take ya gushe ba ta ce, "sosai ma kam, tunda har ya amince da ɗan na sa ya zauna a gidan mu ai kamar wata alama ce ta nuna zai iya hakan nan gaba" juyawa gurin sauran yayi yana faɗin, "abun da nake so daku ku kuma, yaron nan idan yazo ku girmama shi, koda ace kun girme sa, tunda ni ban taɓa ganin sa ba, bare nasan shekarun sa, don haka ku bashi girma, saboda wannan dama ce a gare ni da kuma ku baki ɗaya, kunga idan na rasa wannan damar tofa mun tafka babban asar".
Gaba ɗaya yaran haɗe fiska su kayi da jin maganar mahaifin su, Saleem ya ce, "Dady ya kake magana kamar kai ɗin talaka ne? Ko da ace ka rasa wannan damar taya zai zama abun damuwa? Kar ka manta kana da dukiya mara adadi fah" tsaki Dady ya ja yana kallon Saleem cike da takaici ya ce, "rufe mana baki sha-sha-sha kawai, kai maganar ka ina da kuɗi-kuɗi, ba ce maka nayi ka daina irin maganar nan ba? to bari kaji, ka ga wannan mutumin da nake magana a kai? Da za'a tara mutane masu kuɗi iri na, guda huɗu, to baza su fisa kuɗi ba".
Zaro ido gaba ɗayan su sukayi, gaskiya wannan mutumin ba na wasa bane, "cab ɗi! Wannan kam to ai ko ni sai inwa ɗan na sa biyayya! kace haka suke da ma ƙudan kuɗi?" Cewar Hajiya jin batun zun-zurutun kuɗi, amsa Alhaji ya bata da cewa, "fiye da yadda kike tunani, kuma wannan yaron shine kaɗai jinin sa".
Marwan da ke son magana ya dakata saboda yaji maganar da girma, duk da shima yana ganin taya za'a kawo mutum gidan su ya girmama shi? Miƙewa Alhaji yayi yana kallon Ruki ya ce, "auta na kiramin 'yar-uwar ki, idan ta gama shiryawa mu tafi" "Dady ni ba 'yar-uwa ta ba ce" ta faɗi harda turo baki, "ke, kin manta abin da ya faru jiya ko?" Cewar Saleem, Marwan ma ya ce, "rabu da ita, saboda babu abin da sukayi mata shiyasa take faɗin hakan".
"Dady bari na kira maka ita" Saleem ya faɗi hakan yana wucewa kiran Amna. Barin wurin Dady yayi Marwan ma haka, taɓe fuska Ruki tayi tana maida idon ta kan Hajiya ta fara cewa, "Hajiya wani irin dabara kika samo mana akan shegiyar yarinyar nan? Saboda bai kamata mu barta haka b..." kan ta ƙarisa Hajiya ta miƙe riƙe da wuya, cikin ɓacin rai ta fara magana.
"Zaki rufamin baki ko kuma na hamɓare miki shi? Gaskiyar Marwan da ace ta lasa miki wani abu da baza kiyi zancen ba, kin san yadda naji lokacin da ta shaƙe min wuya ne? Ba sai yadda naji kawai na sanar muku ba? Ana cewa in mutum ya suma taurari uku zai gani, ni kuwa biyar reras n'a gani à cikin maganuwan nan nawa" ta faɗi tana nunawa Ruki idanun ta tana ci gaba da cewa, "sai da naji kamar ƙafa ta ɗaya à duniya ɗaya a lahira, to wallahi idan na kuma jin wannan banzar maganar to sai na maida miki fiska kamar na Saleem da yake yanzu a saɓe" tana ƙarasa maganar ta wuce ta bar Ruki tsaye ƙerere kamar ta haɗiyi taɓarya.
