ayoyi da hadisai .
A ƙarshe suka bashi tabbaci kan cewa jarabawar Rayuwa ce Allah ya masa domin ya gwada ƙarfin imanin sa dan haka ya bar kome ga Ubangiji da idanun sa zai ga sakayya .
A hankali ya dunga jin nutsuwa na safko masa da kafin wani lokaci ya ji baki ɗaya zuciyar sa ta sauƙa wani irin nutsuwar da ya jima bai ji irin ta ba tana safko masa .
Liman da yake malami masanin Alkur'ani ya cigaba da cewa
"sannan shi sihiri gaskiya ne da masu aikata shi kaɗai suka yi imani da shi ,
"babu shakka cikin kur'ani duk wani magani da warakar kowacce cuta yake dan haka ga ayoyin Alkur'ani masu warware sihiri zan faɗa maka idan za ka iya kayi da kan ka Yousssouf idan kuma ka gaza ka bayar a yi maka ina mai tabbatar maka da cewa dukkanin wani sihiri da anka maka sai ya karye da iznin Allah sannan kuma Allah zai baka kariya daga dukkanin wani mgunta da za'a sake nufar ka da shi ta hanyar sihiri ba zai yi tasiri akan ka ba, ka samu takarda da alƙalami ka rubuta a yanzu Youssoufa ayoyin sune kamar haka :
1). Ta'awwizi da Basmala.
2). Fatiha kafa 7.
3). Aya biyar Ta farkon Suratul Bakara sau 7.
4). Ayoyi biyu ta tsakiyan suratul Bakara wato - Wa ilahukum ilahum wahid la'ilaha illa huwa har karshe sau 7.
5). Ayatul kursiyyu Suratul Bakara aya ta 255 sau 7.
6). Ayoyi uku a karshen Suratul Bakara wato daga baikin Amanarrasul Bakara 284-286 sau 7.
7). Shahidallahu a chikin Al Imran aya ta 18 da 19 sau 7.
8). Inna Rabbakumullahi Ladhi khalaqas samawati wal ardh.. acikin Suratul Al'araf aya ta 54 da 56 sau 7.
9). Afa hasibtum Annama khalaqanakum Abasan suratl Mu'minin aya ta 115 da 118 sau 7.
10). Wa Annahu ta'ala Jaddu rabbina mattakhadha..." a cikin Suratul Jinni aya ta 3 zuwa ta 9 shima kafa 7.
11). Aya goma na farkon Suratul Saffat shima sau 7.
12). Aya Uku na karshen Suratul Hashri wato "Lau anzalna hathal Quran.
13). Aya ta 10 na karshen suratul Yasin su ma sau 7.
14). Kulya ayyuhal kafirun sau 7.
15). Qul huwallahu ahad sau 7.
16). Falaqi sau 7.
17). Nasi sau 7.
A rika tofawa a ruwan zamzam ko ruwan sama ko ayi a duka biyun amma dabam dabam a samo ganyen magarya a dandaka guda bakwai-bakwai har gida 7 wato na kwana 7 Safiya da maraice ana sha ana shafe jiki dashi.
Da fatan ka Fahimta Yossoufa ? Sannan a kome kake kada kayi wassa da ibadar ka domin itta ɗin kariya ce mai girma daga dukkanin abun ƙi , ka faɗaɗa ibarda ka yalwata ta , sannan ka yawaita sadakha domin ita ma kariya ce .'
Youssouf da yake gama rubutu ya ɗago kan sa fuskar sa a nutse yace" na fahimta Malam kuma Nagode Allah shi saka da alkhairi .
Daganan ya baro sashin maimartaba bayan ya musu godiya mai tarin yawa , ya bar su suna cigaba da tattunawa .
Sashin sa ya nufa kai tsaye yayi wanka ya ɗaura alwalar sallar la'asar zuciyar sa da take cike da tausayin Falmata da son sanin halin da take ciki ta sa shi dole ya miƙa hanya zuwa sashin Hajiya Umma .
