Me yake faruwa na gan ka haka hankali tashe ?
"Wai Fatima-zahra ta ɓace tun jiya ba'a gan ta ba .
Ya furta hakan lokacin da yake ƙarasawa gaban bishiyoyin da a jiya ta ɓuya bayan su , bai jinkirta ba ya tsallaka bayan bishiyoyin yana ƙiran sunan ta da wani irin sauti .
Sasakai! Siyama tayi tana cikin yanayi mai kama da almara wai Fatima ta ɓata shi kuma Youssouf ya zo neman ta nan bayan shukoki anya Youssoufa ba matsala ya samu cikin ƙwaƙwalwar sa ba ? idan ba haka ba me zai kawo Fatiman nan bayan shuke-shuke'?
Haka ya gaji da bankaɗa ganye ya fito jikin sa duk ya ɗau ƙura idanun sa sun yi jawur .
"Baban Yumna Fatima kake nema anan kuma ?
Cikin duƙusasshiyar murya yayi mata nuni da wajen yana cewa "anan jiya mun ka shiga ɗaki mun ka bar ta, kafin zouwan ki ina tare da itta a can
Ya ƙarasa zancen da nuna mata bakin barandar sa kafin ya ɗora da cigaba da cewa " Ina Fatima zata sake tafiya ta bar ni ?
Kamar ruwa ya cinye ta Siyama tayi shiru , zuwa yanzu ta fahimci abunda yake nufi da neman ta anan ashe ma jiya sun haɗu har sun gana? Ita har sokuwar zuciyar ta ke kambama ta a matsayin wacce ta fara kasancewa da Youssouf ɗin a jiya ashe hasashen ta bai zama gaskiya ba koyaushe alfarmar Fatima take ci daga wurin sa muddin ta samu cikakkiyar kulawar sa to Fatima ce ta mata tubalin ginuwar farin-ciki da nishaɗin sa .
Bata ankara ba ta ga ya sake wuce ta yayi hanyar fita daga sashin nasu , da sassarfa ta bi bayan sa .
Bayan kamar awa biyu labarin ɓatan Falmata ya fara zagaye masarautar bayan shafe fiye da awa guda da bayun gidan suka yi suna neman ta a cikin gidan amma ko wanda yace ya gan ta ma ba'a samu ba bayan masu gadin shiyar Youssoufa da suka bada tabbacin shigar ta da fitar ta daga sashin .
Zaman dirshan Youssoufa yayi a falon Hajiya Umma yana jin wani irin bugu da ya wuce ƙima da zuciyar sa ke yi .
Hajja kuwa zuwa lokacin ta fara sharar hawaye da gefen mayafin ta .
Ubbo wacce take cike da takaicin damuwar da ɗan uwan ta yake shiga ta sanadin Falmata tace
"To wai za ta ɓata ne ? Sai dai idan da ƙafafun ta ta fice doumin kouwa ai hakan bai zama sabon abu ba wajen ta .
Kallon ta Youssouf yayi zai ce wani abu Hafsatouwa wacce ita ce ƙarshen dawowa daga neman Falmata da aka fantsama su tayi gurfano a gaban su hannun ta riƙe da cukurkuɗaɗɗen Mayafi.
Da hannu biyu ta miƙawa Youssoufa kafin ta ɗora da cewa " wannan mayafin can wajen ƙofar fita gida ta ɓangaren kudu na tsinto shi wanda kuma nayi hasashen ya.....
Miƙewar da Youssouf yayi riƙe da mayafin ya sa ta yin shiru duk suka zuba masa ido .
Yana riƙe da mayafin ya kai shi ga hancin sa yana shinshinawa kafin ya ɗago kan sa da wani irin sauti yace "lalle wannan shine Mayafin da ta rufu da shi a jiya .
Ita ma Hajja gyaɗa kai tayi cike da tabbatarwa tace "ƙwarai wannan mayafin Fatima ne to ita tana ina ?
