baki da wani aiki sai tunanin wofi tamkar kin fi kowa damuwa a duniya ,
Saitin da yake Falmata ta maida ganin ta da kalamansa suka tunzuro ta ƙari da takaicin hirar da yake da matan banza a zaton ta ,
Muryar ta babu ƙarfi sosai tace ,
" ai ni miskiniya ce marar ido da bata wuce mabaraciya ba , da zai fi dacewa a cikin matan da kake taɗi da su kullum ka auri ɗaya da zata dunga kula da gida sosai ,
Chak ya tsaya daga tattara kayan wasan Mama , ya maida ganin sa kanta , yanzu ya samu ƙarin haske akan yadda ta sauya yake ganinta koyaushe cikin fushi da ɓacin rai ashe kishi ne ke cin ran ta ,
Murmushi yayi ya bar abunda yake tare da dawowa gefen ta ya zauna ya riƙo hannun ta , tausasa muryar sa yayi yana me tsare ta da ido yace ,
" Fatima ki saurareni , ki ji abunda zan faɗa miki a yanzou domin shi zai amfanar mouna ni da ke , matan da kike ji ina waya da su su biyu ba matan banza bane Matana ne su ma kamar yadda kike Matata .
Kamar ya caka mata wuƙa sai ta zame hannun ta daga cikin nasa , bakin na motsi a hankali ,
Bai kula da yanayin ta ba saboda ya shirya faɗa mata gaskiya a yanzu , ya sake riƙo hannun ta tare da cigaba da magana ,
" Fatima kiyi haƙuri amma yau zani faɗi miki doukkanin haƙiƙanin gaskiya bisa kaina .
Bai jira amsar ta ba ya shiga bata labarin ko shi wanene tiryan-tiryan , tundaga sunan sa na gaskiya, kasancewar sa ɗan sarki , aikin sa zuwan sa Nigeria auren sa da matan sa , abu guda ya ɓoye mata haƙiƙanin dangantakar sa da Yakaka .
Tamkar a mafarki haka Falmata ta tsincin wasu kalmomin nasa , cikin wani irin yanayi da ta gaza tantance wanne iri ne , muryar ta can ƙasan maƙoshi , tace da shi
" Duk cikin labarin da ka bani baka faɗa min lokacin da kuka yi aure da 'yar uwata ba ?
Mukut ! Youssouf ya haɗiye busasshen yawu tambayar ta zo masa a bazata ta yi masa dirar mikiya bai kuma shirya amsar bata ba a yanzu ,
" Fatima zan faɗi miki wannan labarin a gaba cikin lokaci na mussaman ba yanzu ba ,
Cikin rashin yarda da ya mamaye tunanin ta ta fara girgiza kai ,
" a ah yanzu nake so ka faɗa min muddin kana so na yarda da duk labarin da ka bani yanzu ,
zaro ido yayi yana duban fuskar ta da ƙwayar idanun ta da suke cike taf da rikici da tashin hankali ,
Ya ɗan ɗaga sauti yana murza yatsun ta dake cikin hannun sa ,
" Fatima ki nutsu nace zan faɗa miki watarana a gaba ,
Warce hannunta tayi da ƙarfi daga cikin nasa ta matsa daga kusa da shi cikin ɗaga sauti ita ma ta ce masa
" Ba gaskiya bane muddin baka faɗa min yadda kuka yi aure da Yakaka ba kai ba kaine Baban Mama ba ƙarya kake min ,
Tsawar da ya daka mata tare da buga teburin gaban su shi yasa Mama fashewa da kuka da gudu tayi jikin Falmata ,
wannan karon ya kaurara murya da wani irin amo da bata taɓa jin sa da irin ta ba cikin sigar gargaɗi yace mata ,
" Fatima ki min shiru , ki min shiru nace kar ki sake cewa ƙala ,
Fuskar sa tayi jazir , jijiyoyin kansa sun fito ruɗu-rudu , baki ɗayan jikin sa yana rawa , ɓacin rai sosai ya sauƙo masa , zafin zuciyar sa irin ta soji ta hayyaƙo ,
A zabari ya miƙe ya shiga ɗaki , yayi tsaye hannun sa a dunƙule , ya rasa me yake yi masa daɗi wani irin ɓacin rai me tafe da tsoro-tsoro da a lokacin ya rasa tsoron meye ? Shine yake cin sa ,
Jibgegiyar rigar sanyin sa iya guiwa dake ajiye a gefen gado ya ɗauka ya rufa akan kayan sanyin da daman suke jikin sa ya fito daga ɗakin ,
Satar kallon inda suke yayi ya ga Falmatan tayi baya da kanta ta kwantar akan kujerar Mama kuma tana maƙale a jikinta tana kallon sa da raunanan idanun ta ,
Tausayin 'yar sa ya kawo masa , da hannu ya yafice ta , da sauri ta sauƙa tayi wajen sa ,
Ɗaukar ta yayi ya koma cikin ɗakin ita ma ya ƙara mata rigar sanyi tare da sauya mata hular da tafi ta kan ta nawi ya sungume ta suka fito falon ba tare da ya dubi sashin da Falmata take ba ya nufi ƙofar fita ,
Mama da idanun ta ke kan Mamar ta cikin siririyar Muryar ta tace
"Papa ma....
