bai bari tunanin yayi tasiri ba ya kunna karatun Al'qur'ani yana cigaba da saurara .
bai son tuno wani abu da ya shafe ta , ita ɗin ai bata cancanta da kutsowa cikin tunanin sa ba ko kaɗan .
A hankali ta zame ta zauna a jikin ƙofar bayan shuɗewar ƙugin tayoyin motar sa bisa kan kwalta, ruwan saman na cigaba da sauƙa a jikin ta , kukan da take riƙewa tun shigarta motar ta saki da ƙarfi , kukan ha'incin da samy baby ta yi mata , kukan nadamar kuskuren da ta aikata a rayuwar ta, babu abunda take so a dai-dai lokacin irin ta buɗi ido ta ga falmata da mama a tare da ita , ta haƙiƙance sune kaɗai jinin ta a duniya sune baza su taɓa cutar da ita ba ,
Takurewa tayi a wajen tana karkarwar sanyin iskar ɗaukewar ruwan sama da yake busa ta .
Washegari
Samy baby tana tsakiyar baccin ta na tofon gira misalin ƙarfe goma na safe ta tsinkayo bugun ƙofar gidan ta tamkar a tsakiyar kan ta ,
Mummunan tsaki ta jaa , bayan ta miƙe tana haɗa maballan gaban rigar baccin ta , kan ta ko ɗan kwali babu ta fito , dai-dai lokacin da aka kaiwa ƙofar wani mugun bugu tamkar za'a ɓalla ta ,
Kai wai wanne ɗan^ yake ƙoƙarin ɓalla min kofa , tamkar na ci bashin sa ban biya ba ?
Ta furta hakan a tsawace tana ƙoƙarin zare sakatar ƙofar , bata gama zarewa ba ta ji anyi ciki da ita da ƙofar , tayi baya taga-taga ƙiris ya rage ta faɗi ,
A fusace ta ɗago kan ta hannun ta dafe da goshin ta , da ƙofar ta buga
Kutumelesi ,....
Kar ki yadda ki zage ni tsohuwar ƴar damfara , kuɗaɗena na zo ki mayar min da su account , saboda ƙaramar ƴar iskar da kuka haɗa baki kuka damfare ni tun daren jiya ta gudu , dan haka ko naira ɗaya ban yadda a samu giɓin su ba a cikin kuɗina ki dawo min da su yanzu-yanzu .
Wani irin fargaba ne ya dirarwa Samy baby , me Kamal yake cewa ? Yakaka ta gudu ?
Da kƴar ta tattaro guntuwar nutsuwar ta ,
Ta juƴa ta fara taku tana cigaba da murza goshin ta ,
Kamal ka shigo muyi magana a ciki , zancen ba na tsaye bane ,
Ke duba Samira ba inda zan shiga kawai kuɗaɗen nan zaki dawo min da su domin ko hannun ta bata yadda na taɓa ba tayi tafiyar ta tun jiya , bayan wahalar neman ta da ta saka ni cikin ruwan sama ƴar^ ke daman kin san yarinyar nan wata gara ce irin haka har zaki karɓi kuɗina akan ta ? Yi sauri dallah ki dawo min da su , da akwai inda zan tafi daga nan bani da lokacin ɓatawa .
Kallon ba yadda zan yi Samy baby take bin Kamal da shi , ta fahimci a bugen sa yake tatil kamar koyaushe , idan har ta nemi yin gardama kan zancen kuɗin nan kome zai iya faruwa da ita ,
Bani account number
Ta ce masa tana shigewa ɗaki ɗauko wayar ta , daga ƙasan ran ta take jin mummunan ɓacin rai na taso mata akan abunda Yakaka tayi mata , ashe rashin mutumcin Yaks har ya kai haka ? Ta gudu ta jawo mata irin wannan babbar asara ? Allah ya so bata riga ta kacan-chala kuɗin nan ba da yanzu yaya zata yi da tijarar Kamal ? Tabɗi dole ne ta ɗau mataki akan Yaks , ta nuna mata kuskuren ta saboda gaba kar ta sake gwada mata irin wannan mugun wasan .
Cikin mintoci biyar Samy baby ta ɗibga asarar Naira miliyan biyun da suke mallakinta daga jiya zuwa yau , har gumi ne ke tsattsafo mata , lokacin da ta koma falo ta zauna bayan tafiyar Kamal da bai bar gidan ba sai da miliyan ɗin sa biyu ta koma account ɗin sa .
