ina biɗar ganawa da Major Youssouf Abdoul-azuzou Youssouf Baskore .
A ɗan firgice Gnala ta ɗago kan ta tana duban uwargijiyar ta , jin yadda yau ta ƙira sunan Yarima garan-gatsau babu wani sakayawa bare girmamawa , sai dai yadda ta ga fuskarta ta tsorata ainun , dan haka ta miƙe jiki na rawa ,ta fice tana cewa ,
" Allah shi huci ranki Gimbiya ɗiyar Sarki .
sanin da tayi bata da ikon shiga sashin Siyama kai tsaye , sai da kamun ƙafar Rakiya shugabar hadiman sashin da ita ce zata yi mata jagora , yasa ta ratsa dogayen bishiyoyi da shuke-shuken farfajiyar gidan ta cimma Rakiya a shiyar ƴan aiki ,
Da kallon banza suke bin junan su , tamkar kishiyoyin da suke zama bala'i, kamar Mai ciwon haƙori Gnala ta buɗe baki da kyar tace ,
" saƙo dagga Gimbiya tace a shaidawa Matar Yarima , gimbiya na biɗar kaɗaicewa da shi .
Rakiya wacce take cin gyaɗa ƴar marau-marau , ta karkaɗa ƙafa bayan ta afa gƴaɗar ta a baki , ba tare da ta dube ta ba tace ,
" kin ga Gnala ki ɗaga sauti kiyi magana yadda zan iya ji amma kin zo kin tsaya akaina kina wani mui-mui da baki ,yo ce miki aka yi aka yi kunnen nawa zuƙo sauti yake ? Aikin banza .
Gnala ta ƙuta , cike da takaicin rashin mutuncin Rakiya.
da ƙaƙƙarfan sauti ta ɗaga murya cikin faɗa-faɗa tana maimaitawa mata saƙon Uwargiyar ta ,
" ah ke saurara haka kar ki fasan dodon kunne ki fallasheni , kin zo kina min hargagi akai ya ruɓaɓɓan radi'o ,
" Naji , sai ki wuce mu tafi , tace tana miƙewa ta zira takalman ta ,
Da wani mummunan kallo Gnala ta bita kafin ta dafa mata baya , suna tafe Rakiya na rera waƙar Barmani mai coge "cikin waƙar ɗuwawai ," inda take cewa ,
A hayayye ɗuwaiwai dole a zauna da ku , to ko ana so , to ko ba' a ƙauna ,ko da sun tsiyaye , wayyo ladi ko a tsidau , kai koma cikin kwata ne .
Daga bakin ƙofa ta nemi iznin shiga wajen Uwargijiyar ta ta hanya matsa mata ƙararrawar dake shaida isowar ta ,
Siyama wacce ta zuba abinci da zummar fara ciyar da Youssouf sai ta miƙe bayan ta ɗau izni daga wajen sa , fahimta da tayi wani saƙo muhimmi Rakiya take tafe da shi a dai-dai wannan lokacin .
Da buɗe ƙofar ta ci karo da Gnala wacce take tsugunne a gaban ta , ba ɓata lokaci ta isar da saƙon Uwargiyar ta .
Murmushi Siyama tayi cikin ran ta tana aiyana " ai shi daman wanzami bai son jarfa ,
Da baya ta dawo tana sanar da Youssouf saƙon Uwargidan sa , jim yayi ," shi ba da gangan yaƙi zuwa wajen nata ba , rigimar ta yake gudu , baya son ta ƙara masa damuwa akan wacce yake ciki ,
Miƙewa yayi tare da yin baya da kujerar dake gaban teburin , tunda har ta sauƙe girman kan ta na ɗiya mace ta ƙira shi , duk kuwa da laifin sa , shi ya zama dole ya tafi gareta ,yayi aikin rarrashi da neman Afuwar ta tunda zuwa yanzu ai yana da ɗan ƙarfin jikin ɗaukar duk wani bore da zata iya yi masa ,
Sai da ya kai tsakiyar falon ya waigo ga Siyama wacce take tsaye jikinta a sanyaye tana bin sa da kallo , dawowa baya yayi , a hankali ya rungume ta , tsawon wasu daƙiƙai , ya sake ta tare da sumbatar leɓɓan ta a tsanake ,
Daf da fuskar ta , ya kawo tashi fuskar cikin muryar da take tsakanin maƙoshin sa yace ,
" Nagode da kome Ƙamnata , je t'aime pour ça, tu es spécial pour moi seulement ,
Ya saketa a hankali ya juya yana barin falon ,
Tsaye tayi a gurin tana shaƙar ƙamshin sa da yayi saura a gurin , ta lumshe ido tana murmushi kaɗan cikin ran ta farin-ciki ne fal ,
" Da gaske yake da yace yana son ta ? Ita ɗin kuma ta musamman ce a wajen sa ? Ko dai duk farin-cikin kusantar dawowar masoyiyar sa ne ?