'shit
Yace mata yana ɗora yatsan sa manuni akan bakin ta , shiru tayi tana kallon sa suka ƙarasa ficewa daga gidan ya ja ƙofar
Ƙarar rufuwar ƙofar ya zo tare da zubowar kauraran hawayen ta , da duk motsin su daman yana kunnen ta ,
Kuka ta fashe da shi mai sauti tare da jin wani sabon tashin hankali har ta rasa takamaimai da wanne zata ji ?
Shin laifi ne dan ta tambaye shi game da yayar ta ? A sautin sa ta tsinkayo tashin hankalin da yake tafe da rashin gaskiya shin meye yake boye mata bayan wanda a yau ya bayyana mata da ta haƙiƙance ta kuma yarda ɗari cikin ɗari gaskiyar sa ya feɗe mata da ita kuma ganin wannan damar ne ya sa tayi amfani da ita wajen shigo masa da tambayar da ta kwashi shekaru tana cinta a rai ,
" Yaushe suka yi aure shi da Yakaka alhalin ita bata san lokacin ba ??
Tana share hawaye wasu na zubowa ,
"Wai ashe daman har yana da mata biyu ita bata sani ba ?ashe mijin su ne su uku ? Tausayin kanta ta ji ya kawo mata , tabbas ita ba kome bace a wajen sa face wacce ya taimaka ya aure ta sanadin 'yar yayar ta , ba kuma zata taɓa zama kome a wajen sa ba ,
'idan kuwa haka ne dole tayi haƙuri ta haɗiye kome ta kuma bar kome domin ta cigaba da zama a ƙarƙashin sa tare da Mama , a zahiri yake ai shi yafi ƙarfin auren ta , wacece ita ? Miskiniyar ɗiyar talakawa 'yar gudun hijira ? Babu shakka bakin rijiya ba gurin wasan makaho bane ,
Ya zama dole ta bashi haƙuri idan ya dawo ta kuma alƙawarta cikin ran ta baza ta sake yi masa batun Yakaka ba .
Ta ɗau lokaci a haka cikin kukan zuci da damuwa , kafin ta kintata tayi sallar la'asar da take da tabbacin lokacin ta ya shigo ,
A ƙasa inda tayi sallar ta cigaba da zama tunaninnika sun mata yawa , ta ƙagauta ƙwarai ta ji motsin shigowar sa ta bashi haƙuri ,
Daƙiƙoki suka dunga hanzarin wucewa suna zama mintoci har suka ɗebi awannin da Falmata ta ji su tamkar sati guda tayi tayi a zaune ,
Ta tashi ta tsaya yafi a ƙirga ta matsa jikin ƙofa ta laluba , ta kasa kunne ko zata ji motsin su , har dai ta tabbatar sun yi nisa da ita sosai ,
Wani irin mummunan tashin hankali ne ya dirar mata sakamakon tunanin da ya gitta ƙwaƙwalwar ta kan cewa ya ɗauke ɗiyar sa sun tafi sun bar mata gidan , ya sauya muhalli sun yi nesa da ita har abada , ya tafi ya bar ta a uwa duniya ƙasar da bata san kowa ba ko yaren su bata ji ,
Wannan karon kukan da ta fashe da shi tafe yake da amon matsanancin tsoro da ruɗewa ,
Da gudu ta taka tayi nufin fita sai dai karon da ta ci da kujera yasa tayi baya cikin sa'a ta zauna daɓas akan kujerar kusa da ita ,
Ta sake ajiye hannu da zummar miƙewa hannunta taji ya sauƙa akan sandar ta , cikin sauri ta laluba ta ɗau sandar , ta kama hanya fita daga gidan tare da taimakon sandar hannunta,
Bata damu da ta sake ɗora wata rigar sanyi ba illa ta jikinta da take iya guiwar ta sai kuma siririn siket da hular sanyi a kanta ta fice a gidan ba tare da ta san ina ta dosa ba ,
Tsananin sanyin da ya ratsa ƙasusuwan ta lokacin da ta fito waje bai sa ba ta koma illa tafiya da ta cigaba da yi tana laluben hanya da sanda ,
Unguwar da suke shal babu kowa sai tsilla-tsilla motoci ke wucewa haske ya wadaci ko'ina da taimakon fitulun gefen hanya duk kuwa da duhun dare da ya fara mamayar sararin sama.
