ta sashi faɗin "Ogan sama ba."
Saida ya kira sunan kuma saiya riƙe baki yana sake kallon mutumin.
Ogan sama ya yiwa ɗan Hajja wani mugun kallo da nufin zagaye Mahaukacin ya wuce, har yanzu yana a yadda yake ogan sama ya ɗaga ƙafa zai juya cikin wata dakakkiyar murya yaji mahaukacin yace
"You are too late ka riga ka shigo hannu Tasi Maro ko na kiraka da KACA da alama za kafi gane wannan sunan."
Yana kai karshen maganar kuma cikin wani irin zafin nama ya miƙe tsaye yana wa ogan sama wani irin murmushin ka gama yawo sannan cikin jin isa ya sake ce masa "barkan mu da sake haɗu wa a karo na biyu kuma na ƙarshe."
Ya miƙa hannu da nufin riƙe shi ogan sama yayi wani tsalle yayi baya sai kuma ya kwashe da dariya yana tare da faɗin "ƙarya kake Ƙwaya, kai baka isa ka kama niba na wuce tunanin ka, ku kuma kowa yayi ta kanshi." Ya faɗa wa sauran yaransa a tsawace.
Kan suyi wani motsi sukaji ana dirowa daga saman bishiyar da suke tsaye, Sunday ne ya fara dirowa ya tsaya akan kafafunsa cikin Kananan kaya, headmaster ma ya diro, suka saka su Ogan sama a tsakiya ai gaba ɗaya sai suka rude kowa ya fara neman hanyar gudu, Ogan sama kuwa saiya ɗaga ƙafa zai bugata a ƙasa da nufin ya ɓace kamar yadda yake yi aduk sanda ya shiga hannu amma kanya sauke ta ƙasa MM yayi wata muguwar sufa ya daki ɗaya kafar shi yayi sama ya zube a ƙasa, sauran yaran da zasu watse danbe ya kware tsakanin su dasu Sunday.
Mutum biyu suka taka da gudun neman tsira zuwa wajen motar su dake wajen Bahari, ɗaya ya kama jikin motar zai haye yaji an doko shi ƙasa ya faɗo tim saida ya kurma uban ihun azaba dan hannun shi ya bugi ƙasa, sannan Buhari daya doko shi ƙasan da sauri ya naushi wata jijiya a gefan wuyansa take ya suma, wanda ya biyo shi ya juya zai gudu Bahari ya jefe shi a keya da wani mulmulallan ƙwallo take ya faɗi a wajen dafe da ƙeya yana son tashi amma ya kasa saida Bahari yasa musu handcup sannan ya taɓa wani abu kamar Bluetooth a kunne sa da sauri ya fara fadin.
"Operation MF5/1O-08 we are on duty, 1/07MM09 sun shigo hannu, na maimaita Operation MF5/1O-08 on duty masu laifi sun shigo hannu"
Saida ya maimaita yakai sau uku sannan ya kalli wajen ɗan Hajja inda su Sunday suke tuni suka sumar da mutum biyu suka saka musu handcup, MM kuma dambe suke zubawa shida ogan sama.
Bahari ne ya hango Mutum ɗaya daga cikin su yayi cikin tasha da gudu a tsiyace ya rufa masa baya nan fa hankalin mutane ya fara kawowa kansu cikin abinda bai cika minti ɗaya ba Bahari ya kurewa ɗayan gudu ya kama sa, tuni ya sumar dashi mutane suka zagaye sa cikin ɗinbin mamaki dan basu san meya haɗa suba saida sukaga ya zaro wata siririyar igiya ya ɗaure masa hannu sannan mutane suka fara ƙoƙarin tambayar sa meya faru.
Acan rumfar ɗan hajja kuwa Ogan sama ya ƙwaci kansa da ƙyar ya kwasa da gudu yayi cikin tasha headmaster da Sunday suka rufa masa baya, shi kuwa MM bai bisu a baya ba sai tsaiwar sa daya gyara yana kallon yadda Ogan sama yayi cikin tasha ta gudu saida ya gama ƙare masa kallo sannan cikin iyawa ya rarumin Sandar shi cikin zafin nama yayi wani irin jifa da ita cikin iya seti Sandar ta buɗe ta zama igiya take ta harɗe ƙafafun Ogan sama "tim." ya faɗi ƙasa a tsakiyar tashar ɗan nesa da Bahari kaɗan, sai kuma ya fara yunƙurin tashi danya gudu kafin mutane dasu Bahari su farga kaiwa sai ji kake.
