Hajiya yanzu" faɗin Raheena domin ta ji daɗin dawowar da Alhaji yayi don ƙawarta.
Ta kuma cewa, "to ni zan tafi Momy na jira na" "toh shikenan sai goben" "shikenan abun da zaki ce sai gobe?" "Toh akwai wani abin da zance ne?" 'Yar harara Raheena tayi mata ka na ta ce, "eh mana, da kina cewa in gaishe da Momy, amma yanzu baki faɗi hakan ba, jiya ma haka" sai da Amna tayi alamar mantuwa kafin ta ce, "na fa riga da na faɗi hakan a raina, kawai dai ban sanar da ke bane, amma ai bazan manta da Momyn ki ba" "Momy na?".
Bugan goshin ta tayi jin ta kuma kofsawa sannan ta ce, "no Momyn mu nake nufi, baki na ne kawai ke kuskure yau" bugan kafaɗar ta Raheena tayi tana dariya tayiwa Ammu sallama tana wucewa, sai kuma ta ƙara juyowa ta ce, "baza amin rakiya bane?" "Dole ma" Amna ta faɗi suka wuce suna dariya.
#Alhaji ya dawo, to ko yaushe Yazeed ma zai dawo?
Kuna ganin Amna zata yi wannan aikin? To idan zatayi ya zai kasan ce? zata ƙyale Marwan haka ta koma kan su Saleem ko kuwa?
____________________________________________________________________________________________
Part 7️⃣3️⃣▶️7️⃣4️⃣
Hajiya bata samu damar waya da mashawarciyar ta ba, saboda bawa Alhaji kulawa dan dawowar da yayi, ko ba haka ba ma maganar ai bazaiyu a waya ba, da so samune ma Ladingon tazo, to amma ta sanar da ita itama akoi abinda ke damunta, yaron ta babban ya ƙara aure amma matar ta fi ƙarfin ta, domin kuwa duk wata kuturɓar da ta haɗa ba ya aiki, gashi yaron yanzu kuɗi yake samu ba ƙarami ba.
WASHE GARI.
Gaba ɗayan su babu mai sukuni, kowa da maganar Alhaji ya kwana a ransa, musamman Hajiya da kuma Marwan, jiya Hajiya ke sanar wa da Yazeed hukuncin da Dadyn sa ya aiwatar, amma sai ce mata yayi, "Hajiya wannan ai tunani mai kyau ne, kinga ƙila hakan ya taimaka mata ta wani fanni..." katseshi tayi da faɗin, "da'alama har yanzu soyayyar yarinyar nan yana rufe maka ido ko? Idan ba rashin hankali ba ce maka akayi fa shugabar kamfanin zai bata ba wai ƙaramin matsayi ba, amma Kana min wani zantuka daban?" Dan haushi kashe wayar tayi ba tare da ta kuma sauraron zancen sa ba.
Amna batayi yunƙurin yi ma su Hajiya wani abu ba jiya, domin itama da kanta ba isashshen barcin tayi ba, kusan rabin kwana tayi itama da tinanin maganar Alhaji.
Kamar yadda Raheena ta sanar mata, gurin ƙarfe tara tazo da mota, da tinanin kada ƙawarta ta canza magana, amma hakan bai faru ba, ta fiya sukayi suna hira gwanin sha'awa, har suka isa makarantar.
Ko daga nesa ka hange makarantar ka san babu talaka da zai samu zarrar zuwa da sunan wai karatu, idan ba ya samu wata hanyar ba, domin yadda makarantar ta haɗu, A.A royal university, kai daga jin sunan sa ai kasan na 'ya'yan masu hannu da shuni ne, ba ƙaramin kallo Amna ta keyiwa wannan makarantar ba, saboda ko da wasa ba tajin ta taɓa ganin makaranta mai kyawun wannan, "wannan wai makaranta ne?" Ta faɗi a zuciyar ta, yanayin yadda Amnan take ne yasawa Raheena wani kokonto a ranta.