Sauke numfashi tayi tana tunani, duk yadda Hajiya ke tsanar Safna amma yau tsoron ta take yi?. Hajiya da shigar ɗakin ta kenan kiran ƙawar ta ya shigo waya, ɗagawa tayi ba tare da ta faɗi ƙala ba, "hello ko ba kyaji na ne ƙawata?" cikin muryar ta da ke haryanzu bai washe ba cikin haushi ta ce, "niko nake jin ki har da sauraro m'a" Ladingo ta amshe da faɗin, "au ho, koda na ji, saboda yanzu nayi kiran waya amma network ɗin dai dai yake. Dama cewa nayi in kira inji yadda kika ƙare da matsalar ki".
"So kike kiga yadda na ƙare da matsalar tawa?" Cewar Hajiya har ta fara hasala, Ladingo kuwa duk da ta ji muryar aminiyar ta ba a daidai yake ba amma ta amsa da cewa, "eh" "to ki kirani bidiyo ki gani" ba tare da tunanin komai ba Ladingo ta katse tana shiga WhatsApp, kiran numbern Hajiya ta vidéo call tayi.
Hajiya kuwa ɗagawa tayi tana yin gaba da hannun ta, saboda ta ba Ladingo damar kallon rawanin da akaiwa wuyan ta, "subhanallahi! Hajiya me nake gani haka?" "Me za ki gani in ban da abin da kikayi min, Allah ya wadaran wannan shawar da kika bani!!" cewar Hajiya cike da haushi, domin da bata bi shawarar ba da wani labarin ake ba wannan ba.
Fuska a damuwa Ladingo ta ce, "me kike cewa ne Zainab? Na san ba ma haka dake" "Taya baza muyi haka da ken ba? Ina ce ke kika ban shawara akan in tsoratar da Safna? To kin ga sakamakon da hakan ya min, ashe tura ta Nijer ɗin da nayi ta gamu da iskokai, ina matsalar Marwan da Saleem da na fara sanar dake? To ashe dai aljanun ne suka aikata, bayan na yi mata kalaman da kika ƙisa min, ina isa ɗaki yarinyar nan ta ritsani, in taƙaice miki shaƙe min wuya tayi, ta kuma ɗaga ni sama, wallahi har sai da naji kamar leƙawa lahira nayi na dawo, saboda àzaban da naji a wannan shaƙa, da sai dai ki riski mummunar labari".
"Haka akayi?" Faɗin Ladingo, cikin tunzura Hajiya ta ce, "tambaya kike?" "A ah wai naga maganar ce abin dubawa" tsaki Hajiya tayi tana sauke wayar daga kunnen ta.
AMNA. Bayan ta isa ɗaki ɗazu ta sanarwa Ammu maganar Alhaji duk da babu abinda Ammun zata ce, shiga toilet tayi, tayi wanka, bayan tafito ta tsaya gaban walldrop ɗin da ta buɗe, tana kallon kayan da ke ciki ta rasa wanda zata sa, sa hannun ta ciki tayi tana duddubawa har ta janyo wata haɗaɗɗiyar dogon riga atamfa, pink, white and light purple colours, kalar sa ba ƙaramin burge ta yayi ba, juyawa gurin Ammu tayi tana nuna mata rigar haɗi da fadin, "Ammu wannan zai min kyau?".
Murmushi Ammu tayi, hakan yasa ta fahimtar ta ce eh, sanyawa tayi ta kuma gyara kayan basajar ta sannan ta ce, "Ammu ina kayan kolliyar Safna ne? Tun da nazo ban gan su ba" ƙoƙarin ɗaga hannun ta ɗaya tayi tana yi mata nuni da wani wuri, zuwa wurin tayi ta buɗe ta dauka, duk da fauda da jan baki da gazar baƙi ne kawai a wurin, zama gaban mirro tayi tana shafawa, da faɗin, "ita Safna ko kwalliya ba tayi da alama" cikin ran ta.
