daɗi kace yau bajau damu?"
"Kaidai bari yau jina nake a cike an jima zaka rakani na gaida Kakar mutuniya ta (Husna ) nadan bata wani abu da Tawan ma da tana kula ni ai yau dana ɓata ta a garin nan, na kashe mata kuɗi, yawwa kasan meye abun daɗin?" Gambo ya girgiza kai.
"Yanzu mukayi waya da wanda Oga ya haɗa mu ka gane shi ai?"
Gambo ya daga akai da sauri yana faɗin "Eh wanda ya zo kwanaki ko?"
"Shifa yanzu yake faɗa min a sabuwar Shekarar nan Oga zai shigo da wasu manyan kayan dabai taɓa shigo da irin suba Kuma kafin lokacin duk zai zo ya ganmu dan yafi so yana gari za'a wuce da kayan, kasan baya zama abunka da masu garin (masu kuɗi) kullum zakaji yana Saudiyya ko ƙasar turawa yana hutawa, ina faɗa maka kaya ne na manyan kuɗi masu nauyi za su wuce wannan karon Oga yayi mana albashir ɗin kuɗi masu kauri, duk wanda ta ɓangaren shi ba'a samu matsala ba zai ja wata million fa."
"Kai mutumin maliyan fa kake kira?"
Gambo ya faɗa yana zare Ido, Dan Hajja yayi dariyar nishadi yace "haba nawa million nawa take a wajen Ogan sama kasan kuɗin mutumin nan kuwa, bafa iya harkar madarar nan yake ba har shinkafa yana shigowa da ita wallahi harna matsu na ganshi."
Gambo ya gyaɗa kai kamar kadangare yace "lokacin ai ya kusa sabuwar shekarar Bature baifi kwana Arba'in ba nan gaba, Allah dai ya kaimu lokacin nasan zamu wataya mutumi na."
Dan Hajja ya daki kafaɗun shi yace "sosai ma zamuje tsangaya wajen Malam shima a ɗan bashi wani abu dan ya sake batar mana da sahu.
"Eh ya kamata gaskiya ai yana maka aiki babu wasa ya cancanci a jiƙa shi shima yau gidan shi aci fara (shinkafa)."
Suka kwashe da dariya suna tafawa Dan Hajja ya juyo yaga inuwar mutum a bayan bishiya yana zagayawa yaga kurman mahaukaci zaune yana gangaɗi ya rungume Sandar shi a kirji yadda yayi dole ya baka tausayi.
"wa kake dubawa ne?" Gambo ya faɗa yana matsowa wajen.
"Oh ashe ma wannan kurman mahaukacin ne." Maganar Gambo ta tashe shi daga baccin daya fara ɗaukar shi.
Dan Hajja ya zaro sabuwar ɗari biyar daga aljihun sa yace "kaima gashi ka ɗan ɗana arziki." Ya jefa masa kuɗin su kayi gaba.
Kuɗin yabi da kallo sai kuma ya juya ya kalle su suna tafe suna hira da dariya.
Basu jima da barin wajen ba Husna ta zo hannun ta riƙe da ledar kunun shi tace "Yaya ashe kana nan? Inata neman ka sai Indo ce ta ce min kana nan." Ta faɗa tana kallon yadda ya zauna a kasa ya mike ƙafafun shi kanshi jingine da jikin bishiyar yana duban gaban shi.
Kunun ta sake miƙa masa yaƙi karɓa ta tsaya tana kallon shi dan tasan yana san kunun tsamiyar sosai ta gane haka ne ta yadda taga inta bashi baya rage wa duka yake shanye wa, sannan baya sha da sugar dan ta taɓa zuba masa suga yana ɗanawa taga ya cire ledar a bakin sa sai kuma ya yamutsa fuska ya jefar, shike nan bata sake saka masa suga ba.
"To meya hanashi karɓa?" Ta tambayi kanta.
