sannan matan suka rage ife ifen da suke.
Aramma ne yayi masa wanka da taimakon su Mai Kano, Salisu fuskar shi fes babu ciwo ko kaɗan kamar ka kira shi ya amsa, sai kafar shi da gefan cikin shi anan ne jini keta zuba.
Saida aka shirya shi Aramma ya tsuguna yayi masa addu'a ya roki Allah ya yafe masa yace shima ya yafe masa sai anan ne ma wani kuku mai ciwo ya taso masa.
Mai Kano kuwa da sauri ya juya ya kife kanshi da jikin bango, su Baba Adamu suka fara basu hakuri, saida suka yi shiru sannan aka shigo da Dije suyi sallama, ta rungume gawar tana kuka tana surutu addu'ar ma ta kasa yi masa Gaje kuwa da yaran shi kowa yaga yadda suka riƙe makarar suna faɗin bai mutu ba dole su baka tausayi.
Masoya na kuka da ihun kar a tafi dashi haka ɗaru ruwan mutanen gari da baƙin da suka zo suka raka Salisu makwancin sa gidan shi na gaskiya, saidai muce Allah ya gafarta mana da iyayen mu gaba ɗaya.
Ana fita dashi kuma naƙuda ta tasowa Gaje aka rufu akanta, cikin ikon Allah bata jima tana naƙudar ba ta haifi ɗanta Namiji, yadda ya diro duniya maraya yana kuka haka Gaje da sauran al'ummar da suka ji kukan shi suka sake fashewa da kukan tausayin sa.
"Sunanka Salisu, sunanka Salisu, Sunan ka Salisu Aramma ya faɗi haka a kunnan yaron sau uku bayan an gyara yaron an kawo masa shi yayi masa kiran Sallah da huɗu ba da sunan mahaifinsa.
"Allah mai kyauta da ƙari, Allah buwayi gagara misali, Allahu kaike karɓa kuma kaike bayarwa, Allah mun gode maka muna sake gode maka, Allah komai ka tsara mana daidai ne." Aramma ke jerowa Allah godiya su Mai Kano suna zaune a gefan shi suna amsa wa da Amin.
ƙofar gida an shimfida manyan taburmi anata karɓar gaisuwa. Cikin gida kuma ana karbar gaisuwa ana barkar haihuwa tare da taya Gaje murnar fita daga takaba.
_Allah ke nan_
Sai yamma Nana da Ni'ima suka iso, Nana ta shigo gidan da tsohon cikin ta dan harya fito sosai, Ni'ima tayi kukan mutuwar Salisu dan tana son Baba Salisu saboda kirki da kyautatawar shi gare ta.
Haka aka rinƙa karɓar gaisuwa, tako ina mutane zuwa suke dan Salisu mutum ne na mutane, gashi da kyauta kowa nashi ne bashi da wani abokin faɗa.
Kamar yadda ake yi a garin in akayi mutuwa ba'a ɗora tukunya sai bayan sadakar bakwai, to ga mutuwar Salisu ma haka ce ta faru, tun da aka yi mutuwar ba'a ɗora tukunya ba daga ko wanne gida a cikin ƙyauyen ake kawo marar tuwo da miya ana karɓa ana kaɓacewa a ƙwarake, wannan tuwon shi mutanen gidan zasu ci da ƴan zaman makoki, haka da safe za'a rinƙa kawo kwanukan koko da kosai wanda dashi mutanen gidan mutuwar zasu karya, da rana ma haka ko wanne gida sai an kawo abincin rana, kuma ko bakuyi girkin rana ba sai an siyo a tasha an bawa yaro ya kawo ko babba.
Ranar sadakar uku kuma matan abokan shi suka rinƙa kawo waina da gumba kaɓaki kaɓaki.
