haka zai bi hanyar da zata masa bayani akan ƙwayar, in dai tana shan sa to tabbas ta wata boyayyiyar hanya take samu, ranar da na yi magana dashi na ƙarshe ya sanar min da ya samu damar magana da ita, dan kuwa da kan ta ta amince masa".
Juyowa yayi ya dubi Amna da itama kallon sa take yi, amma tana sa maganar sa a mahangan tinanin ta yace "abinda na fiskanta shine, tabbas sun bibiye shi ne, suka haƙa masa rami ya afka ba tare da ya sani ba, ni kaina yanzu ina tinanin ƙila suna bibiya na ba tare da na sani ba, dan haka Amna kema ina roƙon ki da kibar wannan maganar kamar yadda nayi shiru kema kiyi, ki kiyaye dan Allah saboda da ace aboki na ya ji magana ta a wancan ranar da duk hakan bai faru ba".
A jiyar zuciya Amna ta sauke haɗi da lumshe ido tana buɗewa, yayin da wani ƙullutun baƙin ciki da kuma alwashi ya bugi ran ta, "thank you so much Uncle, da ka sanar dani wannan sirrin insha Allah zan kiyaye kamar yadda kace" ta faɗi cikin shaƙaƙƙiyar murya dake nuna maka tabbacin zakanyar Baba ta sha kuka.
Sallama tayi musu akan zata wuce gida, Uncle Tukur ne ya kai ta saboda ya kamata ya duba su Mamma, suna shiga gidan Mubarak yayo gun Amna da sauri cikin murnan ganin ta yace, "Amna ina kika je ne? Kin ƙara samu cikin damuwa".
Ta'aziyya ya ma su Mamma da kuma ƙara basu haƙuri sannan ya tafi.
Wannan daren babu wanda ya rintsa cikin su, Amna tinani biyu tasa a ran ta, 1- tinanin mutuwar Baba, 2- tinanin sanadin mutuwar ta shi.
WASHE GARI.
Yau wa ma yake maganar zuwa wani wai School, mutane da yawa suka zo gaisuwa, yayin da wasu da yawa gulma suke akan abinda ya kashe shi, gulma su ke kai kace 'yan ƙauye ne, --- kun san dai ƙauye da gulma---.
SAFNA.
Kamar kullum sai da ta kintsa mahaifiyar ta sannan tayi shirin zuwa makaranta, a daidai gate ɗin shiga layin ta tsaya, ba'a jima ba saiga Raheena a napep tazo, dama haka suke, ko Raheena ta jira Safna a ƙofar shiga first GRA ko kuwa Safna ta jira zuwan Raheena da napep, inkuma akayi rashin sa'a ɗaya ba lafiya, kokuma wani dalili ya hana ɗaya zuwa makaranta, to sai fa sunyi latti, dan duk wacce tazo gurin ɗaya bata samu damar shigowa ba, to fa jira za tayi, sai idan jiran yayi yawa sannan ta wuce.
Suna zaune ita da Raheena bayan an fitar musu lecture, Raheena take cewa, "Besty nifa bikin Salma bai wani min armashi ba, ko dressing ɗin su bai yi min kyau ba" "Dama zuwa wurin biki kikayi ko zuwa kallon dress ɗin su kikayi? Kin san dai sa'ido babu kyau ko?" Safna tayi mata maganar tana murmushi.
"Nifa na kasa gane kanki wani lokaci malama wani lokaci miskila" Raheena ta faɗi tana dariya, itama Safna murmushin take.
Bayan antashi suka yo hanyar gida, kamar kullum Safna aka sauke, bayan sunyi sai gobe aka wuce da Raheena, ita kuwa Safna tayo gida, a hanyarta ta shigowa falon Ruki ta taɗe ta sanadiyyar sa mata ƙafa da tayi a hanya, fa ɗi ƙasa tayi tana jin zafin buguwan da ƙafar ta yayi.
Dariya ta kwashe da shi tace "kwana biyu kin samu free a gidan nan, kina yadda kika so abinki, to watan ci gaba da kasancewa cikin wahala fiye da baya ya tsaya miki, dan haka ki shirya" ta ƙarashe faɗi da sakin wata dariya, ta yi waje ta bar Safna a ƙasa, sai lokacin ta fara ƙoƙarin tashi.