Muryar Hajiya Mama da ta ratso wajen ta katse musu hanzari inda take cewa "wannan alama ce da take nuna yarinyar nan an fita da ita daga gidan nan ne ta ƙarfin tsiya kuma babu makawa sace ta aka yi .
Wani ƙaƙƙarfan kuka Hajja ta sa wanda ya ratsa zuciyar Youssouf ya tarwatsa duk wata nutsuwa da ta masa saura .
"Innalillahi wa inna ilaihi raji'oon yanzu wanne azzalumin ne ya ɗauke yarinyar nan a wannan yanayin da take ciki na shiga uku ni hauwa'u 'yar mutane ta ɓata a hannun mu .
Hajja ta furta hakan tana rufe fuskar ta da mayafin ta ta shiga rera kuka .
Shigowar Babbar jakadiya yasa kallon su ya koma kan ta , saƙon Maimartaba ta isar inda take shaida musu kan cewa baki ɗaya yana neman su a shiyar sa a yanzu-yanzu da gaugawa.
Ba a ɗau lokaci ba dukkanin su daga kan Hajiya Umma , Hajiya Mama da su Ubbo duk suka cika falon Maimartaba suka yi zaune suna sauraron sa .
Bayan duk sun nutsu yace "wani labari ya zo mana Fada kan cewa wannan ɗiya ta Nigeria ta ɓata a cikin gidan nan yaya gaskiyar lamarin yake ?
Shiru duk suka yi kafin Hajiya Umma tace "Hakane ran ka ya dade amma duk cikin mu babu wanda yake da masaniya kan haƙiƙanin yaya lamarin ya kasance domin ba'a gan ta a gida ba ba'a ga kuma wanda ya ce ya ga ficewar ta ba .
"Rashin tsaro a gidan har ya zama haka da za'a nemi mutum sukutum a rasa ?
Maimartaba ya furta haka da bayyanuwar matsanancin ɓacin-rai a fuskar sa .
A hankali Ubbo tace "Ranka ya dade Allah ya daɗa maka nisan kwana ka cigaba da jagorar mu ni nafi tunanin Yarinyar nan ba ɓata tayi ba sai dai tafiya tayi da kan ta kamar yadda ta taɓa yi daga Niamey zuwa ƙasar su dan...
Da wani irin sauti saɓanin wanda aka saba amfani da shi a masarauta yayin da ake gaban sarki Hajja tace " 'Yar nan wannan zancen naki ba gaskiya bane muddin kuma ya zama gaskiya to kune sanadi , saboda abubuwan da kuke yiwa yarinyar nan na tozarci kaɗai ya isa yasa ta zuciya ta bar gidan nan haba mana shin shi talaka ba mutum bane ? Ko kuwa laifin tayi domin ta auri ɗan uwan ku ? Fatima baiwar Allah yarinya ce ƙarama da take da larura wanda idan har baku gwada mata ƙauna ba bai kuwa dace ace kuna tozarta ta ba yanzu me za'a ce ga iyayen ta da kuka yi sanadiyar da ta gudu ba'a san halin da take ciki ba ?..... kasa cigaba tayi da magana saboda kukan da ya ci ƙarfin ta
Hajiya Umma ta yunƙuro zata yi magana da hannu Maimartaba ya dakatar da ita .
"Me yake Faruwa a gidan da ni ban kai ga sani ba ? Waye yake tozarta Al'umma ciki har ma da mutanen da suke amintattun mu da muka amso amarnar su daga hannun mutanen su ?
Shiru aka yi babu mai tsaurin idon iya amsawa .
Kamar daga sama Muryar Youssouf ta ratso wajen inda yake cewa " Fatima ba gudu tayi ba babu makawa ɗauke ta aka yi ..
Ya ɗan jinkirta lokacin da idanun kowa ya dawo kan shi zuciyar Hajiya Mama ta fara sauya ƙarfin bugu tana dik-dik-dirim-dim.
"Wa kake tunanin ya ɗauke ta ?
