ya fara yi mata rubutu tana wanke idon dashi, da ciwon yaƙi daɗi wata rana Ramma ta same ta a ɗaki tace "Ma'u mai zai hana kije ki samu Garba tunda yana da number Yaya kice ya taimaka ya kira miki Babanki ki faɗa masa ya aiko miki da kuɗi aje asibiti ko ya siyo miki magani, kinga idon naki kullum gaba yake sake yi."
Husna ta amsawa Ramma da "to." Harta juya zata fita ta sake ce mata "Amma fa ki faɗa masa karya bari Lirwanu ya sani kindai san halin shi yanzu sai yace ana kaiwa Yaya munafunci."
Haka kuwa aka yi Husna ta samu Garba tayi masa bayani, take ya kira mata Baban ta suka yi magana yace "babu damuwa Husnah zan turo da kuɗin zuwa asibitin Ramma saita rakaki Doko?"
Husna ta amsa sukayi sallama da Babanta tayiwa Garba godiya ta tafi.
Cikin rashin sa'a Mai Kano bata hannun Garba ya turo da kuɗin ba, kuɗi na shiga hannun Lirwanu shike nan suka zama labari dan tunda ya zuba su a aljihun shi ya fita shike nan ruwa tasha, da Husna tayi masa maganar zuwa asibiti kuma zagi ne ya raba su.
Rashin gata da kulawar uwa tasa harta warke babu wanda ya kula da halin da take ciki, tun daga wannan ciwon ido kuma ta fuskanci ta samu tawayar ganin abin da ke nesa da ita, wanda har kawo yau babu wanda yasan halin da take ciki sai ita, yayin da mutane inta wuce su ko ta nuna bata gansu ba suke ɗaukar hakan a matsayin wulaƙanci.
Akan turmi ta zauna riƙe da baƙar leda Ramma ta dube ta tace "Sannu Ma'u ya kasuwar?"
"Alhamdulillah kasuwa." ta amsa sai kuma ta dubi sauran matan tace "sannun ku."
Mariya ta shaka saboda Husna tayi kamar bata ganta a wajen ba, har zata balbale ta da masifa sai kuma ta tuna abinda ya kawo ta tasan dole saita lallaɓa ta zata yarda.
Kamar gaske a hankali Mariya tace "Ma'u tunda ni ban isa ki gaishe ni ba wajen ki nazo." tayi maganar tana wani harare harare, a ɗage, Husna ta dube ta dan yanzu basa shiri da ƙanwar Baban nata tunda ta gane mugun san kanta ne da ita suka raba hanya, tace
"Gani ai."
"Dama shawara nazo muyi nace me zai hana kizo mu rinƙa yin abincin yamma ina miki kina kaiwa tasha kinga zamu samu alheri har kya samu kidan rinƙa tara sauran ciki (taron kwanuka da yammata ke yi na Aure) kuma ki samu na kashe wa."
Kaf matan wajen sai da suka saki baki da kunne suna jin wani mugun sankai irin na Mariya tafa san suna abincin yamma ita da Ramma amma tsabar mugun san kai da zalama zata kawo wannan maganar.
Husna tayi murmushin da Indo ke kira na rashin mutumci tace "shi kuma wanda muke yi sai a daina ko ƙaƙa za'ayi?"
"E mana ita Rammar ba kuna na rana ba sai ta barmin na yammar muna yin nima na samu." Mariya na dire maganar Husna tace "to bazan yiba, aini na dena yiwa kowa wahala, da de nayi yanzu kuwa an daɗe da rufe wannan shafin, su ƴaƴan ki basu da kan talla saini Husna? to bazan ɗauka ba, kuma babu wanda ya isa ya sani ɗauka."
Maganar ta kular da Dije tace "har ubanki Mai Kano bai isa ba ko? Tunda yanzu kin raina Lirwanu a banza kike ganin shi."
Husna ta dubi Dije tana jin wani baƙin cikin ta a rai tace "a'a shi wannan ya isa har yayi yawa amma fa wallahi inya sani na miki talla zan ɗauka sai dai duk abin da kika gani ke kika siya da kuɗin ki." Tana gama faɗin haka ta ɗauki faran tinta tayi ɗakin Ramma.