Kiran ta aka fara yi a tsallaken titi ta kawo kunu sai ta sake kallon shi tace "Yaya ka karɓa kaga ana kirana a tsallake nakai kunu, karɓi sai naje naga waye me kiran." Ta faɗa tana sake miƙa masa ledar, hannu yasa ya karɓa amma sai taga ya miƙe tsaye riƙe da ledar Kunun.
"Yaya sai an jima."
Ta faɗa tana juyawa ta duba titi saida taga babu mota sannan ta tafi zata tsallaka tayi taku ɗaya kan tayi na biyu taji "Woooof......!" An jawo hannu ta baya da wani mugun zafin nama ana jawota bayan kuma wata ƙaramar mota tazo ta wuce da mugun gudu Husna ta tsorata sosai dan wallahi saura kaɗan motar ta buge ta, ƙirjin ta ta dafe sai kuma ta juya taga wanda ya janyo ta.
Abinda Husna bata taɓa zato da kawowa ranta bane ya faru sanda ta juyo suka yi Ido biyu da mahaukacin yayan ta tsaye a kanta, yau ƙwayar Idanun shi ta fito fili ras Husna ke ganin cikin idanun sa masu ɗauke da wasu manyan blue eyes, cikin su ya turu sosai Blue ɗin yayi duhu bau cikin idanun kuma yayi wani batsi batsin zaiba, idanu ya zuba mata kamar zai maketa da sauri Husna ta ɗauke kanta tabar kallon sa gaban ta na wani irin mugun faduwa dan tunda take bata taɓa ganin mutum da blue eyes ba.
Sake duban shi tayi a karo na biyu sai taga ya mai da idanun ya rufe ya koma baya ya ɗauki Sandar shi daya barta a ƙasan bishiyar bai sake duban inda take tsaye ba ya miƙe titi ya barta anan tsaye tana binshi da kallon mamaki haɗe da tsoron idanun shi.
"Dama akwai Ido irin haka?"
Husna ta tambayi kanta, wata zuciyar tace "shi haka Allah ya halicce sa ko kuma ciwo ne tunda bashi da lafiya."
Husna ta girgiza kai a fili tana yarda da shawarar zuciyar ta na ciwo ne yasa idanunsa yineBlue.
Kamar daga sama taji ance "Tunda ya taimake ki yau kema saiki gode masa oh! Su Ma'u da yanzu an ziyarci barzahu." Maganar Bahari ta katse wa Husna tunani, sai lokacin kuma tunanin wani bai gansu ba yazo mata.
"Dama kana ganin abinda ya faru?" ta jefa wa Bahari tambayar dake cinta, sai taga yayi murmushi yace "ina gani har fa zan yi ihu na ɗauka wani abun zai miki sai naga ashe taimakon ki yayi Allah sarki Bawan Allah ashe mahaukaci ma yasan mai masa rana, kai Allah ya ba shi lafiya."
Husna saita zama lost ta rasa me zata ce tayi gaba Bahari ya bita a baya yana faɗin "ki rinƙa kula in zaki tsallaka titi kinsan motoci gudu suke sosai musamman ma ƙananun nan..." Zuciyar Husna a karye tace "wallahi Bahari na duba ni banga Motar ba shi yasa na tafi zan tsallaka."
Bahari ya maimaita "kin duba baki ganta ba kuma?"
Husna ta ɗaga masa kai, kamar ya sake mata magana sai kuma yayi shiru yace "muje naga sauran kunun na nawa ne ya rage na siye nayi sadaka."
Husna bata dake masa magana ba har suka ƙarasa kan botikin kunun ya duba yace "ai ya kusa ƙare wa."
"Eh."
Ta faɗa a sanyaye dan har yanzu tsoron motar data kusa kade ta bai barta ba.
Kuɗin Kunun ta faɗa wa Bahari ya siye ya bawa masu so, ta karɓi kuɗin ta ya riƙo mata botikin tayiwa Indo sallama suka tafi gida Bahari na biye da ita a baya yana mata zance kamar yadda ya saba ita kuma yau babu baka sai kunne.
