ta leƙo da kanta cikin harshen larabci ta ce da shi yayi haƙuri ya daina yi mana faɗa irin yadda Aichatuwa take yi mana kullum ai ita ta yaga takardun tana so ta yiwa ƴar tsanar ta kaya ,
"Ban san dalili ba sai naga ya sassauta fishin sa , a ƙarshe yace mu tafi kawai ,
"tun daga ranar sai naji tsoron sake zuwa da Rahima domin kar tayi wata ɓarna sa zata sa a kore ni daga aikin wanda albashin sa a lokacin da shi nake yi mana hidimar yau da kullum ni da ita duk kuwa da cewa kaso uku Aichatuwa take raba albashin ta ɗau kashi biyu da rabi ta bani guntun ,
"daɓ dole nake barin ta a gida tana kuka , wani lokacin nima har ta saka ni ƙwalla , nake tafiya na bar ta ,
"ba'a yi sati guda ba wata safiya har na kammala aiki zan tafi , Ambassador Al-mustapha ya ƙira ni , zuciyata cike da tsoro na je na ɗauks batun laifin Rahima ne bai wuce ba ko kuma ni ce na sake yin wani laifin .
" ga mamakina sai naji yana tambayata ina ƙanwa ta take meyasa na daina zuwa da ita ?
" na ce masa tana nan , inajin tsoron kar ta sake ɓarna shiyasa na daina zuwa da ita ,
" sai ya umarceni da mu cigaba da zuwa tare amma na dunga lura da ita kar ta dunga yin ɓarna ,
"shikenan Tun daga ranar na cigaba da zuwa da Rahima ,
"a hankali sabo mai ƙarfi ya shiga tsakanin Ambassador Al-mustapha da Rahimatullah saboda 'yan kayan maƙulashe na yara da yake mata hasafin su ,
"kafin wasu watanni shaƙuwar su da Rahima ta shafeni wanda a ƙarshe cikin shekara guda tsakanin mu ya rikiɗe ya zama soyayya ce mai ƙarfi ,
"duk kuwa da tazarar matsayi da yake tsakanin mu hakanan Allah ya kulla auratayya a tsakanin mu , bayan rigin-gimu da suka taso daga dukkan ɓangarorin biyu , daga Aichatuwa , da bangaren iyaye da 'yan uwa Al-mustapha na jini , wanda suks tirje akan ba zai auri 'yar wata ƙasa ba wacce ba ƙabilar su ta kanurai ba , alhalin ga 'yar uwarsu wacce take dakon jiran sa suyi aure ,
"hakanan ɓangaren Aichatuwa wacce ta bi duk wata hanyar da zata iya bi domin ganin auren mu bai yiwu ba da Mahaifin ka , amma dayake shi aure Kaddara ce daga kaddarorin da Allah yake yi ga bayin sa .
"A ƙarshe aka ɗaura Auren mu ni da Mahaifinka tare da Amincewar kakan ku wanda ya taka har ƙasar mu ya nemawa ɗan sa aurena cikin mutuntawa , bai duba ƙasƙancin mu da shi yake babban Attajiri a ƙasar su kuma mai ilmin addini da na boko tun a wancen zamanin .
" Bayan auren mu mun zauna shekara guda a N'Djamena kafin aikin mahaifin ku ya ƙare da ƙasar mu , muka kuma fara shirin komawa ƙasar su ,
"a kuma tsukin wannan lokacin Allah ya yiwa Mahaifin mu Rasuwa sakamakon sukar sa da wuƙa da wasu ga cikin 'yan firsina suka yi a ƙoƙarin su na gudu daga gidan yari .
"Mutuwar Baban mu ta gigita mu ganin cewa duk wani gatan da muke da shi ya ƙare ,
"a ƙarshe dole muka haƙura , riƙon Rahima kachokam ya dawo hannun mu da duk wasu ɗawainiyar ta Al-Mustapha ke yi ,
"Sauran ƙannena maza suka raɓu da gidajen 'yan uwa , ,
"Ba mu jima ba bayan nan muka koma Nigeria tare da Rahimatullah da kuma kai a lokacin kana ɗan jariri .
