yana zakwaɗin samun tabbacin sahihancin su .
Bayan ya zauna akan kujerar falon sa a kasalance ya ɗau wayarsa tare da ƙiran layin Amnee Khaalty Rahima ce ta ɗaga ƙiran saboda Amnee ta shiga wanka , bayan sun gaisa yace da ita " yunwa yake ji dan Allah a samar masa da abinci ,"
Abincin sa na musamman da daman yake kitchin ɗin sama a ajiye can ta hau ta ɗauko masa tana saukowa suka yi kichiɓus da Yakaka wacce ta fito daga ɗakin su zata shiga ɗakin Amnee ,
Da sauri ta ƙarasa ta karɓi tiren hannun Mamar su tana mata sannu , cike da jin daɗi Khaalty Rahima ta amsa , kafin ta ɗora da cewa yauwa Yakaka ga abincin yayan ku ɗauki ki kai masa , banda ma shirmen ki kina nan kina ta kai kawo mijinki yana can zaune da yunwa ,ki sauya wannan ɗabi'ar tun wuri dan naga alamar duk jaan kunne da nasihar da ake miki ba ganewa kike ba ki sa hijabin ki ki kai masa .
Saƙare Yakaka tayi tana kallon Mamar su , so take ko yaya ta samu ƙafar zillewa amma babu dama , ji tayi ta cigaba da cewa " ki kai ki dawo yanzu idan kuma ba haka ba a tafi a barki na ga ma ko gama shirin baki yi ba .
Ɗaki Yakaka ta koma ta saka dogon hijabin ta akan doguwar rigar da take jikin ta mai guntun hannu da fitowar ta kenan a wanka ta zira ta a jikin ta ta fito ɗaukar kayan ta a ɗakin Amnee shine wannan tsautsayin ya gifta mata , " ah tsautsayi mana haɗuwar ta da Yaya dakta ai ita tsautsayi ne a wajen ta mutumin da babu wanda ya tsana ya ita ?
Cikin takun rashin kuzari ta nufi sashin nasa riƙe da tiren da aka jera abincin akai , tana taɓa ƙofar ɗakin da nufin ƙwanƙwasa ta ƙofar tayi baya a buɗe take ,
Sai ta shiga a hankali siɗak-siɗak ta ajiye abincin aka ƙasa , zuciyar ta ta ɗan yi sanyi ganin baya falon , tana ɗaga ƙafa da zummar barin wajen ta tsinkayi muryar sa a ɓakin ƙofar ɗakin sa , "
Yace " ina ruwa ? Dan Allah a kawo min ruwa , ruwan cikin Fridge na ya ƙare .
Bata juyo ba tace "akwai ruwa a ɗaya cooler ɗin ,
Jin muryar ta ya sa shi ɗago kai da sauri daga goge kan sa da yake yi da towel fitowar sa kenan daga wanka jikin sa sanye da jallabiya ,
Da sauri ya dakatar da Yakaka wacce ta ɗaga sawu tana son ɓacewa daga falon ,
" zo ki zuba min , yace da sauti marar ƙarfi , kanta a ƙasa ta juyo ta ɗau daya daga cikin plate biyu da suke kan faranti ta fara ƙoƙarin zuba aɓincin ,
Da sauri ya dakatar da ita , " kar ki zuba , chak ta tsaya zuciyar ta na harbawa , jinsa tayi daf da ita ya kai hannu a hankali ya zare plate ɗin daga hannun ta , banɗakin sa ya koma ya ɗaureye plate ɗin tare da chokula biyu , ya dawo ya miƙa mata, ta miƙa hannu biyu ta karɓa , da ido ya bi hannun ta da ya sha ƙunshi .
" Ya isa yace , lokacin da ya ga tana ƙoƙarin cika masa Plate har ya tunbatsa , kan ta a ƙasa ta miƙa masa , ya karɓa yana kallon fuskar ta , kafin tayi wani yunƙuri yace mata " ki dakata na gama ci kar ki tafi ,
A ɗarare ta zauna daga gefe a ƙasa ta sunkui da kai , yana daf da kammala cin abincin Amnee ta ƙira wayar sa , yayi hanzarin ɗauka ," tambayar sa tayi ina Yakaka ? Ka turo ta yanzu ta gama shiri kowa ya shirya ita ake jira har wasu sun tafi ,
Cike da nutsuwa da kwantar da kai yace " Amnee wani wajen za'a tafi ne ?
