daga falon farko suka dakata ,
Ita ɗaya ta taka zuwa Falon gaba inda ta tarar da Mairamar sarki tare da Siyama suna karin kumallo , kallo ɗaya Aisha Mairama tayi mata ta mayar da kan ta gefe , Fuskar Siyama kadaran-kadahan ta gaishe ta , ita ma tata fuskar babu fara'a ta amsa tana mayar da ganin ta kan Aisha da tayi tsam daga barin cin abincin da take , kafin tayi magana Aisha ta gaishe ta lokaci ɗaya ta miƙe zuwa cikin ɗakin Umman .
Ita ta yiwa Hajiya Mama iso ta shiga wajen Hajiya Umma .
Bayan gaisuwa shiru ne ya biyo bayan ɗan taƙaiccen zaman da suka yi kowacce tana saƙa a zuci , kafin Hajiya Mama ta gama auna kalmomin da take tafe da su da zummar ajiye su a muhallan da suka dace tace
," Sai kuma wannan lamari mai cike da sarƙaƙiya ya faru ? Wannan yarinya tayi ƙarƙon kifi , ta ɓata nasabar ta , ai kome kyaun nasabar macce muddin bata da hali kamar zoben zinariya take a hancin alade, shiyasa fa ni ban fiye zaƙewa wajen tsantsame zuri'a tafannin auratayya ba, wannan ƙwarya ta bi ƙwaryar bata cika yin ƙarƙo ba sai ki ga anyi gamdakatar da bara gurbi , amma ɗiyan saraki masu son tsalkin nasaba basu gane ba , ai ga irin ta nan Allah dai shi taƙaita , yaya shi jikin Youssoufa? Ya fa kamata ayi wani abu kan Yaron nan Mammadou sabbada kowa ya shaida sharri ne wannan ɗiya take yi masa .
Tunda ta fara maganar Hajiya Umma bata dubi sashin ta ba tana a kishigiɗe yadda take , ɗaya bayan ɗaya kalmomin Hajiya Mama suke sukar zuciyar ta tare da bijiro mata da mummunan fushin da take ƙoƙarin tausa zuciyar ta ta danne kamar yadda ta saba haɗiye dayawa daga cikin munanan abubuwan da Hajiya Mama ta sha yi mata ko a kanta ko akan 'ya'yan ta .
Fuskar ta na bayyana fushi mai tsanani ta miƙe zaune lokacin da zuciyar ta gama aiyana mata "shi fa maƙaho bai san ana kallon sa ba sai an haɗa da zungurin sa,
" Saratu ki dakata daga waɗannan maganganu naki marasa tushe da makama , shi wawa bai san zuru ba sai ya tsinka , ki sani cewa duk wasu kaidi da makirce-makice hadi da ja'iba da ta'annakin da kike bibiyata da zuri'a ta da shi ina sane , ina sane nasan kome tun kafin yau , na yi miki shiru ne saboda nasan shi munahinci dodo shike , muguntar mutum kuma ita ke kawo hallakar sa har inda yayi zaune yana kitsa sharri, sannan akwai ranar da hadari zai taso tare da guguwar da zata wargaza mugaye .
Cikin tsakar idanun Hajiya Mama da ta tsare ta da ido ta kai duba suka yi musayan kallo ,
Ɗan guntun murmushi tayi kafin ta cigaba da cewa ,
"Saratu kika ce akwai aibu cikin tsantsame zuri'a ? To ai rashin tsantsame zuri'a yasa kin ka kawo matsayin da kike bisan sa a yau , rashin tsantsame zuri'a yasa kin ka zama muguwar uwa mai kitsa sharri , Matar kirki 'yar Nasaba da ita Miji ke fariya yana ado da ita tamkar rigar silki , amma Annamimiya mai haɗa bakin wuta a tsakal gida ita ke saka shi cikin ɗimuwa ta dauwamar masa da shiga kunya da baƙin-cikin da har abada zai kasa samun farin-ciki da ita .