"na fuskanci tsangwama da ƙiyayya iri-iri daga kakar ku , da dangin mahaifin ku da baki ɗayan su basa ƙaunar auren mu , idan aka ɗauke Salman wanda ƙani ne na uku ga mahaifin ku da shi babu ruwan sa da duk wasu lamura da suka shafe ni .
"Haka shekaru suka yi ta tafiya tare da nasarar rayuwa , matsala mafi girma da ta zama sanadin rabuwar auren mu da mahaifin ku ya samo asaline daga lokacin da Soyayya ta shiga tsakanin Salman da Rahimatullah ,
"lokacin Rahima ta gama makarantar gaba da primary , kai kuma ka shiga makarantar kwana ta gaba da primary ,
"rikicin an ɗauki lokaci ana yin sa tun bayan bayyanuwar soyayyar su da suka yi shekaru biyu suna boyen ta a tsakanin su ,
"Salman ya doshi mahaifiyar su da sauran 'yan uwan sa da batun auren Rahimatullah , ƙaramin yaki aka yi a tsakanin su saboda lokacin kakan ku ya jima da rasuwa .
"Lamari yayi tsamari da yasa har kakar ku ta ƙira mahaifinku ta masa kashedi kan muddin yana son Albarkar ta , ya zama dole ya raba tsakanin ƙanwar matar sa da ƙanin sa ,
"daga lokacin shima Mahaifinku ya fara nuna adawar sa da soyayyar tsakanin Salman da Rahima domin bin umarnin Mahaifiyar su , da hakan ya kawo saɓanin a tsakanina da shi domin ni ɗari cikin ɗari nake tare da su akan lamarin soyayyar su .
"ana cikin wannan hatsaniyar uwar matar da aka so aurawa Mahaifin ku wacce take ƙanwar kakan ku ce ta zo da wani lamari mai yanayi da tsafi ko kuwa chanfi , kan cewa muddin ba'a yi gaggawar raba tsakanin Salman da Rahima ba to babu makawa guda a tsakanin su zai mutu , domin Malamin ta yace babu aure a tsakanin su , '
"Maganar bata ɗaga min hankali ba sai da naga kamar Mahaifinku ya yarda da batun inda har ya fara maganar ko dai Rahimatullah zata koma N'Djamena na ɗan wani lokaci , idan kome ya lafa ta dawo ,ranar nayi kukan Maraicin mu da rashin gatan mu ,
" an yi haka bai fi da wata guda ba , Rahima ta gama shan kukan ta akan wannan batun , Babban Al'amari ya afku,
"Ranar wata juma'a bayan Rahimatullah da Salman sun gama hira da rabin ta neman hanyar warwaruwar matsalar su suke tare da kaiwa ga cikar burin su ,
"ƙarfe biyu da rabi na ranar bayan sallar juma'a labarin Rasuwar Salman Dilmari matashin Saurayi, ya bazu tare da yin tambari a baki ɗayan birnin Maiduguri kasancewar sa matashin ɗan siyasa da ya yi suna a lokacin ,
"ya rasu a sakamakon mummunan haɗarin mota da yayi akan hanyar sa ta komawa daga masallacin juma'ah mintoci arba'in da rabuwar su da Rahima ,
" mutuwar data girgiza zukata da dama , ta kuma bar miƙi a zuciyoyin wasu da dama , Salman Mai Alheri ne , Allah ya gafarta masa ,
Shiru ne ya ratsa tsakanin su saboda kuka haiƙan da Rahima take yi , kukan tasowar tsohon miƙin dake zuciyar ta da ya tarad sabon ciwukan dake cin ranta a kullum kwanan duniya ,
