho zaki wani ce na baki kuɗin abinci dan gulma."
Kawai saita tsaya tana kallon shi dan abun nasa wani lokacin kamar wanda baya tunani da ƙwaƙwalwa.
Naira ashirin ya ɗakko ya bata yana mita.
"Gashi nan saiki siya abincin."
Husna ta kalli kuɗin ta kalle shi, kawai saita dauki Barkonon tayi gaba tana share hawayen daya cika mata ido.
Yunwa take ji tun ɗazu dan lokacin da zuke zuwa cin abinci har ya wuce, ganin bai ce mata ga kuɗin abincin rana ba yasa ta tambaye shi ashe ma tambayar tata bata da amfani.
Haka ta wuni a kasuwar tana masa talla babu abinda taci, ta riga duka sauran abokan tafiyar ta gama saida barkonon ta.
Lokacin da ta dawo daga sahun ƙarshe Lirwanu ya nade buhhunan shi ya daure Husna na tsaye tana kallon shi saida ya gama haɗa ya nashi ya nashi sannan ya ciro ɗari biyu ya miƙa mata.
Gashi ki tafi gida ni sai anjima zan taho."
Husna tabi hannun shi da ɗari biyun da kallo.
"Bazaki karɓa bane na maida kuɗi na?" Ya faɗa a tsawace, ta karɓi kuɗin kuka na taho mata ta juya ta bar wajen tana share hawayen baƙin ciki.
"Dama nasan Baba Lirwanu bazai bani kuɗin talla ta ba." Ta fada a sarari tana goge fuskar ta.
Suna tafe a motar Naira ana shewa kamar yadda aka saba amma wannan karon banda Husna dan har suka iso gida ta tafasa bata ce ba, Indo ma gajiya tayi dayi mata magana ta kyale ta
.
Suna sauka a motar tayi gida a wahalce ta shigo gidan ga gajiya ga yunwa, Ramma ta rinƙa jera mata sannu cikin tausaya wa.
Sauran kwaɗon ranbon da Ramma tayi da rana ta bata taci tasha ruwa ta kwanta a tsakar ɗaki tana maida numfashi.
Ganin Husna rai a ɓace ga ta shigo da yunwa yasa Ramma bata tambaye ta komai ba dan dama tasan talla tsakanin Lirwanu da Ma'u baza a wanye lafiya ba.
Yauma a dandali Indo na tafiya zance ya zo wajen ya zauna Husna tayi ta masa hira kamar yadda ta saba.
Washegari Asabar suka tashi da baƙin Turawa a garin ƙofar mai gari ta ɗinke da mutane, dama tun da motar su ta shigo garin mutane suke kus kus ɗin baƙin waye.
Kowa da abinda zai faɗa akan baƙin wasu suce daga gidan governoty suke wasu suce a'a ba haka bane.
Husna na gida Indo tazo tana haki tace "Ma'u Ma'u zo muje kinsan me yake faruwa?"
"A'a wani abun ne?" Husna ta faɗa tana duban Indo.
"Ai yau baƙin Turawa ne a gari suna ƙofar mai gari zo muje ki gansu farare tas gashin su wani iri."
Indo tayi maganar tana jan hannun Husna da farko kin zuwa tayi dan bata son zuwa abubuwa irin wannan, a garin zai yi wahala ka ganta a wajen kallon abu Irin wannan, saida Ramma tasa baki sannan tabi Indo suka tafi kofar mai gari.
Ƙofar Mai gari ta cika jama'a suna jiran suji me yake tafe da baƙin Turawa saidai kaf garin an rasa wanda zai shiga tsakani suyi magana da Mai gari, dan su basa jin Hausa shi kuma Mai gari babu turanci, Sunday aka tafi kira yayi musu bayanin abinda turawan ke faɗa sai aka yi rashin sa'a baya nan ya tafi Kano siyan kaya, matar shi kuma babu Hausa, acikin manyan wajen wani yace a kira headmaster.
"Ai yau Asabar baya zuwa." Mutane suka faɗa, anata tunanin yadda za'ayi Bahari ya matsa kusa da Mai gari yace "ranka ya daɗe ko za'a kira Ma'u tunda ita tana jin turanci saita fassara mana abinda suke faɗa."
"A'a Ma'u dai Jikar Aramma Abdussalamu?" Mai gari ya faɗa da mamaki, Bahari ya ɗaga masa kai.
Indo da Husna na daga can gefe suna kallon mutane su basu san wainar da ake toyawa ba saida Aramma ya zo shiga wajen da ɗan aiken Mai Gari sannan ya gansu.