" Ya isa Hajiya Safiyya dan na tako na zou shiyar ki ba shi zai baki damar da za ki ci mutunci na ba , Hajiya Safiyya babu yadda za ki iya da ni , banbancin nasaba da ki ka ɗau shekaru kina ɗaga shi sama kina tutiya da shi bai isa ya sauya mana daidaituwar matsayi ba a cikin gidan nan kuma ko kin ki ko kin so Inkiya ta ita ce Gimbiya Matar Sarki .
Tana huci ta miƙe tsaye ta fara taku tace " na zo nan ne dan na sanar da ke ki sa a gaugauta sakar min ɗa ya dawo saboda ina da masaniyar ke kika sa aka cigaba da garƙame shi ba tare da ya aikata laifin kome ba .
A tsakanin kwanakin da suka biyo baya Bilal da Ubbo tare da Maigidan ta suka tafi india , washegarin tafiyar su kuma Tafeeda shima ya juyo , saboda yanayin aikin sa da bazai bar shi ya cigaba da zama ba a can .
Bayan an gama zaman fada da Maimartaba ya tsawatar akan hana cigaba da batun abunda ya faru da Youssoufa , aka fuskanci abunda ya shafi fada da al'amuran ta kaɗai ,
A daren ranar misalin ƙarfe takwas saƙon ƙira daga Maimartaba ya riski Tafeeda , babu ɓata lokaci ya cimma turakar Maimartaba ƙarƙashin jagorancin jakadiya .
Bayan ganawar da bata wuce mintoci talatin ba Maimartaba ya masa iznin tafiys bayan ya samu duk wasu bayanan da yake son samu daga wajen sa .
Duk da cewa Hajiya Mama ce take da turaka a ranar amma kasantuwar buƙatar ganawa da Hajiya Safiya ya taso yasa Maimartaba aika jakadiya ta masa ƙiran Hajiya Umma .
Lokacin da saƙon ƙiran ya samu Hajiya Umma tayi mamakin Ƙiran nasa sai kuma ta cika da fargabar ko dai wani lamarin ya afku ?
Batun da Maimartaba ya zo mata da shi a lokacin da ta isa turakar sa ya busar mata da maƙwallato , da wani irin yanayi cikin muryar ta tace ,
" Ranka ya dade amma sai nake ganin rashin dacewar Yarima ya cigaba da riƙon amren ɗiyar nan ta Nigeria , wacce ba'a ma kai ga sanin matsayi da tushen ta ba , Ranka ya dade a duba wannan lamarin ayi duba da yadda wannan ɗiya ta agades tazo da ha'inci ita wacce ma take da tsarkin Nasaba ɗiyar girma , ina ga kouma ita wannan da take tsintattar mage a yadda labari ya iske mu ko a can Nigeria basu da wata nasabar da za'a iya haɗa jini da su , ba'a ma san dangin su ba 'Yan Gudun Hijira ne kaddarar rayuwa tare da maƙirci irin na maƙiyan mu ne kawai ya haɗo kasantuwar su tare da ɗan mu me zai hana kawai a raba wannan Amren ?
Cikin tsanaki Maimartaba yake kallon ta har ta gama zantukan ta tayi shiru ,
"Safiyya , ya ƙira sunan ta yana gyara zaman gilashin ƙara karfin gani idon sa .
" Na'am , ranka ya dade ta amsa tana mai kaucewa haɗuwar idanun su , cigaba yayi da cewa
"Yanzou ashe abunda ya faru bai isa zamar miki ishara ba ? Bai isa miki nuni da cewa kyaun nasaba bai nuni da kyaun ɗabi'a da cikar mutuntaka ba ? Bai isa sanar da ke cewa halin ƙwarai baiwa ce da ubangiji ka iya bayarwa ga bayinsa tsakanin talakawa da masu kuɗi , masu mulki da bayun su Iyaye kouma su taya wajen ƙarin gyaruwar halayya da taimakon gwargadon irin kyaun tarbiyyar da suka yiwa ɗiyan su .