Bata san da cewa Ruki ta zuba man gyaɗa a hanya a kusa da wurin ba, tana miƙewa ta ɗauki jakar ta, taku biyu kawai tayi ƙafar ta ya taka gurin maiƙon, zamewa ƙafar ta tayi a wurin, baya-baya tayi zata faɗi taji an riƙe ta, idon ta a rufe dan ta gama sadaukarwa ƙasa za tayi, a hankali ta fara buɗe idon, ganin wanda yayi mata wannan taimakon, domin kuwa tasan da tayi ƙasa tabbas ƙafar ta ne zata karye.
Tana buɗe idonta ta sauƙe su a kan Yazeed da ya saki ido sai ganin fiskar ta yake kamar yaune ganin sa na farko, mamaki ne ya cika ta da ganin yadda yake mata kallo kamar bai san meke wakana ba, alamar motsin da Safna tayi dan ya sake ta ne yasa shi dawowa daga duniyar da ya shiga.
Sakin ta yayi tare da wayan cewa, yana ƙwalawa direban sa dake kusa kira, da sauri yazo yana faɗin "na'am ranka ya daɗe" "ina masu goge-goge suke?" "Suna ɓangaren su ranka ya daɗe" "kiramin su" yayi masa maganar ba tare da ya bar wurin ba, Safna kam kallon ikon Allah take.
Juyowa yayi yaga ta ƙure sa da ido "Ke me kika tsaya jira anan dama ba shigewa ciki za kiyi ba? To maza bar nan salon san gulma ko?" jiki na rawa ta ɗauki jakar ta daya kuma faɗi ta yi hanyar ɗakin su, da kallo Yazeed ya raka ta.
Ita kuwa Ruki da ta laɓe a gefen ƙofa haushi ya cika ta, "kai Yazeed shishshigin ka yayi yawa wallahi, ina ruwan ka, nida har nake hasaso yadda tafiyar ta zai koma ɗingishi ko rarrafe," ta faɗi a zuciya tare da sakin tsaki a fili marar ƙara.
Masu aiki suna zuwa Yazeed ya hau su da masifa, "wani irin aiki kuke yi ne har da za ku zubar da mai a nan, me ya kawo maiƙo falo wani irin iskanci ne haka? To ku saurare ni daga yau kar na ƙara ganin hakan ya faru, this is first and last warning".
Ƙas kawai su Jummala su kayi da kan su, duk da cewa basu san ya akayi hakan ya faru ba, amma sun karɓi laifin sabida ko gaskiya suka faɗa ba yarda zaiyi ba, sai dai ma su ƙara wa kansu wani abun.
"Jira kuke sai na ce ku gyara?" Yayi musu maganar, ai da sauri suka tafi ɗauko kayan aiki, shi kuma ya wuce rai ɓace da bai zoba da wani abun ya samu yarinyar nan.
#A samu wa'ƴan da zasu raka ni zuwa yiwa su Amna ta'aziyya 😥 to amma kodai Baba......?🤭
Gashi dai an sanar da Amna komai, kuna ganin zata yi binciken itama ko ƙaƙa?
Menene tinanin ku a kan Yazeed?
______________________________________________________________________________________________
Part 3️⃣1️⃣▶️3️⃣2️⃣
BAYAN LA'ASAR.
Dogon rigan kanti tasa tare da dogon wandon roba, yayi mata kyau sosai, ɗaure gashin ta tayi da rinbom, kalar gashin ta ba baƙi wuluk, sannan ta sanya hula ta rufe gashin, ta ɗora madaidaicin gele a kai, fitowa da Ammu tayi waje yauma, ta fara mata hira dan ɗebe mata kewa.