A gaggauce ta amsa masa da " eh wajen Dinner ɗin Rahima zamu tafi tare baki ɗaya , ta ƙarasa da cewa " ka turo ta yanzu kaji ko ,"
"Amnee , amm Amma kuma zuwa dinner har da ita ? Da dai ita ta zauna a gida Amnee ba wani amfanin fitar ta a daren nan tun...
Muryar ta a ɗan sama Amnee tace "kai kar ka min tsarin wofi ka turo ta mu tafi yau dai ɗaya tal taje , tunda ita ba'a shirya mata nata bikin ba .
Zai sake yin magana ta kashe wayar tana cigaba da yiwa Khaalty Rahima mitar meyasa ta aiki Yakaka sashin Doctor Hamza ? Ga shi zai kawo mata wani iyayi irin na shi .
Murmushi kawai Amnee tayi tana mamakin rigimar Amnee marar tushe , mutum da matar sa a hana ta yi masa hidima ?
Hankalin sa kwance ya ƙarasa cin abincin sa , cikin ran sa neman hanyar da zai hana fitar Yakaka zuwa wajen wani taron can daban yake , a haƙiƙanin gaskiya baya son ta fita da auren sa cikin wasu ƙattin wofi ,su gama ƙare mata kallo , wanda aka kalla a da ma ya isa , duk da cewa dai wasu maganganun da Suleiman ya faɗa masa sun saɓa sosai da zaton da shi yake mata .
Yakaka ta durkusa ta tattara wajen ta haɗe kome yadda ta zo da shi , a hankali ta miƙe zata fita , cikin rashin sanin ta ta taka bakin dogon Hijabinta , saboda sauri da take ta bar inda yake ,
bata ƙarasa miƙewa ba Hijabin ya taɗile ta tayi ƙasa baki ɗaya farantin hannun ta ya bigi ɗan teburin gabanta , miyar da bata rufe sosai ba ta buɗu cooler ɗin yayi ɗan tsallen da yasa miyar tankwaɓewa ta fallatsuwa har cikin idon ta kafin ta kwaranye mata baki ɗaya a jikinta .
Ɗumin miyar tare da zafin attaruhun ciki da ya shiga mata ido yasa bata san lokacin da ta saki wani ɗan ƙaramin ihu ba .
A ruɗe Doctor Hamza ya miƙe yana jera mata sannu , amma azabar da take ji a idanun ta yaƙi barin ta nutsuwa bare ta ji me yake cewa , ihu ta shiga yi tana cewa " wayyo idona ,
Da sauri ya riƙo ta ya kama hannuwanta duk biyu zuwa cikin ɗakin sa ya zarce da ita cikin bathroom , gefen Bath ya zaunar da ita , duk a ruɗe yake da ihun da take yi ya kunna fanfo lokacin da ya ɗauki handle ɗin shower yana tara ruwa a hannun sa , ruwan ya kai ya wanke mata fuskar da shi ya sake cika hannun sa ya wanke mata ,
Yayi hakan sau kusan huɗu amma bata daina kukan da take yi ba , sai kawai ya juya shower ɗin ya shiga fesa mata ruwan a fuska yana haɗawa da wanke mata idon sosai da ma fuskar ta baki ɗaya ,
Hannun sa ta ture lokacin da ta ji raɗaɗin ya ragu sosai , ta fara ƙoƙarin buɗe ido ,
" ya ya ? Ya fita ? Ya tambaye ta cikin taushin murya bayan ya ɗan yi durƙuso a gaban ta yana leƙen idon nata so yake ya ga ta buɗe su ,
Tana buɗe idon ta runtse su da ƙarfi jin har yanzu da sauran raɗaɗi , bata ankara ba ta ji ya ɗago haɓar ta ya matso da fuskar sa daf ta ta , hannu ya sa ya tallafe ƙeyar ta ya fara hure mata idon a hankali
Sassanyar iskar bakin sa tayi tasiri sosai wajen rage mata raɗaɗi , ta kuma taimaka wajen dawo mata da nutsuwar ta , har ma ta fahimci irin kusancin da yake tsakanin su , zuciyar ta ta ji ta buga ɗas!