"Nasaba ba ita ke tsalkake mutum daga aikata halin banza ba , shi halin Mutum mallakin sa ne daga lokacin faruwar halittar sa da bai da wata alaƙa da wata Nasaba ko ni'imar rayuwar da zai zo ya taras nan duniya .
" Domin ɗiyar Nasaba tayi zalunci bai nufin ɗiyar ƙananun mutane tayi fiye da munin abunda ta aikata mai yiwuwa ne ita ɗiyar talakawan ta bayar da mamaki wajen zuwa da ɗabi'u mafiya kyau wajen ƙwaiƙwayo , wannan ɓangare ne na baiwar Ubangiji kamar yadda na shaida miki , dan haka umarni nake bayarwa kan a tai a zo da ɗiyar da Youssoufa ke amre dagga Nigeria ta kasance ƙarƙashin kulawar mu kafin dawowar Mijinta hakan shine zai nuna cikar ƙima da darajar mu , sam ba dattaku irin namu bane mu bar ɗiyar mutane dauke da amren ɗan mu can a ƙasar su batare da sanin halin da take ciki ba , ba'a kuma sanar da ita halin da Mijinta ke a ciki ba da hakkinta ne ta sani .
Hajiya Safiyya da tayi zugum tana jin sabon damuwa na mamayar ta Allah ya sani bata son cigaba da kasancewar yarinyar nan a matsayin surukar ta ita da son ran ta ne Siyama kaɗai ce zata cigaba da zama a matsayin matar auren Youssoufa , ta ƙuta sannan tace ,
" Ranka ya daɗe a halin da Youssoufa yake ciki yanzou babu tabbacin ko yana son cigaba da zama da yarinyar nan tunda ka ga kou Siyama ai....
" Safiyya ta ban san ki da gardama ba kar kuma ki sakayo ta cikin ɗabi'un ki a yanzou , Youssoufa yana son matar sa duk kouma tunane-tunanen da kike yi kiyi watsi da su domin zai zo miki da saɓanin su , dan haka kamar yadda nace a shirya tafiya a zaɓi mutanen da suka dace cikin matayen da zasu tai Nigeria dole ya zama da na jiki ne sosai zasu yi tahiyar nan , sannan a tanadi kome da ya dace domin zouwa tahowa da ita , a yi kome cikin girma idan ta iso a mata masauƙi a sashin ki kussa da ke daɗa ita ɗin ai ɗiya ce Mai girma a wajen mu , Waziri shi zai jagoranci tafiyar tare da shi da Ɗan Malikin Maradi da wasu zaɓɓaɓu amintattun fada.
Kallon ba yadda zan yi Hajiya Umma take bin Maimartaba da shi har ya gama jawabinsa da cikin muryarsa ta fahimci a tsaurare yayi maganar cike da sautin umarta dan haka bata da wani zaɓi sai yin yadda yace , sai ta miƙe a hankali bayan ta ce " Ranka ya dade da yardar Allah yadda kace haka za'a yi .
MAIDUGURI-NIGERIA .
Fatima , ta ji ya ƙira sunan ta can a ƙasan maƙoshi ,
"Na'am ta amsa tana ɗago kan ta da ta kwantar a ƙirjin sa ,
" Ranar da duk za ki haihu tare zamu yi naƙuda kiyi rabi nima nayi rabi kin ji ko ?
Murmushi mai sauti tayi tana mayar da kanta ta kwantar "Daman ana yin haka ? Ta tambaye shi ,
"Nima ban sani ba Fatima , sabbada duk ɗiyana biyu bana wajen lokacin haihuwar su , amma wannan ya furta hakan lokacin da yake kai hannun sa marar ta ya shafa , "tare zamu yi haihuwar sa , ɗiyana ko ɗana zasu safko a hannuna idan macce ce kin san sunan wa zan sanya mata ?