****
Bayan shigar sa falon Gimbiya Maimounatu wanda yake da rangwamen haske sakamakon ƙasa da aka yi da hasken fitulun falon sosai a tsaye ya hango ta ta juyawa ƙofar baya ,
A hankali ya taka ya isa inda take tsaye , hannunsa ya sanya ya kewaye cikin ta tare da haɗa bayanta da ƙirjin sa sosai ,
Da sigar rarrashi yace ,
" Bana cikin Farin-ciki da ganin ɓacin ran ki princesse, ina bakin-cik...
Da wani sauti daban da wanda ta saba yi masa magana da shi ta katse shi ,
" ya ya kake son samun farin-ciki lokacin da ka kwashi tsawon wasu shekaru kana assasa baƙin-ciki a zuciyar wasu mutanen ?
" ka baranta da farin-ciki ba zaka yi farin-ciki ba har abada kai ma .
Da ƙarfi ya juyo da ita yana laluben ganin fuskar ta , sai dai hasken wajen ya masa ƙaranci .
" kiyi haƙuri Maimounatu ni ɗin mai laifi ne a wajen ki na sani ,
Wani ɗan ƙaramin murmushi mai sauti tayi ,
" haƙuri , laifi ?
Ta ce da sigar tambaya ,
Dariya tayi mai sauti , dai-dai da shigowar ƙira a wayar sa ta cigaba da cewa ,
" Ai ni baka min laifin kome ba kan abunda ka aikata ma rayuwar ka ? To ma menene dan ka rage dare da yaya ka kuma zo ka amri ƙamna ? Ai babu wani laifi ga hakan ni dai ta ɓangarena , dan haka kada ka bani haƙuri bisa wannan ba damuwa ta ce ba .
Jiki a sanyaye Youssouf yake bin ta da kallo , sai yake ganin baki ɗaya ta sauya masa ,
Hasken wayarsa ya kunna tare da cewa ,
" Maimounatu meye ya samu fitilun sashin nan ne ? Hala sun mutu ? Bari za'a sauya wasu ,
" fitilin sashin nan na taya Uwargijiyar su baƙin-ciki ne kamar yadda zuciyata tun-tuni ta kasance a cikin duhun da yake matsananci fiye da wannan , tun a wata ɓakar-rana cikin ranaku da ka sanya bakin bindigar ka ka tarwatsa min fitilar zuciya ta ,
Wayar sa ya mayar aljihu bayan ya ssnyata a silent , da alama sai yayi da gaske da alama ran Gimbiyar ta shi ya kai ƙololuwa a wajen ɓaci , jin yadda take amfani da wasu kalmomin da ya gaza fahimtar su ,
Jawo ta yayi ya zauna tare da ita tana bisa cinyar sa ,
" Duk ki bar waɗannan kalaman Maimounatu , Fatima-zahra ƙaramar yarinya ce , ba zata ƙi ku zauna lafiya ba sann....
katse shi tayi ta hanyar ɗora yatsanta manuni akan laɓɓan sa ,
"shitt , Yarima Youssouf nace kada ka damu ,
Miƙa hannu tayi ta ɗauko tatatcen ruwan 'ya'yan itatuwa da ta sarrafa da hannun ta , ta nufi bakin sa da kofin ,
Jimm yayi yana kallon sheƙin idanunta ta ɗan hasken wajen , dariya tayi yana iya ganin hasken haƙoranta kafin tace da shi
" Sha mana Yarima , abun shan ka ne mafi soyuwa , ni da hannuna nayi sa musamman domin kai .