"Ammu jiya nayi mafarki kin yi magana da muryar ki da na daɗe nake burin ƙara sauraro, kuma kinsan me kika faɗa"? Cewa ki kayi "my daughter akwai wani ɓoyayyen al'amari wanda da daga ni harke bamu san shi ba, amma nan gaba zai bayyana a gare mu insha Allah". "Ammu nah nayi ta nazarin mafarkin nan shin gaske ne kokuwa ƙaryan mafarki ne kawai, kuma abin mamakin ba wai ni kike faɗawa ba, ni a chan gefe na tsaya ina kallon ku, sai dai banga fiskar wacce ki kewa maganar ba domin ta bani baya, amma kasancewar muryarta da ta doki dodon kunne nane yasani fiddo Ido, sabida muryarta sak tawa".
Ƙure ta da ido kawai Ammu tayi, itama fiskar ta alamar nazari, sai dai babu abin da ta fahimta dangane da wannan mafarkin.
"Ah Lallai ba shakka", cewar Hajiya da tayo wurin buguzun-buguzun kamar wacce za ta tashi sama, a tsorace Safna ta juya tana kallon ta, yayin da zuciyar ta keyin ɗar-ɗar, Ammu kuwa kanta na inda 'yarta take sabida ba damar juyawa, itama tana tinanin da abinda Hajiya ta zo yi yanzu, dan zata iya tina kallon ƙarshe da tayi wa Hajiya tun wani lokaci da jikin ta yayi mugun ta shi, a hanyar fita da ita dan zuwa Asibiti ne tayi tozali da ita, ko lokacin ma harara ce kawai Hajiyar ta rakata da shi.
Kamar yadda ta daɗe bata ga Marwan da Saleem ba, sabida ita Ruki kodan ta tsokani Safna tana zuwa ɗakin, sai shi kuma Yazeed da yake zuwa gaishe ta lokaci-lokaci.
Da Hajiya ta aika musu da kallon ƙas-ƙanci sannan cikin ɗagun murya ta ce "wato kamar yadda bayani ya iskeni hakan take kenan? Tunda kika ga kwanan nan ban samu zama ba shiyasa kika samu damar fito da nakashashshiyar uwar nan ta ki waje ko? Dan munafurci harda samun keken guragu, fito da ita ki kayi dan muma ta lamushe mu kamar yadda ta lamushe uban ki?".
Yauma maganar ta ƙara dakan mata zuciya. wato kenan maganar da Ruki tayi mata rannan a bakin Hajiyar taji kenan? ɓangaren Ammu ma hakan take sai dai ita bai wani dame ta ba saboda ba yau bane farkon fitar mummunar kalmar a bakin Hajiyar a gareta ba.
"Tambayar ki nake kin min shiru ga mahaukaciya na zuba zance ko?" Cewar Hajiya tana ƙara hayayyaƙo mata kamar zata rufe ta da bugu, "ranar da tayi rashin lafiya ne doctor yace a rinƙa fitar da ita tana shan iska, kuma Dady ne ya bani damar hakan" Safna ta faɗi hakan cikin tsoron furucin Hajiya na gaba.
"Allaaaaah! Ba shakka wuyan ki ya isa yanka Safna, iyeeee! Wato ni kike cewa Alhaji ya baki dama, to shi Alhajin uban ki ne? Nace shi uban ki ne?" girgiza kai Safna ta hau yi mata ganin fa yau da en muguntan a gaban goshin ta ƙarara. to kari ta kaiwa Safna da ƙafa daya sa ta saurin sauka daga inda take zaune.
"Kiyi haƙuri Hajiya, wallahi ban fito da Ammu dan wata manufa ba" hamɓarin da Hajiya ta kai mata baki ne yasa ta gunmtse bakin na ta tare da ɗaura hannayen ta biyu duka akai, tana bin Hajiya da kallon tsoro.
Jikin Ammu ne ya fara rawa saboda ƙoƙarin miƙewa da take son yi, a hankali ta fara ƙoƙarin tashi daga keken guragun ta, dan so take tayi ido huɗu da Hajiya da bata san idon uwa ba, sai dai kan ta ƙarisa miƙewar Hajiya ta sa ƙarfinta ta ture ta, nan Ammu tayi ƙasa daga ita har keken.