A zaune ya tarar da Hajiya Umma , a falon ta na ciki da Hajja sai kuma Ubbo suna sake jimamin lamarin banda ɓarin nauyayan kalmomi babu abun da Hajja take yi da lokaci-lokaci ubbo kan yi dariyar wasu kalmomin na Hajja .
Zuciyar Hajiya Umma ta sanyaya da ganin Yousouf ya dawo cikin nutsuwar sa har ma ta gagara ɓoye jin dadin ta .
Tayi hamdalah a bayyane .
Bayan sun gaisa ta ɗan dube shi kafin tace " ƙafar Fatima da akwai ciwo domin kouwa da kyar take iya takawa duk da dai na mata tambayoyi cikin amsar da ta bayar tacce bata da wata damuwa sai ta ƙafar da daman akwai tsohon targaɗe a gurin kuma ta sake gurɗewa dan haka nayi magana a ƙira mai gyara a duba ƙafar ko kuwa asibiti za'a ?
Cike da jin daɗin kulawar da ta nuna a karon farko ga Falmata , Youssouf yace "duk wanda kin ka ga yafi dacewa Umma.
"Ka shiga ciki ka gan ta suna ɗaki tare da Siyama.
A bisa ɗaya daga cikin gadajen Hajiya Umma biyu da suke ɗakin ya hango ta a zaune tayi wankan ta fes jikin ta sanye da doguwar riga ta atamfa daga gefe Siyama ce a kusa da ita hannun ta riƙe da wani ɗan kyakkyawan tasa ( Bowl ) da aka zuba ferfesun ƙaza a ciki da chokala biyu a ciki fork da soup spoons,
Ganin shigowar sa bai sa Siyama ta fasa kai soup spoon ɗin da ta cika da ruwan ferfesun bakin Falmata ba sai dai ta amsa sallamar sa da murmushi akan fuskar ta .
Ƙarasowa bakin gadon Youssouf yayi ya zauna a ɗaya gefen yana bin ƙafar Falmata da kallo wanda ta kumbura daga idon sawun .
Kallon sa ya mayar ga Siyama yana jifatan ta da ɗan kyakkyawan murmushi yace
"Siyama kina gatata ƙamnar ki hakka ? Da har kin ka ciyar da ita ba tare da ni kin tuna da cikina ba ?
Ɗan murmushi Siyama tayi kafin tace " ai itta a yanzu marar lafiya ce kai kouwa ka samu waraka insha Allah .
Murmushi yayi yana mayar da ganin sa kan Falmata yace "Fatima yaya ƙarfin jiki ? Ina ke miki ciwo bayan sawun ki ?
Cikin 'yar ƙaramar murya tace "ba ko'ina sai ƙafar tawa.
Tashi yayi daga bakin gadon ya ɗan yi durƙuso kafin ya kama ƙafar falmata a hankali ya ɗago ta ,
Ganin haka yasa Siyama tayi saurin miƙewa bayan ta ajiye kwanon hannun ta akan ɗan teburin gefen gado (bedside cabinet) .
Ta nufi ficewa daga ɗakin " Maman Yumna ina za ki tai ?
Youssouf ya furta haka yana bin ta da kallo
Lumshe idanun ta tayi ba tare da ta jiyo ba tace " zan tai na kawo ma abinci .
Daga haka ta ƙarasa barin ɗakin tana jin yadda suke kokawa tsakanin ta da zuciyar ta da take son ganin baƙin Youssouf da Falmatan.
A hankali ya mayar da ganin sa kan ƙafar Falmatan ya kai ɗan yatsan sa babba ya shafa gurin da ya ɗan kumbura a hankali da yasa Falmata rufe idanun ta a hankali tana jin yadda tsiƙar jikin ta ke tashi tare da wani yanayi da take ji na tausayi mai girma yana huda zuciyar ta , yana bin duk wani saƙo da lungu da ɓurɓushin jin haushin Youssoufa ya maƙale a ran ta kan laifin da take zaton duk yayi su a bisa son rai cikin sanin sa da yin kan sa .