Mutuwar mijinta uban 'ya'yan ta da ta tarar da gawar sa a yashe cikin gona , haka kuma tana ji tana gani ta tsallake shi domin ceton ranta da na 'ya'yan ta ta tafi ta bar gawar sa a daji, tare da ɓacewar manyan 'ya'yan ta da har yau bata da sanin haƙiƙani kan rayuwar ko mutuwar su ta ma fi haƙaƙewa akan Yakaka da Falmata sun mutu kamar yadda harsashi ya samu Baana yayar Bulama ta mutu akan cinyar ta ,
Bakin lafayyar ta Amne ta sanya ta sharewa Rahima hawaye sannan ta cigaba da cewa ,
"Fasalta irin halin da baki ɗayan zuri'ar Dilmari ta samu kanta a ciki bashi yiwuwa ,
"ai ka san lokacin kana da wayo sosai kana secondary School ,
gyaɗa kai Hamza yayi wanda idanun sa suka yi jaa ,
" Rahima ta shiga ɗimuwa marar misali domin har suma ta dunga yi , sai da Maigadin gidan ku na lokacin ya dunga yi mata rubutu , cikin sati guda da mutuwar sa Rahima ta rame tamkar majiyanciya , ni da kaina ƙarfin hali nake yi , nake hana kaina tunani saboda tsohon cikin Rahima ƙarama da nake ɗauke da shi .
"abu mafi muni da ya biyo bayan mutuwar Salman shine takowa da 'yan uwansa suka yi har gida bayan kwana arba'in da mutuwar sa , suka ci mutuncin mu ni da Rahima , a ƙarshe suka danganta mutuwar Salman da cewa ni da Rahima muka lashe masa kurwa muka kashe shi , to waye ya san salsalar asalin mu ??
"Ni kuka Rahima kuka , sannan abun takaicin mahaifinka yana zaune ya gagara hana su ko ɗaukar wani mataki na ba mu kariya , wanda hakan ni kuma ya tunzuro ni , na yunƙuro domin maida musu martani a karon farko bisa duk abubuwan da suke min marasa daɗi ,
"Ga maɗaukakin mamakina sai mahaifinka ya hayyaƙo min ya takore ni daga yin magana har ma yace muddin nace wani abu kome zai iya faruwa ga igiyoyin auren mu ,
"bisa tilas nayi shiru sai hawaye da muke yi ni da Rahima suka gama zage mu tas har da dungurin Rahima da alama ma duka suke da niyyar yi mata sai ɗan uwansu ya rarrashe su ,
'tundaga wannan ranar Rahima ta sake yin sanyi duk ta susuce firgici ya bayyana cikin suffar ta bata da aiki sai tunani ,
"duk da ceqa ina bin duk wasu hanyoyi domin kwantar mata da hankali duk da cewa nima hankalin nawa a tashe yake domin tsakanina da Mahaifinku babu daɗi , nema yake ƙarfi da yaji ya raba Rahima da gidan sa wanda nasan zugar 'yan uwansa ne da ni kuma ko kusa bazan lamunta ba , idan Rahima ta bar wajena ina zata ??
"har zuwa safiyar wata rana da na wayi gari Rahima kin yi gaban kan ki wajen barin Rayuwata , kin tafi kin barni cikin tashin hankalin da ya tunkuɗo min da naƙuda ,
"kika tafi ba tare da kin yi tunanin me hakan zai haifar ba cikin rayuwata ,
"duk wani wajen da nake tunanin zaki je Rahima naje neman ki har ms da wuraren da baza ki ba naje neman ki ,
" a cikin halin nan na matuƙar tashin hankali na haifi jaririyata da tun lokacin da na haife ta na shaidawa mahaifinku sunan ta Rahimatullah .
