yasa na janyo ka ciki".
A jiyar zuciya ya sauke da jin batun ta yana ƙara cewa, "cab gaskiya my beb son kuɗin ki yayi over, nifa da kika min bayanin aikin na ɗauka wanda kika sani ne, kamar yadda aka saba, irin na mutumin da ya baki aiki akan ki ɓata wa Hajiyar aikin su suna, da dai sauran abubuwa da muka sha yi, ashe gaibu kika kama, to amma ya akayi kika samu abunda kika fesa masa mai ƙarfi haka, taya suka baki ba tare da kin ga waye ba?"
"Bayan mun rabu da guy ɗin ne, suka sanar da ni inda zan ɗauka" Cewar Zilla ya kuma cewa, "ok, amma ina ce kina da numbern su, ki kira mana su kiji ya batun kuɗin, in muka samu kuɗin nan ai mun warke" dariya Zilla tayi sannan tace "Shege my love maganar kuɗi ba wasa" "a kinga laifi na?" "To nidai ko na kira numbern baya shiga, sai in sun kira" "gwada kira yanzu" yace mata dan shi har ya fara kasafta kuɗin a ran sa, saboda yasan Beb ɗin sa Zilla n'a ji dashi sosai, yasan tare zasu amfana kuɗin.
Tana dialing kuwa ya fara ringing, da murmushi irin nasu na Bariki tace "duba ya shiga" "yauwa shiyasa nace ki gwada" Cewar Nass cike da murna dan ji yake kamar kuɗin ne suka zo, 50 millions ba wasa ba.
Saida wayar ta kusa tsinkewa aka ɗaga, kan tayi magana taji ance, "à sauka lafiya" cikin wata irin murya mai kauri, "a sauka lafiya kuma?" Sai dai kafin ta kai ga ƙarisawa, hasken wata babbar mota ya dalle su, zaro ido su kayi kamar idon zai fito waje, sabida mutuwar da idon su ya gane musu, na yowa kansu, sai dai kafin Nass ya nemo tinanin yadda zai kauda motar, babbar motar ta bi ta kansu, --sai dai muce Allah yaji ƙan rai.
Fannin masu Fararen kaya kuma, kutsawa cikin dajin suka fara yi, yadda kasan da rana suke tafiya, --ban samu damar ganin hanya da kuma shiga Dajin ba, sai anan gaba zaku ji--.
09:00am
Shocking ɗin wuta da ya ratsa duk wata kafa ta jikin sa ne yasa shi farkawa cikin tashin hankali mai ɗauke da à zaba, hannun sa ɗaure da sarƙa, haka ƙafafun sa, sai Igiyoyin wuta dake kewaye da jikin sa,, zazzare ido ya fara yi a cikin duhun wurin domin kuwa, babu alamar haske ko kaɗan, "waye a nan? Ka fito mana" shine abunda Baba yake ta nanatawa a bakin sa, an ɗau lokaci ba tare da yaji ko motsi ba, sai shocking ɗin da ake kunna mai lokaci lokaci, à zaba yake ji a gaba ɗaya ilahirin jikin sa, idon sa duk ya ƙan-ƙance saboda wahala, sai is kar wahala daya ke furzarwa a bakin sa.
Lokaci ɗaya ƙwan Fitila da ke daidai saman kan sa ya ɗau haske, ya bayyana a daidai inda yake, rintse ido yayi yayin da hasken ya haske masa Idanu, takun ta kalmi ya fara ji a hankali har izuwa inda yake, buɗe ido yayi a hankali, jin alamar mutumin na tsaye akan sa yasa shi ɗaga kansa dan ganin Mutumin?.
Mutumin sanye yake da riga da wando cort Fari, irin manyan mutanen nan ne, ga jiki ga tsawo, sai dai baiga Fiskar Mutumin ba sabida kan sa na saman ƙwan Fitilar, "who are you?" Baba yayi masa tambayar da ƙyar, dariya ya ƙyalƙyale da shi sannan yayi shiru kamar bashi yayi dariyar ba, ya fara magana cikin isa.