Maimartaba ya furta haka cike da nazarin sa ,
Shiru yayi da yasa gumi ya shiga zarya ta cikin rigar Hajiya Mama .
"Maimounatou .
Ya furta hakan da tasowar matsanancin ɓacin rai a muryar sa , ya cigaba da cewa
"Maimounatou ita ta sanya a zo a ɗauke Fatima domin cikar burin ta ta wani fanni sai dai a wannan karon ba zan kyale ta ba dole ne na gwada mata ainashin ɗabi'ar da na ɗau shekaru a wajen koyar ta cikin aikina na na soji .
Muryar Hajiya Mama ita ta ratso wajen cike da wani boyayyen farin-ciki a sautin ta tace " Yarima ni da kaina tunanin da ya fara zowar min kenan ba shakka wannan ɗiyar ta Agades ita ta sanya anka ɗauke wannan yarinya ta ƙwarai kuma dole ayi hanzarin ɗaukar mataki akan haka.
Shiru Maimartaba yayi cikin son yin nazari sai dai hayaniyar da ta fara tashi a tsakanin iyalan sa da duk suka aminta da cewa Maimounatou ce ta tura aka sace Falmata duk kuwa da babu hujja ɗaya da aka samu wanda yake bada tabbaci ga hakan ya dukusar da hanzarin sa musamman lokacin da Youssouf ya miƙe a safure ya taho gaban shi yayi gurfano .
"Ranka shi daɗe zan tai Niamey yanzu zan tai na tadda Maimounatou ta faɗa min ina ta kai iyalina ?
"Youssoufa ka nutsu wannan batu ne da yake buƙatar nutsuwa da tsawaita bincike , ina maka oumarni da ka jinkirta hanzarin da kake yi har a ƙarƙare bincike a samu madogara .
Da kyar Maimartaba ya shawo kan hayaniyar su bayan ya tabbatar da za'a tsananta bincike kafin tunkarar koma waye da aka samu shaidar yana da hannu a ɓatan Falmata
Bayan fitar su daga Sashin Maimartaba Hajiya Mama bata koma sashin Hajiya Umma ba kai tsaye sashin ta ta koma ba tare da ta zauna cikin 'ya'yan ta da suke ta hira kan batun ɓacewar Matar Youssouf da wasu daga ciki ma daɗin lamarin suke ji saboda ta riga ta gina ƙaƙƙarfar ƙiyayya tsakanin su da Youssouf da duk wani abu na bakin-ciki da zai faru da shi su murna suke yi .
Can ƙuryar ɗakin ta ta shiga ta fara kai kawo cike da tunanin kan mataki na gaba da zata ɗauka wajen cigaba da tsare Falmata dan kada a samu wani lamari ya gifta da asirin ta zai shiga hatsarin tonuwa
A ɗan firgice ta waiga jin motsin shigowa ɗakin Hafsatouwa ce ta ƙaraso gaban ta da sassarfa bayan ta rufe ƙofar .
"Hafsatouwa sirrina yana cikin haɗari ya zama dole ki shirya ki tafi Zuru wajen mai jar-tawada ki amso min wani gagarumin aikin da zai kurumtar , ya makantar idan ya kama ya gurguntar da duk wasu da zasu iya kawo min tsaiko kan ƙudiri na ne ma duk ayi .
" a min aikin da zai shafe tunanin ita kan ta yarinyar nan da ta san sirrin na sannan a mantar da duk wasu makusanta nata daga tunanin ta har sai lokacin da na gaji dan kaina da hukunta ta na sake ta , ke Hansatouwa ina so na zama ni nice , kowa kuma ya zama ba kowa ba , ina nufin kowa da kowa na cikin masarautar Maradi su dawo ƙasan iko na a baɗini da fatan kin gane ?
Cike da jin tsoron yanayin da take hango uwargiyar ta a ciki hafsatouwa ta shiga gyaɗa kan ta .
"Oumarnin ki abun bi ne ranki shidaɗe uwargijiya ta mai girma .