Ranar da akayi sadakar bakwai ranar aka yi wa Salisu ƙarami yanka, Salisu Babba kuma akayi taron yi masa sadaka da addu'a, ƴan uwa na nesa dana kusa kowa ya fara tafiya, ƙofar gida ma zaman makoki ya ƙare kowa ya tafi, Nana ma suka fara shirin komawa Kano washegari, a tsarin tafiyar tasu kuma babu Husna dan kuru-kuru Nana tace mata "su Ma'u kuma an zama ƴan matan ƙyauye, keda Kano ai saida yawo."
Hakan kuwa aka yi washegari suka shirya suka koma, halin jimamin mutuwar da ake ciki yasa Aramma baiyi wa Mai Kano magana akan tafiya da ita ba.
Gida ya watse kowa ya kama gaban shi ya zamana gidan babu kowa sai ƴan gida, babu baƙon daya rage sai ƴan gidan kowa ya tafi.
.........Sannu a hankali mutuwar Baba Salisu ta fara nisa, haka a hankali abubuwa suka fara canjawa, rayuwar gidan ta fara juyawa tana canja salo, Gaje na gidan tana renon ɗan ta duk da ƴan uwanta sunso ta koma gida tunda ta riga ta fita daga takaba amma sai Aramma ya hana yace suyi haƙuri tadan sake kwana biyu kanta tafi.
Sannu sannu abincin rana ya fara yanke wa a gidan dama Salisu ne ƙarfin gidan shike sawa ayi, yaran shi kuwa yanzu babu mai basu kuɗin kashewa kona siyan abinci da rana, Aramma na iyaka kokarin shi akan su dan kullam da safe sai ya siya musu kosai, Lirwanu kuwa baiwa ƴaƴan shi bama bare na wani.
Yanzu babu me kawo ruwa gidan saidai Husna da Indo suje su ɗebo, dama Salisu ne ke biyan kuɗi a kawo kullum, to yanzu an wayi gari babu shi, tuni Husna da Indo suka shige sahun ƴan matan garin dake sunturin ɗiban ruwa.
Husna ce kedan jin wahalar ɗiban ruwan saboda rashin sabo.
Ranar da ta sake kukan rashin Salisu kuwa shi ne randa ta tambayi Lirwanu kuɗin sabulun wanki ya balbale ta da faɗa kamar zai yi mata duka, ya koreta.
Tana barin inda yake ta samu waje ta zauna sai kuka, Ramma tazo ta same ta tana kuka tace "meya faru?" Ta faɗa mata akan ta tambayi Baba Lirwanu kuɗin sabulu ne yace inta sake tambayar shi sai ya zane ta.
Ramma tayi shiru tana jinjina hali irin na Mijin su, amma yata iya haka yake bashi da daɗi.
"Kinga karki sake tambayar shi kinji?" Husna tace mata "to wazai na bamu kuɗin siya tinda kinga Dije bata bamu."
Ramma tayi shiru tana tunanin sai kuma tace "zamu nemo wata hanyar, ai Allah na nan."
Dije kuwa wannan mutuwa ta Salisu ba ƙaramin taɓa ta tayi ba, dan Allah ne gatan ta Salisu gatan tata, takamar ta a gidan nan Salisu ne, dan yanzu kuɗin kashewa ma nema yake ya gagare ta, to dama shike basu kullum wanda Mai Kano yake turo musu kuma ya zame mata bonus, yanzu kuwa babu wannan maganar wanda Mai Kano ya aiko shi ne na kashewar ta da sauran bukatun ta.
.......Sannu sannu rayuwar gidan ta fara wargaje wa tana ɗaukar wata hanya ta daban, yanzu kowa ta kansa yake yi a gidan, dumamen safe ana sauke shi a wajen ake kasawa kowa ya dau nashi in baka ɗauka ba kayi jinkiri to bazaka samu ba, tuni Husna ta ɗauki kwanon talla a gari, ita ce tallar kosan safe ita ce tallar Awara da rana, yara da yawa a garin suna talla ne dan su tara kuɗi su sai kayan ƙyali da ado irin na sauran yara amma banda Husna da ita tana tallane dan ta kashe yunwar cikin ta da buƙatun ta na yau da kullum, dan yanzu bata da mataimaki sai Allah sai Ramma baiwar Allah data riƙe amanar da Aramma ya bata da hannu bibbiyu, abincin gidan su kuwa iya tuwon dara ake yi yanzu sauran abinda ya rage da safe a dumama da rana kowa yaci da kanshi.