Dije tabi bayan ta da kallon takaici tace "Kema Mariya ai na faɗa miki wannan tsinanniyar yarinya ba yarda zatayi ba, kuma kina ji dai tace ko an sakata dole baza'a wanye ƙalau ba, wallahi kuma zata aikata kinsan halin Ma'u bata da mutumci in bata so abu ba, kai mu dai Safiya ta haifa mana jaraba, yarinya ƙarama amma ta ishi mutanen gari ta ishi na gida, Lirwanun ma da take shakkar shi yanzu a banza take ganin sa kana mata maganar shi zata ce inya dake ta wajen zai huce."
Mariya da baƙin ciki ya hanata magana saita warci zani ta goya ɗan ta tace "ni na tafi." Fuuuuu tayi gaba ta kusa bangazar Zahara saida ta matsa da sauri tace "kinga bani na kar zomon ba, zaki mangaje ni haka kawai baga uwarta nan zaune tana ji ba." Mariya tuni tayi waje, Dije tace "dama ai ita ke zuga ta tunda tafi kowa morar ta a gidan nan."
Tsaram Ramma ta tashi ta basu wajen, tana tafiya suka kafa gulmar ta.
Husna na kwance a ɗaki Ramma ta shigo tace "Ma'u me yasa kika ƙi yarda? Kinsan cewa za'ayi ni ke zuga ki, gashi can Zahara harta fara faɗi."
Miƙewa tayi zaune tana kallon ta tace "sun daɗe basu faɗa ba, ita kuma Zahara ai dama baƙar munafuka ce."
Ramma ta girgiza kai dan tasan halin ta tunda tace baza tayi ba tofa bazata yin ba, saida ta numfasa sannan tace
"Dama ɗazu aka aiko min an kawo doya zuwan Mariya ne yasa nace bazan siya ba tunda naji meya kawo ta." Ramma ta faɗa, Husna tace "kema dai kiyi ta bari suna miki iskanci, anjima zan je na karɓo mana, yawwa ga sakon naki na siyo." ta turawa Ramma ledar data shigo da ita.
Bayan sallar isha'i yan mata suka taru a Dandali ga farin wata fetal wajen yayi haske, Samari sai kiran ƴan mata suke hira, wasu kuma sun kafa gaɗa anata waƙe, Husna da Indo suna zaune suna cin amaro (gyaɗa mai gishiri) yaro ya zo in da suke yace "Ma'u wai kije inji Dan Hajja yana can ƙofar mai Gari." Kallon inda yaron yake Husna bata yi ba sai Indo ce tace "kai yi tafiyar ka ba zata jeba."
Yaro ya juya yaje ya faɗa wa ɗan Hajja, sai gashi ya sake dawowa wajen kan yayi magana Husna tace "wallahi in ka sake zuwa nan saina maka dukan tsiya." Sanin halin ta yasa yaron ya koma yace wa ɗan Hajja tace "inna koma saita dake ni."
Naira goma ɗan Hajja ya bashi ya tafi shi kuma ya koma wajen abokan su yana ƙwafa.
"Wallahi duk randa kika shigo hannu na Ma'u saina yi miki fata fata, banda ina sonki ai wallahi da yanzu nayi maganin ki." Ɗan Hajja ke tafe yana zancen a ranshi.
Can kuwa Indo ta kalli Husna bayan ta kora yaron tace "Ma'u me yasa bazaki kula ɗan Hajja ba? Kowa yasan fa yadda yake mugun sanki a garin nan yanzu harna Ma'u ake kiran shi."
Wata muguwar harara ta zuba wa Indo sannan tace "me zanyi dashi ɗan iska kawai."
Indo ta gyara zama saida ta kama baki sannan tace
"Hmmmm ai baki sani ba in faɗa miki ranar nan ina ɗaki naji su Ladi suna faɗin halin ɗan Hajja wai cikin da aka yiwa Bari harda shi acikin mazan da suka mata, amma uwarsa ta shiga ta fita ta turowa mai gari kuɗi aka rufe bakin iyayen ta."
Husna ta dubi Indo tana taɓe baki tace "ai ita ma Barin shegiya ce san mazan jaraba gare ta ga kwaɗayi."
"Nima haka nace duk lefin tane muda bama kula su wa zai mana, yawwa wai dan Allah Bahari saurayin kine? Naji ranar ana gulmar a makaranta da muka je wanki randa baki jeba."
Husna tace "ƴan iska su Ummai ne ko?"
"Taɓ ke ai ba'a faɗa miki magana yanzu sai ki tare mutum ku fara faɗa." Indo ta faɗa, Husna ta harare ta "banza matsoraciya, ai nasan sune, Ummai ce ke sanshi shi kuma baya kula ta, amma ni ba saurayi na bane kinsan bani da saurayi."