Tayi tafiya mai nisa lokacin da tsoro ya gama cin galaba akan ta nadamar fitowar ta ya ziyarce ta ,
Matsanancin sanyin da ya fara cin ƙarfin ta sakamakon dusar ƙanƙarar da ya fara sauƙa ya sa ta gaza ci gaba da tafiya gaba ɗaya ji take kamar jinin jikinta ya daskare ,
Durƙushewa tayi a wajen da bata da masaniyar ina ne ?tana jin yadda sanyin wajen da ta zauna yake ratso jikin kayanta yana daskarar da duk wani ruwa na jikinta ,
Idanunta da hancinta suna tsiyaya ta dunƙule jikinta waje guda tana karkarwa ,
A cikin ran ta ta haƙiƙance rayuwar ta ta zo gangara , ashe ita kuma irin tata sanadin mutuwar kenan sanyi ?
****
Biyamuradi Youssouf tunda ya fita saɓe da Mama , yayi ɗan tattaki cike da rashin sani takamaimai ina zasu ??
Ya zaɓi ya fita ne saboda yana da yaƙini zuciyar sa ba zata jure ganin fushin ta ba , da shi kuma a wannan gaɓar bai yarda yayi wani yunƙurin ds zsi fallasa halin da zuciyar sa ke ciki ba a kan ta bai so ta gano lagon sa tunda wuri haka ,
Cigaba yayi da tafiya har ya cimma babban titi , nan ya hango wani shagon sayar da coffee ,
Bayan ya ƙarba musu coffee me zafi ya zaunar da Mama a kujerar da ke fuskantar ta shi ,
Juya ɗan chokalin hannun sa yake yi ya gagara shan coffee ɗin , damuwa tayi masa ƙawanya duk wata walwalarsa ta kau ,
Ko kusa ba zai iya duban ta ya fayyace mata lamuran da suka auku tsakanin sa da 'yar uwar ta ba , yana jin kunya , yana kuma tsoro .
Meyasa ta kasa fahimtar barin abunda ya riga ya wuce a muhallin shuɗaɗɗan lamari shi yafi alheri fiye da tone-tone . ?
Duban sa ya kai ga Mama wacce tayi shiru ta lanƙwasa kai fuskar ta bayyane da damuwa ,
Tausayin ta ya ji domin ya san damuwar ta ta samo asali ne ga abunda ya faru tsakanin sa da Falmata , da shima zuwa yanzu nadamar ihun da yayi mata yake yi ,
Bai yi hakan da wata manufa ba illa ruɗanin da ya tsinci kan sa a ciki da ya sa bashi da wata hanyar daƙile yunƙurin ta tare da kawo ƙarshen maganar idan ba ta hakan ba .
Tashi yayi ya zagaya ya ɗauki Mama suka fito daga Coffee Home ɗin ba tare da ya sha coffee da ya saya ba ,
Sake nusawa yayi bakin titi yana tafe sannu kan hankali har ya tadda ɗan wani killacaccen wajen yin sallah , nan yayi sallar la'asar tare da Mama a gefen sa ,
Bayan ya idar hankalin sa ya kai kan wani fili gaban wasu gidaje da matasa da yara suka taru suna wasan ƴar zamiya akan dusar ƙanƙara Tobogganing , kama hannun Mama yayi suka ƙarasa wajen ,
Ya zauna daga gefe kan kujerar gefen hanya tare da ɗaura Mama a cinyar sa ,
Sosai wasan ya ɗau hankalin Mama ganin yara ƙanana sa'o'in ta nata faɗuwa da tashi cikin dusar ƙanƙara , nan take ta shagala da kallon su har tana taya su dariya idan wasun su sun faɗi ,
Ganin walwalar Mama ya bashi damar zurfafa a tunani , sashi guda na ran sa na shawartar sa akan idan ya koma gida ya faɗa mata gaskiya ksn abunda take son sani , yayin da sashi mafi rinjaye ke ƙwabar sa tare da tsoratar da shi abunda faɗa mata gaskiyar zai iya haifarwa ,
Abunda ya haƙiƙancewa ba zai iya jurar fushin ta da damuwar ta ba domin kusa take sosai da ruhin sa ,
Bai ankara ba har duhun dare ya fara shigowa , dan haka ya sake komawa wajen da yayi sallah , ya sallaci Magarib ,
Yana idarwa ya kamo hanyar gida bayan ya saɓa Mama a bayan sa da tayi laushi tuɓus ,
Ta gaban manyan shagunan sayar da kayan ƙele-ƙele na mata ya zo wucewa , idanun sa suka kai kan wata 'yar kyakkyawar sarƙa da take ɗaukar ido tare da taimakon hasken lantarki da ya haske cikin gilashin da sarƙar take .