......Tunda tazo Dandalin take duban hanya amma ko alamun shi bata gani ba gaba ɗaya sai taji ta damu zaman wajen ya daina yi mata daɗi, Indo tana mata zance da bata Labarin bikin Asure da za'a saka gobe a Dandalin amma Husna gaba ɗaya hankalin ta baya wajen.
"Wai inata miki magana kina juye juye me kike nema ne?" Indo ta tambaye ta.
Husna saita tsinci kanta da cewa Indo "babu komai."
Kafin Indo ta sake mata magana ta miƙe tace "nifa gida ma zan tafi." Indo tayi mata kallon mamaki.
"Baki da lafiya ne Ma'u? naga duk jikin ki yayi sanyi."
"Babu komai kawai bacci nake ji saida safe." ta faɗa tana juyawa tabar Indo da rakata da Ido.
Husna na tafiya a hanya ta haɗu da Dan Hajja da Gambo dan korar sa.
"A'a Budurwar mu ina zuwa kuma? Wajen kifa zamu."
Husna ta ɗaga kai ta dube su a sheƙe sai kuma tayi gaba ta barsu a tsaye.
Gambo da yayi maganar ya dubi Ɗan Hajja yace "wallahi Ma'u yar wulaƙanci ce ji yadda ta ɗebe mu ta zubar kamar ba mutane ba."
Ɗan Hajja ya bugi kafadar Gambo yana raka bayan Husna da Murmushi yace "karka damu saura kaɗan ta shigo hannu, kaji abin da Malam yace mana ɗazu a kanta dole sai mun bita a hankali."
Gambo da takaicin wulaƙancin da Husna tayi musu ya ƙume yace "ai wallahi naso ayi mata kiranye dandai kawai Malam yace ba zai yiwu bane."
"Dama kaika matsa min Gambo shi yasa nawa Malam maganar ta amma banda haka nawa Ma'u take a wajena da har saina haɗa ta da Malam, Hmmm ina sata a gidana fa zance ya wuce duk wannan dage kan zata dena min."
Gambo yayi ƙwafa "kasan Allah inaga Aramma ba haka yabar yarinyar nan ba, banda haka yaushe za'a ce wai komai nata a rufe yake ba'a iya ganin komai a kanta."
"Matsala ta dakai kana da gaggawa Gambo dan Allah muje." Dan Hajja ya faɗa yana yin gaba Gambo ya rufa masa baya.
Babu wanda yasan Husna ta shigo gidan harta shiga ɗaki ta kwanta, dan su Ramma na wajen su, Dije ma tana lungun ta.
Akan gadon karar da Ramma ta siya mata take kwanciya ta zauna tana tunanin mai yasa yau bai zo Dandalin ba. Wata zuciyar tace "koya kwanta bacci da wuri."
Ta ɗanyi jim tana tuna abinda ya faru ɗazu sai kuma can a kasan zuciyar ta tace
"To a ina ma yake kwana?"
"A makaranta mana." Wani bari na zuciyar ta ya bata amsa.
"Allah Sarki ko shi a ina Maman shi take?" ta faɗa a fili.
"Shima bashi da Mama kamar ke."
Husna ta sake faɗa a raunane, sai kuma tayi murmushi a fili tace "wata rana zaka warke Yayan Husna."
Tun tana zance da tunane tunane harta kwanta, duhun ɗakin ya sake taimakawa wajen zurfafar tunanin ta har bata san lokacin da bacci yayi awon gaba da ita ba.
.......shi kuwa tun daga fitowar ta daga gida har lokacin da ta koma komai akan idon shi ya faru, baibar inda ya ɓoye ba saida yaga shigar ta gida yaɗan jima a tsaye yana kallon mutane suna wucewa jifa jifa saidai babu wanda ya kula dashi har yabar wajen ya kama hanyar makaranta.