Ina Yakaka ta kwana ? Shine tambayar da Samy baby take yiwa kanta ,
Zumbur ! ta miƙe tsaye lokacin da ta ayyana inda Yakaka ta kwana , gidan Malama Maryam .
Ɗan siririn mayafinta da yake ajiye a falon shi ta ɗauka ta yafa akan rigar baccin jikin ta , ta fito a fusace bayan ta rufe ƙofar gidan da makulli ta zagaya layin bayan su kai tsaye ta doshi gidan malama Maryam da tunda take sau ɗaya ta taɓa taka gidan , Sai fa yau da zata kuma zuwa .
Ko sallama bata yi ba ta danna kai cikin gidan , ilai kuwa tana shiga falon ta tadda Yakaka tana zaune ta jingina da jikin ɗaya daga cikin kujerun falon da farantin cin abinci a gaban ta wanda bata kai ga sa hannun cikin sa ba .
Da shigowar ta Yakaka ta miƙe da alamun firgici a fuskar ta wacce ta ɗan kumbura kaɗan tayi jaa ,
Anty Samy ..
Da hannu ta dakatar da ita , ki min shiru Yaks , ashe baki da mutumci haka daman? Ƙyat ! tayi Kwafa ki wuce mu tafi gida inason yin magana da ke .
Malama Maryam wacce tashin muryar Samy baby ya sanyata fitowa daga cikin ɗakin ta , ta ƙaraso wajen tana bin Samy baby da kallon nazari
Yayar Yakaka lafiya dai ko ? Anan Yakaka ta kwana tun jiya cikin dare take ta kuka taƙi sanar da mu abunda ya sameta , dan Allah idan laifi tayi miki kiyi haƙuri ki yafe mata
Wani kallon banza Samy baby ta jefawa Malama Maryam saboda ta fara fahimtar duk wani taurin kai da take hango alamun Yakaka zata gwada mata har da taimakon koyarwar Malama Maryam wacce ta lura duk wasu sabbin ɗabi'un Yakaka daga gurin ta ta kwafe .
Ki wuce mu tafi
Ta sake maimaitawa tana mayar da duban ta kan Yakakar
Da wani irin yanayi cikin muryar Yakaka , wanda yake fallasa halin baƙin cikin da zuciyar ta ke ciki , tace
Bazan bi ki ba Anty Samira ni daga nan Maiduguri zan koma wajen Falmata da ƴa ta , bazan taɓa yadda nayi yadda kike so nayi ba . BAZAN SAKE YIN ZINA BA
Kif-kifta ido Samy baby tayi tamkar bata ji da kyau ba ,ta karkata kai tare da ɗage shi sama ta ce :
Kika ce me Yaks ?
Bata jira ta amsa mata ba ta ɗora da cewa .
Maiduguri ?? Sai ta kwashe da wata gajerar dariya ,
Wa kika sani a Maidugurin ? Waye naki a can wa kike da shi a duniya ?
Da sauri Yakaka ta amsa mata har muryar ta na sarƙewa
Ƙanwata Falmata da ƴata Mama !
Hahaha !
Yaks kenan ai Falmata da ƴar jaririyar da kika gudu kika bari duk sun riga sun mutu , au ashe ban faɗa miki ba ko ? Sorry lokacin kina tsaka da jarabawa ne kin san fa ke mayyar karatu ce ...
Kukan kurar da Yakaka tayi ta tura samy baby ta faɗa kan kujerar bayan ta , ta hau ɗare-ɗare kan ta , tare da maƙure mata wuya shi ya hana samy baby cigaba da zancen da ta shiryo shi a yanzu ,
Me na miki Anty Samira ? Me na miki ? Ƙarya kike min koyaushe Ƙarya kike min baki taɓa faɗa min gaskiya ba Ƙarya kike Falmata na bata mutu ba , Ƙarya kike yi bata mutu ba , ki faɗa min gaskiya me kike shiryawa game da rayuwata ? Me na miki ?
Da taimakon Malama Maryam suka ɗaga Yakaka daga kan Samy baby wacce duk Yakaka ta yakushewa wuya , gabaɗaya ta birkice musu kamar me tashin Aljanu , ihu kawai take tana cewa
Falmata bata mutu ba ƙarya ne ,
Addu'o'i Malama Maryam take tofa mata tana riƙe da ita ,
Bata cikin hankalinta ta ɗago kan ta hawaye wani na korar wani a fuskar ta ,
Ummi , ki kaini Maiduguri yanzu-yanzu dan Allah , ki kaini naga Falmata
Zan kai ki Yakaka ki nutsu ki daina wannan ihun babu kyau , kiyi innalillahi wa inna ilahi raji'oon , kiyi addu'a ki bar kukan nan haka .