A hankali ta girgiza kai yace, "Rahamatullah , sabadda haɗuwata da Mahaifiyar ta Rahama ce mai girma Allah shi yi min , Idan kouma ɗa Namiji ne ?, shiru yayi kaɗan , da yasa ta ɗago kan ta tana leƙen fuskar sa , wani irin farin-ciki kalamansa suka ɗarsa a ran ta ," dagaske yake ita tamkar Rahama ce a wajen sa ?
Sumbatar goshin ta yayi a hankali yace " na bar miki zaɓi Fatima ke za kiyi masa zaɓin sunan , wanne suna za ki sa masa ?
Hannun ta da yake kan ruwan jikin sa ta matsar ta lalubi hannun sa ta haɗe tafukan su waje guda kafin ta sarƙe ƴan yatsunsu cikin na juna kamar mai raɗa tace " Babana .
Hannun Yakaka da ta ji ya taɓa fuskar ta shiyasa tayi firgit tana kirkiro murmushin yaƙe , ganin ta ta mayar inda wasu ma'aurata dake zaune suke ta zuba soyayyar su Mijin sai tarairayar matar sa wacce take ɗauke da ƙaramin ciki yake yi kamar zai tayata ɗaukar cikin ita kuma sai zuba shagwaba take tana daɗa narke masa , wayam ta ga basa nan da alama sun shiga wajen likita .
tun zuwan su Asibitin da yau zata fara awu da Yakaka tare da Amnee suka rako ta Amnee ita tayi duk wasu kai kawon da bai cika wahala ba kasancewar Asibitin private ne yasa nan da nan ta buɗe mata file tare da biyan duk wasu kuɗaɗen da aka buƙata sannan aka turo su gurin likitan da zai dunga ganin ta .
mata Uku kawai suka tarar da a wajen , biyun tare suke da Mazajen su sai ita da wata mata wacce da gani ba haihuwar fari bace sune kaɗai ba mazajen su a wajen .
Soyayyar da ta tarar waɗannan ma'auratan na yi ya taɓa ranta , kewar sa da take ta dannewa kuma ta bijiro mata , baki ɗaya a lokacin , "Falmata meyasa kike kuka ? Kin san fa damuwa zata iya sa ki samu ciwo a halin da kike ciki .
Shiru tayi bata amsa ba , kamar yadda hawayen ta ya ƙi tsayawa , a dai-dai lokacin zuciyar ta tayi rauni wajen riƙe ciwon da yake damunta a rai ta hana shi bayyanuwa.
" Kiyi haƙuri zai zo ku tafi ,yana son ki dayawa Falmata inshaAllah a gidan ki za ki haihu .
" bai taɓa ƙiran mu ba tunda muka zo fa Yakaka , watakila ma ya sake ni bansani ba ni tausayin abunda yake ciki na nake yi ban..
" Youssouf ba zai taɓa sakin auren ki ba ya furta hakan da bakin sa kuma a aikace ma ya nuna ki kwantar da hankalin ki kiyi ta addu'a kin ji ko ?
Gyaɗa kai tayi tana share hawayen ta dai-dai da dawowar Amne da ta shiga cikin asibitin yin dubiya , damuwar da take damunta ta ɗan ragu .
Da layi yazo kan ta ita kaɗa ta shiga , su ka gaisa da likitar mace ce , ta yi mata duk wasu tambayoyin da aune-aunen da suka dace , bata da matsalar kome dan haka magungunan da yakamata masu ciki su dunga sha kawai ta rubuta mata .
Rashin ji daga Youssouf ba Falmata kaɗai yake damu ba , har Khaalty Rahima , Amnee da Prof da kan shi , rashin jin wani bayani ko da na ƙiran waya ne daga Youssoufa ya sa su a tunanin makomar auren sa da Falmata ?