*****Washegari da safe Husna taje gaida Aramma ta samu Lirwanu zaune a gaban shi Dije na kusa da Aramma, da alama magana suke mai muhimmanci, Husna na gama gaida Aramma ta gaida Dije da Lirwanu ta miƙe zata fita Aramma ya ce "Asma'ullahi zo nan zauna maganar tamu ai taki ce zo kiji abinda Baban ki Lirwanu ya zo dashi."
Husna ta dawo da baya ta zauna tana fuskantar Aramma yace "Asma'ullahi Baban ki Lirwanu ne ya zo da maganar yana son zai fara siyan Barkono yana kaiwa kasuwa kina siyar masa, kamar dai yadda kuke zuwa yin talla duk ranar kasuwa, to banki ta tashi ba dan zaman banzan da yake ba abune mai kyau ba, sam bana jin daɗi daya ɗauki shawarar mu a baya ma da tuni an dade da wuce nan amma yanzun ma bai makara ba, saidai kamar yadda na faɗa masa bakya nan yanzu ma zan maimaita masa a gaban ki zaki bishi kasuwa kiyi masa talla ne kawai inya yarda duk adadin cinikin da kika yi masa za'ayi lissafi ya cire hakkin ki na ladan talla ya baki kamar yadda kike wa sauran mutane, in ya yarda shike nan sai nace Allah ya bada sa'a in kuma bai yarda ba to ya nemi yaran gari suyi masa talla ya biya su ke kuma kici gaba da yiwa wasu suna biyan ki."
"Amma Aramma ban tari numfashin kaba tsakani da Allah yanzu dan Ma'u ta yiwa Lirwanu talla sai ace saiya biya ta ladan talla? In Mai Kano tayiwa talla za ace ya biya ta ne?" Dije ta faɗa cikin jin haushin maganar da Aramma yayi.
"Kwarai kuwa Hadiza, yau ko Abdullahi Asma'ullahi tayiwa talla saiya biya ta hakkin ta in baya ɗauke nauyin matsalolin ta, kinga saita biyawa kanta buƙata dashi, in kuwa yana yi mata abinda ya dace matsayin shi na uba ita ma saita yi mata kyauta dan neman Albarkarsa." Aramma ya bawa Dije amsa da duka gaskiyar shi.
Lirwanu kuwa ya shaƙi baƙin ciki da furucin Aramma amma sai ya danne ya nuna babu komai a gaban shi dan yasan muddin ya nuna ba zai rinƙa bawa Husna ladan talla ba to tsaf zai hana ta zuwa kuma ta hanu babu yadda zai yi.
Dije zata sake magana Lirwanu ya riga ta da cewa "babu komai Aramma saina rinƙa bata ladan tallar."
"To madallah ke Asma'ullahi kinji ko? In Allah ya kaimu Litinin saiki bishi Beguwar, Allah ya sawa newa albarka."
Lirwanu ya amsa da Amin yana kunshe tsari da shirin shi a ƙasan zuciyar sa, yayin da Husna taji saukar maganar bin Baba Lirwanu Kasuwa kamar bugun guduma a tsakiyar kanta.
"Wai yaushe zata huta ne daga masifa da kuntatawar Baba Lirwanu?" Ta tambayi kanta tanajin rauni rashin gata da rashin madafa na lulluɓe duka illahirin jikin ta, wani ciwon kai mai zafi ta bari ɗaya ya saukar mata take, idanun ta suka canja.
Kasa tashi tayi daga tsakar ɗakin saida Aramma ya yayi mata magana sannan ta miƙe tsaye da ƙyar tana hado duka dauriyar ta waje ɗaya.
"Asma'ullahi koda wani abu ne?" Aramma ya jefa mata tambayar da da zata iya ce masa zatayi "bazan yi wa Baba Lirwanu talla ba saboda cutata zai yi."
Amma maimakon ta bashi wannan amsar data dace da tambayar shi sai ta girgiza masa kai ta fita daga ɗakin da sauri tana jin Idanun ta na mata zafi.
Tana fitowa daga lungun Dije taji ana sanar da lalacewar Famfon cikin gari.