Gƴaɗa kai take ba domin tana fahimtar kalmomin Malama Maryam ba , bakin ta ya gaza furta kalma guda illa karkarwa da laɓɓan ta ke yi , zuciyar ta ke wani irin bugu da tsananin tsoron da yake barazanar tarwatsa mata zuciya , kalmar Mutuwa ga Falmata tayi mata tsauri da girma ta yadda zuciyar ta gaza ɗauka , tunanin ta ya guntule cikin rashin sanin takamaimai a halin da take ciki , ƙiyayyar samy baby sabuwa fil take yaɗo cikin ran ta .
Da baya-da-baya Samy baby ta ƙarasa barin falon tana jin yadda tsoron halin da ta ga Yakaka a ciki na cika mata zuciya ,
Niamey Niger
Cikin makonni uku da ƴan kwanaki visa Falmata da Mama ta fito , Biyamuradi Youssouf bai jinkirta ba wajen fara shirye-shiryen tafiyar su , bayan ya ɗauki hutun sa na kwanaki talatin a wajen aikin sa , tare da gudurtawa cikin ran sa idan kwanakin sun gaza wajen yin abunda ya kai su , zai dawo ya rubuta takardar neman iznin hutu batare da biyansa albashi ba ya koma .
Cikin satin zuwan sa Maradi sau biyu , bayani sosai ya tsarawa Maimartaba tare da hajiya Umma kan cewa aiki ne zai kai shi zouwa ƙasar Amurka ,
Babu shakku cikin ran su suka masa addu'o'in samun nasara kan abunda za shi nema , tare da fatan dawowa lafiya .
Bangaren matan sa ma bai samu matsala da Siyama ba , wacce take da tsananin yarda ga mijinta , dan haka ta hau shirya masa ƴan kayan cimaka da zai iya yin guzurin su zuwa ƙasar da za shi , zuciyar ta cike taf da kewar sa da ta fara tundaga yanzu , lokaci-lokaci tana sharar ƙwalla rabuwa da masoyi duk da cewa ba sabon abu bane shafe kwanaki masu yawa irin haka basu tare , amma haka kawai taji wannan tafiyar tasa ta tsaya mata a zuci ko domin ƙasar zai bari bakiɗaya zuwa wata nahiyar ?
Ga Gimbiya Maimounatou kuwa sam bata gamsu ba da zancen barin sa ƙasar , hasalima batun tafiyar sa ya kawo mata tsaiko ne kan wani Al'amari da take ɗorarwa akan sa , sai take ganin tamkar da gayya ya tsiri tafiyar ,hakan ba kome bane face salo ne na kauda-bara da ya sha faruwa a duk lokacin da take kan gaɓa na son cimma ƙudirin ta , sai dai baza ta fasa ba , ba kuma zata gaza ba wajen cigaba da bibiyar kome a sannu har sai haƙar ta ta cimma ruwa .
Dan haka babu ƙarsashi a tare da ita suka yi bankwana bayan ta haɗa masa ƴan nata kayan cimakan da basu cika yawa ba saboda zuciyar ta da take shaƙare da takaici , duk da cewa tayi iyakar ƙoƙari kamar yadda ta saba ta boye abunda ke binne ƙarƙashin ran ta .
Daga Tafeeda kaɗai ya so samun tangarɗa wanda yake da sani sosai akan harkar aikin su , ya kuma titsiye Biyamuradin da tambayoyi akan aikin da yace zai kai shi US , sai dai ga mamakin sa hanya-hanya da zamiya iri-iri Biyamuradi ya dunga yi masa da ya hana shi sanin takamaimai gaskiyar lamari game da tafiyar ta shi ,
karshe dai ya fahimci babu shakka akwai abu me girma da Aminin sa ke ɓoye ma sa wanda kuma lalle wannan abun ya shafi rayuwar sa ta kurkusa , sai ya ɗiga ayar tambayar . Cikin ran sa ya ƙudurci bin diddigin kome .
Duk wani shirin tafiyar su ya kammala , kamar yadda Biyamuradi ya Alƙwarta ga Hajja , ya ƙira direban da zai kai ta ana washegarin ranar tafiyar su , ya sanar da shi gobe da safe ya zo su kama hanyar Nigeria da Hajja .