"To Aramma kaji dalilin da yasa muka aika kiran ka." Aramma yayi shiru yana tunani bayan ya gama jin bayanin Mai Gari, sai kuma ya numfasa yace "to ranka ya daɗe Allah yasa ita ta gane me suke faɗa ɗin tunda ance basa gane irin turancin da Samarin mu ke musu suma basa gane nasu."
"Aramma ai su nasu a Lagos suka koyo sa ba lallai su gane ba tunda broken ne."
Bahari ya faɗa yana tsaye kusa da Aramma.
"To shi turancin har kala kala ne ke nan, Allah mai iko, to Allah yasa ta gane ɗin, bari a kira ta na gansu nan baya kaɗan ita da Indo." Aramma ya faɗa zai miƙe Bahari ya juya yana faɗin.
"Bari na kirata."
Su Husna na tsaye Bahari ya zo yace taje inji Aramma yana cikin rumfar Mai Gari.
"Lafiya ko?" ta tambaye shi, saida Bahari yayi murmushi sannan yace "ƙarar ki nakaiwa Mai gari zo muje suna jiran ki."
Husna da Indo suka biyo bayan shi, ta ɗaya bangaren da babu cukowar mutane Bahari yabi dasu ata nan kuma Husna taga Mahaukacin yayan ta zaune a kan ice yana kallon su zata je wajen shi Bahari yace "Aramma na jiranki fa."
Saita fasa zuwa ta bishi suka shiga cikin rumfar shi kuma Bahari ya tsaya daga bayan su kaɗan ita kuma ta ƙarasa wajen Aramma.
Aramma yayi mata bayanin abinda zatayi, Husna ta ɗanyi shiru kamar baza tayi magana ba sai kuma ta ɗaga kai.
Mai gari jikin shi har rawa yake ya nuna mata Turawa guda biyu sunsha ƙananan kaya idanun su sanye da farin eyeglasses.
Cikin harshen Ingilishi a nutse ta fara gaishe su, suka amsa suna jin dadin an samu me musu magana.
Mutane suka zuba musu ido musamman Husna dake faɗin duk abinda suka faɗa da Hausa, tna faɗar abinda suka ce wani ɗan kanzagi daga bakin rumfar Mai Gari yana maimaita wa mutanen dake waje.
"Munzo ne daga Cikin Kano mu ƙungiyace mai zaman kanta NGOs wacce take bi garuruwan Nigeria daban daban tana duba inda suke da matsalar ruwan sha sai mu samar musu da famfunan zamani wanda za su rinƙa amfani da hasken rana ba tare da sun biyamu ko sisi ba, wannan aikin namu muna yinshi ne sadaƙatul jariya, idan mutanen wannan gari sun amince zamu fara yi musu aikin samar musu da ruwa a cikin wannan gari gobe."
Baturan nan suka jero wa Husna bayanan su daki daki, tun daga ganin yadda fuskar ta ke murmushi jikin mutanen wurin ya fara rawa baya Mai Gari daya matsu su gama bayanin ta faɗa musu me suka ce.
"Sunce su wata kungiyace daga Kano......"
Tirayan tiryan Husna tayi musu bayanin abida suka faɗa mai shela daga waje yana maimaita wa, Husna tana bayanin mutane suka kaure da iface ifacen murna da sowa, Bahari kuwa yana daga gefe yana Murmushi harda yiwa Husna jinjina, Dan Hajja kuma yana ta can waje cikin abokai yana fasa kai da sake maimata musu Ma'u tashi ce.
Saida Mai Gari ya tsawatar wa mutane sannan wajen yayi shiru Husna ta ƙarasa faɗa musu abinda suka faɗa.
Nan da nan Mai Gari da sauran manyan Garin suka ce sun amince tare da godiya.
Husna ta faɗa wa Turawan abinda Mai Gari da mutanen sa suka ce. Su kayi murmushin jin daɗi.
Bata ƙara ko minti ɗaya a wajen ba ta fice Bahari na binta a baya, Aramma kuwa farin ciki ya cika masa zuciya, mutanen gari sai murna ake ana mai da yadda aka yi da faɗin duk garin Ma'u ce tayi magana da Turawa.
Lokacin da suka fito daga rumfar Mai gari Husna ta duba inda tabar yayan ta zaune ɗazu sai taga baya wajen ya tashi.
Bahari ya ce "ai daga yau Ma'u na canja miki suna zuwa Baturiya, ashe haka kika iya Ingilishi?" Ya faɗa yana riƙe baki, Husna ta harare shi suka tafi gida dan turawan har sun fito sun tafi akan sai gobe kuma in sun zo fara aikin.