Da sauri Safna ta yunƙura dan taro Ammu, sai dai ta riga da tayi ƙasa, durƙusawa tayi tana ƙoƙarin ɗaga ta, hawayen takaici na fitowa daga idanun ta, saida ta komar da Ammu kan keken sannan ta juyo tana yiwa Hajiya wani irin kallo wanda bata taɓa yi mata irin sa ba, ita ma dakan ta bata san tana yi ba.
Zaro ido dan mamaki Hajiya tayi, yau Safna ke yi mata irin wannan kallon? Kallon da ke nuna zalla rashin tsoro a idanuwan ta? "Safna ni kike wa kallo haka? Ba shakka dan na taɓa ruɓaɓɓiyar uwar nan ta ki? To bari in illa ta ta, kinga sai ki nunamin cikakken manufar abinda idon ki keson isarwa". Ta faɗi tana ƙoƙarin ƙara ture Ammu a karo na biyu, aikuwa sai ji tayi an riƙe mata hannu, wa zata gani Safnan ce kuwa.
ƙara sa ɗayan hannun ta tayi aikuwa Safna ta kuma riƙewa da ɗaya hannun, sakin baki sakaka Hajiya tayi tana son fisge hannun ta amma kamar a ƙarfe ya maƙale, ja takeyi amma Safna ko gezau sai ma ƙara ƙure ta da ido da tayi, yayin da ƙwayar idon ta ke shirin sauya kala.
ƙara zaro ido Hajiya tayi, wannan karon harda tsoro ya cika ta, ganin ƙwayar idon Safna na chanzawa izuwa wani launin, Ammu ma kallon mamaki takewa gudan jinin na ta irin sauyawar da tayi cikin ƙanƙanin lokaci.
Dorinar da aka zuba mata a baya ne yasa ta sakin hannun Hajiya tare da rintse ido da ƙarfi, "shegiyar yarinya mayya kawai, Saleem cimin uban ta, naga alama idon ta yayi ƙwari yanzu, nan gaba duka na ma zata yi" Hajiya ta faɗi wa Saleem da shi ne ya zubawa Safna dorina a baya,
lokacin su Marwan suka ƙaraso wurin jin maganar da tayi da ƙarfi, "Hajiya me sheɗaniyar yarinyar nan tayi miki?" Marwan yayi mata tambayar, sai da ta nuna Safna sannan tace "shegiyar yarinyar nan ni take nunawa iya ka ta yau ɗin nan, saboda wuyar ta ya isa yanka, gata ta zama budurwa ba mai iya taɓa ta yanzu".
Amsan bulalan Marwan yayi ya fara zuba mata a jiki, sai a lokacin ta buɗe idon da ta rintse haɗi da durƙusawa ƙasa tana basu haƙuri, dan ita da kanta bata san abinda tayi ba, sai darawa Ruki take tana mai jin annashuwa a ranta, wanda takeji duk san da akayiwa Safna mugunta, saboda itafa ba ƙaramin tsana tawa yarinyar ba, dalili kuwa shine Hajiya tun lokacin da suke ƙanana ta sanya musu tsana mai ƙarfi tsakanin su da Ammu da kuma 'yarta, kai harma da Mai Daraja kafin ya kwanta dama.
Kuka take sosai tana roƙon Marwan yayi haƙuri amma yaƙi, tun tana durƙushe har ta kwanta a ƙasa, miƙawa Saleem yayi shima ya dasa nasa salon muguntan, hawaye keta zarya kumatun Ammu ba ƙaƙƙauta wa, da ƙyar ta sauka daga kan keken ta tana nufan inda ake jibgar mata 'ya, kuka Ammu take sosai amma ko kaɗan bakin ta baya buɗuwa bare sauti ya fito, "bari ni inwuce ciki, ku tabbatar kun lahanta min ita kan kubar ta, sannan ita wannan nakashashshiyar ita ma in ta ƙaraso kusa da ita ku haɗa da ita, me za'ayi da dangin Mayu"? Hajiya ta faɗi tana wucewa.