Ƴar ajiyar zuciya yayi jin alamun ta fara sauƙowa , hannun sa ya ɗora akan nata ya kai kofin zuwa bakin sa , yayi Bismillah ya kafa kai ,
Ya sha sosai saboda ƙishirwar tare da yunwar da ya yini yana ji , ya kuma gagara cin kome sai fa yanzu da ya fara samun nutsuwar zuciya ,
Wata irin damƙa da cikin sa yayi masa kamar kiftawa ido bayan gama sha , shiyasa ya zame Gimbiya maimounatu daga jikinsa ,
Da sauri ya fidda wayar sa daga Aljihu da har lokacin ƙiran Tafeeda bai bar shigowa ba , da hasken shigowar ƙiran ya kai hannu ya ɗau kofin yana haska ciki .
Da wata irin muryar yace ,
"Maimounatou menene cikin wannan juives din ? Meye a ciki ? Meye.. Kasa ƙarasa magana yayi
Gumi ya shiga karyo masa saboda wani irin ciwo mai tsanani da ya ji ya turnuƙe shi tamkar ana filla-filla da kayan cikin sa , zamewa yayi daga kan kujerar bayan ya saki kofin hannunsa zuwa ƙasa ,
Cikin azaba ya ke duban Fuskar ta , yana iya hango wani ɗan guntun murmushin cikar buri da take yi , bata yi motsi ko kaɗan ba wajen ba shi wani taimako
Wani irin gurnanin nishi ya fara yi , ya miƙe a ƙasa yana murƙususu ,ciwon da yake ji bai taɓa jin makamancin sa ba , wani irin duhu mai tsanani yake ji yana sabko masa daga can wani waje mai nisa a kwakwalwarsa Alhalin kunnuwan sa sun samu ƙarin ƙarfin ji ,
Domin yana iya jiyo sautin murmushin laɓɓan Maimounatou , so yake ya buɗe baki yayi ko da addu'a ne amma ya gaza ,
Wani ciwo mai kaifi da ya yanki uwar hanjin sa shi yasa shi burtso da Amai ta hanci da bakin sa , da yasa duhun da yake sabko masa hanzarin ƙarasa saukowa ya rufe masa ido ya daina ganin kome alhalin idanun sa na buɗe da hakan ya yi dai-dai da tsayuwar jijiyoyin jikinsa , kome kuma ya tsaya masa chak .
Da gudu Maimounatou ta tsallake shi tana lalubar wayar ta , jikinta na rawa ta shiga ƙiran wata number ,
Ana ɗaga ƙiran bata jira ance kome ba tace
" ka tahou yanzou aiki ya cika sauran ka ƙarasa naka , ni nagama nawa .
Daga ɗayan ɓangaren Mammadou zuruf ya miƙe tsaye tare da kewaye matar sa ya fita ,
A harabar gidan sa ya tsaya , cikin yin ƙasa da murya yace
" kina nufin yau kin yi nasarar kashe Youssoufa ?
Jin jina kai tayi kafin tace "ƙwarai yau na cimma manufata ta amren sa .
Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kun wayi gari lafiya ?
Alherin Allah ya sadu da mu baki ɗaya .
Nagode [12/29, 9:28 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI
( Hargitsin Rayuwa)
Umm'muaz
46
" Yakaka tana nan zuwa ita ma ,
Ita ce amsar da Falmata ta bawa Maman su , daga nan hira ce ta sarƙe a tsakanin su mai cike da labarin yadda rayuwa ta kasance musu bayan rabuwar su da juna .
****
Tiryan-tiryan Falmata ta basu labarin duk wasu bala'o'in da suka afku ga rayuwar su bata ɓoye kome ba illa mummunar rayuwar da Yakaka tayi da har ta kai ga haihuwar Mama da take jin har abada laɓɓan bakin ta baza su taɓa iya bayyana wannan mummunan labarin ga kowa ba .
Ta cigaba da bata labarin ɓacewar Yakaka bayan haihuwar Mama ba tare da ta faɗi ainahin silar barin su da tayi ba har zuwa kan auren su ita da Youssouf yadda kome ya wakana , da rashin lafiyar Mama har zuwa tafiyar su USA da samuwar lafiyar idanun ta , komawar su Niger da kuma dawowar Yakaka , zuwa kan Mutuwar Mama .
Shiru su duka ukun suka yi bayan gama sauraron ta , zuciyar Khaalty Rahima ta girgiza da jin yadda rayuwa tayi walagigi da 'ya'yan ta mata , tsakanin ƙarya da gaskiya , rayuwar rashin gata ta tsantsar wahala abu ɗaya ne mafi ciwo a gareta yadda duk su biyun suka auri Miji guda a wannan ƙarancin shekarun nasu , lalle wannan ƙaddara ce mai girma .