Ji tayi laifukan sa na gogewa suna shafewa , ƙaunar sa , son sa , tare da tarin tausayin sa masu nawin da bata taɓa jin makamancin su ba saboda ji da tayi kamar zuciyar ta ba zata iya ɗauka ba , kamar sararin dake ran ta yayi kaɗan.
da wani irin tasiri mai girma suke maye gurbin duk wani ɗan taƙi da ta bar wa soyayya mallaki a cikin ran ta .
Tasirin so da take ji a lokacin ya fi ƙarfin rarraunar zuciyar ta da take sabon shiga a fagen soyayya .
Ɗago da kan sa yayi yana kallon ta bayan ya gama tofa mata addu'o'i a ƙafar ta .
Ya ɗan dau lokaci yana kallon ƙaramar fuskar ta da take sake zama 'yar firat yana jin tausayi tare da wannan son nata mai yawa yana masa yawo a zuci .
Jin sa shiru ya sa ta buɗe idanun ta a hankali suka haɗa ido .
"Sannu Fatima insha Allah za ki samu sauƙi kin ji kou ?
Gyaɗa kan ta tayi
A hankali ya miƙe ya ƙarasa ya ɗauki bowl ɗin da Siyama ta ajiye ya dawo ya zauna , ya fara bata ferfesun tana ci a hankali , har sai da ta ɗan ci dayawa kafin tace masa "ta ƙoshi .
Bayan ya ajiye kwanon ya dawo ya zauna tare da riƙo hannun ta ya sarƙe 'yan yatsun su waje ɗaya "Fatima kiyi haƙuri da abunda ya same ki Allah zai miki sakayya cikin gaugawa kuma insha Allah zan zamar miki garkuwar da babu wanda shi issa ya taɓa ki a rayuwa na ƙyale shi , kiyi haƙuri Fatima .
Matsa hannun sa da yake cikin nata tayi kafin ta ɗago kan ta tana saka idanun ta cikin nashi tace " Meyasa bata son ka haka ?
"Nima ban sani ba Fatima cikin rayuwata ban taɓa yi mata laifi ba amma ta zuba min ƙiyayya mai zafi da har da taimakon ta anka nemi raba ni da raina bayan ita ta gurgunta rayuwata ta rarraba ƙiyayyar da take min tsakanina da ɗiyan ta da suke 'yan ouwana .
Kan ta ta mayar ta kwantar a ƙafaɗar sa tana kaucewa kallon cikin idanun sa da suka fara sauya launi tace
"Kayi haƙuri ƙiyayyar ta ba za ta sa ko ta hana kome ba sai fa abunda Allah ya rataya alhakin faruwar sa akan ta .
"Idan ita bata son ka Allah da Manzon Allah su na son ka , Maimartaba yana son ka , Umma tana son ka sauran 'yan uwanka suna son ka , Siyama tana son ka , yaran ka ma zasu so ka .
Ɗan jim tayi kafin ta ɗago kan ta tana kallon cikin idanun sa tace " kuma ni ma ina son ka , Ina son ka , ina son ka dayawa .
A bazata ya tsinkayi kalmomin da bata taɓa furta masa ba , zuciyar sa tayi wani ɗan ƙaramin zillo da yasa shi sake ɗago fuskar ta da sauri ya riƙe ta yana kallon ƙwarar idanun ta , muryar sa a tsakani maƙoshin sa yace "me kika faɗi Fatima sake faɗi naji ? Maimaita min ?
"Ina son ka dayawa dayawa ba adadi
Ta sake furta hakan tana kallon fuskar sa cikin ranta " godiya take yiwa Ubangiji da idan ba shi ba da ƙarfin ikon sa wa ya isa mallaka mata wannan mutumin ma'abocin kyau da cikar zati tare da kyaun nasaba ?
Muryar sa tana sake nitsewa saboda ƙasa da yayi da ita yace "dagaske Fatima ?