Indo tace "Taɓ ke ɗin? Badai kya kula su."
.....Washegari da rana Iro ya kai wa Husna fantekar doyar ta tasha, Bahari na ganin ya aje kayan ya tashi yaje kan kayan ya tsaya Samari suka fara tsokanar shi da "mai gadin Ma'u."
Yana dariya yace "na saba gwanda na jire mata kar kuyi mata gyaran fuska kanta iso."
Kullum haka yake mata ana ajiye kayan abincin ta zaije kai ya tsaya duk da yasan babu wanda zai taɓa mata amma saiya tsaya a kai ya fake da gadi yake mata, tana zuwa kuma ya hau tsokanar ta daga karshe dai shi ake fara zubawa kan a siyarwa kowa.
Iro bai jima da tafiya ba sai ga Husna ta iso hannun ta riƙe da botikin miya.
"Dan Allah zoki fara zuba min wallahi yunwa nake ji kwana biyun nan da bakya yin abinci garin Kwaki nake sha." Bahari ya faɗa yana karɓar bokitin miyar, tasan da gaske yake tunda tasha ji abakin ƴan matan dake saida abinci a tashar suna faɗin in batayi abin siyarwa ba baya siyan na kowa, sai da ta harare shi sannan tace
"Ai yau bazan siyar maka ba." Ya zare ido yace "yasin da wasa kike."
Bahari bai bar wajen ba saida ta zuba masa sannan ya tafi yana faɗin "yawwa na karɓi nawa yanzu kowa ma zai iya zuwa ya sai nasa."
Bata jima da zuwa ba Indo ta iso da nata kayan siyarwar.
Sunday ne ya leƙo daga shagon shi yace takai masa farar doya, ta tafi kai wa taga mahaukacin jiya a zaune ta gefan shagon shi yana karta Sandar hannun shi a ƙasa kamar wani ƙaramin yaro, tausayin shi taji ya kamata tana dawowa daga wajen Sunday ta zuba doya mai yawa taje wajen shi ta basa amma sai yaƙi karɓa, taɗan tsaya tana kallon shi sai kuma ta sake cewa
"Ka karɓa nina baka kyauta."
Nan ma yaƙi ɗagowa ya karɓa, Sunday ne ya fito wanke kwanon shi ya ganta a tsaye tana roƙon shi ya amsa.
"Achalugo ai besan me kike faɗa ba bashi da hankali, sai da nakore shi ashe nan yazo ya zauna."
Husna ta harari Sunday da yayi maganar tace
"Waya cema bashi da hankali? Rashin lafiya yake yi kuma zai warke." Dariya maganar ta ta bawa Sunday saida ya dara sannan ya koma cikin shagon shi.
Husna ta gaji da roƙon mahaukacin ya karɓi abincin data kai masa amma yaƙi amsa, kai ko nuna yasan tazo inda yake ma bai yi ba, haka zuwan ta baisa ya daina tonon kasar da yake yiba, dole ta koma wajen saida abincin ta Indo tace "kema Ma'u an faɗa miki baya karɓar abinci, amma naga yana zuwa wajen Safe mai fura ya bata kuɗin da ake bashi sadaka ta bashi fura, itama data dama mishi a ƙwarya kin karɓa yayi saida tasa masa a leda."
Husna bata cewa Indo komai ba ta tashi ta karɓo leda a wajen Sunday ta zuba farar doya kamar tasa masa miya sai kuma ta fasa ta kai masa.
"Gashi na baka."
Ta sake faɗa a karo na biyu tana miƙa masa ledar hannun ta, ga mamakin ta sai taga yasa hannu ya warce ledar kamar yadda ya karɓi ruwan jiya. tadan tsaya tana kallon shi, sai kuma tayi murmushi.
Ledar ya buɗe ya ɗan yi jim yana kallon doyar kamar mai hankali sai kuma ya fara ci daga cikin ledar.
Husna ta karɓo masa pure-water guda biyu a wajen Sunday ta kawo masa ya karɓa, kaɗan yaci doyar yayi jifa da sauran sai kuma ya shanye ruwan duka sannan ya tashi yabar wajen. Husna ta binshi da kallo tanajin tausayin sa na sake huta mata zuciya.
Bata jima a tashar ba ta saida abincin ta Bahari ya ɗakko mata kayan ta saida ya rakata har ƙofar gida sannan ya koma tasha.