Sau biyu Prof da Amnee suna tattaunawa a tattaunawar su ta ƙarshe prof ya yanke shawarar kan cewa idan har Falmata ta cika watanni biyu a gida , zai tashi ɗan aike zuwa masarautar Maradi dan sanin halin da Youssouf yake ciki da kuma makomar auren 'yar su , saboda rana ɗaiɗaiku ne bai ƙiran layin wayar Youssouf ɗin amma bai tafiya , ya zama dole yayi wani abu akai a matsayin sa na waliyyin auren kuma a yanzu shi matsayin Uba yake a wajen ta .
Falmata taso a bar ta ta dunga bin Yakaka Islamiyar da ko bayan auren ta da Doctor Hamza bata daina zuwa ba .
Da farko Prof ya ƙi yarda domin yace babu iznin Mijinta , tayi zamanta kawai a gida sai dai yadda a kwana biyun take yawan zaman shiru damuwar ta kamar ƙaruwa tayi tun bayan zuwanta awu , har 'yar rama tayi gaba ɗaya bata walwala .
daga Yakaka ta tafi islamiyyar da take kusan yini a can dan ƙarfe tara na safe take tafiya sai huɗu da rabi na yamma suke tashi kafin ta iso gida biyar saura .
Shikenan Falmata sai ta zama shiru a ɗaki ita ɗaya ƙwal, tun Khaalty Rahima na nunawa Amnee kar ta damu kan ta indai Falmata ce daman tun asali ita ba mai yawan son shiga jama'a bace kamar Baban ta take marar son hayaniya
Har ita da kan ta Khaalty Rahima ta fara damuwar saboda sai ta yini a ɗaki abinci ma da kyar take fitowa ta ci , Hajja ce daman mai shiga ɗakin ta dame ta har sai ta fito da ita , ita kuma wannan satin duk tana wajen danginta ana biki bata zauna ba .
Dan haka sai Amnee ta sake yiwa Prof maganar shiga islamiyyar Falmata ta sake masa ƙorafin zaman kaɗaicin da Falmatan take yawan yi kar ya sa mata ciwo .
Prof yace " zai duba lamarin .
Ranar asabat da safe kafin lokacin tafiyar Yakaka makaranta , Amnee ta shiga ɗakin su Yakaka hannun ta riƙe da baƙar leda da kaya a ciki ,
" Yakaka har kin fara shiri ne ?
Amnee ta tambaya tana ɗora ganin ta kan Yakaka wacce take sanya safa a ƙafar ta , da sauri ta ɗago fuskar ta da murmushi tace " Eh Amnee sannu da shigowa ,
" Yauwa sannu takwara ta furta hakan tana sauƙe ganin ta akan Falmata da take kwance akan gado ta basu baya ,
Ledar hannun ta ta ajiye a bakin gadon , kafin tace " Fatima tashi ki shirya yau dai ke ma za ki fara zuwa islamiyyar , tun kwanaki biyu na sake yiwa Baa Alaji zancen kin ga ashe an miki register ga Uniform ɗin ki ma da litattafan ki duk kin samu sai tafiya makaranta kawai ..
Falmata wacce tunda Amnee ta fara bayani ta tashi zaune tana murmushin da ta zarce da dariya jin ƙarshen bayanin Amnee da sauri ta sauƙa daga gadon tana cewa ," Amnee nagode , nagode Allah ya saka da Alheri ki yiwa Baa godiya , inason islmiyya sosai wallahi .
Ta ƙarasa zancen da nufar banɗaki domin watsa ruwa , Yakaka da Amnee suka bi bayanta da kallo fuskokin su ɗauke da murmushi .