Duk halin ciwon kan da take ciki sai da ta ɗanyi turus dan tasan yau ɗiban ruwa zai yi wahala tunda Famfon cikin gari ya samu matsala saidai su tafi na makaranta indai suna son samun ruwa da wuri.
Ramma nayi mata magana ta wuce ta ta shige ɗaki ta kwanta a ƙasan leda tana mai da numfashi, baƙin ciki ke cinta ga wani kuka daya maƙale mata a wuya wanda bata son yinshi saboda ciwon da idanunta ke mata duk lokacin da tayi kuka saita kwana biyu cikin idan ta na mata ciwo kan ya daina.
"Ma'u wani abun ne ya faru?" Ramma data biyo ta ɗakin ta tamabaya tana zama a bakin gado.
"Babu komai kaina ke ciwo."
Husna ta bata amsa muryar ta a ƙasa.
"Ayya sannu bari na samu yaro ya siyo miki paracetamol a shagon Sunday saiki sha."
Ramma tayi maganar tana miƙe wa Husna ta tashi zaune tana dafe gefan kanta tace "barshi kawai ɗiban ruwa zamu, nasan yanzu an fara tafiya makaranta tunda an sanar da ɓacin Famfo, gwanda naje da wuri kada layi yayi yawa." tayi maganar tana fita daga ɗakin, Ramma ta raka ta da Ido, a zuciyar ta tana jin babu daɗi dan tasan dole akwai abinda ya faru kawai ba zata faɗa bane tunda tasan tana da zurfin ciki zai yi wahala kaji Husna tayi ƙorafi, tunda ta rasa gata ta koyi dauriya da kafiya kamar Namiji.
Har akayi sallar azahar Husna sahu biyu na ruwa ta kawo gidan, wannan karon data koma tana sa layin jarkokin ta ta koma gefe ta zauna ta kife kai tana mai da numfashi dan sosai yanzu kanta ke mata ciwo inta shiga rana kuwa ji take kamar ana zuba mata ruwan sanyi.
Har wajen ƙarfe uku bata sake kawo ruwa ba, Lirwanu ya shigo Zahara uwar ƴan ƙorafi da mita tace "yau dai fa gidan nan namu babu ruwa, bana jin kona saka sanwar dare zamu samu."
Lirwanu ya dube ta sai kuma yace "Ma'u bata kawo ruwan bane?"
Kan Zahara tayi magana Ramma tace "ta kawo sahu biyu, kasan yau Famfo zai yi layi tunda babu na cikin gari."
"Wanne zancen banza ne kuma wannan, rashin Famfon cikin gari sai ya hana a samu ruwa? Da da yake lalacewar a samu ruwam fa? Iskanci ne kawai irin nata da in bata gadamar yin abuba saita ɓatawa mutane rai."
Lirwanu yayi maganar a zafafe, dai-dai lokacin kuma Husna ke shigowa da Ruwan a bakin randar Dije ta ajiye Sagar ruwan data debo maimakon ta juye saita zauna a ƙasa tana maida numfashi dan wallahi da ƙyar ta iya kawo ruwan gida dan ma Indo ta tayata buga ruwan da ba zata iya debowa ba.
Shiru shiru bata tashi ta juye ruwan ba, ran Lirwanu ya ɓaci da ganin ta zauna a bakin randar bata juye ruwan ba.
A zafafe yazo kanta yana mata magana, saita ɗago da jajayen idanun ta da ƙyar ta kalle sa, babu tausayi ko kula da yanayin da take ciki ya kwashe ta da marin da saida ta kifa saboda zafin shi, sai kuma ya balbale ta da masifa yana cewa.
"Ke saboda kin raina mutane ana miki magana kikayi banza, tun safe ana jira ki kawo ruwan sai yanzu kike shigowa da shi kuma sai ki zo ki sake zauna wa, to uban waye zai zuba miki sauran ruwan? ko kuma salon dare yayi kija ana zagina a gari."