"Tas....tas...tasss..." Karar bunduga ta sauka a kunne jama'ar tashar har wanda bai san me ke faruwa ba saida ya taso a tsoroce, ihun azaba Ogan sama ya kurma dan harbi ukun da MM yayi masa duka ya same sa a ƙafa ɗaya, su Sunday na ganin haka suka tsaya, cikin ƙarfin hali Ogan sama ya ɗaga ɗayar kafar zai gudu ji kake "Tauuuuu....."
Ya sake harbin shi a ɗaya kafar, nan fa mutane suka rude tare da juye juyen neman ta inda harbin ya fito.
Mamaki da tsoro ya daskarar da mutane sanda suka yi Ido da wanda suka sani a matsayin mahaukaci yana tahowa hannun sa riƙe da bunduga ƴar ƙarama, cikin ainahin tafiyar sa ta kakkarfan Namiji maji karfin dantse da jarumta saf...saf....saf haka yake takowa da sarssarfa a ainahin MM ɗin sa, tun kan ya iso wajen Sunday ya aje masa benci a gaban Ogan sama dake kwance a tsakiyar tasha warwas yana ihun neman ceto, mutane kuwa tsoro da tu'ajjibi yasa kowa ya kame daga inda yake yana kallon ikon Allah.
"Sagir....."
MM Ya kira sunan da wata irin murya mai zurfi da faɗi.
"Yes Sir." Headmaster ya faɗa yana kame wa a gaban sa.
"Kaida Fasal ku ƙaraso da sauran mutanen nan." Yayi masa maganar cikin bada umarni, yana rufe bakin sa ya juya da sauri.
"Chike." Ya kira sunan, da sauri Sunday ya matso gaban shi ya zuge zif din gaban jallabiyar jikin sa take ta zame ta faɗi ƙasa, saiga wasu riga da wando bakake a jikin shi, baƙin abun daya saka a hannunsa ya zare take fararen sangalalin hannunsa suka bayyana da wasu irin murɗadɗun damatsa dakai ba sai an faɗa maka maisu ya tara ƙarfi ba.
Chioma dake tsaye a wajen tun ɗazu ta jefowa Sunday wata bakar jaka ya cafe, a ƙasa ya aje ta ya bude cikin ta saiga wasu takalma boot baƙake, ya tsugunna a gaban MM dake zaune akan bencin yana kallon ogan sama da wanda Bahari ya sumar, saida ya zare baƙin abun kafar sa sannan ya fara saka masa takalmin, asalin halittar kafarsa ta farar fata da kwantattun bakaken gashi suka bayyana, shi kuma sai yasa hannu ya ɗaye gemun daya cika masa fuska, gashin kansa ma ya cire hular asalin kammanin sa suka bayyana Blackrehy eyeglasses mai kyau Sunday ya miƙa masa yasa take mutane suka ƙara shiga mamaki.
Fuskar sa babu gashi ko kaɗan bashi da gemu haka bashi da gashin baki, girarsa a cike dake baƙa ƙirin, kasan kuwa kitsone guda huɗu all back jelar kitson an tufketa waje ɗaya.
Sunday yana gama daura masa takalmin daidai lokacin Bahari da headmaster suka gama kawo sauran mutum biyar ɗin nan, ya dube su ɗaya bayan ɗaya, yace "Kun ɗakko wancan Yaron a kofar shagon shi." Suka juya a tare suka tafi dakko ɗan hajja daya dade da suma.
"Victoria." Chioma ta bayyana a gaban sa, kallon ta kawai yayi ba tare da yayi magana ba tace "yes Sir."
Ta juya kan ogan sama daya fara galabaita ta fara ƙoƙarin cire masa bulet ɗin kafafun sa.