Washegari ma haka ce ta faru, Husna ta bawa mahaukacin nan abinci, da tayi Kunun yamma ma ta zuba masa a leda kuma ya karɓa sai taga shi bai rage ba duka ya shanye har saida tace "na ƙaro maka?" Yayi mata banza, ganin ba zai amsa ba yasa tabar wajen tana waiwayen shi.
Tun daga lokacin kuma take bawa mahaukacin abinci, tunda ta gane baya karɓa a roba sai take siyan leda a wajen Sunday ta zuba masa, haka ruwa kullum saita siya masa.
Sauda dama Indo in taga tana wa mahaukacin magana takan ce mata "kema Ma'u ina kika taɓa ganin mahaukaci yasan daidai daba daidai ba? saiki rinƙa tambayar shi ya koshi ko me yake so? Sai kace wani mai hankali."
Duk sanda Indo tace l haka sai dai Husna tayi murmushi tace "Indo ba mahaukaci bane wannan sai dai mara lafiya, tunda kinga shi baya duka kuma baya ɗaukan kayan kowa."
Sannu a hankali ya fara gane ta, yana ganin ta zo tashar zai zo kusa da inta take ya tsaya, har mutane suka fara gane dan ita yake zuwa wajen tunda ita kaɗai ce me bashi abinci, sannan inba zuwan tayi ba baya zuwa wajen, haka baya shiga cikin mutane kuma baya shiga cikin gari, kullum zaka ganshi zaune shi kaɗai ko a kusa da masallaci gefan wajen da su Aramma ke zama ko ka ganshi tsakanin shagon Dan Hajja da rumfar Bahari, in kaga ya zo wajen shagon Sunday to ruwa yake son sha, wannan yasa ko Husna bata ganshi ba sai wani yace mata "Ma'u ga mutumin ki can."
Sam baya zuwa inda mutane suke kullum yana gefe guda yana tona rami da Sandar shi, ganin bashi da faɗa yasa mutane babu ruwan su dashi haka Aramma da kanshi ya hana yara tsokanar sa.
Yauma zuwan Husna tashar ke nan ta hango shi can kusa da majalisar Dan Hajja tsaye a jikin bishiya yana kallon titi.
Bahari na karɓar abincin shi ta biyo shi da ledar data zuba masa nashi abincin suka jera suna tafe yana mata hirar gobe zashi gida yaga matar shi tace "In kaje kace ina gaishe ta kuma kace nace Mijin ta Bahari ƴan mata gare shi da yawa a garin nan."
Buhari ya sheƙe da dariya yace "kut amma dai bani ne zankai wannan sakon bako? Ai na faɗa miki ko sakon gaisuwar ki ban taɓa faɗa mata ba, ke kinsan kishin Matata kuwa?"
Husna tace "Allah dai ya haɗa ni da ita wata ran saina faɗa mata duk kula kulan matan da kake yi."
Kan ya sake magana tayi gaba, Bahari ya zauna a kan bencin shi ya fara cin abincin sa.
Yana tsaye yana kallon titi kamar me lissafa adadin motocin da ke wucewa, ya dogare kafar shi da Sandar da baya rabo da ita Husna ta ƙaraso wajen tayi masa sallama kamar yadda ta saba yiwa kowa.
"Ga abincin ka."
Ta faɗa tana miƙa masa ledar hannun ta, bai waiwayo ba saida ta sake maimata wa sannan ya juyo, maimakon ya karɓi ledar abincin sai taga yaɗan tsaya yana kallon fuskar ta, ita ma kallon shi take saidai ita bata iya ganin asalin fuskar shi saboda tarin gashin daya cika fuskar, haka bata iya ganin asalin ƙwayar Idanun sa dan girar shi data cika da suma, gashin Idanun sa masu tsayi suka sake taimakawa wajen ɓoye Idanun sa.
"Ka karɓa mana."
Ta sake faɗa tana miƙa masa ledar.
Kanshi ya ɗauke ya maida kan titi yaƙi karɓar abincin abun ya bawa Husna mamaki dan tunda ta fara bashi abinci bai taɓa kin karɓa ba, sai dai yaci kaɗan yayi jifa da sauran.
"Yau bazakaci ba?" Tayi masa tambayar da sanyin murya kamar wacce take magana dame hankali.
Daga bayan ta taji ance "A'a yau mutumin naki baya son abincin ne?"