Da hanzari ta buɗe idanun ta da suka ɗan rine suka kunbura kaɗan , suka yi musayan kallo da ita da shi , nitsar da idanun sa yayi cikin nata yana yawo da ƙwarar idanun sa a tsakanin nata , ji yake tamkar wata dama yau ya samu na gano tare da tsamo abunda yake hangowa a cikin ƙwarar idanun ta da yake kashe masa jiki a duk lokacin da ya fiye kallon su ,
Tsintar kan ta tayi da gaza janye idanun ta , fuskar sa dake daf da ta ta take ƙarewa kallo , sajen da ya bari da yake ta sheƙi a hasken lantarki ya ɗau hankalin ta , kamar ta kai hannu ta taɓa ,
Ganin yadda ta shagaltu da kallon fuskar sa yasa shi hure mata ido , da sauri ta sake rufe idanun nata ,
Kamar an farkar da ita sai ta miƙe tsaye da sauri , ta ɗan matsa daga kusan shi sosai sai lokacin ta ankara da jiƙewar da kayan ta yayi sharkaf ,tundaga kan hijabin jikinta har rigar ta ta ciki .
" shine ka jiƙa ni haka ? Yanzu ya zan yi ?
Ta furta hakan muryar ta cike da shagwaɓar dake nuni da damuwar da zuciyar ta ke ciki ,
Miƙewar shima yayi ya ɗan wara hannu kafin ya nuna mata nasa jikin da yake jiƙe shima , yace
" ku ji ta kamar ba ke kika ruɗani ni ba kika sa na jiƙa jikina , raguwa kawai kin sa yanzu dole na sauya kaya .
Kewaye ta yayi ya fita kai tsaye wardrobe ya nufa ya zaro wata jallabiyar ya tuɓe ta jikin sa yana warware ɗayar Yakaka da ta matse ruwan jikin kayan ta ta murɗo ƙofar a hankali ta fito ,
Da fitowar ta da hango shi ba riga da komawar ta cikin banɗakin ta rufo ƙofar da ƙarfi duk cikin abunda yake ƙasa da minti guda ta yi su ,
Doctor Hamza da duk abunda tayi akan idanun sa , har A'uzubillah da tace kafin komawar ta cikin banɗakin duk ya ji ta ,
Ɗan wani guntun murmushi yayi lokacin da wani tunani ya gifta masa nan take , rigar da yayi niyyar sawa ya ajiye a gefen gadon , a nutse ya nufi ƙofar banɗakin , ba tare da ya taɓa ƙofar ba yace ,
" ki fito ki tafi kar a gaji da jiran ki .
Daga ciki ta ce " to ka gama shiryawa ko ? Dan Allah kayi haƙuri ɗazun ban san kana shiryawa bane ,
Ɗan mitsitsin murmushi ya kuma yi yana cije leɓensa na ƙasa a taƙaice yace " eh na shirya ki fito .
Kan ta a ƙasa ta fito , a ɗan sace ta ƙyallo sa ,ta gan shi yadda yake a ɗazu da sauri sake juyawa sai dai kafin tayi wani yunƙuri ya naɗo ta ta cikin jiƙaƙƙen Hijabin ta ya haɗa ta da jikin sa ,
A ruɗe Yakaka ta fara ƙoƙarin ƙwacewa , bakin ta ya gaza furta ko kalma guda , matsera kawai take nema ,
" Meye kike haka , kamar wacce bata saba ganin Maza a tuɓe ba ? Kar ki min kinibibin ku na mata .
Doctor Hamza yace haka laɓɓansa ɗauke da murmushin da yafi kama da na mugunta , cikin zuciyar sa yana sake haƙaƙewa da abunda yayi niyya , ya juyo da ita da ƙarfi ya ɗago fuskar ta da idanun ta ke runtse , hasken da ya haske fuskar shi ya bashi damar ganin hawayen da suka jiƙa mata fuskar ta ,
Shagala yayi da kallon kowanne ɗigo na tudu da ƙwarmin da yake fuskar ta , kallo yake mata irin wanda bai taɓa yi mata irin sa ba , a idanun sa kome na fuskar ta tsararre ne da ya dace ƙwarai da muhallin da Ubangiji ya ajiye mata shi .