Hannuwan ta tasa akan nasa kafin tace "da duk gaskiyar zuciyata ina son ka dayawa ,
Wani irin sanyi yake ji tun daga ƙasan ran sa yana taso masa yana nitsar da idanun sa cikin nata yace " son da nake miki yafi wanda kike min yawa Fatima , son da nake miki ba shi da iyaka , ni ban san iyakar sa ba, kin yarda na gwada miki ɗigo dagga cikin sa ?
Kan ta ta gyaɗa masa tana murmushin da yake bayyana haƙoranta ,
Tazarar dake tsakanin su ya haɗe yana manne fuskar sa da ta ta , tare da shauƙin son da suke yiwa junan su suka himmantu wajen gwadawa junan su tatatciyar soyayyar da suke yiwa juna .
Ƙwanƙwasa ƙofar da Aka yi yasa su sa rabuwa da jikin juna ,
Ba'a jinkirta ba aka murɗo ƙofar a hankali ta shigo bakin ta ɗauke da Sallama .
Siyama ce ta shaida musu zuwan mai gyaran ƙafa .
Yousaouf ya masa iznin shigowa bayan ya gyara mata mayafi.
Ba ƙaramar azaba Falmata ta sha ba kafin ƙashin da ya fita ya koma saboda tsamin da ƙafar tayi kwana huɗu da targaɗe .
Siyama da Youssouf su suka dunga rige-rigen share mata hawaye da gumin da ta haɗa sharkaf duk kuwa da sanyin ɗakin .
Bayan ta dawo cikin nutsuwar ta lokacin Youssouf ya bar ɗakin daga ita sai Hajja da ƙaramar murya ta cewa Hajja " Hajja ki bani wayar ki zan ƙira Mamana da Yakaka .
Ɗan jim Hajja tayi kafin da sigar rarrashi tace "Uwarɗakina Amma fa kar ki shaida musu abunda ya faru da ke domin ba'a sanar da su ba tun da Allah yasa kin fita lafiya kar ki faɗa musu kuma zuciyar su ta kasa nutsuwa da zaman ki anan .
"Ba zan faɗa musu ba Hajja kawai so nake naji muryar su mu gaisa .
"To babu laifi ga wayar ki ƙira su .
Sun jima suna Hira da ita da iyayen ta Khaalty Rahima da Amnee inda har suka yi ƙorafin cikin kwana biyun sun yi ta ƙiran layin Hajja bata ɗauka musamman ma a jiya da Yakaka ta koma Abuja .
Cikin ɗoki Falmata take sake tambayar su 'Yakaka ta tafi gidan ta ?
Amnee ta bata amsa tana dariya da cewa "jiya suka tafi tare da yayan naku takwarata an zama 'yan Abuja ( kamar Ammi Haseen 🤣)
Cikin zaƙuwa Falmata ta fara ƙiran layin Yakaka bayan sun yi Sallama da su Amnee.
Sai dai ƙira biyu tayi ba'a ɗauka ba , yamutsa fuska tayi tana sake danna ƙiran take mitar " Yakaka ko ina ta ajiye wayar ???
ABUJA NIGERIA
Kai-kawo Yakaka ta cigaba da yi a cikin banɗakin da take tsaye , karo na barkatai ta sake sunkuyawa tana leƙe ta ƙafar ɗan makulli , da sauri tayi baya tana sakin wani ƙaramin ihu ƙiris ya rage ta faɗi saboda santsi jikin ta na karkawa ta dafe ƙirjin ta tana mayar da numfashi .
Idanun ta ba ƙarya suka mata ba tirƙeƙen karen da take hangowa tun safe a can nesa daga tsakiyar ɗakin wani lokaci kuma ta hango shi a gefe shine ta gan shi daf da ƙofar a yanzu kamar ma shima leƙen ta yake ta inda take leƙawa dan babu shakka sun yi ido huɗu ita da shi..
Zamewa tayi ta zauna a ƙasa dirshan cikin banɗakin daga inda take tana iya jin wayar ta dake ƙara lokaci zuwa lokaci tsawon yinin amma ba damar fitowa ta ɗau wayar saboda tirƙeƙen karen da yake ta shawagin sa a ɗakin har gado yake hawa yana sauƙa .