Duk wannan faɗi tashi da ake kuma har zuwa wannan lokaci Mai Kano bai daina yiwa Husna aiken kuɗin kashewa sabulun wanka na wanki da man shafawa ba, kai wasu lokutan harda abun taɓawa yake siya ya aiko mata da shi, saidai kamar yadda bai daina ba haka Dije bata daina karɓe wa ta hana ta komai ba.
Cikin lokaci kankani Husna ta canja tayi wani iri tuni ta fara sajewa da sauran yaran gari.
Yau tun safe Indo ta tashi bata jin daɗi wannan yasa Husna ce kadai taje ɗiban ruwa, hakan kuma yasa bata samu kawo ruwan da wuri ba saboda dama Indo ce ƙarfin ɗiban ruwan, gashi tana kawo sahun farko Zahara ta kwashe tayi wanke wanke da wanka, wannan yasa har yamma gidan babu ruwan kirki.
Lirwanu ya shigo ya tadda gidan babu ruwa ya hau faɗa da zugawa Indo da Husna zagi, yana cikin faɗan Husna ta shigo da ruwa.
Babu jira babu bin ba'asi ya bita da faɗa ya hau zage zage, ran Gaje yayi mugun ɓaci daman kuma a wuyan ta yake tana kulle dashi, ai kuwa ta fito cikin gidan suka fara cacar baki.
"To wallahi tunda abun naka iskanci ne da wulaƙanci Indo ta dena ɗiban ruwa a gidan nan, ai ba baiwar ka bace da kana can tasha zaman rashin abunyi, suna maka wahala kuma kazo kana zagin su harda cin alwashin duka to wallahi baka isa ba."
"Na isa har nayi yawa kuma ɗiban ruwa a gidan nan yanzu Indo ta fara, ke komai akan ƴaƴanki saikin shiga sai kace ke kaɗai ce mai yara." Lirwanu ya faɗa yana huci, Gaje tayi shewa tace "sannu isasshe to maji kuma ma gani Indo dai nice na haife ta kuma nice uwar ta, nace ta daina ɗiban ruwa, in kuma da ubanda ya haifa min ƴaƴan sai naji, inta dena ɗiban ruwan kuma daga yau ka dena mata abinda kake mata, asarrare mara zuciya."
Gaje ta mayar masa da martani a zafafe.
Nan fa rigima ta kaure a tsakanin su, Lirwanu yaƙi bar mata ita kuma yana rufe bakin shi zata ɗora nata.
Faɗan yaƙi ƙarewa saida aka kira Aramma sannan suka yi shiru.
"To kai Lirwanu me yasa kake haka ciwo ai yana wuyan kowa kuma yaran nan suna kokari." Aramma ya faɗi haka ranshi ɓace yana duban Lirwanu bayan ya gama jin abinda ya haɗa faɗan.
"To ya zata zo tana zubawa mutane iko a gida, ai dole a faɗa mata bata isa ba." Lirwanu ya faɗa bakin shi na kumfa.
Aramma ya rufe shi da faɗa ya kuma ce kada ya sake yaji ya daki wani yaro a gidan.
Tun daga wannan faɗa da aka yi Gaje ta kafa ta tsare Indo ta dena zubawa kowa ruwa a gidan, iya karta randar ta.
Husna kuwa da bata da gata sai Allah hawalar saita ƙara mata yawa, kullum ita ke zuba ruwan gidan randa aka samu matsala bata zuba akan lokaci ba Lirwanu ya sakata a gaba da ruwan ashar, tunba in Aramma baya gida ba ai in ba Allah ne ya taimke taba harda duka saiya haɗa mata.