"Chike ina son ganin Garba da.....mene sunan ta?" Yayi maganar da na kusa da shi ne kawai zaiji dan ko haƙorin sa baya fitowa waje bare na nesa yayi tunanin magana yake, Bahari da isowar su wajen ke nan kuma yaji me MM yace sai yace "Ramma."
"Yes Inason ganin su yanzu, Faisal....!" Ya kira sunan da Babbar murya.
"Yes."
Minti biyar ne damu ta taho tare da....?" Ya ɗanyi shiru yana tauna sunan da zai faɗa.
"I understand." Bahari ya faɗa yana wani shegen murmushi sai kuma ya juya inda ya hango Aramma a tsaye, yana zuwa yace "Dan Allah Aramma muna son ganin Baba Ramma da Ma'u please bamu da lokaci." Bahari ya faɗa cikin girmamawa da roƙo.
Aramma ya rasa mema zaice masa, dan wallahi shi kansa ganin komai yake makar a mafarki.
"Please Aramma." Bahari ya sake faɗa da asalin muryar sa sai kuma ya juya yana duba inda Garba yake ba tare daya tsaya yaji amsar Aramma ba, can nesa ya hango sa, Garba yana ganin Bahari ya doso shi yuuuuuu mutane suka bisa da kallo Garba kuwa jikin sa saiya ɗuru ruwa ya fara fadin.
"Wallahi banyi lefin komai ba." Ya faɗa a mugun tsorace.
"Karka damu Boss ke son ganin ka, am sure babu abin da zai yi kama."
Bahari ya faɗa yana kamo hannun sa suka taho wajen tare.
Cikin abinda baifi minti biyu ba Chioma ta cire bulet ɗin jikin Ogan sama yana ihu yana komai babu kashe zafin ciwo babu tausaya ta cire su ta zuba wani ruwa a wajen take kafar ta fara rawar azaba jijin ya tsaya cak.
Ta cikin baƙin gilashin idon sa yake kallon komai harta gama.
"Wu...wu..wu...wu....."
Ƙarar jiragen sama masu saukar ungulu ta cika garin, dama gashi zancen mahaukaci ya kama Ɗan Hajja da wasu mutane a tasha tuni ya fara shiga cikin gari, ƙarar saukar jirage akan titin tsakiyar tasha kuma saiya sake jawo hankalin jama'ar garin, nan da nan tashar ta cika da mutane suka zagaye su kowa da abin da yake faɗa.
Helicopter na farko daya fara sauka a tsakiyar titin matasa biyu ne suka diro daga ciki, sanye da bakaken kaya ga bundugu a jikin su bayan su an rubuta SS, ɗaya jirgin kuma ɓaro ɓaro a jikin sa ga rubutun NDLEA nan da manyan harfa.
Su Bahari dake amsa sunan Faisal tuni suka zura takalma da jacket baƙake tuni ya yage gemu da sajen daya rufe masa fuska wasu kuma ja an subuta NDLEA a jikin ta.
Ogan sama daya dade da suman azaba aka fara sawa a Jirgi wasu suka shiga saida aka gama kwashe su duka sannan ya juyo ya kalli Garba dake tsaye jikin sa na rawa, dai-dai lokacin kuma Ramma ta iso wajen Aramma na binta a baya, Bahari yana hango ta ya tafi inda take mutane suka matsa ta shigo wajem yuuuuuuuu akan bisu da kallo.
Ƙasa ƙasa ya yiwa Bahari magana wanda shi kaɗai yaji me yace, Bahari ya daga masa kai ya dubi Garba yace "wajen da nake saida fetir yace an bar maka shi harda jarin gaba ɗaya." Garba ya ƙwalalo ido waje cikin ƙarfin hali yace "Uhm me kace Bahari?"
Bahari ya sake cewa "Eh ya ce an baka kyauta saboda ka taimaki Ma'u."
Bahari yana gama faɗin haka ya matsa ya bawa MM hanya ya matso gaban Ramma saida ya cire p-cap ɗin kansa alamar girmamawa sannan cikin maganar sa ta cikakkun Maza ya fara magana.
"Mama mun gode sosai da kula da ita da kikayi." Sai kuma ya juya wajen Aramma yace "Allah ya ƙara girma Aramma bamu da time amma zamu sake haɗuwa soon, Shagon Sunday Mama an baki kyauta duka kayan dake ciki naki ne saboda Alkhairin da kikayi mata."