A hankali ta saki wani sabon kukan da aƙalla tayi irin sa fiye da sau goma daga safe zuwa yanzu da ta tabbatar yamma tayi rana kuma tana gaf da faɗuwa .
Assalamu Alaikum masu karatu da fatan kuna lafiya ?
Yau dai bakina da goro ba zan ce kome ba bayan fatan alheri da nake muku a koyaushe.
Nagode.
[4/15, 10:16 PM] Zuraiyah Zuzu 🌟: Mafari.
. ( Hargitsin Rayuwa )
Umm'muaz
53
Tsayuwar minti ɗaya zuwa biyu tayi tana kallon ta kafin ta ƙaraso gaban gadon ta zauna ba tare da tace mata ƙala ba .
Hakan da tayi ya sake ƙular da Sofia dan haka a fusace tace " zaɓi na zo baki ko dai yini tare da Sam ko kuwa ki fice daga gidan nan ki tafi can inda kika saba zuwa yawon ki a garin nan idan shi da ya ajiye ki ya dawo kin dawo dan yinin ki da ni a gidannan bana jin zan iya jurewa .
Yakaka wacce kan ta ke ƙasa har Sofia ta gama bayanin ta bata ce mata kome ba tamkar dai bata jin yaren da Sofia take yi ta miƙa hannu a hankali ta ɗau wayar ta ta fara dannawa ba tare da tasan me take yi ba '
Hakan da tayi ba ƙaramin tunzura Sofi tayi ba a fusace tace "Dan Ubanki watau ga mahaukaciya tana magana kin wani yi banza dan....'
Kamar an safure ta Yakaka ta miƙe daf da Sofi ta zo ta tsaya idanun ta ƙyar akan ta cikin muryar ta da bata cika ƙarfi ba tace "Duk wani cin mutumci da zage-zagen ki ya tsaya a iyakar kaina , kar domin kin ga ina yin shiru kiyi zaton za ki iya zagin iyayena na ƙyale ki .
" ban ajiye iyayena kurkusa ba idan ke kin raina naki iyayen na.....
Turo ƙofar da aka yi yasa su duk biyun waigawa .
Doctor Hamza turus yayi yana kallon su kafin ya ƙaraso fuskar sa cike da mamaki ya tattara ganin sa kan Sofi wacce har kawo lokacin bata farfaɗo ba daga ruɗanin da ta shiga kan ji da tayi Yakaka ta mayar mata da Martani har ma tana ƙoƙarin rama zagin da ta mata.
"Sofia me ya faru ? Me kika zo ...
Sai yaƙi ƙarasawa ya ɗan riƙo hannun ta ganin wani irin huci da take yi ,so yake ya jaa ta waje .
Amma sai ta ƙi da ƙarfi ta warce hannun ta kafin ta fashe da wani irin kukan baƙin-ciki .
"Na shiga ukuna Yakaka ni kike zagi ? Iyayena kike zagi Ni-ni kika zaga ? Yakaka uwata da ubana kike zagi ? Daga kawai na shigo na tayar da ku Sallah ?
Yakaka wacce ta cika da mamaki da tsoro ta ɗago kan ta fuskar ta ɗauke da mamakin makircin Sofi da bata saba da irin sa ba tayi rau-rau da ido tana kallon Doctor Hamza wanda shi ma ita yake kallon fuskar sa a ɗaure , ta juya ga Sofia tace "ki ji tsoron Allah ni na zage ki ? Ba ke kika zage ni ba ? Ina ke ce kika shigo kawai kika fara zagi na har da Babana ?
Sofia ta zaburo zata yi magana Doctor Hamza ya dakatar da ita da cewa "saurara Sofia wai me yake damun ki ne ? Ya za ki shigowa mutane ɗaki haka da sassafe ?
Zata yi magana ya sake katse ta wannan karon muryar sa a kaurare yace "Sofia bana son tashin hankali da fitina , ran ki zai yi mummunan ɓaci muddin kika ce ...