Tana à haka Saleem ya turo ɗakin ya shigo, hakan ya ɓata mata rai rashin sallamar da baiyi ba, juyawa tayi tana kallon sa, hakan yasa shi sauke kai ƙasa ya furta, "Dady na kiran ki" "ina zuwa!" Juyawa yayi zai wuce sai kuma yaji maganar ta, "idan zaka sake zuwa ka rinƙa sallama, ka kuma nemi izini, saboda ba ɗakin ka bane" yadda tayi masa maganar ya ɓata masa rai amma ya danne ya fice waje.
"Kamar ba musulmai ba, na lura dukkan su haka suke yi ko gaishe da Ammu baiyi ba, kamar bai san da zaman ta a ɗakin ba" ta faɗi tana sakin tsaki, Ammu da ke can gefe ta saki murmushi jin maganar da Amna tayi, ɗaukar gele da kuma takalmi tayi ta sa bayan ta kammala kolliyar, tayi kyau matuƙa gaya, fiskar ta ya ƙara fitar da haske baza ka tantance ba idan aka haɗa ta da balarabiya, kafin ta fita ƙaramar wayar ta tayi ƙara, zuwa da sauri tayi ta ɗauka da sallama, wannan karon bai riga ta magana ba, sai da ta gaishe sa ya amsa a dake ka na ya ce.
"Sannu da aiki" shiru tayi Tana tunanin dalilin da yasa ya faɗi hakan, "à tunanin ki bansan abun da ki keyi a gidan bane? To ki sani na san duk abin da kike aikatawa" sai da ta ɗan fiddo da manyan idon ta jin maganar sa, kenan ya san duk abinda nake yi? Tayaya? Hakan na nufin ina laifi kenan? Duk take faɗi a ran ta, n'a ta tsinkayi maganar sa yana ci gaba da cewa, "kar ki damu domin ba ƙaramin ƙoƙari kika yi ba, saboda haka na jinjina miki, dama abin da nake buƙata kenan" sauke dadɗa-ɗan numfashi tayi, jin ba tayi laifi ba, "yanzu ne zaki fara abin da ya kawo ki gidan, mayar da hankalin ki sosai za kiyi a Mai Daraja cotton company".
"Kenan dama mining ɗin M.D kenan? Kuma kamfanin auduga ne?" Amsa ya bata da cewa, "da me kika ɗauki mining ɗin sa? Companyn auduga ne, shine babba daga cikin sauran, kuma shi ne mafi riba akan sauran, sai dai baya samun kula da ya dace, dan haka idan kika je ki tabbatar kin mayar da hankali a kowani ɓangare, kafin ki tambayi familyn ki suna lafiya, idan kika tafiyar da komai daidai zaki gan su". Yana kai ƙarshe ya katse wayar.
"Dama aikin sa kenan" ta furta, sai kuma tayi saurin sallamar Ammu da cewa inta fita zata samu 'yar aikin da za ta kula da ita kafin ta dawo, Ammu tayi mamakin maganar ta, wani 'yar aiki hajiya zata bari ta zo kusa da ita?, ta faɗi cikin ran ta ba tare da ta san wainar da Amna ta gama toya wa ba, da sauri ta fita tsakar gidan don ta san ba ƙaramin ɗaukar lokaci tayi ba.
Duk da ta fita ne ba tare da tabbacin a ina Dady yake ba, amma sai ta gan shi yana ƙoƙarin zuwa wata haɗaɗɗiyar mota blue colour, da sauri ta nufi inda yake, "I'm so sorry Dady" ta faɗi bayan ta isa, juyowa da murmushi yayi ya furta, "baki makara ba 'yata" Itama murmushi tayi ta ɗora da faɗin, "Dady dama inason in sa masu aiki kula da Ammu kafin na dawo" "ok bismillah" ya bata amsa da lama da hannu.