Dukan ta sukeyi kota ina ba ƙaƙƙautawa, Ruki ma tana mata na ta hanyar to kari da ƙafa, tun tana roƙon su har bakin ta ya mutu, gurin da shekaran jiya ta bugu ne ya fara fitar da jini sakamakon bulalan daya taɓa wurin, duk da cewa 'yan aikin suna kallon abunda ke wakana amma babu wanda yayi jarumtar zuwa wajen, domin kowanne tsoro yake kar yayo abinda zai sa a kore shi, daga nesa suke aika mata da kallon tausayawa.
Ammu tayi nasarar zuwa kusa da Safna, amma babu tausayi babu tsoron Allah Saleem ya zuba wa Ammu bulalan kamar yadda Hajiya ta basu umarni, wani irin azababbiyar azaba ne ya ziyarci Ammu to dama ga yadda jikin na ta yake, cikin tashin hankali Safna ta zaro ido ganin abinda akayiwa mahaifiyar ta, saidai bata da kuzarin miƙewa, domin jiri-jiri ne ma ke ɗiban ta yanzu.
Yana ƙoƙarin zubawa Ammu na biyu, Yazeed yayi kukan kura ya hankaɗa shi gefe, ya amshe bulalan ya fara zuba mishi, har da Ruki, nan suka fara ƙara, shigowan sa kenan yanzu, dan motar sa ma a waje yayi parking ɗin ta, saboda dawowar gaggawa ne yayi dan ɗaukar wani abun sa, sai kuma ya tadda faruwar hakan.
ƙwace bulalan Marwan yayi, Saleem da Ruki suka yi gefe riƙe da inda ke musu zugi, Marwan yace "kai Yazeed miye haka?" juyawa yayi rai ɓace yace "tambaya na kake ko kuwa ni zan tambaye ka? baku da hankali ne zaku rufe ƙaramar yarinya haka da duka? saboda rashin imani harda wacce take matsayin uwa a gare ku?" Ya faɗi har jikin sa na rawa sabida ɓacin rai.
"Sai dai mahaifiyar ka ba dai tamu ba wallahi kuma ma kasan abinda tayi ne?" Mauji ya kaiwa bakin Ruki tana ƙarasar da zancen, "kai Yazeed enough, ya isa haka" "bai isaba, look your self, kaida yakamata ka hanasu amma harda kai a ciki, baka chanchanci zama babba ba sai dai babban Kobo".
"Ni kake gayawa wannan maganar Yazeed?" "Of course kai, akwai abinda za kayi ne?" Cike da ɓacin rai Marwan yayi kan Yazeed dan yin kokuwa da shi, saboda ya kaisa maƙura da maganar da ya faɗa masa, ƙarar motan Dady ne yasa shi fasawa.
Shi kuwa Yazeed kallon sa ya maida inda Safna take kwance ga Ammu kanta tana kuka da alama ma dai suma tayi, da sauri yayi wurin ta yana jijjiga ta, sai dai jikin ta ya saki, cikin tashin hankali ya sunkuce ta ya nufi waje inda motar shi take, Dady da direba ya buɗe masa ƙofar mota ya fito ya bi Yazeed da kallon tuhuma.
Kafin ya kai ga zuwa gate Baba Hambali ya buɗe masa ƙofar gidan, haɗi da fita buɗe masa na mota, baiyi wata-wata ba ya sa ta cikin motar ya ja ta da mugun gudu ya nufi Hospital da ita.
Tambayar abunda ya faru Dady yayi yana kallon ko wan nen su da fiskar sa tanuna rashin gaskiya a ciki, suma dai sun ɗan tsorata kaɗan ganin sumar da Safna tayi, babu wanda ya amsa masa saima wucewa da su kayi, ba wani abun damuwa bane dan basu tanka masa tambayar ba, saboda akan tarbiyyan hakan suka tashi, wanda shima da kansa ya bada gudummawar sa cikin koyar dasu wannan tarbiyyar.
Kawai sa masu aiki shigar da Ammu ciki yayi da kuma kulawa da ita sannan ya shiga ciki, Ammu ta shiga ɗimuwa sosai da tsoron kardai wani abu ya samu gudan jinin ta, addu'a kawai take ta jerowa a zuciyar ta.