Hakan yasa tayi mata tambaya da cewa, "besty ya kike kallon makarantar kamar yaune mafarin shigan ki? Ko ya sauya miki ne?" Juyowa Amna tayi tana kallon ta, a ranta tana faɗin, "Amna ya kike haka ne? Ai ko gurin zinari za'a kaiki bai kamata ki yi abun da kikayi yanzu ba, haba ba sai a raina ki ba, bare kuma kinsan basaja kikeyi fa",
Ta ku gaba tayi ba tareda ta ba Raheena amsa ba, hakan yasa Raheena itama a ranta tana faɗin, "kar dai na taɓo 'yan Safnan da suke kanta, ta dawo kamar da, ni da nake murnan ƙawata ta canza" a fili kuwa tafiya tayi ta cin ma Amna tana murmushi ta ce, "kai besty ni fa ba maganar haushi na faɗa ba" "to ni cewa nayi kin yi maganar haushin?" Cewar Amna ba tare da ta kalli Raheena ba, "To me yasa kika yi min shiru?" Tsayawa Amna tayi ta juyo tana kallon ta yanzu fiska a haɗe, itama Raheenar tsayawa tayi tana kallon Amna.
"Matso in sanar da ke abinda yasa nayi shiru" faɗin Amna, matsowa rayi tana cewa, "faɗa min" jaƙul-ƙuli Amna ta fara yiwa Raheena haɗi da faɗin "shine wannan" da sauri Raheena tayi baya tana dariya kamar yadda Amna ma abinda take kenan, haka dai suka ƙarisa ciki.
Akan hanyar su ta dawowa bayan sun samu damar amsan dukkan takardun su, Amna ta hangi wani ƙaton chemist, umartan direban tayi da ya tsaya, tsayawa yayi kamar yadda tace Raheena na yi mata kallon mamaki, "kar dai kice baza ki ƙarasa gida a mota ba?" "Not that inason inje chemist ɗin can ne" "to amma what.." Amna bata bari ta ƙarasa ba ta buɗe ƙofar ta ce da ita, "akwai kuɗi a wurin ki?".
"Eh akwai" Raheena ta faɗi tare da buɗe hand back ɗinta ta, "kamar nawa kike so?" Ansan jakan hannun Raheenar kawai tayi tana faɗin, "ban sani ba amma bari na tafi da jakar duka, duk kuɗin da yaci shikenan, in mun koma gida inmayar miki".
Tana faɗi ta wuce, zuwa tayi ta siya abubuwan ta, daga bisani ta dawo, tana shiga motar ta cewa direban Raheena, "zamu iya tafiya" ba tare da ta sanarwa Raheena abin da tayi da kuɗin ba.
Direba ko ya tada motar suka cigaba da tafiya.
DARE YAYI.
Hajiya Marwan da kuma Salim da Ruki suna zaune kan dining, Amna ta taho tana shirin zama, bata gama sallamar da jikin ta kan zama a kan kujerar ba Hajiya ta miƙe haɗi da janta gefe, jan da tayi mata ya haɗa da haushin da ta kwana kuma ta wuni da shi na Amna, kan maganar Alhaji.
Kallon ta Amna tayi kamar bata san abinda tayi ba, cikin ɓacin rai da tsana Hajiya ta fara magana, "na ga alamar iskancin na ki ƙaruwa yake ƙara yi ako wace rana, wallahi kar ki ƙure ni idan ba haka ba, sai insa Marwan da Saleem su lakaɗa miki duka yanzun nan" "Saleem dai don ni bana ciki" Marwan ya faɗi haka kansa a ƙasa.
domin babu abinda zai sa ya ko taɓa Safna bare ayi maganar duka, domin kuwa bai manta alƙawarin da ya ma aljannu ba, ƙafafuwan sa har yanzu Jan su yake basu daina yi masa zugi ba, domin ko jiya zuwa yau, yayi tsammanin ƙara ji daga garesu amma yaji shiru, yana kyautata zaton ko sun yafe masa ne, tunda ko kallon banza baiyi wa Safnan ba ƙila shiyasa, domin kuwa har girma yake ɗan bata idan yayi tozali da ita, to akanme yanzu kuma zai ɓata rawansa da tsalle? Abinda bazai saɓu ba kenan.