"Da kyau to ya ya kin yi abunda nace kiyi ?
"Ranki ya daɗe tuni nayi .
"Kin ji motsin ta ko kaɗan daga inda take ?
" ba wata alama dake nuni da cewa akwai rayayyen mahaluki a bigiren da alama yarinyar bata da taurin kai .
"Idan ta yi haka ta sauƙaƙawa kan ta riskar wasu daga cikin tarin horon da nake mata tanadin su .
"Kina iya tafiya yanzu , idan buƙatar son ganin ki ya zo zan aika a min ƙiran ki .
" To ranki ya daɗe godiya nake .
Gaf da Azahar bayan hankulan mafi yawan mutanen gida ya tafi ga haramar sallah Hajiya Mama ta kashe jiki ta nufi tsohon sashin babar ta kuma Uwargidan Sarki Azizou Baskore "Hajiya Uwa .
Da tun bayan rasuwar ta sama da shekaru goma sha takwas babu wanda ya sake zama a sashin ya zama tamkar kufai , sai fa Hajiya Mama da jifa-jifa take zuwa sashin tana yin wasu abubuwan da ta ce raya sashin take yi da yake a matsayin na uwa a gare ta wanda kuma a baɗini daga Allah sai ita sai kuma tsirarun mutanen da tayi haɗakar ƙulla sirrukan ta da su , suka san ainashin abunda take aikata a sashin a duk ƙarshen kowanne wata .
Bayan ta gama nazarin wajen ta tabbatar babu wani mahaluki a wajen da zai iya jin abunda za ta yi ta sanya ɗan makulli ta buɗe ƙofar falon bayan ta ɗau wata leda da take yashe daga kusa da ƙofar .
Kan ta tsaye ta shiga falon ta tura ƙofar ta rufe tana mayar da ganin ta kan Falmata wacce take takure daga can gefe cikin datti da ƙurar da ta maye gurbin shimfiɗar ɗakin ya zama duk inda ka ɗora ganin ka datti ne da tankaɗaɗɗiyar ƙasa kamar an kwaso an zuba ba'a ko iya ganin ainashin dandaryar ɗakin .
A hankali Falmata ta ɗago kan ta dake tsakanin cinyoyin ta da ta haɗa su ta takure ba'a ce mai ciki bace .
Taku tayi ta ƙarasa gaban Falmata tashin sautin ta ya biyo bayan ledar da ta wurgawa Falmata
" wataƙila kina jin yunwa ki ɗau abinci ki ci ya rage naki ki cinye shi duk ko kuma ki rage dan anjima .
Falmata da fuskar ta ta kumbura saboda kuka ta buɗe bakin ta da take ji ya mata nawi muryar ta bata fita sosai tace "Sallah nake so nayi ki nuna min wajen da zan yi Alwala .
Wani kallon banza Hajiya Mama ta mata kafin ta ƙuta , sai da ta mula sannan tace " ga rairayi nan kina zaune a cikin sa ki buga ƙasa kiyi taimama .
Bata jira ba ta cigaba da cewa " ina sake jaddada miki muddin kina son tsira da rayuwar ki to ki kiyaye abunda zai sa a san kina nan , idan kuwa kin ƙi ji .?
Da zubowar sabbin hawaye Falmata tace "Hajiya Dan Allah ki tausaya min , ki ji tsoron Allah mahalicci da yake kallo tare da jin kowa da kome , ban yi miki kome ba .....
"Ke .
Hajiya Mama ta daka mata tsawar da ya sa Falmata yin shiru " kina son karya doka ta ne ?
Da sauri Falmata ta girgiza kai .
"Tashi , tashi nace ko ?
Da kyar Falmata ta miƙe saboda ƙafar ta da ta ji ciwo a jiya ga yunwa da ƙishirwa , sun sa har jiri take ji bayan ciwo mai tsanani da kan ta yake yi , ta ɗingisa dakyar ta bi bayan Hajiya Mama wacce tayi gaba zuwa wata ƙofa ran ta cike da fatan "Allah yasa afuwa zata mata ta fitar da ita daga wannan wajen .