Jakar matafiya karama da Babba Ya kawo musu ,
Ya miƙa Babbar ga Hajja , yana cewa
Hajja ga wannan jakar ki shirya suturun ki ciki , wannan ƙaramar kouma na Fatima ne , kayan ta kaɗan zata ɗauka ba wasou masou yawa ba kawai aboubouwa masu muhimmanci da zata iya bouƙata su zata zouba a ciki, ita kouwa Mama ba sai an ɗauka mata wasu suturu ba , kaya biyu kawai sun isar mata idan munka kai can duk za'a saya wasu suturu sabouda yanayin mu da nasou ba ɗaya bane .
Au Babban soja wai da ni har mun shirya kayan a cikin manyan akwatuna ? Fiye da rabin kayan nasu ma ai mun loda su a akwatuna har huɗu , ashe tafiyar ba ta guzurin kaya bace ikon Allah .
Ɗan murmushi yayi , a ah hajja a ajiye waɗannan suturu a gida zamu sayi wasu a can .
To ai babu kome , huta-roro ( waken gizo ya ƙi 'Ya'ya ) wannan babu neman masu dakon kaya a tashar jirgin sama , oh duniya kullum cigaba ake watau ita turai ba'a zuwa da kayayyaki dayawa ? Dayake ma can gidan kaya ne , kamfaninnika ne da su na suturu sai ka zaɓa ka darje , kuma fa irin atamfofin nan namu arhar bulus ne da su a can ko Babban soja ?
Cikin gundura da hirar hajja , yace
hajja ai can basou sanya tufafi hakka irin namou , su suturun su duk kananun kaya ne sai kouma kayan sanyi ,
Firfito da idanu tayi bayan ta rafka tagumi fuskar ta cike da alhini ta ɗora da :
Ƙananun kaya ni hauw'u ? Da kai da Falmatar watau duk ƙananun kaya za ku dunga sawa ? O'o ana bariki a turai , to ita dai Mama ku dunga suturtata da kyau saboda yanayin lafiyar ta daman ba kumari ta cika ba . Kai tir da rayuwa da ba ta Musulunci ba
Sai kuma ta ɗan saki murmushi tunowa da tayi da wani abu ,
Kuma ka ga ƙananan kayan zasu amshi jikin ku Babban soja , musamman ma ita Falmata , ƴar riga da wondon nan na zamani ka daure ka saya mata ɗanɗasa-ɗanɗasa ba ƙaramin haska ta zasu yi ba .
Ɗan zunkuɗawa yayi akan kujerar jin an taɓo masa inda yake masa ƙaiƙayi ,
Hajja ina Fatima tare da mama sun ka tafi tun shigowata ban ji motsin su ba ,
Nan suka shiga gidan su Zainaba ta je ayi mata kitso da kunshin tafiya . Ai tana gaf da shigowa ma .
Ƙunshi kuma hajja ?
Tafiyar mu ai ta neman lafiya ce hajja ba'a buƙatar duk irin wannan shirye-shiryen ,
Ta gefen ido hajja ta dube shi , Babban soja ai shi ƙunshi ado ne ga ɗiya mace ...
Sallamar Falmata ita ta hana ta ƙarasa zancen ,
Da gudu mama ta saki hannun Falmata da take yiwa jagora ta nufi Baban ta
Papa bienvenue , ta ƙarasa shigewa jikin sa da ya buɗe mata hannunwan sa , ta kwantar da kan ta a ƙirjin sa , ya shafi kan ta yana sauƙe idanun sa akan Falmata da take ƙarasowa wajen jikin ta sanye da dogon hijabin ta har ƙwauri ta zauna daga ƙasa a gefe ,
Sashin da take hasashen yana wajen ta fuskan ta cikin nutsuwa ta gaishe shi fuskar ta kadaran-kadahan .
Ya amsa yana bin fuskar ta da kallo da kitson da aka mata ya sake fiddo ƙyallin fatar ta tare da bayyana hasken goshin ta ,
Hajja wacce bata zama a tsakanin su ta yunƙura ta miƙe riƙe da jakankunan a hannu ta nufi ɗaki , tana ƙiran mama wacce tayi biris da ita taƙi amsawa sai ma sake lafewa da tayi a jikin baban ta .
Fatima ya shiri ? Kin kammala kou ?
Eh mun kammala tace
To madallah gobe insha Allah zamou tafi ku zama cikin shiri kin ji kou ?
Toh ta amsa tana gyaɗa kai !