Yana shiga harabar babban Hospital ɗin, ya ɗauke ta ya nufi shiga cikin asibitin da Safna a hannu, da sauri likitoci suka karɓe ta, suka shiga da ita ɗakin bada kulawa, "jiramu a waje" cewar Doctorn da turanci, dan ba Bahaushe bane, "a'a badamuwa ayi komai a gaba na" Cewar Yazeed shima da English.
Allura suka fara yi mata wanda zai taimaka mata gurin rage zogi sannan suka yi mata duk abinda ya dace, yadda ake ƙara wanke mata goshin ta da yake ta zubar jini kamar yau abin ya same ta ne yasa shi rintse ido, ita akewa amma shi yake ji a jiki, shi da kansa baisan dalilin hakan ba.
#Hmmm a wani number kuka sa muguntar Hajiya da 'ya'yan ta?
Ya Hajiya zata ji yayin da labari ya iske ta na Yazeed ya kai Safna Hospital? Bayan duk tsoron da takeyi na karya faɗa kogin soyayyar Safna?
Amma fa nidai Yazeed ya biyani😊
kuma Yazeed ya birgeku?.
______________________________________________________________________________________________
Part 3️⃣3️⃣▶️3️⃣4️⃣
A haka har aka gama mata, bai matsa daga wurin ba har lokacin da ta farka 05:55. "How are you feeling now? da sauƙi? ko akoi wani wurin da ke miki ciwo? kina da buƙatar wani abu?" A jere yayi mata tambayar.
da kallon tsoro kawai take binsa ba tare da tace masa uffan ba, sai sauke ajiyar zuciya take, ya fiskanta hakan shiyasa ya ƙara cema ta, "karkiji tsoro kontar da hankalin ki" ya faɗi yana kama hannun ta tare da cigaba da yi mata kallon tausayawa, ganin yadda fiskar ta yake a kunkumbure.
Saurin ƙwace hannu tayi tana faɗin. "ina Ammu wani abun ya same ta?" "Babu abin da yasame ta, tana lafiya kece abin kulawa yanzu" ya faɗi cikin sassanyar murya wanda bata san yana da shi ba, ganin kallon da yake mata yasa ta sauke kanta ƙasa, nufin kunya da kuma fargaba.
"Please Yaya Yazeed inason komawa Gida" "babu inda zakije sai kinyi one week before Doctor zai sallame ki" saurin ɗagowa tayi tana duban sa jin abinda yace, Lokacin doctor ya shigo ya basu 'yar takarda da kuma wasu magun-guna haɗi da yi musu baya ni akan maganin.
Da ƙyar take taka ƙafafuwan ta, sabida gaba ɗaya jikin ya kumbura kamar wacche tasha yis, kota ina sai yi mata tsami yake, lura da hakan yasa shi ɗaukar ta sama cak, ganin yadda ya haɗe fiska ne yasa ta gimtse bakin ta da take shirin magana.
shigar da ita gaban motar yayi shima yakoma gurin zaman diriver yaja su zuwa Gida, ko atishawa bai shiga tsakanin su ba har isowar su gidan, Baba Hambali ne ya buɗe musu ƙofa jin hon ɗin da yayi, ya tsaida motan ya fito.
a ƙoƙarin ta na buɗe ƙofar dan itama ta fito ne ya katse ta da buɗewa, kallo kawai ta bisa da shi kan ta zuro ƙafan ta ƙasa nan ma ya ɗaga ta, jin abun take wani banbaraƙwai duk da so tayi ya barta ta ƙarisa ciki da kanta kodan gudun idon wasu, amma yadda ya haɗe fiskar sa tamau ne yasa ta yin shiru har suka nufi hanyar falon, duk da a tsorace take kuwa.
Hajiya ce zaune a falo ta kasa ta tsare, ta cika ta ba tse, tana jiran dawowar Yazeed ta sauke masa buhun masifa, tun da shi yace baya gane hannun ka mai sanda.