Da kallo ta bi ɗakin da su shiga wanda ba kome a cikin sa bayan tulin ƙura da yanar-gizon da ya zarta na falon sai fa wani karmamin gadon katako da duk gara ta cinye shi shi ɗaya ƙwal a ɗakin.
"Anan za ki cigaba da zama , ga banɗaki nan a ciki amma bani da tabbacin rasa macizai da kunamu a ciki sai ki kula wajen amfani da shi idan ba haka ba kin ga sun hutar da ni daga kashe ki.
Daga haka Hajiya mama ta juya da kusan tare suka juya da Falmata wacce ta zube a ƙasa tana wani irin kuka ta riƙe ƙafar Hajiya Mama tana shisshiƙa kamar ran ta zai fita tace "Hajiya Dan Allah , Allah .....
Hanɓare ta Hajiya Mama tayi ta taka da sauri kafin Falmata ta yunkura ta fita ta rufo ƙofar ta murɗa ɗan makulli .
Tare suke da page 51b
[4/15, 10:16 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
( hargitsin Rayuwa )
Umm"muaz
51b
Duk yadda Maimartaba yake tunanin za'a yi samu wata alama da zai nuna ina Falmata take anyi amma babu nasara har aka kwana aka yini babu wani bayani takamaimai na inda take .
Zuwa lokacin kuwa Biyamuradi Youssouf gaba ɗaya ya gama birkice musu ya kuma matsa lamba kan son zuwa Niamey wajem Maimounatou dan ta faɗi inda ta kai Falmata.
A ƙarshe ba yadda maimartaba ya iya ganin yadda ɗan nasa ya zama yasa ya masa umarnin tafiya bayan ya masa nasiha akan haƙuri da mallakar zuciyar a duk lokacin da rai ya ɓaci sannan ya gargaɗe shi da gujewa ɗaukar mataki cikin fushi .
Ƙarfe goma na ranar jirgi ya ɗaga da shi da Bilal da zai masa rakiya zuwa Niamey .
Bayan tafiyar Youssouf Hajiya Mama ta ƙira Hafsatouwa ta umarce da cewa gobe da sassafe ta kama hanyar Zurun Jahar kebbin Nigeria bayan ta danƙa mata isassun kuɗin da zasu ishe ta .
Duk da cewa Falmata baƙuwa ce a masarauta Maraɗi amma hakan bai hana masarautar ta zama cikin alhini ba kasantuwar ta riga ta zama wani ɓangare na gidan , ko'ina ka ratsa za ka ji bayun gidan suna batun ɓacewar Gimbiya Fatima da cikin jikin ta .
Hajiya Umma da kan ta ta shiga damuwa musamman da ya zama Maimartaba yana ganin har da sakacin ta wajen ɓatan Falmata da har a jiya da dare ya tabbatar mata da hakan cikin fushi .
Hajja kuwa ƙurewar tashin hankali ta shiga tayi kuka har ta bawa aku lada ta haƙura ta rungumi charbi tana addu'ar Allah ya baiyana mata uwarɗakin ta a halin lafiya .
Niamey .
Lokacin da Youssouf ya isa Niamey daga airport kai tsaye babban ofishin 'yan sanda ya nufa inda har lokacin ake cigaba da tsare Mammadou da Maimounatou sakamakon rashin sanin halin da shi yake ciki da hakan ya kawo jinkirin miƙa su kotu a musu hukunci .
Bayan ya cike takardu aka masa iznin ganin su da Mammadou ya nemi ganawa a farko .
Lokacin da aka fito da Mammadou , Youssouf da yake zaune bai san lokacin da ya miƙe ba da sauri ya taka ya taro Mammadou da yake tangaɗi , ba tare da ya damu da tsami da warin da yake tashi daga jikin Mammadoun ba ya kama shi suka zauna .