" da ɗanyen jego na dunga fita kusufa-kusufa neman ki da hakan ya tunzuro Al-Mustapha yace muddin na sake fita neman ki da kaina a bakin auren mu ,
" a wannan ranar nima zuciyata a taurare take da zafin rashin ki dan haka nima na taso masa , a take a wajen na nemi da ya sawwaƙe min auren sa tun a nan domin kuwa fita neman ki yanzu na fara har sai ranar da na ganki ,
"shima da alokacin yake ganin zallar laifin ki na cewar ai ke da kan ki kika ga damar tafiya dan haka zaki dawo ,
"a fusace a wajen ya datse igiyar auren mu ba tare da yayi la'akari da irin raunin dake tare da ni ba ,
"Ban kwana a gidan ba na tafi tare da jaririya Rahima , na bar masa Hafsa da Zainab Hamza kuma yana makaranta,
" nayi neman ki Rahimatullah har N'Djamena naje an tabbatar min da baki zo ba ƙarin tashin hankalina shine duk sauran ƙannena a cikin matsanancin talauci suke ,
" Na tattara musu duk wasu 'yan kuɗaɗen da na tafi da su na basu , na sake dawowa Nigeria , tare da taimakon ƙawayena biyu Hajiya Hadiza da Hajiya yaana , na sayar da tarin sarƙoƙi da ƴan kunnayena zuwa wara-waren zinare da nake da su , na sayi gidannan da muke ciki , na ɗora neman ki daga inda na tsaya saboda na tabbatar kina Nigeria wataƙila gari kika sauya , meyasa kika min haka Rahima ????
"aina kika rayu ? Ina mijinki kina da wasu 'ya'ya ne bayan wannan na cinyar ki ? Idan kina da su suna ina ??
Amnee ta ƙarasa bada labarin rayuwarsu da ɗora tambaya ga Khaalty Rahima wacce idanun ta yayi jazir tsabar kuka ,
B
Tausayin yayarta ya cinye zuciyar ta , ashe haka ta shiga damuwa akan rashin ta ??
ƙasa take son sharewa tayi rubutu ,
Amnee ta miƙe ta kawo mata takarda da biro , ta sanya hannu biyu ta karɓa ,
taƙaitatcen rubutu tayi a jikin takardar ,
" tsoron kar na zama sanadin rabuwar auren ku da Yaya mustapha yasa na tafi daga gareku ukhtee Amina ki yafe min , bansan ba zan zama sanadin tarwatsewar jin daɗin rayuwar ku .
"Mairambiri shine sunan ƙauyen da na rayu tsawon lokaci a cikin sa kafin zuwan yan tawayen boko haram su tarwatsa garin su kashe mijina da manyan yarana biyu mata da suma nake zaton sun mutu , Amina da Fatima shekaru shida yanzu da mutuwar su .bayan su ina da wata 'ya da ita ma harsashi ya same ta ta mutu , a yanzu Bulama shine kaɗai ɗana .
ASSALAMU ALAIKUM
'Yan uwa ina miƙo saƙon gaisuwata tare da fatan Alheri gare ku baki ɗaya , ina kuma mai yabawa bisa ga yadda kuke nuna ƙaunar ku ga littafin nan ,
nagode .
[11/22, 12:05 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
39
Duk yadda Falmata take tunanin daɗin dake ga mallakar idanu ta tadda shi ya wuce haka , jin kanta take tamkar sabuwar halitta ,
Har bata so bacci ya shiga tsakanin ta da ganin hasken duniya , karambani kuwa babu irin wanda bata yi , har girki take karambanin yi Yousssouf kuwa yana taya ta ,
Shima a ɓangarensa baya gajiya da duk wasu tambayoyi da ko karambanin da zata yi , wani irin son ta yake yana riritata ,
Mama da kanta tasan cewa yanzu Mamarta ta samu waraka saboda wata kulawa na musamman da idanun ta sun hango mata wani ɗan datti a jikin kayan Mama zata yi maza ta gyara ta ta sauya mata wani ,
A kullum ta Allah sai ta miƙa godiyar ta ga Youssouf kamar yadda cikin duk wasu sallolinta sai ta ƙara godewa Allah akan wannan babbar kyauta da ya yi mata na dawo mata da ganin ta ,
Godiyar da take yiwa Youssouf ba a fatar baki kaɗai ta tsaya ba , har a aikace take gwada masa ta yadda take nuna masa ƙauna tare da ɗaukar buƙatun sa ba tare da gajiyawa ko ƙorafi ba .