Wannan hali da Husna ta tsinci kanta a ciki ya sake saka rayuwar ta acikin mugun duhu da kunci, gashi yanzu Babanta sai yayi wata biyi kanna uku baizo garin ba, kayan sawarta tuni suka fara fari saboda garin soda da suke sha wajen wanki, dan yanzu bata wanki da sabulu Soda take siya ta jiƙata da ruwan ɗumi dan tafi arha, wannan yasa atamfofin ta duk suka fara koɗewa, dogayen rigunan ta kuwa wasu duk sun dage mata.
Yau sunada Aro (party) babar ƙawar suce ta haihu zasu je gidan suna, Allah ya taimaki Husna da wuri ta gama ɗiban ruwa, tayi wanka Ramma tace "ko zaki je gidan Mariya kice ta baki wani a cikin kayan ki kisa kinga duk kayan ki babu wani na kirki yanzu." Husna tace "to." Ta tafi gidan Mariya tayi sallama, a inuwa ta same su suna surfe, ta gaida matan gidan sannan ta cewa Mariya "kayana na wajen ki zaki bani nasa zamuje Aron gidan su Funi."
"Wanne kaya kuma? Ka jimin yarinya zata min iyayin banza, kin tafi kin bani waje ko sai naci uwarki a nan." Mariya tayi kan Husna da faɗa tana bambamin wani kaya zata bata.
Ramma tayi shiru tana sauraren abinda Husna tace Mariya tayi mata, sai kuma ta sauke ajiyar zuciya tace "dama nasan za'ayi haka, bari mu duba ko a cikin rigunan kine dogwayen saiki saka wata."
Ramma ta faɗa tana burkita akwatin Husna, da kyar aka samu rigar data ɗan sakko mata tasa ta dakko awarwaron data ɓoye a ɗakin Ramma ta saka, yanzu ma baya zama a hannun ta yayi mata yawa dole ta cire ta sake ɓoye wa kamar yadda Ramma ta koya mata.
Gidan suna ya cika yara suna ta wake saiga Sajida ƴar gidan Mariya sanye da wani lace ɗin Husna tana ta fasa kai da ƙumi (yanga), Husna ta kalleta ta kalli kayan jikin ta, nan fa babu zato babu tsammani faɗa ya tashi tsakanin su dan Husna taci kwalar Sajida tace saita cire mata kayan ta dake jikin ta.
Sajida tasa kuka tana ƙaryata Husna nan fa sauran kawayen su suka hau yiwa Sajida ihu da shewa, abunda ya sake rura wutar faɗan ke nan dambe ya kaure tsakanin su.
Sajida ta ɗauka zataci ribar faɗa da Husna saida faɗan yayi nisa sannan ta gane tayi kuskure dan ɗan karan duka Husna tayi mata sannan ta yaga kan ɗinkin rigar lace ɗin.
Sajida taje gida ta faɗa wa Mariya abinda ya faru sai ta saɓo gyale tayi gidan su da burin taje ta samu Husna taci mata mutumci amma sai tayi rashin sa'a dan tana zuwa gidan ta iske Aramma yana nan, taso tayi maganar a gaban shi Dije tayi wuf ta hana ta.
Saida Aramma ya fita Dije tace "ashe baki da wayo ban sani ba? Yo wannan magana yanzu kina yinta a gaban Aramma ai saiya saka kin fito da sauran kayan wajen ki gaba ɗaya, kinga yanzu kama hanya ki koma gida zanyi maganin Ma'u inta dawo gidan nan."
Haka Mariya ta sake sabar gyale ta koma gida tana huci dan ba haka taso ba.
Tun daga lokacin kuma kamar wanda aka yiwa Husna huɗu ba, duk sanda taga Sajida da kayan ta sai sunyi faɗa kota rinƙa yi mata ihu da gorin kayan tane aka ɗauka aka bata, wannan yasa yaran gari suka saka Sajida a gaba da tsokana, bata isa da fito da kaya mai kyau ba koba na Husna bane yanzu yara zasu ce kayan Husna ne suka kwashe.