Da wani irin yanayi a fuskar sa mai tsauri yace "Mammadou ƙaƙa ka zama hakka ? Shin baka da lafiya ne ? Ko kouwa horo ake maka ?
Mammadou da zuciyar sa ta cika taf da farin-cikin ganin Youssouf ya riƙo hannuwan sa duk biyu kafin ya fashe da matsanancin kuka cikin kukan yake cewa "Youssoufa kai min gafara , ka yafe min ɗan ouwana na tuba ka yafe min , nayi nadama marar amfani na kouma yi tir da muguwar uwa irin tawa tare da.....
Da sauri Youssouf ya katse shi yana cewa "Mammadou kar ka tsawaita zance domin ba shi da wani amfani dan kouwa ba zai yi gyara cikin abun da ya wouce ba kouma zouwa ma nayi mu tai gida tare nan ba wajen yin zance bane Mammadou .
Cikin wani irin sauti Mammadou yace "da gaske Youssoufa zowa kayi ka tafi da ni gida ?
Miƙewa Youssouf yayi yana zube hannuwan sa cikin aljihu ya fara taku yana barin wajen ƙarƙashin rakiyar idanun Mammadou da ya bi shi da kallo sai da ya kai ƙofar ficewa daga wajen bai jiyo ba yace "ƙwarai yau kake kwana a gida Mammadou .
Daga haka ya fita yana jin yadda tattaurar zuciyar sa ke son tasowa ta hana shi duk wani afuwa da sassauci da yayi niyyar yi ga ɗan uwan nasa .
Ya juya baya ga ƙofar shigowa lokacin da aka taso ƙeyar Maimounatou ta shigo inda yake idanun ta da suka shige ciki ta ware tana kallon sa a take ta shaida ko wanene a gaban ta , sannan 'yar murna da ta fara safko mata jin cewa an zo ganin ta ta koma ciki fargaba mai girma ya mamaye ta da yasa har wasu siraran gumi suka fara tsiyaya ta cikin rigar ta .
cikin raggon taku ta nufi inda yake sai dai kafin ta ƙarasa ya juyo baki ɗayan sa yayi tsaye ƙem a gaban ta da juyowar sa tayi hanzarin sauƙe idanun ta ƙasa tana jin wani yanayi da ta gagara tantance a wanne matsayi zata ajiye shi "kunya ce ? "Nadama ce ? Ko kuwa tsoro ne ?
Bata ankara ba ta gan shi daf da ita kamar an tunkuɗo shi hannuwan sa zube cikin aljihun wondon sa da sautin sa mai amo da ya sake kaurarara yace "Madame, êtes-vous surprises ?
Wani murmushin yaƙe Maimounatou tayi da ya taho da ɗoyin da bakin ta ke yi , ta ɗago kan ta ta saci kallon sa kafin ta wani karya kai gefe ɗaya cikin muryar da ta saba hilatar sa da shi wacce yau ta sake matsewa tace "Pas vraiment, tu ne m'as pas surpris, je sais que tu reviendras vers moi.
Hannun ta ta miƙa da nufin taɓa shi ya jaa baya da sauri yana kokuwa da ɓacin ran sa da idanun sa da suka yi jaa ya mata wani kallon gargaɗi da ya kaɗa mata ciki .
Da baya-baya ya dangana da kan kujerar da take gaban ɗan teburin da yake cikin ɗakin ya zauna yana harɗe ƙafafun sa ɗayan kan ɗaya yace.
" idan kin ka yi tounanin kina da watta sauran dama guda da ta rage miki a gareni kin yaudari kan ki yau ba rana ce ta wassa ba don haka Arrêtez de jouer avec votre propre cœur et de vous dupe.
Wani murmushin ta sake yi kafin ta yi ɗan taku kaɗan tana juya baya ga barin fuskantar sa cikin ƙarfin hali tace " Bana neman watta dama dagga gare ka a yanzou sabbada kuwa duk watta dama na riga na same ta har ma......