Zuciyar sa take buɗuwa tare da tashin tsikar jikin sa, bai san lokacin da ya haɗe tazarar da bata wuce tudun yatsa guda da yake tsakanin fuskokin su ba , ya haɗe fuskokin su waje guda , tare da ratsa hannuwan sa ya kewaye ta da su sosai ,
Da wani irin yanayin da ya zarce yadda yake da nufin yi , ya shiga yin abubuwan da zuciyar sa ta raɗa masa da ya yi a matsayin gwada Yakaka ya ga ko kalaman Suleiman gaske ne Yakakar kamilallar mace ce , tsautsayi tare da kaddarar rayuwa ce suka faɗa mata ?
Sai ga shi ya gaza tantance Yakaka yake son gwadawa ko kuwa martabar sa ta ɗa Namiji yake aunawa ? Domin kuwa a tsakanin lokacin jin sa yake kamar wannan ne lokaci na farko da gangar jikin sa ya fara raɓar na wata ɗiya Mace .
Yakaka da ake yiwa gwaji ita ta yunƙura ba tare da tayi amfani da ƙarfin kirki ba , ta zare jikin ta daga na shi , bata tsaya ba kamar yadda bata yadda ta bari idanun su sun haɗu ba ta taka da gudun gaske ta fice daga ɗakin da sashin nasa ma baki ɗaya ,
Bata tsaya daga gudun da take yi ba sai da ta tabbatar ta bada tazara mai ɗan yawa daga sashin sa .
Zama tayi akan wani ɗan tudu tana mayar da numfashi harabar wajen babu mutane alama dake nuna an riga an tafi Dinner an bar ta .
Kalaman Doctor Hamza ta tuno ," me yake nufin da cewa ta saba ganin maza a tuɓe ? Kenan nufin sa ita wata ƙasurgumar karuwa ce da ta saba cuɗanya da Maza , shi yasa ya mata abunda ya yi mata yanzu .
Hawayen ɓakin ciki ya zubo mata , tayaya zata yi rayuwa da mijin da yake zargin ta irin wannan mummunan zargin ?
Da jaan ƙafa ta nufi cikin gida , kai tsaye ta zarce ɗakin su inda ta tarar da Falmata ita ɗaya ƙwal tana kwance lamo akan gado
Bata ce mata ƙala ba kamar yadda ita ma Falmatan bata nuna alamun ta san da shigowar ta ba , ta cire jiƙaƙƙun kayan jikin ta sauya da wasu , a hankali ta zo bakin gadon ta zauna , ta ɗan dubi Falmata da jikinta yake bata ba bacci take ba ƙoƙarin haɗiye damuwar ta take lokacin da tace , " Falmata baki tafi wajen Dinner bane ?
Ba tare da ta motsa ba muryar ta can ciki tace " Ban tafi ba Yakaka Amnee tace na zauna nima tunda ke ma Yaya Dakta ya hana ki tafiya , kuma ma bana jin daɗin jikina bayana ciwo yake min .
Shiru su dukkanin su biyun suka sake yi , zuciyar kowaccen su na sake ƙuntata da damuwar dake cin ta a rai , can ta tsinkayi muryar Falmata tace , "Yakaka yau kwanan mu ishirin da ɗaya da dawowa daga Niger ko ?
Ɗan waigowa Yakakar tayi ta dube ta , ba tare da ta bata amsa ba tausayin ta ta ji ya kama ta , babu shakka tasan damuwar Falmata ba zata wuce akan Youssouf ba da shima yake gwada nashi walaƙanci a zaton ta ta hanyar yin shaƙulatin ɓangaro da ƙanwar ta .
Washegari duk baƙi na nesa suka fara watsewa ciki har da Malama maryam da duk wasu dangi na nesa suka yi tafiyar su bayan Amnee ta cika su da kayan biki fal .
Zuwa yammaci gidan ya rage sai su isu 'ya'ya da dangin Amnee , lokacin ne kuma Baa ya aika aka ƙira masa Doctor Hamza , bayan sun gaisa nasiha ya shiga yi masa mai ratsa jiki tare da tarin tunasarwa akan nawin da ya ƙaru akan sa , da kuma wuyar da yin Adalci yake da shi wanda kuma dole ne ya tsayar da shi a tsakanin matansa muddin yana son dacewa da samun Rahamar Ubangiji .