Nufan gurin ɗakunan su tayi tana tinanin wa zata sa wannan aiki? Sai Jummala ta faɗo mata rai, domin matar tana da kirki, hakan yasa da taje wurin ta fara kiran sunan ta, fitowa Jummala tayi domin yanzu ta daina mamakin kiran ta da Safna take yi mata, "na'am Safna'u" "yauwa dan Allah so nake na baki aikin kula da Ammu, ba yau kaɗai ba, gobe zan fara zuwa aiki, dan haka zaki rinƙa zuwa ki kula da ita kafin na dawo".
Cikin ɗan tsoro Jummala ta ce, "amma Safna'u Hajiya baza ta barni ba" "Wace Hajiya kike magana? Kinga, abinda na faɗa miki za kiyi, idan Hajiya ko ɗaya daga cikin su ya hanaki kula da Ammu to ki sanar da ni" Tana gama faɗi ta juya, sauke numfashin da ta riƙe tayi, dole tayi abinda Safna ta ce mata, tun da bata san me ta taka ba ta faɗa mata haka, don Safnan yanzu ba ta son raini ko kaɗan.
Shiga motar Dady tayi ya ja su, wani tunani ne ya faɗo mata rai, hakan yasa ta gyara zama ta juyo ta dube shi ta ce, "Dady ina son roƙan wata alfarma" "ina jinki 'yata faɗi duk abinda kike so" "dama ina da buƙatar ƙarin kayan sawa, sannan ba nida waya, ina ganin kamar ya kamata na samu wayar riƙewa zai min amfani" ta faɗi domin ya kamata ta samo ko da dogayen riguna ne na zuwa office, saboda baza ta iya da riga da skirt da kuma da zani ba, inba haka ba wata rana fa ɗi zata yi in tana tafiya da su.
"Wannan ba abun damuwa bane 'yata, nima ya kamata ace nayi tunanin haka tun tuni, saboda na daɗe ban baki kuɗi ba, bayan mun kammala abinda ya kai mu, sai in haɗa ki da driver ya kaiki shopping da kuma gurin sayen waya" "thank you Dady" "don't worry that's my responsibility".
#Muje dai zuwa😊
____________________________________________________________________________________________
Part 8️⃣3️⃣▶️8️⃣4️⃣
Tunda Dady ya doso wannan wuri Amna ta daina ƙwaƙƙwaran motsi, kallo wanda ake kira kallo take wa wannan wurin da take ganin Dady na dosa da su, ƙofa ce ga tsawo ga kuma faɗi, sannan ga security shida, uku ta ɓangaren hagu uku ta dama, suna sanye da kaya kamar na 'yan sanda amma ba shi bane, su nasu kayan kalar brown ne saɓanin baƙi, tsaye suke ƙam yadda kasan à barikin sojoji suke.
Motar Dady na isowa wurin suka sara masa, biyu daga cikin su ne suka je dan buɗe masa ƙofar, sauke glass ɗin motar yayi yana duban sauran da suka taho suna yi masa gaisuwan girmamawa, ɗaga musu hannu kawai yayi yana ƙoƙarin danna hancin motar ciki, bayan biyun sun fara buɗe ƙofar, yana shiga ciki ta kuma ƙara zare idon ta, tana kallon girman wannan kamfanin, kamar wani unguwa ne sukutum a ciki, a haka ma acikin mota take bata gmna hango wasu gefen ba.
Can wani gefe ya nufa yayi parking ɗin motar, tun kan su ƙarasa fita daga motar, mutane uku da kuma wasu security biyar suka taho inda suke suna yi wa Alhaji gaisuwan shugaba, nan ma ɗaga musu hannu yayi kawai, sai kallon Amna suke suna kallon balarabiyar budurwa da ke tare da Dady. Ita kuwa ganin ikon Allah kawai ta ke, yadda ta ga Dady yanzu wani taƙama yake yi, itama gaisuwan suka yi mata ta amsa musu da lafiya.