"Akanme Saleem kawai? Kenan kai baza kabi umarnin uwar ka ba kenan?" Cewar Hajiya gaba ɗaya suna kallon sa, saboda Ruki ta fara shafa mata cewa Marwan n'a wasu ɗabi'u akan Safna yanzu, amma rashin nutsuwa da bata yi bane yasa bata bibiyi lamarin ba, gashi kuwa hakan na tabbata, kardai furucin da suke yi mata na mayya ya kamata, zata lamushe mata ɗa a banza domin kuwa ta san tun fil'azal Marwan ba son Safna yake ba, gwara da Yazeed ne ma.
"A sha re zancen kawai Hajiya ki zauna mu zuba abinci muci shine maslaha" cewar Marwan yana janyo plate domin dama basu fara cin abincin ba suna jiran fitowar Alhaji. Saleem barin kallon da yake wa yayan sa yayi ya maida kan Amna ya ce haɗe da ɗaure fuska, "get out of here, dama anan kike cin abinci ne? In banda iskanci" suma Hajiya da Ruki wurin Amnan suka juya da kallo, kowa ya buɗe baki zai ƙara yi mata wani magana ta ce.
"Kar ku damu yanzu zan wuce ma, babu buƙatar wahar da bakin ku" tana faɗi ta wuce tana murmushin da ita kaɗai ta san dalilin hakan, ba ɗakin Ammu ta nufa ba, zama can gefe tayi inda baza su gan ta ba.
Su kuwa Hajiya Dady na zuwa a ka fara ba ciki haƙƙin sa na dare, Dady kaɗan yaci ya tashi ya koma ɗakin sa, sakamakon kiran da ya shigo wayar sa, Hajiya da zuri'ar ta kuwa sai da suka yi hani'an sannan kowannen su ya miƙe, "wayyo Hajiyaa! Ciki na" cewar Ruki haɗi da riƙe cikin ta yayin da ta fara ji tamkar ana yamutsa mata kayan cikin.
Hakan yasa Hajiya saurin riƙota tana faɗin, "me ne...?" Sai dai bata samu damar ƙarasawa ba saboda kamar Ruki ta harbe ta, domin kuwa itama ji tayi kamar ana muƙur- ƙusa mata kayan cikin ta, su Marwan zaro ido su kayi suna kallon abinda ya faru da Hajiya da Ruki, ai kan suyi wata ƙwaƙƙwaran motsi ko wanne a cikin su shima ya kama cikin sa.
Kowa da yadda yake sakin ihunsa, sai kuma suka fara jin kamar zawo na ƙoƙarin samun hanyar fita daga masubur-buɗan sa, Ruki ce ta fara sakin nata tusan sai Saleem ya amshe, haba wa ba sai Marwan ma yace baza ayi babu ni ba, dariya Ruki ta sa jin ƙarar na Marwan ɗin ya fito wani zuit dashi kai kace an cewa bodari gyara zaman ka, Hajiya kuwa maƙe na ta tayi domin kuwa koba komai ai bai kamata yaran ta suji ƙarar fitan na ta ba, wannan ai abun kunya ne.
Sai dai fa tusa ya ce, ba da ni ba Hajiya dole na antayo nima na shana akan me za'ayi babu ni?. Ƙafar da Hajiya ta sa dan wucewa ba sai ya ba wannan tusar damar fitowa ba, ji kake baaam kamar ƙarar fa ɗin nucléaire, haba saiga Hajiya apuja jan tana nufan upstair, su Ruki cika bakin su da iska su kayi suna kallon kallo, haba kawai suka fashe da dariya, sai dai fa dariyar na su baiyi tsawoba suma suka kama hanyar ɗakin su, domin samun sarari a toilet, sakamakon yadda cikin su ya ke sake wani ƙa ra ƙulu-lululuu, suna tafe suna sake boma bamai abin su kowa da kalar ta sa.