"Kana son sanin ni waye? Sanin waye ni ba shida amfani a gare ka, Ɗan Jarida mai ƙaramin Ƙoƙolwa, amma karka damu zan sanar da kai kafin ka wuce garin da ba'a dawowa" ya faɗa hakan haɗi da jawo kujerar da ke kusa ya zauna.
Duk da har yanzu hasken na hana shi damar ganin fiskar sosai, amma ya daure ya ɗaga idon sa kan mutumin, baƙi ne irin wuluk ɗin nan, wanda yake kyautata zaton cikin zuciyar sa ma haka take, sai ƙananun idanuwan sa Jawur "ko kasanni ne?" Mutumin ya faɗi haka ganin yadda Baba ke kallon sa.
Ya cigaba da cewa "Kai wawan Ɗan Jarida ne, ba tare da wata wahala ba sai ga ka a hannu na, na ɗauka kama ka zai zama kamar kama Kare ne, ashe ko Mage baka kai ba" ya ƙarashe da dariya.
"Bincike akan Ƙungiyar mu kamar wasa da rayuwar ka ne, kokuwa ince ka yi wasa da rayuwar ka, ko bataliyan Sojoji basu isa sukawo ƙarshen kungiyar mu ta POSPA ba bere kai Kiyashi, babu wanda ya isa ya ga Sirrin Shugaba ZABBA BA, koda kuwa mu ne, bere kai ƙaramin alhaki".
Ba ƙaramin nauyi Bakin sa yayi masa ba, da ƙyar ya iya buɗe bakin sa ya fara magana cikin rarraunar murya "kenan ba kai bane Shugaban? Ku wasu irin marasa imani ne? Kun lalata tarbiyyan al'umma da dama, kun kashe wasu da dama, kuma har yanzu kuna kai, saboda tsaban hatsarin ku kuke kashe duk wanda yayi yunƙurin fito da gaskiya a kan Ƙungiyar ku".
Shocking ɗin da ya ƙara ziyar tan Baba ne yasa shi yin shiru, jinkin sa yahau karɓar shocking ɗin sai rawa yake, hatta leɓen Bakin sa, ba tare da tsayar da matsa madannin Igiyoyin ba Baƙin mutumin yace "dogon lokaci babu wanda ya sake fito da maganar POSPA sai kai yanzu, tun daga lokacin da sunan ƙungiyar mu ya yawaita ta akan binciken ka Idon mu ke kan ka, mun ɗauka a iya maganar ƙwayar zaka tsaya, amma neman inda kungiyar take dan ka ruguza ta babban kuskure ne"
Tsaida maganar yayi da cire hannun sa kan madanin, a jiyar zuciyar wahala mai ƙarfi Baba ya sauke, lokacin da shocking ya sake shi, da ƙyar yake fitar da numfashi, har ƙolla ido sa yayi sabida a zaba, "duk abinda kuke yi Allah na kallon ku, yadda kuke cutar masa da Bayi, tabbas ku jira yi na ku sakamakon nan bada daɗe wa ba" Cewar Baba cikin murya ƙasa-ƙasa dake ɗauke da raɗaɗi.
Cigaba da magana Baƙin mutumin yayi, "gode min za kayi da na zaɓan maka mutuwa mai sauƙi, yau zaka baƙunci lahira idan kaje sai ka haɗu da wa'enda su kayi kuskure irin na ka" Yana ƙara she maganar ya miƙe haɗi da matsa madannin shocking ɗin, take ta cigaba da aikin ta a gaba ɗaya jikin Baba.
Dariyar mugun ta ya sake kwashewa da shi, ya nufi hanyar fita.
AMNA.
Dukkan su hankalin su ya tashi ganin cewa tun yamma ba Baba bai kira su ba, bayan tun da ya tafi hakan bai faru ba, sannan wayar sa ba ta shiga.
Suna zaune tsakar gida kamar kullum in za suci abincin safe ko Dare, sai dai yau ga abincin amma kowa ya kasa ci, Amna ce ta kira numbern Uncle Tukur a bokin Baba, take tambayar sa ko yaji labarin Baba, amma yace "a ah nima tun safe bamuyi magana da shiba, amma ku kwantar da hankalin ku, tayu wata 'yar matsala ce ta hana shi kira".