Murmushi yayi lokacin da idanun sa suka hasko masa sarƙar a cikakken wuyan Falmata ,
Da hanzari ya shiga shagon ya sayi sarƙar da take ta farin zinare ƙirar ƙasar Amurka suka zare kuɗin su ta katin sa tare da zura masa akwatin sarkar cikin 'yar jakar da take ɗauke da tambarin Manns jewelry .
Cike da fargaban halin da zai riske ta ciki ya nufo gidan , zuciyar sa na aiyana masa wataƙila tayi ta kuka ,?wataƙila kuma ran ta ya sake ɓaci da shi, koma menene zai bata haƙuri ys rarrashe ta ta bar maganar nan ,
Da Sallama ya tura ƙofar gidan ya shiga ,
Shiru ya ji bata amsa ba ,
Ya lalubi wutar falon ya kunna ,
Idanun sa akan ɗan wajen kunna witar ɗumama ɗakin da har wutar ta mutu , hakan ya sa ɗakin ya ɗau sanyi
cikin ran sa babu daɗi , Ya zaunar da Mama akan kujera , yayi tsaye yana saƙe-saƙe , jikinsa gaba ɗaya yayi sanyi da barin ta da yayi ita ɗaya ,
Takawa yayi ya ƙarasa bakin ƙofar ɗakin ya ɗan ƙwanƙwasa ,
" Fatima , mun dawo
Ya furta haka da sauƙaƙar murya ,
Shiru ya sake ji babu alamun motsi ,
Sai ya murɗa hannun ƙofar ya shiga ɗakin , cikin 'yan daƙiƙai ya fahimci bata ɗakin , da sauri juyo , kai tsaye ya leƙa cikin ɗaya ɗakin , babu alamarta
Tamkar an safure shi haka ya dunga bin kowanne lungu da saƙo na gidan yana neman ta tare da ƙira sunan ta ,
A ƙarshe ya hiƙanƙancewa kansa tabbas bata gidan , ta fita ne ? Ko an sace ta ? Shikenan shi kam ya shiga ukun sa , ta shi kuma ta same shi .
Da gudu ya sunkuci Mama ya fito , dusar ƙanƙara na sauƙa a kan su yayi tirus a harabar wajen , ina zai fara nufa neman ta ? Wa zai dosa ya tambaya akan ta ?
Gidan da yake maƙwaftan na su ya nufa da sauri ya danna musu ƙararawar neman iznin shiga gidan ,
Zuciyar sa na ayyana masa wataƙila ta shiga gidan ,
Tunanin sa ya katse lokacin da aka buɗo ƙofar wani mutum magidanci yayi tsaye yana kallon sa ,
Da harshen turanci ya gabatar masa da kan sa a gurguje kafin ya ɗora masa tambaya kan ko matar sa ta shigo gidan su ?
Da harshen larabci mutumin ya miƙa tambayar ga matarsa da take daga bayansa a tsaye ,
Nan suka tabbatar masa da babu wacce ta shigo musu ,
Har ya juya sai kuma ya dawo ,
Rokon su yayi akan su taimaka su riƙe masa 'yar sa zai je neman matar sa ,
Basu musa ba suka karɓi Mama da tayi rau-rau da ido tana shirin kuka ganin Babanta zai tafi ya bar ta hannun waɗanda bata kai ga sanin su ba ,
Bai kula ba ya juya da sassarfa mai haɗe da gudu ya kama doguwar hanyar da tayi cikin unguwar sosai yana tafe yana dube-dube da waige-waige , hankalinsa yayi ƙololuwar tashi , maƙogoran sa ya bushe , idanun sa har raɗaɗi suke yi masa ,
"Yaa Allah Fatima ina kike ? Yaya za ki min hakka Fatima , ? Meyasa kika fita ?