Hajiya tana isa ɗaki ta nufi toilet, sai da ta fitar da wannan cutar ka na taji sala ma, fitowa tayi ta zauna a bakin kujera tana sauke numffarfashi kamar wacche ke gasar numfashi, sai dai cikin nan bai kuma yi mata amana ba, domin ko wani gagarumin zawo ne ya kuma tahowa, "wayyo Allah na ni Zainabu! Wannan wace iriyar bala'i c..." bata ƙarasa kalmar ba ta ruga zuwa toilet ba tare da tayi shirin hakan ba. A ɓangaren ukun ma haka yake domin babu mai minti uku waje ba tareda ya kuma shigewa banɗaki ba. Marwan kuma abu ya haɗe masa goma da ashirin, ga cangala ƙafa ga kuma iftila'in yanzu.
Hajiya ce zaune kan carpet tayi ɗai ɗai, domin kuwa yadda ta zauna sai kace wacce akewa ruƙiyya, Alhaji zaune kan kujera ya tasa ta gaba yana cewa, "ke ko kunya bakya ji? Dubi yadda kikayi zaman nan, ba kyajin kunya ɗaya daga cikin yaran nan yazo ya tadda ki haka?" "Daga baya kenan wai an tambayi biri kana cin ayaba? Ni da nayi ƙatuwar tusa a gaban su, wanda ni da kaina saida fitar tusan ta bani tsoro, to me ya rage kuma" cewar Hajiya cikin ranta a fili kuwa ko sannu bata ce masa ba, saboda it kaɗai ta san yadda cikin ta yake murɗa har yanzu.
"Look toilet ɗin ma a buɗe kika barshi, ji yadda ɗakin nan yake wani tashin hamami, da girman ki baza ki iya fesa ko air..." sai dai fa shima Dady a halin yanzu bai samu nasarar ƙarisa wa ba, jin cikin sa na yi masa kukan ƙwari, da sauri-sauri shima yayi toilet ɗin Hajiyar da ɗazu yake binsa da kallon ƙyama, ɗakin ma yake son barin sa, sai ga shi yanzu ya shige ciki ba tare ya shirya hakan ba.
"Waya gaya maka borno gabas take, gashi kaima ka shiga layi, kaji inda daɗi" Hajiya ta kuma faɗi cikin ran ta.
Amna dake manne à ƙofar su Hajiya ce riƙe da bakin ta, tana danne dariyar da ke neman kufce mata, barin wurin tayi tana kallon ɓangaren su Marwan da ta baro yanzu tana kuma sakin dariyar ta ƙasa-ƙasa.
Bayan ta koma ɗakin Ammu take cewa Ammu, "kinji wani tusar da suka saki a jere ɗazu kuwa Ammu?" Ta faɗi tana ƙara tintsirewa da dariya, nan ta fara sanar wa Ammu abinda tayi musu, "saida na tabbatar da masu aiki sun kammala kai musu abincin dining, naje na buɗe gaba ɗaya kulolin na zuzzuba maganin sa zawon da na siya ɗazu a hanyar dawowar mu ni da ƙawar Safna, kafin su zo harna bar wurin, shine fa bayan sun zauna nima nazo da niyyar zama suka hanani, saboda tsabar ƙiyayyar da suke wa Safna basu san ni kawai zuwa nayi dan neman tsokana ba, amma na so ace Alhajin nan bai ci ba, saboda shi mutumin kirki ne, amma dai ba matsala tunda kaɗan ya ci duk shima zai ɗan ji jiki, yauwa ina faɗa miki Ammu bayan sun gama ci suna miƙewa dan barin wurin magani ya fara aiki, to dama shi maganin sha yanzu magani yanzu ne, sai kinji yadda kowa ke sakin ta sa tusar"
Tsayawa da maganar tayi tana dariya ta kuma cewa cikin dariya "suna can kowa na fama da jikin sa" Ammu kallon ta kawai take yi, da zata samu dama da itama ta yi dariya sosai yau, taso ace abun a gaban ta ya faru, lokacin da take ƙarama itama ba ta ɗaukar reni ko kaɗan idan anyi mata abu bata cika haƙuri ba, domin ko zaman da sukayi da Hajiya à baya kafin ko mai ya sauya, to fa ba ta lamuntar abinda Hajiyar zatayi mata, nuna mata take ba ta jin tsoron ta, hakan yasa a baya Hajiya ba ta yin mata abu a gaban idon ta, kuma yazo mijin ta ne babba, amma yanzu da taga ba ta da kataɓus sai take yi mata duk abinda take so, Safna kuwa halin Mai daraja ta ɗauko, à halin mahaifin ta kaɗan ne t'a baro.