Ta fiya ya fara hakan yasa ta bin bayan sa, yayin da wa'yan nan ukun ma suka rufa musu baya, amma su security kam komawa bakin aikin su sukayi, ci gaba da ba idon ta abinci tayi sosai, domin irin wannan wurin ba wanda zakawa kanka rowan gani bane, ko ƙasar da take takawa à ciki ya isa tasan ba ƙaramin kamfani bane, tana biye da Dady harya nufi wani ɓangare.
__bazan iya zanyyano muku wannan kamfani sosai ba, saboda ni kaina sai da na ruɗe, amma dai na bar muku ku kai idanuwan ku duniyar mahanga don hango kyawun M.D cotton company__
Lifta suka nufa haɗi da shiga, sauran kuwa wani liftan suka shige, hatta cikin sa Amna ƙarewa kallo tayi, ta zama 'yar ƙauye ta ɗan lokaci, sama sosai sukayi, har suka kai ga inda abun zai tsaya, yana buɗewa ya fice ta cigaba da bin bayan sa tana kuma kallon wurare, duk mutanen da suka haɗu da shi, sai sun gaishe sa cikin girmamawa amma babu abin da yake musu sai ɗagun hannu, ita ko Amna sai murmushi kawai take sakar musu.
Wani babban mutum ne ya taho gun Alhaji da sauri yana faɗin, "your welcome sir!" Shima cikin girmamawa, shine kaɗai Amna taga Dady ya amsawa da thank you, mutumin ne ya koma gaba, har suka isa wani haɗaɗɗen ƙofa, buɗe ƙofar yayi haɗi da tsayawa à gefe har sai da Alhaji da Amna suka shiga ka na ya shiga shima.
Wayyo haɗuwar office ɗin sai dai rufe baki, juyawa Dady yayi yana kallon Amna ya ce, "ga kujerar ki" saurin kai duban ta ga kujera da yake yasha bamban da irin ko wani kujerar office da ta sani, ta kuma dawo da kallon ta kan dady, fiskar ta alamar tambaya, zatayi magana ya riga ta da cewa, "je ki zauna" yana faɗin haka ta fara taku har izuwa gun kujerar, tana zama ta ji kamar ta zauna akan auduga saboda laushi.
Zuwa Dady yayi ya zauna a kujerar dake gaba da ƙayataccen table ɗin ya zauna, yana maida duban sa ga mutumin nan ya ce, "ina fatan duk abinda na sanar an gabatar da shi?" Da sauri mutumin ya amsa da, "ƙwarai kuwa mai gida, domin mutane sun fara hallara sosai" lokacin mutane ukun ɗazu suka shigo, "su Marwan sun zo?" Dady yayi tambayar, amsa masa da "eh mai gida, sai dai kamar basu da lafiya, sabo..." kafin ya ƙaraDadyya ce "its ok, nan da twenty minutes ya rage kowa ya hallara, kuje kuyi sauran shirye shiryen" "toh mai gida" gaba ɗayan su suka amsa suna wucewa.
Amna da tabi mutanen da kallo har suka ɓacewa ganin ta ta ji muryar Dady na cewa, "yata wannan shine Office ɗin ki a yanzu, minti ashirin kaɗai ya rage kowa da ke cikin wannan kamfanin ya shaida ki matsayin jagorar kamfanin, ta shi in nuna miki Office ɗinki da kyau ki gani" ba bakin magana tashi kawai tayi kamar yadda ya ce.
Zuwa wata ƙofa sukayi yana sa hannu ya buɗe ta, ciki da falo ne da kuma bayan gida à ciki, komai na cikin falon white and light blue ne, tsarin ɗakin yadda kasan à ƙasar waje, wani sabon kallo, "wannan ɗakin hutu ne, a duk lokacin da kike da buƙatar sara-rawa to sai kizo" ya faɗi yana kuma yin gaba zuwa uwaɗɗaka, shi kuma only white ne komai na ciki, aljannar duniya Amna ta furta cikin ranta tana ganin wurin da bata taɓa kwatanta ganin sa ba koda kuwa a mafarki ne.