Ya ɗanyi shiru yana rufe idanunsa ta ciki gilashin sai kuma ya buɗe, Bahari ya matso da wani envelope fari ya karɓa ya kama hannun Aramma yasa masa yace "Nagode sosai babu abinda zanma naji daɗi amma wannan ka samu wani ya rakaka dutse akwai komai aciki inama addu'ar yin Umrah me albarka, sai mun sake haɗuwa."
Ya karasa maganar da nufin juyawa Aramma ya riƙo hannun sa yana faɗin. "Asma'ullahi ta bar garin nan ɗazu Yayar Maman ta tazo ta tafi da ita, amma ta barmin sako tace na faɗawa yayanta ta tafi sai wata rana"
Aramma ya faɗa masa maganar yana ƙare masa kallo, saukar maganar a kunnan sa tasa yaji wani abu a ransa mara daɗi, dan yaso ya ganta yanzu amma sai ya dake cikin jarumta ya ɗagawa Aramma kai ya juya yaci gaba da tafiya ba tare daya sake juyo ba.
Bahari ya bawa Ramma mukullan shagon Sunday ya juya da gudu ya haye Jirgin su, MM ne ƙarshen shiga nasu jirgin yana zama jirgin ya fara tashi mutane suka raka su da ido, dai-dai lokacin kuma Hajja da mugun labarin kama ɗan ta yaje mata ta iso tashar hankali tashe, saidai ina ta makara dan kuwa tuni harsun lula sama ta zube a wajen tana kurma uban ihu.
Mutanen garin kuwa sai suka fara maida yadda akayi, Aramma da Ramma suka bar wajen jikin su babu karfi, zance kuwa tuni ya zama on top topic ɗin da ake tattaunawa a ciki garin, wasu suce ƴan sanda ne wasu suce sojoji ne, kowa dai da labarin da yake bayar wa.
TO FAH!!!!
_*Littafi MUTUWAR AURE na ɗaya kyauta ne, littafi na biyu na kuɗi ne a Telegram zamu yisa. Zamu tafi hutu har sai mun samu adadin mutanen da muke so kafin mu fara 2, ku yi gayya, ku ba da labarin littafin MUTUWAR AURE labarin Husna da Mansur Mahmoud Mas'od Al-alfeey ba Andalus (Spain) ku sanar da wanda bai karanta ba da ya fara kar a barshi a baya. Ina da kyakyawan yakini akan abin da na rubuta kuma ina mai ba ku tabbacin za ku samu labarin nan fiye da hasashenku, In sha Allahu ba zan ba ku kunya ba, ku biya kudin karatun ku Naira ɗari biyar kacal da zaran kun kai adadin za mu fara kuma ba jira har sai mun gama in sha Allahu*_
AKWAI CAKWAKIYA A GABA...
_AMMA KAFIN NAN INADA TAMBAYA..._
SHIN HUSNA DA MAHAUKACIN YAYAN TA ZASU SAKE HAƊUWA?
SHIN KUNA GANIN HUSNA ZATA SAKE KOMAWA ZAMA GIDAN BABAN TA?
INTA KOMA YANZU WANNE IRIN ZAMA ZASUYI DA NANA?
TSAWAN SHEKARUN NAN DA HUSNA TAYI A ƘYAUYE ME YASA SAI YANZU RANA TSAKA DANGIN MAMANTA SUKA ZO DAUKAR TA?
ME KUKE TUNANIN YA KAWO AUNTY MANSURA ƊAUKAR HUSNA?
INA LABARIN MAMAN HUSNA DA YAYAN TA BAFFA?
HURRY AND JOIN TELEGRAM GROUP WITH JUST 500 NAIRA 💃💃💃💃
PAY INTO
5198163035 AISHA ABDULAZEEZ UZAIR MONIEPOINT
OR
8063789370 A'ISHA ABDUL'AZEEZ UZAIR OPAY
YOU CAN WATSAPP ME WITH EVIDENCE OF PAYMENT VIA +2348039352725
THANK YOU FOR SUPPORTING ME❤️
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 31 Chapter of 31