Buɗe bakin ta tayi ta fara yiwa Amna murmushi haɗi da ɗaura hannun ta a kan ta.
#MU HAƊU A NEXT PART IN ALLAH YA KAIMU GOBE. DON JIN YADDA SU HAJIYA ZASU ƘARE DA MUGUNTAR DA AMNA TAYI MUSU.
ALƘALAMIN TAKU HAR KULLUM... KU ƘARASA MIN😊
____________________________________________________________________________________________
Part 7️⃣5️⃣▶️7️⃣6️⃣
Tsaye gaba ɗayan su suke à falo inka ɗauke Amna da bata cikin su, fiskokin su harya rame saboda zawayin da sukayi babu ƙaƙƙautawa, fiskar Dady ne mai ɗan dama-dama da kuma Marwan amma sauran kam ba'a magana, bare ma Ruki yadda idon ta suka firfito waje domin tsayuwar m'a ta kasa yinsa, zama tayi a ƙasan kapet ɗin falon.
Dady ne ya ɗago agogon dake hannun sa yana kallon time ƙarfe biyu na dare, lallai wato awanni suka shafe suna fama da cutar bayan gida kenan?
Mai da hannun n'a sa yayi yana kallon ko wannen su, sannan ya ce, "what is the reason for this happening? Taya za'a ce abu irin wannan ya faru da mutane dayawa haka?" "Dady That's what I was thinking too" "anya ba tsinannun 'yan aikin nan bane suka sanya mana wani abu a cikin abinci? Saboda n'a tabbatar da cin sa ne ya sanya mana lalacewar ciki" Cewar Ruki hakan yasa gaba ɗayan su suka shiga nazarin maganar na ta, Hajiya da har yanzu take jin cikin ta ba'a daidai ba ta ce, "a ah bana tunanin zasu yi hakan, wa'yanda ba sa ƙaunar kalmar kora? Daga ka furta zasu fara roƙe-roƙe, kaga kuwa ai basa yi abinda zai sa akore sun ba"
"A koi wanda nake zargi" cewar Saleem yana kallon su duka, "kai banason shashanci, wa kai kuma kake zargi?" Faɗin Dady tare da kafe sa da ido, "Safna!" Saleem ya bada amsa, "what are you saying?" "Yes Dady zata iya aikata hakan, saboda tun da ta..." Hajiya tayi saurin rufe bakin Ruki daga ƙarashe maganar, ta san cewa zatayi tun da Safna ta dawo daga yawon ta, shi kuma Alhaji ya tambayi wani yawon?, daganan kuma magana ya dawo wani zancen daban.
"Ya kika rufe mata baki?" Alhaji ya faɗi hakan, Hajiya ta ce, "Alhaji na rufe mata baki ne saboda nima akwai tunanin da nayi" "wani tunani?" "Maganar yaron nan da kwai ƙamshin gaskiya fa, tabbas na san yarinyar nan ta ci abincin, idan kuwa hakan ya faru, to ya kamata itama cikin ta ya dame kamar na mu, dan haka muje mu duba mu gani, idan har ya kasance babu abinda ya same ta to itace tayi mana hakan, idan itama ya faru da ita tofa daga masu aiki ne, sai mu bincike su".