Amna tace "Uncle mun kira wayar sa baya shiga" "to ƙila ko wayar ba caji ne, amma mujira zuwa gobe" "toh Uncle nagode Allah ya kaimu" Amna ta faɗa masa tare da yi masa sallama.
"Allah yasa lafiya, dan ni hankali na yaƙi kwan tawa" Cewar Mamma cikin damuwa, Mubarak yace "insha Allah Mamma yanzu dai kuci abinci, Domin kunsan Baba baya son rashin cin abincin ku, idan yaji kunƙi ci zai yi fushi" Ummee tace "hakane to muci ko".
Amna kuwa shiru tayi kamar mai tinanin wani abu, sai da Mubarak ya taɓo ta tukunna ta farga da tinanin.
#To Ƴan-uwan arziƙi, kun dai ji yadda ta kasance da Zilla ashe saka ta akayi.
ta tafka zunubai da yawa, ta yi sanadiyyar sa mutane da yawa cikin matsala, duk akan kuɗi, sai gashi ajalin ta yazo cikin ƙanƙanin lokaci ba tare da ta tuba ba.
Ya Allah ka kare mu da aikata abun da ka hanemu da yinsa, wa'enda suke da hali irin na Zilla, Allah ka shirye su.
Ga Baba kuma cikin Uƙuba, shocking zai kashe sa ko kuwa?
Me yasa Mutanen nan sa kaya Fari?
Nasan kuna nan kuna wasu tambayoyi a zuciyar ku,
To ku cigaba da kasan cewa tare da Alƙalamin taku {Mrs Umar}
______________________________________________________________________________________________
Part 2️⃣7️⃣▶️2️⃣8️⃣
WASHE GARI.
Abu kamar wasa basu ji kiran Baba ba, Mamma ce tayi tinanin kiran wani daga cikin 'Ƴan-uwan Takori, sakamakon wayar da sukayi yasa su shiga cikin tashin hankali, domin kuwa an tabbatar musu da cewa Baba bai je ba, ko alamar sa ma basu gani ba.
Amna da kamar ta fara fahimtar wani abu ta je ɗakin Ummee, ta jira Ummee ta idar da Sallan Azahar, sannan taƙarisa dab da ita ta ce, "Ummee inason zuwa gidan Uncle Tukur". "Me za kije yi"? Ummee tayi mata tambayar daidai shigowar Mubarak.
Zama yayi a gefe shima, lokacin Amna ta ce, "Haka kawai Ummee please ki bar ni inje, ba daɗewa zan yi ba" ta ƙarashe faɗi haɗi da marai-raice fiska, dan so take taje sabida wani dalilin ta, "muje tare" cewar Mubarak, "a'ah ba inda za ka, kaida kake fama da jikin ka" Amna ta faɗa mai haka, Ya ƙara cewa, "naji sauƙi ai yanzu".
Maida kallon ta tayi gurin Ummee tana ƙara roƙon ta, "kije amma karki daɗe kamar yadda ki ka ce" "toh Ummee na gode sai na dawo" ta faɗi tana miƙewa tafita a falon, Mubarak yana mata maganar tare za su, amma ko juyowa bata yiba, saboda ba ta son rakiyar ta sa, 'yar ƙaramar shiri tayi, sannan ta sa glass ɗin ta, sai wayar ta a hannun ta, shiga Napep ɗinda ta tara tayi.
A ƙofar gidan sa aka sauke ta, da sallama ta shiga, gaishe da matan sa guda biyu tayi, suka sanar da ita bai dawo ba yana office, babu ɓata lokaci ta fita daga gidan ta kuma taran wani napep ɗin zuwa gurin aikin Tukur.