Shiru ne ya ɗan gitta tsakani , kafin mama ta ɗago kan ta daga jikin Baban ta ,
Papa , an mana kitso ni da Mamaa na ka gani yayi chau ?
Ta janye hular kan ta , manyan kitson chuku da aka mata suka bayyana , duk da kitson manya-manya ne amma sun yi kyaun zane kasantuwar ta me yalwar gashi sai ya ƙarawa kyaun kitson armashi .
Shafa kan nata yayi yana murmushi yace ,
wow c'est très beau ,
Da dariya ta bar jikin sa ta nufi Falmata tana zuwa ta fara kici-kicin buɗe mata kai ,
Mamaa ke ma ki nunawa papa kitson ki , yafi nawa ma chau ko papa ?
A hankali ya gyaɗa mata kai yana jingina bayan sa da jikin kujerar ba tare da ya janye ganin sa daga kan su ba ,
Ture hannun ta Falmata tayi ta ɗan ɗaga sauti ,
Ki bari mama ba na hana ki buɗe min kai ba ?
Ba tare da ta sauke hannuwan ta daga kan falmata ba tace
Ai papa ne zai gani .
Tsawa tayi mata lokacin da take son ta sauƙe mata hijabin a tilas ,
Firgita tayi ta ja baya ta rakuɓe tana ƙwalan-ƙwalan da ido tare da raba kallon ta tsakanin mamar ta da baban ta ,
A hankali wasu siraran ƙwalla suka silalo daga gurbin idanun ta ganin an mata abunda ba'a saba yi mata ba ba kuma tare da an rarrashe ta ba ,
Cikin ran ta taji shirun da tayi tare da sanin manufar sa , dagulewar zuciyar ta ya zo dai-dai da zubar hawayen Mama ,
Hannu ta ɗaga ta fara lalubar inda take jin tashin shisshiƙar kukan ta , ta jawo ta jikin ta tare da ɗaura ta akan cinyoyin ta ,
Kwantar da kan ta tayi da ƙarfi a jikin mamar ta gami da fashewa da kukan da tayi tanadin sa ,
Kamar ruwan maɗaci haka take jin ɗacin sautin kukan ta daga cikin zuciyar ta, dan haka ta fara aikin lallashin ta ,
Hannu ta kai ta zame hajibin nata , ƙananan kitson da aka mata yir-yir suka bayyana
Ta karya murya cikin kuikoyon muryar mama tace :
Papa ka ga kitso na yayi chau ??
A hankali ta ɗago kan ta daga jikin ta idanun ta jage-jage da hawayen rikici , ta washe ƴan haƙoran ta lokacin da take kama dogon jelar kitson shade ,'( me hawa biyu ) da aka tufke shi ya sauƙa kan dokin wuyan ta , ta waiga tana duban Baban ta wanda duk abunda suke yana bin su da ido ,
ransa cike taf da ƙauna tare da shauƙin soyayyar dake tsakanin uwa da ɗiyar ta .
Muryar ta kamar ba ita ke kuka yanzu ba tace ,
Papa ka ga kitson mamaa na yayi chau ko ?
Yunƙurawa yayi ya matso sosai gaban kujerar da yake kai ,
Yana ƴar dariyar yadda fuskar falmata take a ɗaure tana wani takurewa yace ,
Ai tayi nissa daga can bani ganin kitson nata , ta matso nan kussa na gani kou ? Ya ƙarasa zancen yana karya wuya .
Eh Mamaa ki zo ya gani ,
Ta jawo hannun Falmata , gudun rikici ya sa Falmata ta biye mata ta taso ta biyo ta , gaf da ƙafafun sa Mama ta zaunar da ita ,
Idanun sa ya sauƙe akan kitson da suke yir-yir kamar inji ne ya jera , ƙwarai kyaun kitson ya birge shi .
Basu yi aune ba ta jaa hannun Baban ta ta ɗora akan Falmata ,
Papa ka ga ni ?
Ta ce tana washe masa haƙoranta .
Kasa janye hannun nasa yayi daga kan ta , saboda wani irin yanayi da yake ji yana zagaya illahirin jikin sa ,
Tundaga kan yatsar kafar ta taji tashin tsikar jikin ta , da wani yanayi da ya tsinka gudun jinin jikin ta , irin yadda bata taɓa ji ba a rayuwar ta , bakiɗayan jikin ta babu kuzari ,
Ganin shirun su ya tsawaita ya sa Mama ta raba ganin ta a tsakanin su , kafin ta ɗan turo baki ,
Papaa , baka ce kitson mama yayi kyau ba ??