Sofia wacce take jin zuciyar ta kamar zata fashe ganin Doctor Hamza yana shirin birkice mata kuma a gaban Yakaka .
Nan take ta haɗiye kukan kissar ta ta murje ido cikin salon ta na goggagun matan da suka raina mazajen su kunya kuma ta mata nawin ɗauka ta gatsina fuska da buɗaɗɗiyar murya tace
"Wannan wane irin rashin adalci ne kake fara rabawa a tsakanin mu tun yanzu ? Kenan dan tana ɗakin bani da ikon shigowa ɗakin ka a duk lokacin da na so ?
"Sofia ki wuce ki koma ɗakin ki kar ki ɓata min rai ki ɓata min lokaci .
Buɗe baki tayi kamar zata ce wani abu sai kuma ta fasa tana mayar da ganin ta kan Yakaka wacce ita ma ita take kallo , da haƙoran ta ta cije leɓen ta na ƙasa tana yiwa Yakaka wani irin mugun kallo tayi ƙwafa kafin ta juya a fusace ta fita a ɗakin tana wani irin bugo ƙofar da har sai da Yakaka ta firgita .
Tsoron Sofi da ya ɗan yi ƙaura saboda zuciya da tayi da ta zagi Baban ta taji yana dawowa sabo fil ,ta tuno da zaɓin da tace ta bata kan ta zauna ta yini da kare a ɗaki irin na jiya ko kuma ta fita ta bar gidan to ta tafi ina ?? Yaya dacta ma ai ba zai bari ta fita ko da ƙofar gida bane kuma a can ma an mata nasiha kan fita ba mutumcin matar aure bane a dunga ganin ta a titi haka siƙau muddin ba lamarin zumunci mai ƙarfi ko aiki ko kasuwanci zata fita yi ba .
Hannun sa da ta ji a ƙugun ta shi yasa ta sauƙe ajiyar zuciya , tana jin lokacin da ya sako fuskar sa ta gefen wuyan ta ƙamshin turaren sa na game mata hanci , muryar sa kamar ba shi ya gama kurara Sofi yanzu ba yace "tunanin me kike yi Wafaa ? Bana son kina yawan tunani na faɗa miki .
A hankali ta juyo ba tare da ta fita a tsakanin hannuwan sa da ya kewaye ta da su ba tana yin ƙasa da murya tace "Yaya Dacta wallahi ban zage ta ba ku....
"Shitt yace yana ɗaura hannun sa akan laɓɓan ta da yasa ta ɗago kan ta tana kallon ƙwarar idanun sa da suke cike da tausayin ta
"Ba sai kin min bayani ba Wafaa na san halin Sofia , kiyi haƙuri zan ɗauki mataki ba zan bari ta ci zarafin ki ba da ke da ita duk matan Aure na ne kiyi haƙuri kin ji ko ?
Wata sassanyar ajiyar zuciya tayi jin daɗin bai yarda da sharrin da ta so ƙulla mata ba " Nagode Yaya Dacta .
Murmushi ya yi mata kafin ya sake matso da ita jikin sa kamar mai raɗa yace "mu je mu kwanta kafin lokacin tafiya ta aiki .
Da sauri ta girgiza kai kafin tace "Yaya Dacta kitchen zan tafi na yi girkin abin karyawa kafin ka tashi bacci.
Zama yayi a bakin gado yana zaunar da ita a cinyar sa yace "No Amarya ce ke Wafaa bai ma kamata kina shiga kitchen ba har sai mun gama amarcin mu ko ?
Ya ƙarasa da sigar tsokana yana ɗaga mata gira .
Ɗan murmushi tayi tana miƙewa tsaye "zan tafi kitchen Yaya Dacta bana so ka tafi office baka yi breakfast ba .
Da gama faɗin haka ta taka tana barin ɗakin , fuskar sa ɗauke tattausan murmushi ya bi ta da kallo salon kulawar da ta gwada masa ya burge shi daban da na Sofi wacce bata iya kula da duk wasu lamuran nasa ba sai fa gwada haukar So a sarari .