Wayar ta ce tayi ƙara, numbern abokin ta Wali ne akai, tana ɗagawa tace "Wali ya kake, sorry ina ɗan wani uzuri ne, inna gama i will call you back". "No Amna listen, wani abun tashin hankali zan sanar dake, nasan kinfi Mubarak dauriya shiya sa nake..." sai kuma yadakata, sabida abinda yake son sanar da ita shi kansa, ya shiga cikin tashin hankali da ganin sa, amma yana da tabbacin bata gani ba sabida Amna ba gwanar shiga internet bace.
"Wali faɗamin mana, meyafaru dan daga jin ƙarar kiran da ka mini na tsinci kai na cikin wani yanayi" cewar Amna haɗi da buɗe kunnuwan ta dan jiye mata abinda Wali keson faɗa, "Kin kalli labaran GT kuwa? kina ina ne?" Yayi mata tambayar, "a'ah, just tell me what you want to say"? "Bazan iya faɗa ba, saboda, amma dai ki shiga labaran GT dake wakana yanzu, sabida suna ta nanata lamarin, Gidan Radion nan na Kaduna".
Katse wayar tayi ba tare da ta yi masa wani magana ba, ta buɗe Data, dan ganin meke faruwa, tashin hankali ba'a sa maka rana, hoton Baba taci karo da shi an maƙala a kan labarun GT mai kawo rahoton yana cewa.
"Labarun GT kuke saurara, Assalamu alaikum Jama'a barkan ku da wannan lokaci, labarin mu na yau shine, yau an tsinci gawan wani bawan Allah anan garin Kaduna, ya mutu ne bayan yayi shaye-shayen sa yayi maƙil, a gefen titi aka tadda shi, a binciken hukumar, gawan ba na yau bane, a ƙalla zai yi kwana biyu, hakan yasa aka bada damar yi masa jana'iza ba tare da nemo iyalan sa ba".
Saurin fita daga wurin tayi ba tare da ta ƙarashe jin maganar ba, ta rintse Idanuwan ta da ƙarfin gaske, gaba ɗaya jikin ta ya ɗau kyarma, buɗe idanun tayi har sun fara canza kala, ambaton sunan Allah ta farayi cikin tashin hankali, ganin abinda ke faruwa yasa mai napep ɗin cewa, "Hajiya lafiya dai?" Baki na rawa tai masa magana da ya maida ta Gida, tare da sanar dashi sunan unguwar.
Tinanin zasu iya sake labarin nan a tashan labaran da Ummee take gani ako da yaushe tayi, hannun ta na rawa ta duba numbern Mubarak, yana ɗagawa cikin ɗimuwa ta ce, "Mubarak ina Ummee?" "Mamma na ɗakin ta, Ummee kuma i think taje kallon labaran duniyar da take gani da rana" ƙara shiga tashin hankali tayi ta ƙara cewa "yi maza kaje Kasan yadda zaka hana Ummee kallon labaran nan".
"Sabida me? lafiya kike kuwa? Ya naji voice ɗin ki haka?" "Stop asking, just do what I say" Cike da rashin fahimta yace, "ok" tare da nufan falon Ummee, sai dai mai afkuwa ya afku, domin kuwa daidai lokacin da aka kawo fiskar Baba ya shigo, yayin da mai kawo rahoto yake zubo maganganu.
Zaro ido waje Mubarak yayi yana faɗin, "a'ah, no, noooo" Ummee kuwa numfashin ta ne ke niyyar barin jikin ta, saboda tsaban shock da tayi da jin abinda aka faɗi a kan mai gidan ta, Mamma ce ta shigo tana tambayar "lafiya"? Sai dai itama idon ta ya gane mata, kunnen ta ma ya jiye mata.
A take shock ɗin Mamma ya fi, domin kuwa ita sakin jikin ta tayi, tayi ƙasa, tashin hankalin su ne ya ƙaru, ganin abinda ya samu Mamma, lokacin mai napep ya sauke Amna a ƙofar gida, sai dai fa yau duk wanda yayi tozali da idon Amna sai ya tsorata, sabida yadda fiskar ta yake ɗauke da tashin hankali muraran, duk da bata cire glass ɗin ba.