Babu wanda ya fita sanin halayyar 'ya'yan ta duk kuwa da cewa sun jima da rabuwa daga yin rayuwa guri guda , amma ai ita ta haife su dan haka ta san halin kowaccen su tun kafin su mallaki hankalin da zasu iya boye abu a ran su .
Daga zaman Falmata a gabanta kawo yanzu ta fahimci lalle akwai wata damuwa mai girma da take cinta a rai , wanda farin-cikin haɗuwar su bai sa ta manta da damuwar ta ba , ji tayi hankalin yana neman tashi , tana jin kamar akwai wani abu da Falmata take ɓoye mata da tafi danganta shi da Yakaka , dan haka ta muskuɗa tana kallon fuskar ta cike da nazari tace ,
" Falmata kin samu labarin bayyana ta ne kika zo ? Ko kuma kawai dai kin zo ne ?
Murmushin yaƙe tayi kafin tace
" Maman mu ban san kin zo ba , ban San kina nan ba, ta cigaba da cewa Mama ina Yaana da Bulama suke ? nayi kuka nayi kuka na damu akan sanin ina kike ko kina raye ko kin mutu ? shekaru suka yi ta tafiya ba tare da mun san halin da kike ciki ba , har na fitar da rai da sake haɗuwar mu a duniya , na koma yi miki addu'a iri ɗaya da wacce nake yiwa Baban mu , kan Allah ya jiƙan ku .
Ƙwallar tausayin ta ya taru a idanun Khaalty Rahima , kafin tace
" Yaana ta rasu a kan hanyar mu ta shigowa maiduguri , Bulama kuma yana nan ya girma , anjima kaɗan ma za ki gan shi ya dawo daga islamiya ,
Ta cigaba da cewa ,
" Falmata ni na wanke gawar Mahaifin ku a cikin gonar na binne shi , ban yarda gawar mutumin kirki irin sa ta walaƙanta a hannun dabbobin daji ba , bayan na koma neman ku ban same ku ba , na dawo wajen ƙabarin sa mun rayu kwana biyu ni da Yaana da Bulama ina yi ma sa addu'a , kafin mu bar gurin , Allah sarki Mutumin ƙwarai mai tawali'u Allah ya masa Rahama ,
" Amin Mama Amin ,
Falmata ta amsa tana share hawayen da suke zubo mata ,
Amnee ita ta katse musu hirar ganin duk fiye da rabin ta koke-koke suke yi da jimamin rayuwar su da ta wuce .
" Ukhtee Rahima ku bar koke-koken nan haka , Fatima mu tafi ɗaki kiyi wanka ki shirya kafin a kawo miki abinci , "me zaki ci 'ya ta ?
Ɗan murmushi Falmata tayi "kome ma zan ci , amma da zan samu tuwo miyar kuka da man shanu ,
Dariya Amnee tayi tana kama hannun ta " muje kiyi wanka ki shirya , abinda kike so shi zaki ci .
Bayan tayi wanka ta shirya cikin riga da zanen da Amne ta zaɓo mata daga cikin kayan Rahima , tsumu tayi zaune a kujerar gaban madubi ,
" wani irin yanayi take ciki marar kan gado , ga dai ta a gida ta dawo kamar yadda ta zaɓarwa kan ta , take kuma ganin hakan shine zai raba ta da ɓacin-ran da take ciki , daɗin-daɗawa ma ta dawo ta tarar da farin-ciki mafi ɗaukakuwa a wajenta watau haɗuwar ta da Mama ,
Amma sai farin-cikin nata ya gaza kaiwa ga matakin da take so , baki ɗaya a hagunce take jin zuciya da ƙwaƙwalwar ta sun gaza tsayuwa gu ɗaya bare su taya ta samun gamsasshen farin-cikin da zai wanke mata rai .