Tsawar da ya yi haɗi da buga teburin gaban sa shi yasa ta juyowa a firgice , a tsaye ta gan shi fuskar sa da ta duba a lokacin ji tayi marar ta ta cika fam.
Ya matso daf da ita yana nuna ta da yatsan sa ya ce "kadda ki min wassa , ni damisa ne da ban juri wasa ba ban ɗauki wargin mazaje ba a fagen daga na sanya bakin bindiga na fasa ƙoƙon kan su na sa ƙafafu na taka cikin su kar kiyi zaton zan miki sassauci ,
hannun sa ɗaya da yake cikin aljihun sa ya zaro da yake riƙe da ƙaramar bindiga , yayi taku kaɗan zuwa baya kafin ya cigaba da cewa "zan iya tarwatsa kan ki da harsashi bayan na tattaka ki muddin kin ka cigaba da min fi'ili .
Kafin ya mayar da numfashi Maimounatou ta zube akan guiwowin ta ta haɗa tafukan ta biyo tana sakin wani mitsi-tsin kuka mai tafe da sautin tsoran da ruhin ta ke ciki tace jikin ta na ƙyarma tace ,
" Dan Allah kayi haƙuri kar ka kashe ni , wallahi sharrin shaiɗan ne ya sa na aikata abun da na maka ka yafe min .
Wani guntun murmushi Yayi kafin tace
"Ashe kina tsoron Mutuwa ? Ni kuma kin ka nemi kashe ni ? Babu yafiya a tsakanina da ke ko afuwa ba zan iya miki ba muddin baki sanar dani dalilin da yasa kin ka nemi raina ba?
Da sauri Maimounatou tace "wallahi zan faɗi dalili .
Komawa yayi ya zauna yana ƙoƙarin sassauta fushin zuciyar sa yace "Vous avez seulement 30 minutes.
Kamar an kunna radio Maimounatou ta shiga ba shi labari tiryan-tiryan tana yi tana kallon sa tana karya wuya da sharar hawaye .
Bai katse ta ba har sai da ta kai ƙarshe
Kan sa a ƙasa yace "menene gaskiyar cewa da kika yi Mammadou ya kawo gubar da kin ka ciyar da ni ?
Girgiza kai tayi cikin ƙaramar murya tace .
"ba shi bane ni na aiki Gnala ta sayo min . sannan cikin kuka ta cigaba da cewa
"Amma wallahi nayi nadama iyakar nadama dan Allah ka min afouwa ka sake bani dama na gyara kuskurena wallahi wannan karon da dukkanin zuciya ta zan zauna da kai zan tallafi soyayyar da kake '.....
Ɗago da kan sa da yake sunkuiye yayi yana ɗan buga tafin hannun sa akan teburin gaban sa yayi wani murmushi mai ciwo .
"Soyayya ? Yanzu kina zaton har kawo yanzu akwai sauran ɗigon na alamar son ki a raina ? Bayan duk abun ƙi da kin ka wanzu wurin aikata shi a gareni..
Huci yayi yana danne ƙiyayyar ta da yake ji mai karfi tana naso a cikin ran sa daga lokacin da ta ambaci sunan Ghaddafi Yacouba Dango a matsayin mutumin da ta nemi kashe shi a kan sa bayan irin ha'intar sa da tayi ta dunga yaudarar sa da sunan soyayya har ya aure ta bayan sun gama tanbaɗewar su da wannan riƙaƙƙen ɗan ta'addan haƙiƙa Maimounatou guba ce ba domin yana yaƙar zuciyar sa da babu abunda zai hana ya harbe ta a lokacin .
Ya tsaya faɗa mata matsayin da take kai a wajen sa a yanzu tamkar ɓata lokaci ne ko kuwa bata wani matsayi na daban da ya wuce wanda takai kai yanzu a wajen sa dan haka ya mayar da ganin sa gefe daga kan fuskar ta da alokacin yake ganin ta da muni fiye da duk wani mummunan abu da ya taɓa cin karo da shi a tsawon rayuwar sa .
"Ina kin
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 90 Chapter of 103