Wannan rigima tsakanin Husna da Sajidar Mariya bata mutu ba saida aka dangana maganar da gaban Aramma dan Dije tayiwa Husna zagin dacin mutumcin amma a banza haka tasa Lirwanu ya dake ta amma tana fita ina taga Sajida da kayan ta saita sake tara mata yara.
Sanda Aramma yaji kan zance ran Mariya da Dije yayi mugun ɓacin da basu yi tunani ba dan cewa yayi Mariya saita biya kayan data ɗauka, da ƙyar dai aka samu zancen ya mutu bayan dogon faɗan da Mariya tasha, Husna kuma da kanshi ya bata haƙuri tare da alkawarin zaisa Baban ta ya sake ɗinka mata wasu.
Wannan sulhu da aka yi shiya kashe rigimar gaba-daya.
________________________
_BAYAN SHEKARA BIYU A 2011_
Yamma ce sakaliya Motar Naira data ɗebo ƴan mata daga cin kasuwar Litinin beguwa ta tsaya a tasha suka fara Sakkwato suna shewa kowa yana maida yadda aka yi da yadda kasuwa ta kama.
Indo da Husna ne karshen sakkotawa ko waccan su taci damara da gyalen ta, Husna ta ƙara girma da tsayi sak ta saje a cikin matasan yan matan garin, gaba ɗayan su baza su wuce shekara goma sha huɗu huɗu ba.
Husna da farantin silver ta ta fito Indo tace "kai Ma'u yaufa kinci kasuwa koda yake dama ke fa mai sa'a ce komai kika ɗauka sai kin siyar." Sauran yan matan suka fara cewa "kai ai Ma'u badai kasuwa ba."
Husna na jinsu tana murmushi dan ta daɗe da sabawa da jin irin wannan maganganu a bakin ƴan garin bama Kawayen su kadai ba, sukan ce wai "ko kwantai kake in Jikar Dije ta dau kayan ka saiya ƙare."
Aramma kuwa in yaso tsokanar ta yakan ce mata "kaga Jikar Dije kan talla."
Musamman yanzu data zama uwar kanta gashin kanta take ci a gidan, inka cire Ramma da Aramma kuwa babu wanda take ragawa, ko Dije tayi mata yanzu ramawa take sai dai in Lirwanu ya dawo tasa ya dake ta ita kuma tace duka baya kisa, gobe ma inta shiga sabgar ta saita shimfiɗa mata rashin mutunci.
Gaje ta daɗe da komawa gidan su har tayi sabon Aure anan cikin gari, Indo kuwa da Sa'a suna gidan su Gaje wajen kakar su ta wajen uwa, Indo bata ma fiya zuwa gida ba sai ta kama, ita da Husna sun ɗinke sun zama kawaye sosai.
Rayuwa tasa idan Husna ya bude da neman kuɗi sosai ba tallar cikin gari ba harta ƙauyuka tana yi, ta kasuwa kuwa dama wannan ta zama kamar al'adar ƴan matan garin duk ranar kasuwa sai sunje tallar barkono.
Indo ce ta zungure ta tana nuna mata Sunday tace "kinga Sunday can shida sabon mahaukacin dana ke faɗa miki, kome ya haɗa su yake korar shi oho."
Husna ta ɗaga kai taga Sunday riƙe da zabgegen karan dawa yana korar mahaukacin shi kuma yana dagewa yaƙi tafiya.
"Zo muje."
Husna ta faɗa tana yin gaba Indo ta biyo ta a baya....
_*WRITING.....✍🏻*_
*_MUTUWAR AURE.....!_*
_(Ƙaddarar wasu ƴaƴan)_
*_Kanawa ne👌🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
_BOOK 1_
*_FREE PAGES_*
________________
*_WHATSAPP GROUP👇🏻_*
https://chat.whatsapp.com/LaVfMaCQz1C2WcC7zGfSL3?mode=gi_t
https://wa.me/+2348064789370
_________________
_EPISODE 18_
"Sunday me yama zaka dake shi?" Husna ta faɗa sanda ta iso wajen.