Ƙiran sallar La'asar da aka yi , yayi dai-dai da gilmawar tunanin da take ta yunƙurin danne sa tuntuni , wani sashi na zuciyar ta ya tunbuƙo da tambayar ta ƙarfi da yaji ,
" a wanne hali Yakaka da Youssouf suke ciki ? Wataƙila sunyi ta neman ta sun gaji , wataƙila kuma ba su ma wani neme ta ba , dama ce suka samu ta tsara yadda rayuwa zata musu a gaba , ƙila ma ya saki auren ta zuwa yanzu ,
Nan take ta runtse ido Zuciyar ta na tsananta bugu ,
Da sauri ta miƙe ta shiga banɗaki gami da ɗauro Alwalar La'asar ,
Har ƙarfe huɗu tana kan Sallaya tana addu'o'i domin yaƙi da tunane-tunane , sai da Amnee ta matsa mata ta zo ta ci abinci sannan ta tashi suka koma falon tare , inda suka tarar da Khaalty Rahima ita ma ta idar da sallar ta nan bisa darduma ,
idanun ta kan falmatan tana duban ta da murmushi irin na zallar farin-ciki ,da ƙauna , ita ma falmatan da murmushi ta tafi a hankali ta zauna a gefen ta ,
Farantin da aka jera abinci akai amnee ta tura mata gaban ta , " ki cinye duk kin ji ko ?
Sama-sama take chakalar abincin duk kuwa da an girka shi yadda take so , miyar ta sha haɗin kayan ƙamshi na gargajiya , ga kuma man shanu gangariya ,
Sallamar Yakaka da ta sauka a kunnen ta daga bakin ƙofar falon shi yasa ta mayar da lomar da ta ɗauka da nufin kaiwa bakin ta ,
A hankali ta ɗago kan ta tana ganin shigowar ta ,da kai tsaye Yakaka ita ta doso bata kai ganin ta kan kowa da yake wajen ba ,
Ganin yadda ta taho yasa Falmata ta tsorata , dan haka ta janye kwanon abincin gaban ta , zuciyar ta na bugawa bata taɓa ganin Yakaka a fusace ya irin haka ba .
Yakaka tana ƙarasowa ta riƙo kafaɗun Falmata da karfi ta jijjigata , muryarta a tsaurare tace ,
" Falmata me yasa kika min haka ? Meyasa kika tafi ki ka barni ? Ashe kinyi girman da za ki iya yin gaban kan ki a rayuwa ? Ashe ni matsayina a wajen ki daman bai wuce na ƴar jagora ba da yanzu kuma lafiya ta samu wajen ki shine kika sanya kan ki a hatsari wajen yin gaban kan ki ? Wallahi da wani abu mummuna ya same ki bazan yafe miki ba Falmata .
Kukan da take riƙewa ya taho mata , sakin kafaɗun ta tayi ta zauna daɓas akan kujerar gefen ta , muryar ta cikin kuka ta cigaba da cewa ,
" Falmata kin manta ne da kusancin dake tsakanin mu ? Ashe har akwai wani laifin da ni zan miki ki kasa yafe min ?
Zuwa lokacin ita ma falmatan hawaye ke sauƙa a idanun ta , ganin kukan Yakaka ya karya mata zuciya , a hankali ta zauna a gefen Yakaka , muryar ta na ɗan rawa tace " Yakaka , kiyi haƙuri ba yadda zan yi ne , kin san... Kawai bazan iya zama bane .
Da wani irin yanayi Yakaka ta ɗago tana kallon ta , baza ki iya zama a gidan auren ki ba saboda ni ko Falmata ? Saboda mummunan kuskuren da na aikata ko ? Saboda...
Da sauri Falmata ta katse ta tana nuno mata inda Khaalty Rahima da Amnee har da Hajja duk suna tsaye suna bin su da kallo ,
"Yakaka kin ga fa Maman mu a tsaye , ga ta nan tana kallon ki , bata mutu ba ,ga Maman mu Yakaka .
A hankali Yakaka ta bi inda take nuna mata da kallo cikin ran ta da ɗarsuwar tunanin ko dai Falmata ta samu jirkituwar tunani ne ?
Tunanin ta ya tsaya chak na wasu ƴan daƙiƙoƙi lokacin da idanun ta suka kai kan fuskar Khaalty Rahima wacce take murmushi tana raba ganin ta a tsakanin su biyun cike da nishaɗin sake samun damar ganin su tare a gaban ta .
A hankali Yakaka ta mike tana kusantar inda take bayan tsayuwar kukan ta chak , zuciyarta cike da wasi-wasin gaskanta sake ganin ta , sai dai kuma ko a cikin mafarki ta ga Mahaifiyar su ai ba zata gagara gane ta ba ko me kuwa jirkituwar kamanni da ta samu mai-kyau ko mai-muni .