Mutane ma duk sun watse sai manyan gari a cikin rumfar Mai Gari suna sake maida zance.
Aramma na dawowa gida yasa aka kira masa Husna tana zuwa ya bata wani rubutu da garin magani a ƙwarya yace "Maza shanye Asma'ullahi maganin baki ne, yau kin ɗakko magana a garin nan ko ina ka gifta sunanki kaiwa ake kira."
_*WRITING.....✍🏻*_
*_MUTUWAR AURE.....!_*
_(Ƙaddarar wasu ƴaƴan)_
*_Kanawa ne👌🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_BOOK 1_
*_FREE PAGES_*
________________
*_WHATSAPP GROUP👇🏻_*
https://chat.whatsapp.com/LaVfMaCQz1C2WcC7zGfSL3?mode=gi_t
https://wa.me/+2348064789370
_________________
_EPISODE 23_
_Washegari_
Turawan nan suka dawo tare da ma'aikatan su, nan da nan suka fara aiki gadan gadan babu kama hannun Yaro.
Yayin da wannan abu daya faru a garin ya sake mai da Husna wata selebirity a garin, Dan Hajja kuma ya sake haukacewa akan ta ko ina ya zauna zancen ta yake yi kamar taɓaɓɓe.
Ta ɓangaren masu aikin ruwa kuwa cikin yan abinda baifi kwanaki ba aikin yayi nisa na ban mamaki dan aiki suke babu dare babu rana.
Ta ɓari ɗaya kuma Husna taci gaba da rayuwar ta kamar yadda ta saba.
Yau tana aje abincin siyarwar ta a tasha Headmaster yazo yace ta kawo masa, ƙuru-ƙuru tace masa "bana siyarwa bane."
Abun ya bashi mamaki dan yana gani ta rinƙa siyarwa wa mutane, Indo kuwa da tasan kwanan zance sai dariya take ganin headmaster ya tsaya yana kallon Husna cikin mamaki.
Chioma ce ta ce Husna ta kai mata farar doya, tana dawowa daga wajen ta taga headmaster yana korar Mahaukacin yayanta kamar zai dake sa harda zagi, abunda yayi masa ya matuƙar ƙonawa Husna rai har saida tace "Wai kai me yayi maka ne ka tsane shi? Naga dai baya shiga harkar kowa, amma duk kabi ka takura masa."
Headmaster ya tsaya yana kallon yadda Husna ta haɗe rai tana masa magana kamar wani sa'an ta.
"Ke baki da kunya ko? Ni kikewa magana haka?"
"Kai kuma baka fahimci me asalin kalmar humanity take nufi ba shi yasa kake korar mutum kamar dabba."
Husna ta faɗa da tsiwa, sai kuma ta juya inda ya koma ya raɓe yana kallon yadda take zuba masifa tace
"Yaya muje ka koma can ka zauna karka sake zuwa kusa da shi kaji? wannan bashi da tausayi."
Headmaster ya dube ta sai kuma ya kalli mutanen wajen da suke masa dariyar abinda Husna tayi masa, yace "is he her brother?"
Ganin kowa yayi masa banza sai ya dafe kai yace "Oh ashe fa baku gane me nace ba. Nace shi ɗin yayan tane da gaske?"
Garba ya zubawa ƙeyar Headmaster harara dan dama haushin sa suke ji tunda aka kawo shi garin ya fiya iyayi da kallon mutane a banza.
"A'a Baban tane." Garba ya faɗa yana barin wajen, aka bar Headmaster da budaddan baki.
Saida Husna taga yayi wajen Masallaci sannan ta koma kan abincin ta, tana Sallamar mutanen dake kanta ta siyo ruwa ta zuba abincin shi a leda ta tafi takai masa.
A bayan rumfar Bahari ta ganshi zaune yana kallon kamar sa da jini ke zuba.
Husna nayin ido biyu da kamar ta ƙaraso wajen da sauri ta aje kayan hannun ta a kasa a rude ta fara tambayar sa meya samu kafar shi.
"Yaya maika taka?" Ta sake tambayar sa Idanun ta harya tara hawaye, ta kai hannu zata taɓa kafar ya janye da sauri, jinin dake zuba ne ma yafi bawa Husna tsoro ganin ya hanata taɓa kafar saita miƙe da sauri ta tafi wajen Bahari.
"Bahari dan Allah zoka gani Yaya ne ya taka wani abu jini nata zuba a ƙafar sa." Hawayen daya cika mata ido ya ƙarasa zubowa.
Da sauri Bahari ya biyo bayan ta har zuwa inda yake zaune har yanzu a yadda ta barshi a haka yake.