"Heee Achalugo welcome." ta harare shi, cikin broken ɗin da har yau ta kasa iya wa tace "you want to put yourself in trouble abi? Wetin this man did to you?"
"Achalugo this madman ba hmmm, he just comes and carry my pure-water."
"Kuma shi ne zaka dake shi?"
Husna ta faɗa tana kallon mahaukacin dake tsaye har yanzu yaƙi tafiya, sai kuma tace "Nawa ne kuɗin ruwan na biya ka, kai wallahi ka fiya san kuɗi shi yasa baka kyauta baka sadaka." tayi maganar tana ciro kuɗi, Sunday ya washe baki yace "Naira Ashirin ne yasha ɗaya ga ɗaya a hannuna dana ƙwace."
Husna ta bashi kuɗin shi, Indo na tsaye a gefan su tana kallon ikon Allah, ɗayan ruwan ta karɓa a wajen Sunday ta miƙa wa mahaukacin yaƙi karɓa, saida ta sake miƙa masa tare da cewa "karɓi na baka kyauta, bazai dake kaba." sannan ya miƙa hannun shi da yayi busu busu da datti ga wasu zaƙo zaƙon farata masu tsayi ya warce ruwan ya juya Husna tabi bayan shi da kallon mamaki, dogone sosai dan a tsaye zai kai shararren jarumin Indian nan Phrabas (Bahubali) tsayi, saboda tsabar cikar da fuskar shi tayi da gashi ko kaɗan bazaka iya gane kamanin sa ba bare ka ƙiyasta shekarun sa, gashin kansa yayi yawa sosai yayi tozo babu kyan gani ya taho ya zagaye fuskar shi da saje mai yawa har gemun shi ya taru sosai yayi tsayi, gashin girar sa kuwa harta haɗe waje ɗaya itama tayi yawa wannan yasa ba'a iya ganin idanun shi, gaba ɗaya suma ta yiwa fuskar shi rumfa, bazaka iya gane asalin yanayin zubin jikin saba saboda wata ƙatuwar jallabiya dake jikin shi me dogon hannu dan tayi masa yawa, duk tayi baƙi da dauɗa, tsabar ɗaudar da tayi baka isa ka faɗi asalin kalar rigar ba, ƙafafun shi banu takalmi sai wani baƙin abu daya rufe kafarshi mai kama da safa, a tsaye ƙam yake tafiya cikin sauri da sassarfa, yana tafe yana gyaɗa kai kamar yaro. hannun shi ɗaya riƙe da wani farin sanda (Stick ) siriri kamar na masu matsalar ido.
Husna bata daina binshi da kallo ba har saida taga ya hau gefan titi ya miƙe yana tafiya, sai taji ya bata mugun tausayi, a can ƙasan zuciyar ta tace "Allah sarki ko ina yan uwan shi suke?"
Saida Indo ta taɓa ta sannan ta juyo ta kalle ta sai kuma tayi gaba ba tare data ce komai ba Indo ta biyo bayan ta suka jera suna tafiya a tare kamar yadda suka saba.
Suna tafe Indo na sake bata labarin mahaukacin.
"In faɗa miki Ma'u yau befi kwana biyu da zuwan shi garin nan ba, dan dai kwana biyu bakuyi abincin yamma bane shi yasa baki ganshi ba amma dakin ganshi, in faɗa miki tsirfa gare shi in fa mutane suka bashi sauran abincin da sukaci sadaka baya karba, amma in aka bashi sadakar kuɗi saiya karɓe kinga yadda ya warci ruwan da kika bashi ɗazu?"
Husna ta dagawa Indo kai alamar tana sauraren ta, ita kuwa sai taci gaba da faɗin.
"To haka yake karɓar kuɗi in aka bashi, kuma baya kula kowa baya faɗa, a can kusa da masallaci yake zama ko bayan rumfar Mutumin ki Bahari."
"Ikon Allah ko daga ina yake?"