Sosai fara zuwa makarantar ta ya rage mata damuwa domin kuwa yini suke karatu bata samun damar zurfafa tunani ,
Yau da ƙafa ma suka taho daga makarantar da yake tazarar tsakani ba mai yawa sosai bace Falmata tace, "Yakaka nafi jin daɗin makarantar nan fiye da Ecole ɗin mu ta Niamey wallahi ,
"Meyasa ko kin fi gane karatun nan ?
" A ah saboda a can ko na tafi ecole tunanin Mama baya bari na gane karatun sosai , Allah sarki Mama ta kusa watanni biyu da rasuwa amma koyaushe ji nake kamar ɗazu ta bar ni .
Murmushi Yakaka tayi , "ke da Mama ƙauna ku mai girma ce ai, nima naso Allah ya bani damar yin rayuwa tare da ita ko da ba mai yawa bane da nima na samu ladar jinyar ta da sanadin haka Allah zai bani lada mai yawa .
" da kuma za ki so ta dayawa fiye da son da kike mata domin Mama 'yar baiwa ce a cikin yara sa'o'in ta wayon ta daban ne kaifin hankalin ta yafi na shekarun ta .
Murmushin Yakaka tayi tana jin kewar 'yar ta na zagaya jinin ta , kewa kuwa mai tarin yawa ,
Ajiyar zuciya Falmata tayi daga nan ta shiga ba wa Yakaka labarin wayo da iyayin Mama wanda daman kusan rana ɗaiɗaiku ne da ba ta bata wasu labarai da suka shafi Mama .
Tun a harabar gidan suka fahimci akwai baƙi a gidan saboda baƙin motoci da suka gani har uku ,
"yau baƙi ne a gidan ko su waye ?
Yakaka ta furta hakan tana bin motocin wajen da kallo , can daga ƙasan ran ta tana fatan Doctor hamza baya cikin su .
" To Allah yasa baƙin alkhairi ne ,
Falmata ta furta hakan lokacin da suke nufar ciki
Tun kafin su shiga falon ƙamshin da ya karaɗe illahirin harabar wajen yake basu tabbacin baƙin na girma ne .
Da Sallama suka shiga falon , idanun su akan hamshaƙan mata huɗu da suke kan kujerun falon sai kuma Amnee da take a tsakanin su fuskar ta fal fara'a .
Ɗan taƙaitattcen kallo Falmata ta yi musu da taimakon gilashin idanun ta ta shaida fuskar Ammi , yayar Biyamuraɗi Youssouf , fuskar ta na nan zane a zuciyar ta kamar yadda munanan kalmomin da suka jefa musu yake rubuce tsaf a cikin kwakwalwar ta ,
Dan haka sai taƙi tsayawa kamar yadda Yakaka ta tsugunna gaishe su ,duk kuwa da cewa ita ma ta gane Ammi ,
sai ita ta ratsa ta bayan kujerun falon tayi hanyar ɗakin su .
Yadda tayi sam bai yiwa Amnee daɗi ba , dan haka ta ɗan ɗaga sauti tace " Fatima zo nan , zo ku gaisa da surukan ki mana ko baki gane su bane ? Yanzu suka iso .
Jaa tayi ta tsaya kafin ta waigo cikin rashin kuzari ta dawo baya kaɗan ta yi durƙuso daga nesa tace " Ina wunin ku ?
" Kadaran-kadahan Ammi ta amsa ,"da lafiya lau , tana janye ganin ta daga kan ta
Asma'u wacce tun shigowar su take faran-faran cike da kissa tace " tashi tashi ƙamna ta durƙuso ba naki ne ba , ɗaga yayar ki daga durƙusso Mairama .
Da sauri Aisha Mairama ta miƙe fuskar ta ɗauke da faffaɗan murmushin ganin Falmata , kafin ta ƙaraso Falmata ta miƙe akan ƙafafun ta guntun murmushi ta yiwa Aisha bata tsaya ba tayi juyawar ta ba tare da ta yadda ta sake duban kowa ba ta nufi ɗaki .
" Mama kar ki tafi ki barni ki jirayeni Mama , nan ina ne muka zo Mama ?