Kamar yadda likita yace tana cigaba da zuwa ana dubata , babu wata sabuwar matsalar da ta ɓullo tunda aka yi mata aiki .
Idan tana da wata damuwa to ta lafiyar Mama ce wacce kwana biyu ciwon ta yake ƙoƙarin tasowa suna danne shi da tarin magunguna gami da ƙara ƙaimi wajen kulawa da ita , amma duk da haka kallo ɗaya za'a mata a iya hango tarin raunin dake tare da ita tun daga cikin raunanan idanunta da suka ɗan sauya launi zuwa ruwan ɗorawa har zuwa ƙafafunta da hannayenta da suka ɗashe suke yawan ɗaukar sanyi ,
Gaba ɗaya Falmata da shi kansa Biyamuradi Youssouf basa tare da walwala sosai ,
"Baban Mama ko dai za'a sake komawa asibitin nan ne maganar aikin Mama ,
Youssouf wanda yake shafa kan Mama wacce take kwance cikin jikin sa lamo , ya ɗago kan sa yana duban idanun Falmata da suke nuni ƙarara da damuwar da ruhin ta ke ciki ,
"Fatima duk wassu bayanai da zamu sake samu daga Doctora basu wucce batun baya da sunka faɗi muna , wanda kouma mun bar Lamari ga Allah zouwa lokacin da za'a samu damar yin aikin ,
Shiru tayi tana cigaba da kallon sa , cike da damuwa , so take yayi wani yunƙuri kome ƙanƙantar sa ,
Ji yayi gangar jikinsa na karban sakon dake fitowa daga cikin ƙwarar idanunta masu kyaun kallo ,
"idanun ki suna da kyau idan kina kallon Mutum da su Fatima , lokacin da basu da Lafiya kyan su bai kai haka bayyana ba , kina da sassanyan kallo Mai cike da nutsuwa ,
Murmushi tayi kaɗan , kafin ta ƙira sunan sa ,
"Baban Mama ,
Sai kuma tayi shiru ,
Kamo hannunta da yake kusa da shi yayi ya riƙe ,
"Ummh ina jinki menene ?
" daman nace ko zamu je ni ɗin a gwada ni ?
"gwaji Fatima wanne irin gwaji , akwai damuwa ne ga lafiyar jikin ki ?
Sunkui da kan ta ta sake yi tana jin nawin zancen akan harshen ta , sai dai tana jin zata iya yin kome domin ganin Mama ta samu lafiya , muryar ta a ciki tace ,
"ko Allah zai sa a dace un-un ko wai a jikina akwai abunda da za'a iya amfani da shi wajen yiwa Mama maganin ,
Kiris ya rage Biyamuradi Youssouf ya kwashe da dariya , sai dai ya gintse saboda yana son jaan ta ,
" Fatima kin manta likita yace ke baki iya bada jinin ki ?
Cikin sauri ta katse shi ,
" ai ba jini na ba , wai a auna ko akwai cikin ?
" ciki aina ?
Yace da dariya a cikin sautin sa,
Ɗago kanta tayi tana iya hango hasken haƙoransa da yake dariya,
" un-un a jikina ko ?
Dariya ya kwashe da ita , cikin ransa ƙaunar ta na sake yawaita , kunya da kawaicinta yana burge shi haɗi da salon rashin wayewarta da baya sa ta fidda tsagoron ƙauyencin ta .