"Subhanallahi meya taka haka? kai." Bahari ya faɗa yana duban kafar Husna tace "Dan Allah Bahari me za'a saka jinin ya daina zuba?"
Husna ta yi wa Bahari tambayar yadda kasan tana tambayar likita, Bahari yayi shiru yana tunanin sai kuma ya dube ta yace "Yawwa ki kira matar Sunday ta duba masa kafar mana ba kince likita bace?"
Da sauri ta ɗaga masa kai, yace "to jeki kirata saita duba masa wajen."
Husna ta amasa da "to."
Tana juyawa da sauri zata bar wajen sai kuma ta tsaya tace "Bahari dan Allah ka tsaya a wajen shi babu abinda zai yima yanzu zan kirata na dawo." Bahari yace "Naji jeki kina sake ɓata lokaci." Ta tafi harda gudun ta.
Duk wannan maganar da suke yi yana zaune yana jinsu amma ko motsawa daga inda yake baiyi ba har Husna ta dawo tare da Chioma, sai kuma fur yaƙi bari Chioma ta taɓa masa kafar saida Husna ta tsugunna a gaban shi tana kuka tace "Yaya nasan kana jina dan Allah Yaya ka bari ta dubama ciwon kaji?"
Ya ɗauke kanshi gefe yana jawo sandar sa zai tashi ta riƙe masa hannu abinda bai taɓa zato ko tsammani ba ke nan, Bahari ya ware ido yana kallon gefe da gefan su dan kar wani ya gani. Husna kuwa ko a jikin ta ita harga Allah da zuciya ɗaya take masa magana.
"Dan Allah fa nace Yaya?" ta faɗa tana sake sakin kuka kawai saiya koma ya zauna yana sunkuyar da kanshi ƙasa, Bahari daya mutu a tsaye da mamakin Husna sai ya jinjina kai, Chioma ta matso kusa da kafar ta fara dubawa.
Husna na tsaye tana kallo Chioma tasa wani ƙaramin almakashi ta fara ƙoƙarin yanke jikin baƙin abunda ya rufe masa ƙafa saida ta yanke gefan abun inda jinin yafi zuba sannan ta saka auduga ta fara rage jinin kanta fara wanke masa wajen, Husna ta rintse ido da sauri sanda taga Chioma ta zuba masa haidirojin akan ciwon.
A hankali Chioma take wanke masa wajen ciwon har sai da ciwon ya daina jini, a tare Husna da Bahari suka kalli inda ciwon yake yanka ne mai ɗan girma ata gefan tafin kafar shi yankan ya danyi zurfi, Husna tabi gefan kafar shi da kallo ta wajen da Chioma ta yanke baƙin abun duk da iya wajen ciwon ne babu baƙin abun da Husna ta kira sa da safa amma tana iya ganin wata farar fata sosai kwance a wajen da bakaken gashi a saman ta sai dai ba sosai kake iya gani ba saika saka wa wajen ciwon ido sosai.
"Gaskiya sai an ɗin ke wajen nan, sannan dole ayi masa Allurar Totonos dan kamar da ƙarfe ya yanke." Chioma ta faɗa ba tare kuma data jira cewar Husna da Bahari ba ta juya da sauri tana faɗin "ina zuwa."
"Sannu Yaya."
Husna ta faɗa tana zaman dirshan a kusa da shi ita ko tsoro ma bata ji.
Bahari ya kalli Husna ya girgiza kai a ƙasan zuciyar shi kuwa saiya saki Murmushi, Chioma bata jima ba sai gata ta dawo da sauri riƙe da wata yar jaka baƙa, a kusa dashi ta tsuguna ta fito da wata allura a cikin jakar yadda kasan wacce ta shirya wa samuwar ciwon ko zuwan wannan ranar haka take haɗa komai daki daki, saida ta gama haɗa ruwan Allurar Husna da Bahari na kallon ta.
"Please someone should help me to do this." Chioma ta faɗi maganar tana duban su, sai Husna ta kalli Bahari fuskar ta gwanin ban tausayi tace "Bahari dan Allah ka taimaka mata tayi masa Allurar." Ido ya zare yana kallon ta ita kuma saita karyar dakai gefe guda tana duban Bahari cikin roko tace "Please babu abinda zaima." Sai kuma ta juya wajen shi tace "Yaya Bahari zai taimaka wa Chioma tama allura kaji?" Bata jira amsawar shiba dan tasan ba amsar zaiyi ba.
Bahari da kana ganin shi kaga wanda yake a tsorace sai ya matso kusa dashi ya riƙe masa hannu Chioma ta daidaita inda zata
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 25 Chapter of 31