Husna ta yunƙura ta taso da ƙyar tana jin cikin idanun ta kamar zasu faɗo ƙasa saboda ciwo tace
"Baba Lirwanu kaina ciwo yake bazan iya ɗebo ruwan ba." ta faɗa tana layi kamar zata faɗi ƙasa Allah ya taimake ta ta dafe jikin ican rumfar Dije.
A tsiyace ya kalle ta daga sama har ƙasa yace "Ni zaki renawa wayo? A'a mutuwa kike ba ciwon kai ba, kin wuce kin kawo min ruwa gidan nan ko saina ɓalli tsimagiya na nuna miki jikin ki yanzun nan."
Yayi maganar da hargowa, zuciyar Husna na wani irin ciwo mai raɗaɗi ta saka hannu ta ɗauki sandar sagan ruwan tasa ajikin jarkokin ta saɓa a kafadar ta ta juya tana tangaɗi ta kama hanyar fita daga gidan.
Data fito maimakon ta tafi saita samu waje a ƙofar gida ta zauna ta sunkuyar da kanta da take jinshi kamar ba'a jikin taba.
Bata san adadin tsayawan lokacin da ta ɗauka a wajen a zaune ba sai da taji maganar Aramma yana kiran sunan ta.
"Asma'ullahi....ke....Asma'ullahi lafiyar ki kuwa? Me kike yi nan a zaune?" Aramma ya jero mata tambayoyin yana isa inda take.
"Subhanallah! Baki da lafiya kike zaune a nan?" Aramma ya faɗa yana zare hannun shi daga wuyan ta da yaji yayi mugun zafi kamar garwashin wuta.
Da taimakon Aramma suka shiga cikin gidan yasa yara suka shigo da jarakunan ciki, shi kuma ya kamata saboda jikin ta rawa yake kamar ana kada mata gangi zazzaɓi mai zafin gaske ya rufe ta, Ramma na gano shigowar su ta taso tana tambayar.
"lafiya?"
Dan dama tun fitar ta daga gidan hankalin ta yaƙi kwanciya.
Kamata ku shiga ciki Zazzaɓi ne ya buge ta can na ganta zaune a ƙofar gida, ina Iro yake? Yazo ya siyo mata maganin zazzaɓi tasha, Allah ya sawake." Aramma ya faɗa yana ƙwala wa Iro daya hango acikin kewaye kira, Naja da sauran matan su Baba Adamu sai sannu suke jerawa Husna, Yaron Zahara Ramma tasa ya shimfida mata taburma a kewayen su ta kwantar da Husna dake ta rawar sanyi, ɗakin ta ta shiga ta dakko zanin gado ta rufa mata.
Tana zaune a kusa da ita Iro ya kawo maganin da Aramma yasa ya siyo, saida ta ɗebo ruwa sannan ta tashi Husna ta bata maganin, da ƙyar ta iya karɓa tasha tana rawar sanyi, ta koma ta kwanta Ramma ta sake rufe ta da zanin gado....
_*WRITING.....✍🏻*_
*_MUTUWAR AURE.....!_*
_(Ƙaddarar wasu ƴaƴan)_
*_Kanawa ne👌🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_BOOK 1_
*_FREE PAGES_*
________________
*_WHATSAPP GROUP👇🏻_*
https://chat.whatsapp.com/LaVfMaCQz1C2WcC7zGfSL3?mode=gi_t
https://wa.me/+2348064789370
_________________
_EPISODE 21_
Har bayan la'asar Husna na kwance, har lokacin kuma Ramma na tare da ita musamman da yake ba ita keda girki ba saita maida hankalin ta akan Husna, sai wajen ƙarfe biyar na yamma sannan zazzaɓin ya sauka gumi ya karyo mata, Ramma ta taimaka mata ta zauna dai-dai lokacin kuma Aramma ya shigo gidan Lirwanu na biye dashi a baya, randa ya buɗe zai sha ruwa yaga wayan Ramma najiyo shi a cikin gida yana faɗin "yau saina zane yarinyar ace har yanzu bata kawo ruwan nan ba."