Husna ta faɗa daidai sun zo wuce rumfar Bahari mai saida fetir ya fara tsokanar ta kamar yadda ya saba.
"Ma'u kwana biyu bakya abinci wai ko dai kin karye ne? Ki faɗa kawai in kin karye saimu temaka mu ɗora ki." Buhari ya faɗa yana dariya Husna ta zuba masa harara.
Indo tace "kawo jarin na kai mata gida."
Bahari yayi dariya yace "ki bata ko kisa a aljihun ki. Kawai kice ta dena mana ƙumi tazo na taimaka mata."
"Ai wallahi kasan nafi ƙarfin ka taimaka min nawa ne ɗan jarin man naka da har zaka ɗora wani?"
Husna ta faɗa tana banka mishi harara, tayi gaba Indo ta biyo ta da sauri, suka bar Buhari da dariya yana sake faɗar
"Ma'u ki sauke kai ƙasa na taimaka na ɗora ki." Shi kaɗai yake maganar yana dariya dan tuni Husna da Indo suka bar wajen da yake.
.....Kaf garin Bahari ne saurayi ɗaya tilo da suke shiri da Husna, shima ba asalin ɗan garin bane ta dalilin abokin shi Ya'u da suka haɗu a Lagos wajen neman kuɗi ya zo garin har ya fara saida fetir.
Kaf Samarin garin suna son yi mata magana, amma bata kula su, su Indo har sun fara zance.
Husna bata da saurayi ko ɗaya dan duk sanda Babanta ya zo inta rako shi waje zai tafi saiya ja mata kunnen yace kar ta sake yaji ta kula kowa, wannan yasa ko an aiko ana kiranta bata zuwa, Dije tayi ta zagin ta tana mata gori amma bata damuwa.
Hamisu (Ɗan Hajja) shi kaɗai ne saurayin daya maƙyale mata yayi ta cewa Samarin garin ita budurwa shi ce duk da bata taɓa kula shi ba, shi kaɗai yake kidan shi yayi rawar sa, haka zai zo har gida ya gaida Dije ya bata kuɗi ta amshe, duk dan Husna ta kula shi amma har kawo wannan lokacin bai ishe ta kallo ba, kuma tunda ya gane Dije mayyar kuɗi ce shike nan yake yawan zuwa ya gaishe ta ya bata kuɗi ita kuma tayi ta zagin Husna tana kozanta ɗan Hajja.
Har goro yake aiko wa Dije gida, da yake yaron akwai kuɗi a hannun shi sosai yake baza ƙarya da ƙafafar shi a gari, ƴan mata suyi ta binshi yana musu yanga shi sai Husna.
Hamisu da gaske ɗan Hajja ne dan uwar shi tana Makka kuma sosai take bashi kudi, yana cikin samarin dake fantamawa a garin har shago gare shi babba a tasha wanda yake saida kayan awu, haka kaf cikin garin shine mutum na farko daya ɗora ginin kwangiri (bulo da bulo) wannan gini da akaga ɗan Hajja nayi a garin ya sake siya masa mutumci da girma a idan mutane musamman kuma da yake yana da kyauta sam bashi da rowa, amma fa baya ji ko kaɗan saidai da yake yana da kuɗin shi kuma abinka da ƙyauye sai kaji shiru ko yayi wani abun ashshar ma maganar bata zuwa ko ina take mutuwa murus.
Da sallama Husna ta shiga gidan su tun daga nesa ta hangi mutanen gidan Zazzau ne amma bata gane su waye ba saida ta iso wajen sannan ta gane waye da waye a zaune dan yanzu bata iya gane waye a waje daga nesa saidai ta hangi alamar mutum amma indai bata matso kusa ba bata iya gane waye, kuma hakan ya faru da ita ne tun wani mugun ciwon ido da tayi mai wahalar gaske, sosai tasha wahala duk wani maganin ciwon ido da ake siyarwa a garin babu wanda batayi amfani da shi ba amma ido yaƙi warkewa daga baya sai Aramma
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 19 Chapter of 31