Dady ya ce "Akan me zaku sa tinanin nan à kan ku? Safna baza ta taɓa yin makaman cin hakan ba" "Dady muje mu tabbatar kawai" cewar Saleem, domin ɗazu bayan ya fito daga toilet ya fito ya tsaya a step yana kallon falon ba tare da ya sauko ba, riƙe ƙarfen yayi da ɗayar hannun sa ɗaya kuma a cikin sa, a nan ne ya hangi Amna kamar tana cikin annashuwa, hakan ya ɗar sa masa kokonto a ran sa, duk da dai yasan Safna ba tada mugun hali amma tun da ta dawo yake karo da ita cikin wani yanayi, hakan yasa bai yarda da ita ba.
Nufan hanyar da zai sa da su daga ɗakin su kayi, Hajiya na roƙon Allah yasa Safnan ce ta aikata musu haka, ai kuwa da yau sai ta tantance kiɗi da karatu a hannun ta, Dady kuwa ba don yaso ba yabi su, domin ya san 'yar sa Safna baza ta aikata kotan-kocin hakan ba, haka har suka isa ƙofar, Ruki ce gaba zata buɗe ƙofar, amma kanta sa hannu dan bude ɗakin suka fara jin sautin ƙaran ta.
"Waai wai ciki na, wayyo zan mutu, ciwo" abinda su kaji Amna na cewa kenan, cikin tashin hankali Dady ya shige ɗakin yana nufan inda take can gefe a durƙushe, ta riƙe cikin ta tana ci gaba ƙara, suma sauran shigowa su kayi cikin rashin kulawa suke kallon ta, Marwan ne kaɗai bai mata wannan kallon ba, "yata kema cikin n'a ki ne ke ciwo?" Cikin nuna bata san hakan ya faru da su ba, ta ce, "Ddady kumma hakan ya same ku ne?" Tayi maganar da muryar da ke nuna ba ta daidai.
"Saleem jeka ɗaki ka ɗauko akwatin neman agaji da sauri" cewar Dady ba tare da ya dube sa ba, haɗe fiska yayi jin wai shi ne wanda zai ɗauko akwatin neman agaji, kuma Safna za'a wa aiki da shi, ko motsi daga inda yake baiyi ba ya ce,
"Dady forget her, muma babu abinda muka sha, kuma ba munji sauƙi ba?" "Tinanin hakan ne bai zo muku ba" cewar Amna ƙasar leɓe, "kinyi magana 'yata?" Faɗin Dady jin kamar yaji sautin fitar magana daga bakin ta, rintse ido tayi tana ci gaba da matse cikinta daga bisani ta ce, "Dady cewa nayi cikina ya fara lafawa" "da gaske?" Ya faɗi yana ɗan sake fiska, ya kuma juyawa gun Saleem ya ce, "jeka mana".
Sai da Saleem ya ja tsakin sa ciki-ciki kan ya wuce, Ruki sai tattamuƙe fiska take, Marwan da Hajiya kuma suna kallon Amna, yayin da Hajiyar ke ji ina ma zata samu hanyar rabuwa da yarinyar nan, ai da ta huta.
Miƙa mata magani Dady yayi bayan Saleem ya kawo akwatin, amsa tayi tana kallon sa a zuciyar ta ta ce, "mutumin nan yana da kirki sosai, amma me dalilin da yasa M.R ya ce in sanya masa ido?" A fili ta ce, "ba damuwa Dady akwai ruwa a nan zan sha dashi" cewar ta cikin muryar shan wahala daga raɗaɗi, dan taga alamun kamar so suke ta sha a gaban su, to ita da babu abinda yake damunta kuma me zatayi da magani?.
Fita su kayi suna komawa falo, ita kuwa tana jin takun su ya tsagaita ta kuma fitowa tana sanɗa, gashi idan tana sanɗa baza kaji alama ko kaɗan ba, da dabara take aikata komai.