"Harda barci in kina buƙata 'yata, dan komai da kika gani anan mallakin ki ne a yanzu" ya faɗi yana komawa, ita kuwa tafiya ta farayi à hankali tana nufan wani ƙofa da ta gani duk da tafi zaton toilet ne, aikuwa tunanin ta bai faɗi a banza ba, toilet ne amma ba muna toilet ba fa, saboda ba ƙaramin ƙera shi akayi ba, to ai idan aka ce maka ɗakin kwanan ka nema sai ka gode🙃.
Barin wurin tayi harda zama a kan gado, wani laushin da taji jikin katifan ne yasata jin ya ma fi na kujerar ɗazu, wannan kai ai ta samu gurin zuwa, kiran ta da Dady ya soma yi ne yasa ta fitowa tana amsawa, wata computer ya ɗago yana nuna mata, yadda zatayi amfani da shi, "koda ace kin shigo wannan sashin dan hutawa, idan abu ya taso na ujila ana son yi miki magana amma kina wannan sashi, zai miki ƙara da kuma alama, idan kika ji haka, sai ki dannan wannan filin dan sanin dalilin da yasa aka ne meki, idan na fito wa ne sai ki fito, saboda babu wanda zai shigo ɗakin nan, bayan masu gyara, suma sai lokacin da kike so, shima a can Office ɗin akwai in munje zan nuna miiki".
Duk da cewa koya mata amfanin wannan na'urar da yayi ba kowa bane zai ɗauka farad-ɗaya amma ita babu abin da bata fahimta ba, wata ƙofa dake can gefe wanda labule ya rufe suka je, da mamaki take ganin wurin don batayi zaton akwai wani abu mai suna ƙofa ta wurin ba, sanya wa Dady ido kawai tayi ta ga ya fara dannan wasu numbobi da ke jikin ƙofar, kawai sai ga ƙofaya buɗe, binsan tayi tana fita sai taga wani sashe ne daban amma ba ɗaki ba.
"Wannan hanya ce da zata kai ki ƙofar da zaki iya fita ta baya, amma sai da babban dalili zaki bi ta" ɗaga kai tayi alamar ta gamsu da bayanin sa, maida ƙofar yadda take yayi, sannan ya sa Amna zaɓi wasu numbobi don canza mata yadda zata yi amfani da su gurin buɗe ƙofar, tun da à yanzu ƙarƙashin ta wurin yake. Daga nan suka koma office, nuna mata yadda zata yi amfani da na office ɗin ma yai, sannan ya ce, "muje sun riga da sun haɗu yanzu" ya faɗi bayan ya duba agogon da ke hannun sa, tare da ɗaukar wayoyin sa uku da ya ijje akan table.
Marwan da Saleem ba ƙaramin mamaki sukayi ba ganin yadda aka ƙawata wannan gurin, sannan ga mutane bila adadin sun zo kamar za'a naɗa sarauta, Saleem sanye da face mask gudun kada kumburin fiskar sa ya fito, za 'à iya raina shi, shi kuma Marwan ƙafar ta sa ta dawo dai dai, sai ɗan abinda ba'a rasa ba.
Cikin masu aiki kuwa kowa na kace nace akan wacche za'a kawo, mace kuma wai itace zata ja goranci wannan kamfani, koya zata kasan ce a zubin kamanni?, wasu wa'yan da suka ga Amna kuwa tuni sun sanar wa abokan su yadda take, duk da basu da tabbacin ita ɗin ce sabuwar shugaban ta su, yayin da su kuma wa'yan da aka shafa musu yadda take suke jira don tabbatar wa don an faɗa musu ƙaramar yarinya ce. su kuma wa'yan da basu gan ta ba suna jira kawai suga yadda abun zai kasance.