Tun daga Ƙofar gida take jin ƙarar Ummee da Mubarak, yadda ta iske Mamma sai ya ƙara ɗora ta cikin wani tashin hankalin, ba tare da ta ƙarasa ciki ba, "Muje Asibiti, mu kai ta kada wani abun ya same ta" Cewar Ummee cike da fargaba sai kuka take, Mubarak kuwa duk da cewa namiji ne shi, amma hawaye ne ke ta zarya a kumatun sa.
Da sauri ta ƙarasa inda Mamma take tare da cire glass ɗin idon ta, tayi wulli da shi "Ummee ku dai na kuka ba sai an kai ta hospital ba zata tashi" ta faɗi bayan ta taɓa kai da wuyan Mamma, ita kaɗai ta ɗaga Mamma ta mayar da ita ɗaki zuwa kan gado, ta lulluɓe ta da bargo ta koma gurin su Mubarak, sai dai har lokacin ko ɗigon hawaye bai fito daga cikin manyan Idon ta ba, sai launin ja da ya kewaye farin, yayin da zuciyar ta kuma ke cike da tashin hankali, amma gwara ta daure taji da na familyn ta.
A yadda ta barsu ta dawo ta same su, "Mubarak ɗin Baba ka daina kuka ka ji, kaida yakamata ka rarrashi Ummee amma kake kuka?" Ta faɗi tana riƙe masa hannu alamar rarrashi, komawa gurin Ummee tayi, tana bin ta da kallon tausayawa, tace "Ummee nah ki daina kuka..." katseta Ummee tayi da faɗin.
"Amna cewa fa su kayi Baban ku ya mutu ko baki ji bane? kuma wai sanadin....!" sai kuma ta fashe da kuka, ana haka sai ga shigowar wasu daga cikin maƙoftar su, jin kamar da matsala a gidan, nan suka fara taimakawa Amna gurin rarrashin su Ummee.
Lallai gaskiya Amna jaruma ce, irin wannan jarumta haka, yadda ta daure ta ɓoye duk tashin hankalin dake zuciyar ta--
Komawa ɗakin Mamma Amna tayi, lokacin kuwa Mamma ta fara motsi, wucewa kitchen tayi da sauri ta ɗibo ruwa a glass cup ta dawo, a hankali ta ɗago ta haɗi da gyara mata zama ta bata ruwan ta sha, hawaye masu zafi Mamma ta fara fitar wa, tana faɗin, "shiyasa na hana shi zuwa amma yaƙi, me yasa zai min ƙaryan zuwa ziyara, ashe abinda zai je yi kenan".
"Dan Allah Mamma nah kar kice haka, kece mutum ta farko da zaki ba da labarin Baba, kinsan ko à mafarki bazai aikata hakan ba" kuka Mamma ta sa tana ƙara cewa "nasan haka, amma me dalilin sa nayin ƙarya?" "abinda yakamata in sani kenan" cewar Amna a cikin zuciyarta.
Su Wali, Zarah da Nabila ne suka zo suma, dan su rarrashi abokan na su, kusan magriba suka koma, Ummee da Mamma ko magana babu sai ido kawai musamman Mamma, suna zaune gaba ɗayan su a ɗakin Mamma, Amna ce ta tashi kamar antsikare ta, ta wuce uwaɗɗakan Ummee, tana shiga ta durƙushe a ƙasa, sai a lokacin take ji kamar yanzu ne abin ya faru.
Kukan da ta jima bata yi ba ne ta fara sakin sa mai ratsa zuciyar mai sauraro, kuka take sosai kamar ran ta zai fita, komawa gefe tayi, ta haɗe ƙafafuwan ta da hannu guri guda, tana ci gaba da kuka, idon ta ya canza kala, gashin ta da ya warware daga ƙullin da tayi masa tun da safe, sai ya barbazu a kan fiskar ta.
"Me nene yake faruwa ne? Baba menene yasa ka ƙi sanar damu dalilin...?" ba tare da ta ƙarashe maganar ba ta miƙe tana tinanin wani abu, sai kuma ta ciro wayar ta dake cikin aljihun wandon ta, da sauri-sauri take ƙoƙarin ƙara kamo labarin, zama tayi tana ƙara sauraron abinda suke cewa a ciki daidai wurin da, "a binciken hukumar, gawan bana yau bane, a ƙalla zai yi kwana biyu".