Chak ta tsaya a bakin ƙofar ɗakin zuciyar ta na sauya bugu wannan muryar ta Mama ce , Mama ce take ƙiran ta , da kitsima hakan cikin ranta ta juyo da sauri laɓɓan bakin ta na ƙiran Mama .
Idanun ta suka sauƙa kan 'yar yarinyar da bata kai Mama a girma da wayo ba sai tsantsar kamanni da take yi da Mama , tana kokawar riƙe hannun Mamar ta da suke sauƙowa tare daga ƙafar benen a tare Khaalty Rahima na bin su a baya ,
"Yumna
Ta ƙira sunan ta da ƙaramin sautin da bai hana Yumna ta jiyo ta ba , a hankali ta ɗora ganin ta kan ta tana wara manyan idanun ta masu cike da wayo , sai ta sake matsawa jikin mamar ta tana riƙe hannun ta da kyau lokaci guda ta haɗa da maƙale kafaɗa .
" Yumna ki je wajen Mamar ki tana ƙiran ki , Siyama ta furta hakan tana ƙoƙarin zare hannun ta daga cikin na Yumma ,
A hankali Falmata ta ɗaga idanun ta ta ɗora ganin ta kan kyakkyawar doguwar matar da take tsaye gaban ta tana jifan ta da tsadaddan murmushin da yake sake fiddo zallar kyau da wayewar ta , ba sai an faɗa mata ba ta fahimci ita ce Mahaifiyar Yumna , kenan wannan ce Siyama matar Youssouf tuno da matsayin da suke kai a wajen juna ya sa tayi saurin juyawa ta ɗaga taku tana barin wajen , zuciyar ta cike da tunanin abunda ya kawo su haka ? Ko sakin nata aka zo kawo mata tare da matar tasa ?
Karɓa irin ta girma da girmamawa ita iyalan Maimartaba suka samu daga wajen Prof da nasa iyalan , duk kuwa da cewa ba'a san da zuwansu ba , hakan bai hana a shiga hidima da su ba ka'in da na'in babu ƙyashi Prof ya buɗe bakin Aljihu aka shiga hidima da su kamar daman can an san da zuwan su dan haka basu tarar da gidan tare da wata alama ta ƙasƙanci ba .
Gidan Attajiri suka tarar da ya matuƙar birge su a matsayin gidan su Matar da Youssoufa yake aure , duk sai jikin Ammi da Asma'u '( yar Hajiya Mama ) yayi sanyi da daman su biyun ne suka zo da wata manufa ta daban , sai suka ga ko su sai dai su gwadawa gidan su Falmata sarauta amma ba dai su ƙasƙantar da su ba . ( Daman Bare-bari ai ba daganan ba indai fagen bajinta ne ) .
Tunda Falmata ta shige ɗaki bata fito ba a ciki tayi sallar ta ta magarib da isha'i ta hau gado ta lulluɓu bayan ta kashe wutar ɗakin , ta rasa takamaimai halin da zuciyar ta take ciki , farin-ciki ne ko saɓanin sa ?
"watau sai yau ya waiwayo ta ? Bayan yasan ya mata laifi , yasan cewa dole tana jiran sa , yasan kuma a halin da take ciki da halin da ta baro wajen sa a ciki .
Can ƙasan ranta kuwa , So take ta ji ko da tashin ƙamshin sa ko kuwa amon muryar sa dan ta san cewa ya zo amma ko alama bata ji ɗuriyar sa ba a gidan .
Sai juye-juye take yi akan gadon , juyi ta sake yi lokacin da taji an turo ƙofar an shigo gami da kunna wutar ɗakin haske ya gauraya da sauri ta miƙe zaune bayan ta yaye mayafin da ta rufu da shi ,
Khaalty Rahima ta gani a tsaye a bakin ƙofa , daga inda take tana iya hango
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 84 Chapter of 103