Tana ƙarasowa gurinta ta kai hannu a hankali tana tattaɓa jikin Khaalty Rahima, muryar ta a dishe da kukan da tayi tace ,
"Maama ke ce ? Ke ce Mama ?
Hannun ta da yake taɓa jikinta khaalty Rahima ta riƙe , tana cewa , "Ni ce Aminatu , Yakaka na , ni ce ,
Yakaka tana wata ƴar Dariya-dariya , kuka-kukan da yake fallasa tsantsar ruɗanin farin-cikin da take ciki , ta waigo ga Falmata tana mai mancewa da Falmatan ta riga ta haɗuwa da Mama , ɓakin-cikin da ta shigo da shi yana zagwanyewa tace ,
"Falmata wallahi Maman mu ce , kin ga Maman mu ? Zo ki gan ta , ta ƙarasa magana tare da yafito Falmatan da hannu ,
Sai kuma ta juya ta rungume ta da ƙarfi tana cewa ,"Mama na, Alhamdulillah , Alhamdulillahi .
****
Daren ranar ba suyi wani baccin kirki ba su duk huɗun hira kawai suke yi inda cikin labarin da Yakaka ta basu ta bayyana musu ainahin yadda haɗuwar ta da Youssouf ya kasance da yadda ta haifi Mama , samy baby ta yaudare ta, da kuma duk abubuwan da suka kasance tsakanin ita da Youssouf da danginsa baki ɗaya bayan zuwan ta Niger har zuwa guduwar da Falmata tayi ta bar ta a Niger .
A Zuciyar ta ta ƙudiri aniyar tsage gaskiya kome ɗacin ta , ita bata ga Alfanun ƙarya ba , babu wata rana da ƙarya zata iya yiwa mutum illa sada shi da ranar Nadama .
Daga Khaalty Rahima har Amnee sun koka kan yadda mummunar kaddara ta faɗawa Yakaka sanadin duhun jahilci tare da zun-zurutun rashin wayo , haɗi da raunin wayewar mu'amalantar jama'ah , da kuma rashin wani babba majiɓanci a cikin rayuwar su .
Yadda zuciyar Yakaka ta cika da tsoron ko zasu yi mata faɗa ko ma su yi fushi da ita sai ta ga akasin haka , domin daga mamar su har Amnee tausayi kaɗai take iya hangowa a fuskokin su , dan haka sai ta ji ta samu nutsuwar zuciya irin wanda bata taɓa samu ba tunda igiyar rayuwa ta fara jan ta .
A gareta yau ce rana ta farko da wasu nata makusanta na haƙiƙa suka fahimce ta ba tare da sun ƙalubalance ta ba , babu shakka babu kamar uwa Mahaifiya, ƙaunar ta ga abunda ta haifa daban ne , haka ma yawan sani da fahimtar ta ga 'ya'yan ta daban ne kamar yadda yawan uzuri da afuwar ta gare su ya hauhauwa .
Amnee ita ta katse shirun tsakanin su inda ta cigaba da cewa ,
"Amma takwarata , raba auren ƙanwar ki da Youssouf da kika so yi , ko kusa ba hanyar samar da mafita ba ce ba , idan kika duba yadda sharri ya biyo ta hannun sa haka nan ma Alkhairi ya zo ta hannun nasa , ki duba yadda ya riƙe auren ƙanwar ki har ma ya zama hanyar samar da lafiya a gare ta ? Bai walaƙanta ta ba duk kuwa da tazarar banbancin matakan matsayi ta kowacce fuska na rayuwa da yake tsakanin su , Baki ga yadda ya jajirce kan rayuwar ƴar sa ba har sai da Allah ya ɗauke ran ta ba tare da ya bari ta walaƙanta ba , kamar yadda sauran mafi akasarin ƴaƴan da aka samar ta wannan hanyar suke rasa tudun-dafawa iyayensu duk biyu na kƴamatar su musamman ma uba , amma sai shi ya kasance mai bata kariya da dukkanin ƙarfin sa , hatta a gaban dangi da Al'ummar sa .
"Babu shakka laifin sa maigirma ne sannan alkhairin sa kuma mai yawa ne , na fahimci irin ciwon da kika ji , kike kuma kan ji bisa dalilin faruwar kome , ina nufin auren sa da Fatima , to amma kiyi haƙuri ki rungumi kaddarar ki , ki yafe masa domin 'yar uwar ki da ya alkintawa rayuwa , ki bari su cigaba
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 75 Chapter of 103