Tsaidawa tayi, tana faɗin, "taya zai zama kwana biyu?" Nan kuma ta ƙara tina lokacin tafiyar ta sa, "Allah ya baka nasara akan Ƙungiyar POSPA Aboki na, dan Allah duk abinda ake ciki ka rinƙa sanar da ni" "tabbas haka naji Uncle Tukur ya ce masa wancan ranar" . Cewar Amna a fili sannan ta ƙara cewa "ya kamata inje in samu Uncle yanzu ya faɗamin abinda Baba na yaje yi Kaduna" ta ƙarashe faɗi tana share hawayen ta, ta fice daga ɗakin.
Ba tare da ta sanar da su Mamma fitar na ta ba, ta fice daga gidan ko glass bata sa ba, kai tsaye gidan Uncle Tukur ta sake nufa, tana shiga suka fara mata kallon tausayawa, sabida sun san abin da ya faru, sai dai sunyi mamakin ganin ta ba tare da tabarau ba, koda yake tashin hankalin da take ciki ai zata iya mantawa da komi.
Wannan karon bata gaishe su ba, kawai tambayar su Uncle Tukur tayi, uwar gidan sa ce ta sanar da shi zuwan Amna, yayin da ta tadda shi shima yayi tagumi sabida tashin hankalin mutuwar abokin sa, dama yanzu yake son zuwa gidan su Amnan.
"Kice ta zo" kawai ya furta ba tare da ya kalle ta ba, fita tayi ta sanar wa Amna, ai kan ta ƙara sa, Amna ta yi hanyar ɗakin na sa, yanayin yadda ta shigo ne yasa shi saurin miƙewa, kallon ta yake yi cike da tausayi, da kuma ganin yanayin fiskar ta da bai taɓa gani ba.
"Amna kiyi...!" katse sa tayi da faɗin, "Uncle please tell me, ka faɗamin gaskiyar abin da na gani yau, kace min ƙarya ce haɗawa kawai a kayi, ai kasan Baba bazai aikata hakan ba ko?" Tana ƙarashe faɗi ta durƙusa tana zubar da hawaye masu zafi.
#Chakwakiya, ina tausayawa su Amna na rashin jigo da su kayi🥺.
To amma anya babu wani abu a ƙasa kuwa? Tabbas a kwai abinda ke faruwa wanda sai nan gaba zaku fahimta.
______________________________________________________________________________________________
Part 2️⃣9️⃣▶️3️⃣0️⃣
"Uncle please tell me, ka faɗamin gaskiyar abin da na gani yau, kace min ƙarya ce haɗawa kawai a kayi, ai kasan Baba bazai aikata hakan ba ko?" Tana ƙarashe faɗi ta durƙusa tana zubar da hawaye masu Zafi.
Zuwa kusa da ita yayi cike da tausayawa yace "ni kaina naji mutuwar Aboki na har cikin rai na, kiyi haƙuri Amna, ke musulma ce kin san cewa mutuwa da rayawa duk na Allah ne, addu'a yake buƙata a halin yanzu, bawai kuka ba", shima ya faɗi idon sa nason kawo ƙwalla amma ya daure.
Miƙewa tayi tana share hawayen ta tana faɗin, "nasani Uncle, nasan cewa dole kowa zai mutu in lokacin sa yayi, amma dalilin mutuwar mahaifi na ƙarya ce, kuma nasan kasan hakan". Cikin mamaki yace, "ƴata me kike son faɗa ne? Ni bansan komai dangane da mutuwar sa ba".
"Dan Allah Uncle Tukur kar kace haka, ka sanar dani dalilin zuwan mahaifina wannan garin, mutuwar sa ba ta Allah da Annabi bane, akwai abinda aka ƙulla masa, cewa fa su kayi wai kwanar sa biyu da rasuwa, bayan kuma ko jiya munyi magana da shi" ba tare da yayi magana ba ya wuce inda kujerar falon take ya zauna, itama binsa gurin tayi dan jin me zai ce.