Bai kwanta ba sai ya jawo littatanfan sa na addini ya shiga karatu.
A kitchen cike da azama irin na matan da suka gogu da aiki Yakaka ta ɗora ruwa kafin ya tafasa ta kwaɓa fulawa da baking powder sai 'yar zuma da ta sa a madadin sugar .
Lokacin da ruwan ya tafasa ta wanke shinkafa fara ƙal ta tuwo ta zuba tare da Sugar sannan ta zuba spices da ake amfani da su wajen haɗa shayi .
Kafin shinkafar ta nuna , ta ɗora mai ta fara soya pancake da har ya fara tashi saboda ɗumin wajen '
kafin ta gama shinkafar ta tayi ligib dan haka ta dama madarar gari mai yawa ta juye akan shinkafar ta da tayi ligib tana juyawa yayi kauri kamar talge shinkafar kuwa tabi cikin madarar, ɗan manshanu kaɗan ta zuba aiki ta kashe Sugar ta bari.
Da ta gama soya pancake bata bar kitchen ɗin ba sai da wanke kwanukan ta goge ko'ina tsaf .
Sannan ta buɗe fridge ta ɗauko Strawberry ta wanke shi tsaf ta yanka shi a tsai-tsaye bowl ta ɗauko mai kyau tazuba basisen da yayi nar-nar da shi ya kwanta fari ƙal , sai ƙamshin man shanu da kayan ƙamshi yake yana ɗaukar Ido .
Bayan ta zuba iya adadin yadda ta ke ganin yayi sai ta jera Strawberry ɗin a kai , ta rufe , ta ɗau wani bowl daban kuma ta zuba pancake .
Bata juya ba amma jikin ta ya bata da tsayuwar mutum a bayan ta dan haka ta juya da sauri ,
Ajiyar zuciya tayi ganin Doctor Hamza ne shirye yake tsaf cikin shirin sa na zuwa wajen aiki a hankali ya tako har inda take yana bin fuskar ta da kallo da ita ma shi take ta kallo cike da burge ta da yayi kamar wani bature ya tsuke cikin lounge suit launin shuɗi Mai duhu .
Yana mata murmushi ya shafa kumatun ta , "Wafaa wannan kallon fa ? Yace da sautin da yake tsakanin maƙoron sa .
Sunkuyar da kai tayi a dan kunyace da 'yar ƙaramar murya tace "ba kome har ka shirya ? Nima na gama girkin .
"Naso na makara ma wafaa , me kika girka mana ? Ya furta hakan yana zarcewa da hannun sa ya buɗe abincin da ta haɗa , da kallo ta bi fuskar sa cike da son ganin yanayin da zai nuna .
Buɗe baki yayi cike da jin daɗi sai kuma yayi murmushi "Basisee ? Wow Wafaa ashe kin iya girki ? Kamar kin san na daɗe rabo na da na ci Basisee .
Murmushin jin daɗi tayi tana ɗaukar farantin da abincin ke kai tace "Yaya Dacta to muje ka ci tunda ka ga har ka makara .
Bayan ya zauna a kujera ta Zuba masa basise a Plate ta ɗeba masa pancake ɗin ta zuba a gefe.
Duk abunda take yana bin ta da kallo cike da so da sha'awa komen ta a tsaftace dai-dai da yadda yake so .
Bayan ta zuba masa yayi bismillah ya ɗau pankcake ya dangwali Basisen ya kai bakin sa ya gutsura
Daɗi da ƙamshin girkin ya ratsa shi , a karo na biyu Yakaka bata tsammata ba ta ga ya nufo bakin ta da Pancake ,
Noƙewa tayi tana kallon shi tace "idan ka gama nima
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Chapter 93
Chapter 94
Chapter 95
Chapter 96
Chapter 97
Chapter 98
Chapter 99
Chapter 100
Chapter 101
Chapter 102
Chapter 103
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 92 Chapter of 103