Bayan ya gama masa nasiha da hannu ya masa nuni da saitin akwatuna biyu da adadin su yake kai ɗaya kawai launi da sumfurin su ne ya shabanba , kowanne guda takwas , ya ɗora da cewa " Wannan lefen Matan ka ne ɗayar ka kaiwa Safiya da hannun ka , ɗayan kuma na Amina ne , kamar yadda muka yi da kai nan da ƙasa da watanni biyu nake so ka samarwa da matar ka wajen zama a kusa da kai , idan ma kuma wajen zaman ya samu a yau
ko gobe ne ka dawo ka ɗauke ta ku tafi abun ku Allah ya bada zaman lafiya .
Godiya Doctor Hamza ya dunga yi ƙaunar Mahaifinsa na daɗa ratsa shi tare da ƙarin ganin ƙima da darajar sa , har ya miƙe zai tafi Baa ya sake dakatar da shi wata ɓakar leda da take nannɗe ya miƙa masa "wannan kuma wasu kuɗaɗe ne da aka bani na baka a matsayin gudumawa , ka ƙara wajen kula da gida ,
Da sauri Doctor Hamza ya noƙe hannun sa ," Baa ka bar su ayi amfani da su anan , ni ina da kuɗin da zasu isa nayi kome da su Nagode Baa nagode .
Da murmushi a fuskar sa yace" karɓi mana ai ni na baka .
Ƙarfe biyun rana Doctor Hamza yayi Sallama da iyayen sa zai koma Abuja a yau ɗin saboda gobe yana da tarin aiyuka a office da bashi da damar ɗaukar musu uzirin jinkirta yin su .
Dangin Amnee ma ya musu Sallama bayan ya bada kuɗaɗe masu yawa da yace ayi musu sayayyar duk abunda suke so kafin tafiyar su , sannan ya tsawaita godiyar sa a gare shi .
Da Khaalty Rahima ma sallamar su ta musamman ce da suka keɓe suna yi ta inda ita ma ta ɗora masa 'yar nasihar ta a ƙarshe ta ba shi shawara kan ya lallashi Safiya sosai kar ya bari ƙarin auren da yayi ya ɓata zamantakewar su .
Ƙannen sa mata ma duk Sallamar yayi da su har da Rahima amarya da ba'a riga an miƙa ta gidan mijin ta ba saboda iyayen sa ba 'yan nan bane 'yan ƙasar katsina ne , kuma a halin yanzu duk suma shirye-shiryen komawar su suke can ƙasar America inda suke rayuwar su a can , nan da ƙasa da sati biyu zasu tafi tare duk har da Rahima .
Lokacin da ya gama Sallama da kowa da ya dace , ciki har da Falmata, sai ya shiga ɗan jefa ido waje-waje ya gagara tashi ya tafi , sai daɗa jaan hirar su yake shi da ƙannen sa .
Hajja wacce ita ma tun a waje da ita ya fara cin karo tana tattara harabar gidan suka gaisa har ma ya mata sallamar tafiyar sa ta jero masa addu'o'in da yake jin daɗin irin su ,
Ita ce ta shiga tana ganin sa tace ," Babban likita har yanzu baka tafi ba ? Kai kuwa na ga baka saba tafiyar dare ba garin Abuja ai ba kusa ba , dan ma dai ku manya ne .
" yanzu zan tafi Hajja , yace yana ƙoƙarin miƙewa , Hajja ta shige ɗakin ta tana cewa " Allah ya tsare hanya Babban likita .
Tana shiga ɗakin tayi turus ganin Yakaka kwance akan katifar ta tana buga game da wayar Rahima ,
Salatin da Hajja ta ɗauka sai da ta dire shi da tafa hannuwa sannan ta ɗora da cewa " ni hauwa'u me zan ji me zan gani ? 'yar nan kan ki ɗaya ?
Yakaka ta ɗago kai tana kallon Hajja ,
" me nayi Hajja ko dan na hau 'yar katifar ki ? to bari na tashi , ta ce tana miƙewa ta sauƙa daga katifar ,fatan ta shine Hajja tayi shiru kar a jiyo muryar ta a san tana nan .