Yana rufe baki Aramma ya fito yana gyara nadin rawanin sa yace "kai me yasa baka da lissafi ne Lirwanu? Kasan me ya hanata zuba ruwan kake wannan furuci haka? kai kullum kana girma kana sake shiga jeji, to gata can kwance a lungun ka zazzaɓi ya rufe ta tun ɗazu saini na shigo da ita gida, saika ɗauki Saga ka karo ruwan tunda yau baiwar taka babu lafiya."
Aramma ya faɗa yana yin gaba kana ganin yadda yayi maganar kuma kasan ranshi a ɓace yake.
Dole uwar naki Lirwanu ya fita ya karo sahu biyu yana mita dan shi gani yake ciwon Husna iskanci ne kawai da lamɓo.
........Mahaukacin yayan ta kuwa tun rana yake zagaya inda suke zaman saida abincin rana amma sai yaga bata nan har aka yi sallar la'asar ya koma can bayan rumfar Bahari ya zauna yana kallon hanyar da take fitowa, yana jiran yaga ta zo ta wuce da Kunun yamma, nan ma shiru babu ita babu dalilin ta har rana ta fara faduwa babu Husna babu alamar ta.
Bahari ne yaga yanata zagaye tsakanin inda su Husna ke zama da hanyar da take biyo wa yazo makar zai wuce ta kusa dashi yace "Ma'u kake nema ko?"
Bai tsaya ba kuma bai ce masa komai ba shima Bahari be yaji ya bashi amsa ba tunda sunsan baya magana amma duk da haka sai ya ɗaga murya yace "Nima tun ɗazu zaman jiran ta nake yau ko abincin rana batayi ba Kunun yammar ma shiru Allah dai yasa lafiya dan yau bata zuwa talla ƙyauyu ka."
Bahari ke babatun maganar sa shi kaɗai dan shi tuni yayi nisa da inda yake.
Yana tafiya Bahari ya gano Indo tana taho wa zata wuce ya tsaida ita da tambayar.
"Ina Husna yau naga bata fito ba lafiya kuwa?" Indo ta tsaya tace "nima ban sani ba amma ɗazu tare muka ɗebi ruwa da ita a makaranta sai dai ta cemin kanta na ciwo inaga shi yasa basu yi kunu ba." Bahari ya jinjina kai yace "Eh inaga haka ne nagode to."
Ya koma ya zauna akan bencin da yake zama ita kuma Indo ta wuce.
Tunda aka yi sallar isha'i ya tafi can bayan bishiyar daya tsaya jiya ya zauna yana jiran ganin fitowar Husna Dandali, yana zaune a wajen har yan mata suka hura wuta suka fara waƙe baiga Husna ta wuce ba.
Can ya ɗago kanshi yaga Indo tana ƙwala wa Ummai kira, saida ya bari suka gama maganar su yaga tayi hanyar gidan su Husna, a hankali yake binta a baya ba tare data sani ba har ta shige gidan ya koma can cikin duhuwa ɗan nesa da gidan kaɗan ya tsaya yana jiran fitowar su.
Shiru shiru babu Indo babu Husna har tsawan wani lokaci sannan yaga Indo ta fito ita kaɗai ta sake komawa Dandali.
Ji yake kamar ya bita ya tambaye ta ina Husna take to amma ta yaya zai tambaye tan? Jikin shi yaji yana saki haka kawai shi kansa baisan me ya saba amma sai ya tsinci kansa cikin damuwa da rashin walwala, bashi da wani buri yanzu da yafi yaji kuma yasan halin da take ciki, ransa yaji ya ɓaci damuwa ta lulluɓe zuciyar sa, bai tafi ba haka yaci gaba da tsaiwa a wajen har zuwa wani lokaci mai tsayi sannan ya juya ya tafi yana jin babu daɗi.
Abu kamar wasa washegari ma haka ce ta faru gare shi dan babu Husna
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 31