"You see? Nasan 'yata baza tayi haka ba, tana da tarbiyya" "Alhaji ya kamata kasan Safna fa ba 'yarka bace, domin ina ganin kamar kana mantawa, taya zaka ba taa yarda haka? Wani lokaci kamar kana nuna kafi sonta akan wa'yan da ka haifa da cikin ka" Hajiya ta faɗi hakan don hakan ba ƙaramin sosa mata rai yake ba, samun guri Dady yayi ya zauna kan kujera, wani irin murmushi ya saki yana bin Hajiya da kallo yana cewa.
"Idan ba 'yata bace 'yar waye ne? Ita ce kaɗai 'ya ga yaya na Mai daraja, a yanzu kuma baya nan, to idan ban ba ta kulawa ba waye zai mata hakan? Ko tana da wanda zata ɗauka matsayin uba bayan ni?" Shiru Hajiya tayi ba tare da ta kuma magana ba, "hakan na nuna cikin masu aikin nan ne aka samu wanda ya aikata, dan haka tomorrow a taramin su inyi magana da su" cewar Dady, nan kowa yayi hanyar makwancin.
Jin jina kai Amna tayi jin maganar da Dady ya faɗa, nan girman sa ya ƙaru à idon ta, da alama mutumin babu abinda yake a ransa sai taimako, komawa ɗakin Ammu tayi tana zama gefen gado haɗi da sauke ajiyar zuciya, "wato su in anbarsu wannan dabara ce koh? Azo a tarda ni à ɗaki don agane ko nice n'a zuba magani" Ta faɗi tana sakin dariya, sai kuma ta tashi don cire kayan basajar ta.
WASHE GARI.
Bayan Dady yasa an tara masa masu aikin girki, nan ya fara tuhumar su, jikin kowacce a cikin su kyarma yake yi, sai rantse-rantse suke, Amna kuwa ganin ana shirin ɗaurawa wasu laifin da tayi ne yasa ta zuwa wurin ta gaishe da Dady, amsawa yayi tare da tambayar ta ya jiki? Ta amsa mishi da yayi mata sauƙi sosai, sannan ta ɗora da cewa.
"Dady ina ganin da kayi haƙuri ka rabu da su, tun da hakan bai taɓa faruwa ba, ta yu sunyi amfani da kayan dafa abincin da gurɓatacce à ciki, saboda wani lokaci yin amfani da abunda ya fara ɓaci ko kuwa rashin wakewa da kyau yana iya haddasa makaman cin haka, me zai hana baza'a yafe musu ba? Inyaso sai à gargaɗe su na gaba" jin jina kai yayi da maganar da ta sanar dashi ya gamsu, amma à gefe ɗaya kuma abinda ba ta taɓa yi masa bane tayi masa yau, wato ta kalleshi ido da ido tayi magana da shi, ba tare da rusunar da kai ba, da kuma nuna kunya. Sai dai bai damu da hakan ba.
Sallamar su yayi daidai saukowar Hajiya daga step, "Alhaji taya zaka sallame su da wuri haka? Ba tare da an hukun ta su kan abinda ya faru ba?" Ƙarar wayar da akayi masa yasa shi tashi ya bar wurin bai ba ta amsa ba, da kallo Amna ta bishi, "me yasa baya son amsa waya à cikin mutane?" Tayiwa kanta tambayar, sannan ta juyo da kallon ta kan Hajiyar da itama da kallo ta bi shi, "Hajiya antashi lafiya?" Da à rashin lafiya kika ganni?" Cewar Hajiya harda harara, "Allah ya baki haƙuri" Amna ta faɗi itama ta wuce.
Amna yatsan ta 'yar manuniya take bubbugawa gefen goshin ta tana tunanin abinda zata aikata a gaba, ƙyafta yatsun tayi tana murmushi haɗi da furta, "iihiiiim" wato dai ta samu idea.
Saleem na zaune kan kujerar garden yana shan iska haɗi da latsa wayar
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 19 Chapter of 56