Ya furta hakan muryarsa na karkarwa , bayan hannun sa ya sa ya goge fuskar sa da iskar dusar ƙanƙara ta watso masa ,
Ganin har ya kusan ƙure unguwar bai gan ta ba ya sa shi komowa baya , yana cigaba da neman ta , addu'o'i iri-iri yake yi ,
Zai iya cewa tunda yake bai taɓa shiga tashin hankali irin na tsuƙin lokacin nan ba , bai taɓa sanin ita wata kadara ce mai maɗaukakiyar daraja a wajen sa ba sai a wannan gaɓar da yake gaf da rasa ta ,
bazai yafewa mummunar zuciyar sa ba idan har wani abun cutarwa ya same ta ,
Sakin hanya yayi ya nufi wata doguwar hanyar da tayi gefe a tsakankanin dusar ƙanƙara
Fatima , Fatima , Fatima
Yake ƙwala ƙiran sunan ta ,
Ya ƙure hanyar bai ko ga alamun sawun ta ba sai zunzurutun sanyin a yake ratsa sa ,
Dawowa yayi da baya ya sake kama wata hanyar ta daban nan ma yana tafe yana kiran sunan ta ,
Durƙushewa yayi a gefen hanya yana jin tamkar ya ƙwala ihu ko ya ji sauƙin tashin hankalin da yake ciki ,
Kamar a sama ya fara jin amon Murya ta daga nesa , tana ƙiran sa
Da gudu ya nufi inda yake jin tashin sautin ta ,
A gefen hanya zaune cikin dusar ƙanƙara ya hango ta ,
Hannuwan sa duk biyu ya sa ya ɗago ta , ya riƙo kumatun ta dama da hagu ,
"Fatima meyasa kika fito ? Ina za ki je ? Fatima kar ki sake tafiya ki bar mu .
Ta kifta idanun ta da suka bushe ƙemas saboda sanyi tace ,
"Baban Mama ku na fito nema , dan Allah kayi haƙuri kar ka sake tafiya ka bar ni , bazan sake yi ma laifi ba ,
Kamota yayi suka miƙe tsaye , yadda take rawar sanyi ya tashi hankalin sa , "
Juyawa yayi yayi durƙuso
"Fatima kama ni hau bissa bayana mu je gida ,
Duk da wahalar da take ciki , noƙewa tayi , muryar ta na rawar sanyi tace ,
"Baban Mama zan iya tafiya da kaina mu taf....
Bata ƙarasa zancen ba ta ji ya ɗaga ta ciɗak , ya ɗauketa , da sauri ta riƙo rigar sa , ya nufi gida da ita .
Duk da tafiyar akwai tazara amma bai gajiya ba ko dan kasancewar sa ingarman sadaukin soja ne ?
Yana ajiyeta akan kujerar falon su ya shiga haɗa wuta ,
Muryar ta can ƙasa tace masa ,
"ina Mama ,
" zan ɗauko ta tana gidan daura da mu ,
yace
Da sauri ya dawo ya zauna a gefenta ya shiga zare mata safar ƙafafunta da suka ɗau sanyi , ya zarce da cire mata hular sanyin kan ta ,
ɗaki ya shiga ya ɗauko ƙaton bargo ya rufa mata har kan ta
Ya kamo ta ya dawo da ita gaban wutar sosai ,
Hannuwan sa biyu ya shiga karawa a gaban wutar su ɗau zafi sosai sai ya cire ya sa mata a ƙafafunta ,
A karo na biyu ta sake cewa ,
"Baban Mama , Mama tana waje ko ? Kar sanyi ya tada hargitsin ciwon ta ,
Da ido yake bin kyakkyawar fuskar ta da kallo , yadda fuskar ta ke da kyau haka ma zuciyar ta , ya aina hakan cikin ran sa , duk laifin da yayi mata , duk wahalar da ta sha a sanadin sa , ita ta lafiyar 'yar sa take ,
"bari na ɗauko ta , ya miƙe
Har ya kai bakin ƙofa , ya waigo
"Fatima kadda ki matsa dagga gaban wuta ,
Bai jira amsar ta ba ya fita da sauri , ya shiga ya ɗauko Mama wacce har tayi bacci ,
Godiya sosai ya yiwa maƙotan sa da suke musulman larabawa ,
Kai tsaye ya wuce da Mama Kan shinfiɗar ta ya ƙwantar da ita a ɗaki tare da haɗa wuta a cikin ɗakin ,
Inda ya barta nan ya dawo ya tadda ta kamar yadda ya umarceta bata motsa ba , kamar yadda bata daina rawar sanyi ba