Marwan da Saleem basu gama fita daga wancan mamaki ba sai ga zuwan manyan mutane sanye da kayan lauyoyi kusan su goma, suma da kan su sauran mutanen sunyi mamakin haka, abinda bai taɓa kasan cewa a cikin wannan kamfani ba. Mutanen sun zone akan naɗa 'ya ga Mai daraja jagorantar kamfanin mahaifin ta, kuma haƙƙin ta, babban abinda ya kawo su shine su tabbatar da rubutaccen wasiyyar mahaifin ta wato Mai daraja.
Kowa ya zo a yanzu ya rage su Dady kawai ake jira, bin bayan Dady kawai take yi, ba tare da ta san inda zasu ba, gani tayi sun doso inda aka ƙawata, suna tafiya har suka sha kwana nan ta ga zun-zurutun mutane wanda zata iya tabbatar da da alama ba iyaka 'yan kamfanin bane, Amna mace ce mara tsoro hakan yasa duk yawan mutanen nan bai sa taji tsoron kasan cewa a gaban su ba.
Kallon su take sosai yadda suka nutsu suna kallon ta ita da Dady, nan ta ga Marwan da Saleem a gefe, suma sai wani ƙa fafa suke yi, tuni wasu a cikin mutanen suka fara 'yan surutai, kowa na ayyana kyau da wannan baiwar Allahn ke da shi, yarinya kamar à India, ko kuwa balarabiya?
Babu ɓata lokaci Dady ya fara gaisawa da wa'yan nan lauyoyi da kuma mutanen, yayin da lauyoyin suke farin ciki da Allah ya kawo su lokacin da zasu sauke haƙƙin da ya rataya a wuyan su shekara da shekaru, wani ne ya fara gabatar wa mutane sanadin haɗuwar su a wurin duk da suma sun san haka, tun daga nan Amna ta fara ayyanawa a ranta wannan ba ƙaramin abu bane, musamman maganar da ɗayan lauyan yayi wa Dady kasan cewar suna kusa, "alhamdulillahi, Alhaji muna taya ka murna da mu kan mu akan wannan rana, da Allah subhanahu wata ala yasa za mu sauke haƙƙin da yake a kan mu tsawon shekaru"
Da turan ci yayi maganar, tun da ya faɗi hakan take tunanin wani haƙƙi suke magana a kai ne? Sannan kuma mutumin ya juyo gare ta yana yi mata murna da zagayowar ranar haihuwar ta, ita kuwa godiya kaɗai tayi masa.
Babu wani ɓata lokaci Dady ya hau munbari yana gabatar da Amna a matsayin Safna, da kuma taya ta murnar cika shekaru ishirin da uku à duniya, sannan ya ɗora da tabbatar wa da mutane ita ce zata jagoranci M.D company, wato dai ta zama C.E.O na su.
Bayan ya kammala bayanin da zaiyi ya sauka daga munbarin, sai babban lawyer wanda ya fi sauran matsayi shima ya hau ya fara magana yana kallon Amna, "muna yi miki murna da samun wannan matsayi Safiyya Abubakar mai daraja, wanda dama ƙwarya ce aka dawo da ita gurbin ta, ba ma wannan kamfanin kaɗai ba, harda sauran kamfani huɗun duk à ƙarƙashin ja gorancin ki suke a halin yanzu, sai dai wakilan ki da suke a can, Allah ya taya riƙo, yasa ki kasan ce ƙarin ci gaban wannan kamfanin na har abada".
Ji sukayi kamar anbuga musu rodi cikin ƙirji, domin har gwara maganar Dadyn su akan na wannan lawyern, ƙila da Hajiya ta zo wurin nan da tabbas suma zata yi, saboda jin kalaman mutumin nan.
Da Ameen ko wa ya amsa, amma Amna kam abin har ya fara sa mata wani tunanin, mutumin nan ya sanar cewa, gaba ɗaya kamfanunuwan shi kuma Dady abinda yace daban, abun ya matuƙar ɗaure mata kai.
Ba ta izini akayi itama akan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 22 Chapter of 56