"Koda mutane sun yarda da ya aikata hakan, bazai dame mu ba, saboda mu munsan halin sa ai" "a'ah Uncle, taya bazai da memu ba bayan anayiwa mahaifin mu mummunar zato"? Ta faɗi tana hawaye, Ta cigaba da cewa, "ranar da Baba zai tafi naji kuna maganar wata ƙungiya mai suna POSPA, Baba ya sanar damu cewa ziyara zaije amma abun ba haka yake ba, kuma kai kaɗai ne kasan sirrin sa, dan Allah ka faɗamin"?
Miƙewa yayi kamar ya shiga cikin damuwa yace "a'ah 'yata bakiji da kyau ba ne" ya ƙarashe maganar da roƙon Allah yasa karta ƙara yi masa wannan maganar, saboda mutuwar abokin shi ya zame masa izina, kamar yadda hausawa ke cewa, "in kaga gemun ɗan uwan ka ya kama da wuta, to ka shafawa na ka ruwan sanyi".
SU MAMMA.
Shiru basu ji motsin Amna ba, dubawa su kayi nan ma basu gan ta ba, suna kiran wayar ta sukaji ƙarar ta ɗakin Ummee, wannan yasa hankalinsu yaƙara tashi akan ina taje? Ta ina zasu fara neman Amna?
AMNA DA UNCLE TUKUR.
"Na roƙe ka dan girman Allah kar ka ɓoyemin komi, kasanar dani abun da mahaifi na ya ɓoye mana, karkayi sanadiyyar ɓatanci a gare shi bayan ya mutu, tun da har kana da hanyar kuɓutar da shi daga hakan", ta ƙarashe maganar tana fashewa da matsanan cin kuka, Amaryar tasa ta shigo sabida jin kukan Amna da tayi.
"Baban Asma'u lafiya kuwa?" "Bakomai jeki kawai" shine abinda ya ce mata, sannan ya ɗanyi ajiyar zuciya yace, "ƴata ki daina kuka, tashi ki koma kan kujera, ta shi kinji"? Ya faɗi mata shima yana zama akan kujerar, miƙewa tayi tana sharar hawaye ta zauna, ashe tsawon lokacin da tayi ba tare da ko ɗigon ƙwalla ya zuba daga idanuwan ta ba, rashin abin kukan ne.
Ƙura masa ido tayi, sai da ya ni sa sannan ya fara magana, kamar haka, "tabbas mutuwar sa shiryayye ne. mahaifin ki mutum ne mai kishin ƙasa kuma mai taimakon al'umma, kamar yadda kika sani ne yayi taimako da dama a cikin aikin sa na Jarida, sai dai tun da ya fiskanci wata babbar matsalar da take faruwa a ƙasar sa na shaye-shaye kuma samari da 'yan mata dayawa sun lalace sanadiyyar wata ƙwaya, ya fara bincike, a kai, saboda ƙwayar tana zama kamar jaraba ce ga wanda ya fara shan ta, ya shiga tashin hankali lokacin da yaga abinda ƙwayar take haifarwa mutane sosai, domin kuwa har hawaye yayi lokacin, nan ya fara tinanin ta yadda zai kawo mafita a kan lamarin, nan ya ƙara faɗaɗa binciken sa a kan Ƙungiyar POSPA, da kuma shugaban su ZABBA BA, sai dai tun da ya fara binciken sa akan wannan Ƙungiyar nake hana shi amma ya ƙi, ni da kaina nayi masa binciken bayan ya roƙe ni da nayi masa, na sanar dashi hatsarin su da kuma abubuwan da suka aikata amma yaƙi janyewa". Ya dakata da maganar yana tina lokacin da akayi hakan.
Ya cigaba da cewa "zuwan sa Kaduna yayi ne sabida ya gano reshen Ƙungiyar, saboda alamar zargi da yake akan wanchan garin, ya faɗamin cewa ya haɗu da wata 'yar bariki, ya samu information akan ta, tasan duk wata ƙwaya sabida babu wanda ba ta sha, dan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 7 Chapter of 56