"Zanyi Sallah tace da shi ,
Bayan ta idar da magarib ya ja su isha'i ,
Da suka idar kai tsaye ya nufi shayi me zafi ya haɗo mata ,
Da chokali ya ɗan sisita shi ya shiga bata a baki tana kurɓa kadan-kaɗan , yadda take rawar sanyi yana damun sa dan haka ya ajiye kofin hannun sa ,
ya kusanto da ita sosai cikin jikin sa , bayan ya rage kayan jikin sa ya rage 'yar rigar sa ta ciki ya ware bargon da lulluɓa da shi ya rufa musu su biyu ,
Hannun sa ta ji ya buɗe zif ɗin rigar sanyin jikin ta , kafin ta ankara ya zura hannuwan sa ya kewaye ta da su tare da ƙwanto da ita kan kirijn sa sosai ,
Ɗumin jikin sa tare da firgici suka yi tasirin da suka hanata ƙwaƙwararan motsi har zuwa lokacin da ya ƙarasa zare rigar sanyin jikinta da ta ɗau sanyi na ban mamaki yayi cilli da ita gefe ,
Habar sa a tsakiyar kanta ya rungume ta tsam a jikin sa tana iya jin bugun zuciyar sa da yake tashi sannu kan hankali ,
Wani irin yanayi mai cike da daɗi da nutsuwar zuci da gangar jiki suka tsinci kan su ,
" Fatima ,
Ya ƙira sunan ta muryar sa ƙasa-ƙasa ,
"na'am
Ta amsa masa a hankali ,
"Kar ki sake tafiya wani waje ke kaɗai ba tare da iznina ba kin ji ko ?
Bata amsa ba illa kan ta da ta gyaɗa a hankali ,
Shafar bayanta yayi da hannuwan sa masu ɗumi ,
"Fatima ɗazu kin tsorata ni na shiga tashin hankali , kada ki ɓata a ƙasa irin US ,
" kayi haƙuri Baban Mama neman ku na fita sai kuma na kasa gane gida ,
" kan ta ya ɗago daga kirjin sa ya riƙe fuskarta ba domin yana ganin ta ba saboda duhun da yake cikin bargon ,
A hankali ya sumbaci goshin ta ,
"Na haƙura Fatima, ke ma kiyi haƙuri da faɗan da nayi miki ɗazu , kin haƙura ?
" kan ta ta mayar cikin jikin sa ta sa hannuwanta biyu ta zagaye bayan sa cikin shauƙi tace
"ni baka min laifin kome ba Baban Mama idan ma kayi min na yafe ma ,
Murmushi yayi da sauti , ya sumbaci kafaɗar ta , yana jin tilin ƙaunar ta da yake binne cikin ramsa suna tunɓuƙowa da wani irin shauƙi da yasa ya gagara mallakar kan sa a karon farko ya shiga gwada mata zallar ƙaunar ta da yayi raino tun wasu shekaru a baya da tsiron sonta ya fara ɗarsuwa a ran sa ,
ita ma bata ƙi ba , bata kuma bijire masa ba ta ɓuɗe tafukanta ta tallafi muradin sa , tare da miƙa masa abunda yake halalin sa ..
daga falo ai sai aza room ko kuwa ??
Assalamu Alaikum Masoya !
Da fatan kuna cikin ƙoshin lafiya tare da ƙwanciyar hankali ?
Ina mai baku haƙuri bisa ga jinkirin da ake samu wajen cigaba da rubutu , ajizanci ne irin na ɗan Adam.
Nagode .
[11/14, 11:02 AM] Zuraiyah Zuzu 🌟: MAFARI..
( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
38
Washegari sun tashi cikin farin ciki tare da walwala marar misaltuwa , musamman Biyamuradi Youssouf da yake jin kan sa tamkar yau ya fara angwancewa a tarihin rayuwar sa ,
Zallar ƙauna tare da tattali yake gwada mata da ita kuma take ta zille-zillewa tare da jin tarin nawin sa , gefe guda na zuciyar ta tsiron ƙaunar sa ya fara yaɓanya yana baza rassa .
Da dukkanin daƙiƙa guda yana wucewa ne tare da tunanin sa dake manne cikin ƙwaƙwalwar ta duk kuwa da ga shi
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 61 Chapter of 103