Husna ta juya su kayi ido biyu da Dan Hajja, tunda ta tsaya a wajen ɗan hajja ke kallon su daga kofar shagon sa ganin ta daɗe a wajen mahaukacin yasa shi tasowa yazo inda suke.
Kallo ɗaya Husna tayi masa ta watsar, sai kuma ta juya da ledar abincin tana jin zuciyar ta babu daɗi, Ɗan Hajja yabi bayan ta da kallo yana girgiza kai a fili yace "wallahi Ma'u saina Aure ki duk masifar ki saina shafe mazaunan nan."
Ran Husna a ɓace ta aje ledar Indo ta ta kalle ta tace "a'a yau be karɓa bane?"
A takaice tace "e."
Sai kuma ta tafi wajen Sunday ta karɓi pure-water guda biyu takai masa, yanzu ya karɓa, ta saki Murmushi lokacin da ya warci ruwan a hannun ta ya fara sha, ta zuba masa ido sai yaɗan tsaya dashan ruwan kamar wanda aka tsayar sai kuma yaci gaba da sha, Husna nata kallon shi saida taga ya shanye duka sannan ta juya ta tafi.
A hankali sabo ya fara shiga tsakani Husna da mahaukacin da babu wanda ya taɓa jin ko tarin sa, ita kanta bata taba ganin ko haƙorin saba bare taji maganar sa.
.......Yau ranta a mugun ɓace ta fito tashar saboda kuɗin ta da take tarawa a wajen Ramma ɗazu da safe tace ta bata sai ce mata tayi, tayi hakuri Lirwanu ya karɓe su jiya, taso ta hanashi ya fara zuga mata zagi dole ta ɗauka ta bashi.
Kuɗin da take tarawa dan ta siyi hijabin yayin da za'ayi wannan shekarar shi ne ya karɓe, dama ya saba yi mata haka duk lokacin da ta tara kuɗi saiya bi baya ya karɓe.
Saboda baƙin ciki Husna har kukan kuɗin saida tayi dan tasan ruwa tasha ke nan sai dai kuma ta nemi wani, wannan yasa ta fito tashar yau a tunzure, Bahari yazo harkan ta yana mata magana taƙi kula shi dole haka ya koma wajen saida fetir ɗin shi ya rabu da ita, dama ya san halin ta duk randa aka kunno ta daga gida bata kula kowa.
Duk halin baƙin cikin da take ciki bata manta da shiba tana hango sa ta zuba abinci takai masa ya karɓa yau bata tsaya taga ya fara ci ba ta baro wajen ruwan ma sam ta manta bata kai masa ba.
Tana zama Indo ta fara bata labarin Gaje ta bada kuɗin Hijabin su ita da sa'a ɗan koli in yaje Kano zai taho musu dashi.
"Ma'u ki bada naki kuɗin ya siyo miki kinga in Sallah ta matso kuɗi zasu ƙara."
Wannan magana ta Indo ta sake tunzura zuciyar Husna, ita shi ke nan bata isa tayi abun kanta irin na sauran yara ba, komai ta ajiye sai Baba Lirwanu yabi ya karɓe, inta faɗawa Baban ta ya siya mata kuma har yayin abun ya wuce ba zai aiko mata dashi ba, sai dai in yazo garin yace tayi haƙuri mantawa yayi, wannan yasa gaba ɗaya ma yanzu ta dai na tambayar shi abu, gaba ɗaya Baban ta ya canja ya zama kamar wanda aka kaɗewa hankali a kanta kwata kwata baya ta tata sai in ya zo garin, yana tafiya kuma shi ke nan, gashi yanzu baya yawan zuwa sai ya dau dogon lokaci bai shigo ba.
Ita ce kullum gantalin talla amma bata da kayan sawar arziki, bata da kayan ado irin na sauran ƴan mata, tsakanin ta da Babanta kuwa dinki sai na Sallah shima kala ɗaya ne zai mata da hijabi ɗaya shike nan sai wata sallar kuma.
Harta gama saida abincin ranta a cunkushe yake ta ɗauki fantekar ta da kanta dan Bahari bai sake zuwa inda take ba tun da yasan yau kozai kwana yana mata magana baza ta kula shi ba.