"Fatima ciki ai sai ya nuna Alamunsa tukun ake zouwa ayi gwaji , hakanan bai yiwuwa aje ga gwajji sai a mouna dariya ,
Shiru Falmata tayi tana ganin wautar kan ta , to ita ya zata yi ne ? Ta matsu Mama ta warke ta samu lafiya kamar sauran Yara , tsintar kanta tayi da addu'ar Allah ya nufe ta da samun ciki nan kurkusa domin lafiyar Mama ,
Daren ranar basu samu bacci ba saboda jikin Mama da ya tsananta idan banda nishe-nishe da ƙananun kuka babu abunda take yi , hankalinsu baki ɗaya a tashe , Falmata ta rungume ta anjima Youssouf ya ɗauke ta ya ɗora a jikinsa , haka suka yi ta fama .
Asubar farko a cikin tsananin sanyi suka nufi asibiti a take likitocin ta suka shiga bata kulawa ,
Ba'a fi awa guda ba ciwon ya lafa ta samu bacci , tana rungume a jikin Falmata
Ƙarar wayar sa ya sanya shi miƙewa daga kujerar da yake zaune ya ɗan taka zuwa wajen ɗakin yana ɗaga ƙiran da ake masa wanda yake daga Tafeeda ,
" Youssoufa akwai Al'amari maigirma da muni da yake tunkaro ka ,
Sune kalaman da Yaji Tafeeda ya furta masa ba tare da sun ko gaisa ba ,
Ji yayi ya cigaba da cewa ,
"Bayan tsawon shekarun da ka kwashe kana ɓoye kuskuren da ka aikata yanzu kome yana daf da bayyanuwa batare da ka farga ba mutanen da suka ɗau lokaci suna bibiyar sawun duk wani motsi naka ba tare da ka kai ga hankalta ba gaf suke da cimma nasara akan ka ,
"Ya zama dole ku dawo tare da kai da 'yar taka da matar da ka aurawa kan ka kafin kome ya lalace , mafi girman lamarin shine nan da kowanne lokaci Maimartaba tare da Hajiya umma zuwa kan iyalai tare da 'yan uwanka zasu iya sanin Mummunar Fuskar ka ,
" Maƙiya kuma zasu samu damar kassara ka , wanda kafi kowa sanin me hakan ke nufi ??
"Ta-Tafeeda , meke Faruwa ne yi gaugawar sanar min ,
"ni a matsayina na 'dan ouwa a gareka zan yi dukkanin bakin ƙokarina wajen ganin lamura basu munana fiye da ƙima ba , duk kuwa da cewa ni ai ba bakin koume nake gareka ba ,
Ɗut-ɗut !
Yaji ƙarar Alamun yankewar ƙiran
Tashin hankalin da ya zo masa a lokacin maigirma ne , me Tafeeda duk ya faɗa masa ??
"Tayaya ya san cewa tare yake da Fatima da Mama ?
"Su waye maƙiyansa masu bibiyar rayuwar sa ?
"Fallasuwar Asirinsa a gurin iyayensa hakan na nufin ɗebe ƙaunar sa daga zukatan su ,
"wai shin me yake shirin faruwa ko kuwa ya ma riga ya faru ??
Ya zama dole ya koma gida ,
Da sauri ya shiga neman layin Tafeeda sai dai har ta gama ƙara bai ɗauka ba , ya sake gwada ƙira a karo na biyu nan ma ba'a ɗauka ba ,
Tashin hankalin sa ya yawaita da har Falmata ma ta kai ga Fahimta , damuwar sa ta ƙara mata damuwa , sau biyu tana tambayar sa ko me yake damunsa ? Yana ce mata ba kome .