Cikin dai-daita nutsuwar sa ya janye hannun sa daga kan ta ya janyo Mama Zuwa jikin sa ,
Kitson Maman Mama yayi kyau sossai
très belle .
Batare da ta ƙara daƙiƙa guda ba ta miƙe , tana nufar hanyar ɗakin hajja , zuciyar ta na cigaba da tsananta bugu , cikin kowanne takun ƙafafunta take jin idanun sa na yi mata rakiya .
9:30pm
Falmata ta sake muskuɗawa tana rufe bakin ta daga gajerar hamma da take yi akai-akai saboda bacci da ya fara cin ƙarfin ta ,
Ita bata kaiwa dare sosai take yin bacci a yawancin lokuta ƙarfe takwas da rabi na dare sun yi bacci ita da Mama , shiyasa yau da hajja ta buƙaci son suyi magana ta zo kuma ta tadda ta tana shafa'i da wutiri , bayan ta idar kuma ta ɗora da addu'o'i , duk sai zaman jiran ya gundure ta bacci yake kawo mata samame ,
Falmata , Falmata . Ko kin yi baccin ne ?
Na'am hajja idona biyu .
To taso ki zo nan kusa da ni magana nake so muyi ,
a hankali ta taso ta taho inda take jin tashin muryar hajja ta zauna daga gefen ta bisa dardumar sallah .
Fatima ki nutsu da kyau ki saurareni , da kunnen basira , kin ga wannan tafiyar da za kuyi ke da Mijinki tamkar wata babbar dama ce Allah ya baki da za kiyi ƙoƙari ki dai-daita zaman ku ke da shi , ki ƙarbo martabar ki ta ɗiya mace , cikakkiyar matar aure , ke yanzu ba yarinya ƙanƙanuwa bace ba , da za'a zauna ana yi miki bayani dalla-dallah baƙi da fari akan aure , shekaru biyar ana cikin na shida da yin auren ku , lokaci yayi da yakamata ku kawo ƙarshen wannan zaman kai da ƙafar da kuke yi a tsakanin ku , ku haɗa kai ku rungumi junan ku cikin inuwa da alfarma irin ta aure ,
Ke kece mace bance ba ki bada kan ki ba , amma ki yunƙura kiyi hoɓɓasa cikin dabarun ki na ɗiya mace da Allah yayi miki baiwa da su , ki karkato da hankalin mijinki kan ki , tunda jajayen sawun ki , da sauran damar ki , kina kuma tare da makaman yaƙin da zasu taya ki karɓo kambun ki tun kafin damar ki ta kufce miki , futsanci , jin kai , halin ko inkula da miji ba naki bane , yanzu anwuce wannan zamanin , zamani ne muke ciki na tarairayar miji a gatata shi ta yadda za'a masa riƙon tsauri da kufcewa zata masa wahala , kin dai ji na faɗa miki .
turai zaku je , kiyi ƙoƙari ki sau jiki , ki shige masa , ƴan kananun kayan nan da yace ana saka su a can ki sa ya kawo miki su dayawa kullum ki dunga yi masa ado da su , daman ga ki da kyakkyawan jiki.....
Ƙananun kaya fa kika ce hajja ?
Falmata ta katse ta tana yamutsa fuska .
Eh su nace to meye ba mijinki bane ? Wani ma yayi rawa bare ɗan makaɗi ? Cewa nake kowa a garin su yake sawa ? To ke meye laifin ki idan kin yiwa mijinki ado da su ? Ji min rashin wayo .
Ta mula kafin ta cigaba da cewa :
Ƴar rangwaɗa da kisisina irin ta mata dunga yi masa , ki raba kan ki da ƙwalafacin Mama ki fara tunanin hanyoyin da za ki bi ki faranta ran mijinki saboda kin ga dai dai-dai gawargado shi yana nuna miki kulawa ke kece kike ƙin bada haɗin kai , to ki sake zane tun dundumin ki da danshi , shi mijin mace huɗu ne .
Ga ƴan magunguna nan na karɓo miki su musamman a wajen uwar zainaba , ta tabbatar min da ingancin su su ma zasu taimaka miki ƙwarai da aniya .
Anya hajja idanun nawa kuwa magungunan nan zasu min aiki ? Amma dai ba na sawa a ido bane kin san fa a asibiti sun hana ni zuba magani
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 56 Chapter of 103