Ta bayan masallaci tabi maimakon ta shige gida saita zauna a kan wani ɗan ice da aka aje a wajen saboda masu alwala, wajen ya daɗe da zame mata wajen faɗin duk halin da take ciki na damuwa duk lokacin da aka yi mata wani abu mara dadi nan take zuwa ta zauna tayi kukan ta ta more babu wanda ya sani, tayi suturun ta kamar wacce ta samu matsalar taɓin hankali, duk sanda tayi haka kuma sai taji zuciyar ta tayi sanyi.
Yauma kamar yadda ta saba kwanunkan ta tasa a gaba ta kife kai akan cinyarta ta fara kuka, kuka take sosai duk lokacin da Indo ta bata labarin Gaje ta siya musu abu, ko tsautsayi yasa ta taɓa kayan Zahara tayi mata gorin uwa da rashin gata babu wanda ke faɗo mata a rai sai Mamanta da yayan ta, tasan da suna nan a tare babu abinda zai kawo ta nan garin, a hankali muryarta na rawa saboda kuka tace "Nasan yanzu kin manta dani ko Mama? kin daina sona, Yaya kaima ka dena sona ko?"
Tayi maganar kamar tana kallon su, sai kuma ta yi murmushi tana share hawayen fuskarta tace "nima yanzu bana son ganin ku amma Inason ganin ƙanina da kika haifa Baba yace min yana wajen ki, Mama dan Allah karki bawa Baba shi, Nana zata dake shi Baba kuma zai kawo shi ƙyauye kamar ni, kinga nima tunda ya kawo ni bai zo ya mai da niba, kuma yasan kowa baya sona a nan sai Aramma da Ramma, Yaya kullum sai nayi talla na ɗebo ruwa, kaga yauma Baba Lirwanu ya karɓe min kuɗina da nake tarawa, yanzu shike nan bazan siyi hijabin yayi ba, nasan inna tara wani ma kwacewa zai yi....."
Sai kuma kuka yaci ƙarfin ta ta kasa ƙarasa maganar.
Motsin da taji a bayan ta yasa ta ɗago a ɗan firgice ta juya dan tasan wajen ba hanyar wucewar mutane bace, kuma ba lokacin sallah bane bare tace wani ne ya zo yin alwala.
Tana ɗago kai ta ganshi tsaye a kanta yana riƙe da Sandar shi.....!
da mamaki Husna ta mike tana kallon shi sai kuma ta tuna kuka fa take, da sauri tasa hannu ta share hawayen fuskar ta tace "me kazo yi nan?"
Kamar yadda ta kwana da sanin ba magana zai mata ba haka shima baice mata komai ba, sai ƙare mata kallo da yake ta ƙasan ido.
Ko kaɗan Husna bataji tsoron ganin shiba haka bata kawo wa ranta komai ba ta ɗakko Naira Ishirin ta miƙa masa tace "gashi kaje wajen Sunday ya baka ruwa ɗazu mantawa nayi ban kawo maka ba."
Bai Karɓi kuɗin ba haka bai bar wajen ba kamar yadda bai dena kallon taba.
"Yunwa kake ji?" Nan ma yayi mata shiru sai kallon ta da yake yi..
"To matsa naje na siyo ma ruwan da kaina."
Ta faɗa tana barin kayan kwanunkan ta a wajen kamar wanda ya gane me take nufi saiya matsa gefe ya bata hanya ta wuce yabi bayanta da kallo sai kuma ya ɗauke kansa zuwa gefe guda, Allah ya taimake ta harta siyo masa ruwan ta dawo Aramma bai ganta ba dan ya hanasu bita wajen.
Saɓanin yadda ta barshi yanzu zaune ta same shi a inda ta tashi yasa kwanukan ta a gaba yana caccaka rami da Sandar hannun shi, harta iso wajen bai ɗago ba saida ta miƙa masa ruwan tana cewa "gashi to."
Sannan ya ɗago ya amsa yana kallon gefe.
Ga mamakin Husna sai taga yau bai warci ruwan kamar yadda ya saba ba a nutse ya karɓa kamar wani me kan gado.
bata kuma duban inda yake ba ta dibi kwanukanta tabi ta gaban shi ta shige cikin gida, shi kuwa ya raka bayan ta da kallo.
Tunda Ramma ta hango ta tana shigowa ta kewaye tasan yau ƴar riƙon nata sai a hankali, ita kanta ba'a san ranta take bawa Lirwanu kuɗin taba, to amma babu yadda ta iya, randa ta taɓa hanashi kuɗin shida Dije ba ƙaramin zagin cin mutunci suka yi mata ba, dan Lirwanu bai ɗauki zagin mace a bakin komai
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 31