Hajja ta ɗora da cewa " tambayar ki nake kan ki ɗaya ? Yanzu ace Mijinki na can shirin ɗaukar doguwar hanya ke kina nan kina latse-latsen wofi ? Bawan Allah shi yasa mana ya gagara tafiya ashe ke ce baki masa abunda ya dace ba wanda zai ƙara masa kuzari da nishaɗin tafiya , tashi nace sakaryar mata , tashi ki fice min a ɗaki , ki fita ga mijinki can yana jiran ki kuyi sallama .
Hafsa da zainab da duk abunda Hajja ke cewa daga ɗaki suna jin ta sarai saboda sama-sama take maganar sai suka haɗa ido kafin su duka ukun su kwashe da dariya , Falmata ma sai da ta ɗan dara , a ran ta tana aiyana wannan kaɗan ne daga halin Hajja , yadda aka san bata da wani aiki sai na faɗin yadda mace za ta farantawa miji Ho Hajja , ya dace a bawa Hajja shugabantar wata ƙungiya ta faɗakar da mata kan yadda ake tafiyar da Miji .
Hafsa ita ta rage dariyar ganin yayan su na tsaye yana kallon su , ita ma sai ta ɗan ɗaga murya lokacin da take miƙewa tsaye tace , "Ƙanwata Amarya ki fito kuyi sallama big bro zai tafi idan kuma ma mu kike jin kunya , kun ga ku zo mu bar wajen tace da sauran 'yan uwan ta , nan take suka miƙe suka yi ɗaki suna ƴar dariya tare da sake yiwa yayan su fatan Allah kiyaye hanya ,
Doctor Hamza da yake tsaye hannun sa a zube cikin Aljihun rigar rigar jumfa jikin sa , ya ɗan gyaɗa musu kai da murmushi a fuskar sa , shi ɗaya ne ƙwal ya rage a falon .
Ganin sa ya mayar kan ƙofar ɗakin Hajja lokacin da Yakaka ta buɗo ƙofar ta fito kan ta a ƙasa fuskar ta kadaran-kadahan , ɗan matsawa kaɗan tayi ta bayan kujerar falon ta ɗan durkusa , " ina yini yaya dakta ,
Bata jira ya amsa ba ta ƙara da cewa " Allah ya kiyaye hanya ,
Bata yarda ta dubi sashin da yake ba bare ta san cewa ya matso kusan ta sai da ta miƙe tana shirin wucewa ta shige ɗakin su da yake kusa da ita , sai kawai ta ji ya riƙo hannun ta ,
A hankali ya jawo ta ya kusan haɗe jikin su , hannuwan sa yasa ya kewaye kunkumin ta , yana kallon fuskar ta da taƙi yadda ta ɗago kai , muryar sa ƙasa-ƙasa yace " haka ake yin sallama ? Babu addu'a ? Baki ji Hajja tace ki min abunda zai bani kuzari bane ?
Da sauri ta ɗago kai , signal ya mata da duk girar idanunsa biyu , yana 'yar dariya da fararen haƙoran sa da suke da kyau sosai akan fuskar sa mai rangwamen haske .
Ɗauke kai Yakaka tayi gefe can cikin ranta tana mamakin meyasa ta hango kamar sauyin mu'amala a tare da shi daga jiya zuwa yau ? muryar ta cikin sanyin tace " ai nace Allah ya kiyaye hanya na yi addu'a ,
Hannun yasa ya sake juyo da fuskar ta saitin sa , ya zarce da sanya ɗan yatsan sa ya shafa saman idon ta , da yasa Yakaka ta lumshe idanun ta da sauri , " Ya idanun ki sun wuce ko ? Basu sake damun ki ba ko ? Ya tambaye ta da ragwan sauti ,
gyaɗa kan ta tayi tana ƙoƙarin kautar da fuskar ta , amma ya ƙi bata damar haka sai ma hannuwan sa duk biyu da yasa ya tallafi fuskar ta yana shafa kumatun ta masu taushi yace ," to ina saurarar ki ki min Duas kuma ki min abunda Hajja tace ki min , ko bakya so na samu kuzarin tuƙin ne ?
Sallamar wata baƙuwa ya sa Yakaka ta fisge jikin ta da ƙarfi da daman baki ɗaya a takure take damar gudu take ta son samu ,
Sai dai bai bata damar gudun ba ya riƙe hannun ta lokacin da suke gaisawa da matar ya san ta ɗaya daga cikin mutanen Amnee ce , ta zauna akan kujera.
" Ba za ki min Duas ɗin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 82 Chapter of 103