Gaban ta ne ya bada rassss Miƙewa tayi haɗi da fiddo Ido da kuma sakin baki ga la la, ganin shigowar Yazeed ɗauke da Safna a hannu kamar wanda ya riƙo jaririya, "kai Yazeed!" Hajiya ta kira shi da ƙarfi ganin yana shirin wucewa kamar bai san da zaman ta a falon ba.
Dakatawa yayi tare da juyowa inda take, Safna kuwa tsoro ta shiga sosai dama hakan ne babban abinda take gudu, saboda tasan Hajiya ɓaɓɓalla ta za tayi dama ya aka ƙare bare taga hakan ai sai tayi zaton wani abun daban, "I'm coming Hajiya" shine kawai yace mata yana nufan sashin su Safnan.
Hajiya kuwa bushewa tayi da mamaki, me hakan ke nufi? Shin Yazeed ya shiga komar yarinyar nan ne ko kuwa? Nashiga uku!, shine abinda ta faɗi a ranta haɗi da komawa kan Kujera tana faɗin "inaa! Hakan bazai taɓa faruwa ba cab a ah".
Ganin cewa fa Yazeed shigar da ita ɗakin Ammu zai yi, domin kuwa ɗakin ya dosa yasa ta jin wani abu, taya zai shiga da ita ɗaki ɗauke da ita a hannu kuma Ammu ta gani, hakan yasa ta sakin marayan kuka tana faɗin "dan Allah Yaya Yazeed ka sauke ni, zan taka da ƙafana, dan Allah".
Sauke ta yayi ganin kukan da ta saki domin sam baiji daɗin saukar kukan a zuciyar sa ba, a hankali harta shige ɗakin yayin da shi kuma ya juya dan ɗauko magungunan da aka bata.
Gurin Ammu dake kwance kan Gado tayi a tinanin ta ma bacci Ammun ta ke, sai dai bata sani ba cewa Ammu baza ta iya rintsawa ba batare da taga lafiyar ta ba, tana isa kusa da Ammu, a hankali ta sanya hannun ta kan na mahaifiyar ta, ta yi mamaki jin Ammu ta damƙe mata hannu, kenan ba baccin take ba.
Alamar son ta shi tayiwa Safna, hakan yasa ta taimaka mata gurin tasar da ita, ta zaunar da ita, cike da damuwa take bin gaba ɗaya jikin 'yarta da kallo, ganin damuwa a fiskar Ammu yasa Safna cewa, "na ji sauƙi ammin alluran rage zugi, shiyasa yanzu banajin zafi ko kaɗan, dan haka Ammu na karki damu kan ki kinji".
Ammu bata daina kallon ta ba, sai ma wasu sabbin hawaye dake fitowa daga cikin fararen idon ta, domin kuwa duk da cewa jinyar shekara da shekaru ta keyi bai hana haske da kuma kyawun ta ya disashe ba, "Ammu kuka?" Ta furta cikin shiga matsanancin damuwa, domin kuwa abu mafi girma da yafi sata a damuwa shine taga wani abu ya sami mahaifiyar ta.
"Ammu me yasa ki kuka? Kodai jikin ki na miki ciwo ne? Ɗazu Yaya Saleem ya miki duka ko? Kodai shine yasa miki jiki ciwo?" Tayi mata tambayoyin cike da damuwa tana share mata hawaye da hannu, da ido Ammu tace mata, "a ah 'yata ba babu abinda yasame ni, kece kike fama da raɗaɗin wahalar da kika sha sannu kinji?".
Sauke numfashi mai ɗumi Safna tayi sannan tace "Ammu na ba fa wani abunda nake ji yanzu, dan Allah karki zubar da hawayen ki mai tsada a gare ni kinji?".
Tsayawa kawai yayi yana kallon soyayyar Uwa da 'Ya gwanin ban sha'awa, bai san lokacin da murmushi ya kufce masa ba, hatta fararen haƙorar sa sai da suka bayyana, gyaran murya yayi bayan ya gama kallon su sannan ya shigo, Ijje maganin yayi ya fice batare da ce musu komai ba, da ido suka raka shi.
"Ba shakka! yanzu Yazeed ni zan maka magana amma kaƙi kula ni? Ina ganinka ka shigo da ita a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 56