Kafin dare Mama ta warware dan haka suka koma gida ,
"Falmata ta haɗa ruwa mai zafi ta yiwa Mama wanka ta shirya ta cikin jibga-jibgan kayan sanyi , kasantuwar cikin magunguna da Alluran da aka yi mata akwai masu sa bacci bata jima ba bacci ya sake ɗauketa ,
Itama wankan tayi ta shirya cikin wondo wide-leg da Rigar sanyi ribbed sweater ta ɗaura hular sanyi akanta ,
Ta fito ta cimma masa yana zaune a ƙasa ya jingina bayan sa da kujera , hannun sa biyu tallafe da ƙeyarsa ,
Babu wadatar haske a falon saboda duhun dare da ya shigo fitilar falon kuma ɗaya ce a kunne , kasantuwar idanun nata ba gani suke sosai ba , ya sa bata ma kai ga ganin sa a wajen ba sai duhu-duhu take gani ,
"Fatima ,
Ya ƙira sunan ta lokacin da ya ga ta kashe ƙafa daga ƙofar ɗakin , alamun tana buƙatar ɗan jagora ,
"zo nan ,
Yace da ita
Inda take iya hango duhun sa ta nufa a hankali ,
kallo yake bin ta da shi ganin yadda kayan suka karɓi jikinta musamman ɗan wondon da bai kai ga sauka ƙasa ba , daga ƙungunta ya zauna ɗas saboda ɗaura shi da tayi akan rigar .
Hannun ta ya kama ya ƙarasa zaunar da ita akan jikinsa yana jin yadda ƙamshin daddaɗan turaren da ta fesa yana ratsa hancin sa ,
Lamo tayi a jikin sa tana jin damuwar rashin walwalar sa na damun ta ,
" Alhamdulillah Mama ta samu sauƙi ko ?
Tace da shi da dabarar son jin maƙasudin damuwar sa ,
"Mama ta samu sauƙi Alhamdulillah ,
Ya ce yana ƙanƙameta a jikin sa ,
"Har hankalin mu ya kwanta , bana son ciwon Mama ina tausayinta ,
"Fatima zamou kassance cikin shiri zouwa wassu kwanaki nan gaba zamou koma gida ,
" ɗago kanta tayi da son ganin fuskar ko Allah zai sa ta fahimci damuwar sa ,
"Baban Mama na ɗauka sai an samu lafiyar Mama ?
Zai yi Magana wayar sa tayi ƙara ,
Ganin sunan Hajiya Umma a fuskar wayar ya sa zuciyar sa tsinkewa ,
Da sallama ya ɗau wayar , sai dai yadda ya ji ta amsa masa ya sa jin hankalinsa ya sake tashi ,
Sama-sama ta amsa gaisuwar sa , bayan nan abunda ta sanar da shi shine kawai duk me yake ya nemi izni ya taho gida cikin kwanakin nan kusa .
Shiru yayi bayan ya ajiye wayar , tabbas akwai abunda ke wakana game da shi a gida .
"Baban Mama...
Ya katse hanzarin ta
"Fatima zamou kouma gida , a gaba zamou dawo neman lafiyar Mama ,
Sai ta mayar da kan ta jikin sa tayi shiru , baki ɗaya walwalar da ta ɗan samu na murnar samun sauƙin Mama ta kau ,
Daren ranar babu wani armashi agare su musamman ma Falmata da damuwar da take ciki ta haifar mata da zazzaɓi da ɗan ciwon kai , dan haka washegari ta tashi haka sukuku ,
Karin kumallo ma sama-sama suka yi ,
Bayan sun gama karin kumallo su dukkanin su biyun sun yi shiru sai mama ce take ɗan wasan ta ,
" J'ai réservé notre vol, nous rentrerons à la maison le 18 le mois prochain , ( nayi mana tanadin jirgin komawa , zamu tafi ranar sha takwas ga watan gobe , )
Muryar sa ratso shirun wajen ,
"Allah ya kaimu Baban Mama , ko zaka sanarwar da Hajja itama ta fara shiri ko ?
"Eh zan sanar da ita idan ya ragge kwanaki goma mu tafi sai tayi shiru cikin kwanaki biyar , idan ya rage
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 64 Chapter of 103