hanyar fita ya nuna ni da baki yace,"sai anyi bikin wannan ƴar zan koma, nima na gaji da ganinta saboda tana shigar min cikin al'amura".
ko da na shiga wanka na jima acikin bathtub cikin ruwan zafi kafin na fito, dan sai da na tabbatar ruwan zafin ya ratsa ilahirin jikina ta yanda gajiyar zata yi saurin sakata, ina tunawa da karatun test ɗin da nake da ita gobe.
na shirya cikin wata riga armless na zauna a dining ɗin da yake acikin ɗakin nawa na shiga zuba abinci. kuma fara cina kenan wayar Sweety ta shigo cikin tawa, na daɗa kallon sunan Ya Ahmad ɗin da ke yawo akan wayar fuskana ɗauke da tarin murmushi na jin daɗi, ban ɗaga ba sai da kiran yazo gab da yankewa tukunna.
ajiyar zuciyarsa na fara juyowa a kunnena kafin kiran sunana ya fito daga bakinsa. "me kyauna". laɓɓana suka tale da kyakykyawan murmushi na amsa da cewar,"na'am Yaya nah". murnushinsa mai sauti ya fito yana cewa,"me kyauna yau nayi kewanki da yawa, duk kinsa na shiga damuwa da rashin jinki". cikin sigar lallashi da ban haƙuri nace da shi,"sorry Yaya Nah, wallah yau munyi busy ne da yawa a school, baka kalla ba ma duk na gaji, jikina sai ciwo yake min". na faɗa ina shagwaɓe murya da fuska kaman ina gabansa ne. muryarsa ta fito cikin tausaya min da faɗin,"ayyah sannu Me Kyau nah, sannu kinji, ina ma ace munyi aure da na kawar maki da dukkan gajiyan da ke tare da ke...kinci abinci?". na kaɗa kai kaman yana ganina ba tare da na amsa da baki ba, kuma shi ma kaman yaga hakan sai yace,"to please ki samu kici abinci sai ki kwanta ki huta, kiyi bacci mai yawa please". nace da shi,"tom Swty". "albishirinki". nayi saurin amsawa da,"goro". "tomorrow by now insha'Allah ina tare da ke, zanzo na ganki me kyau nah, na gaji da rashinki a kusa da ni, wannan 2weeks ɗin da ya rage ji nake kamar shekara biyu ce nan gaba". na doka wani tsallen murna da jin daɗi ina faɗin,"Allah ya kaimu goben, Allah ya kawo min kai lafiya...Allah nima Yaya kewanka na ke sosai, wataran har sai naji kaman nayi kuka". duk da ba kallonsa nake ba a lokacin amma nasan ya kaɗa kai kafin yace,"a'a kar ki kuka plss, kinga hawayenki masu tsada ne, bana so ake zubar min da su anyhow, duk da cewan akaina ne za'ayi". na gyaɗa kai kawai, da haka muka ci gaba da hiranmu ta masoya, haka mu kai ta hiran ina cin abinci har naci da yawa ba tare da na sani ba, gaba ɗaya shauƙin sonsa daɗa tsarga min yake yi, Ya Ahmad ɗina bai yarda da na ƙoshi ba sai da muka yi vedio call ya kalleni sosai sannan yace na haska masa cikina tukunna ya gyaɗa kai yace na yarda, tun da ga cikin nan ya zama ƙato kaman nasa, saura bacci kuma, shi ma kar a tashi sai na tashi me kyau da kaina.
a cikin baccin da na kwashi mintuna ashirin ina yi na jiyo daddaɗan ƙamshin turaren Mamina ya karaɗe min cikin hanci da cikin kaina, na buɗe murfin idona a hankali ina dubanta, tana tsaye bakin dressing mirrow ɗina tana maƙala sarƙata a wuyanta, sai nayi murmushi kamin na tashi zaune na dubeta ta cikin madubin da ƙwayar idonta ke kallona ta cikinsa. nayi ƙasa da kaina ina wasa da yatsuna nace,"Ummi ce ta saya min". murmushinta me ƙarfin sauti ya fito kafin tace,"na sa ni ƴar gidan Mami, aro za'a bani please". sai na ɗago kaina ina dubanta ta cikin madubin kamar yanda ta ke dubana nace,"duk yawan sarƙoƙinki sai kin ɓige ata aro Mamin Alhassan, wannan fa me ƙaramin kuɗi ce ba dai-dai da sawarki ba ce". ƙwayar idonta ƙyam akaina, talewar da leɓenta yay da murmushi tun ɗazu har yanzu tace,"na sa ni ƴar gidan Ummi, yau ɗin banjin saka nawan ne, na aro na keso, na aron ma wannan, ko ba za'a bani bane?". na ɗauke idona daga ƙwayar idonta na kaishi ƙasa sannan nace,"kar ki taɓa min abina, ki aje min ban ba ki izini ba". ba kallonta nake ba, amma ina jin san da ta zare sarƙan daga wuyan nata ta buɗe akwatunta ta saka, sannan tace,"kiyi haƙuri na taɓa maki kaya ba tare da neman izininki ba, ba zan ƙara ba insha'Allahu". na ɗago fuskata da tayi shaɓe-shaɓe da hawaye cikin ƙanƙanin lokaci, na kalla har ta kai bakin ƙofa zata buɗe ta fice daga ɗakin, sai na maida kaina ƙasa nasa tafukan hannuna na rufe fuskata, kuka ya kuma ƙwace min.
sai naji tausassun hannunta akan nawan su na ƙoƙarin buɗe fuskar da na rufe, daga nan kuma ta janyoni jikinta gaba ɗaya ta rungumeni tsam wanda har ina iya jiyo bugun zuciyar da ke harbawa a ƙirjinta, a hankali ta ke shafa gyararriyar sumar kaina da ta sha gyara, bata hanani kukan da nake ba har sai da na gaji dan kaina na tsaya, na tsayar da kukan a sa'ilin da na shiga mata magana cikin shashsheƙar kuka.
"Mamina...". ban iya cewa komai ba wani sabon kukan ya kuma zuwar min. sai naji ta sauke ajiyar zuciya a hankali kamin ta fara magana. "na sani Maryam, Na san dalilin hawayenki. ba ki min laifin komai ba, Maryam kunyarki nake ji shi ne dalilin da ya sa nake kasa sakewa da ke". na ɗago kaina daga jikinta ina dubanta nace,"Mami wacce iriyar macuciyar kunya ce wannan da za ki bari ta kassarar da ƴarki? Mami ba zan yarda da wannan furucin naki ba, saboda haka kar ki yaudareni da batun cewar wai kunyata kike ji shi yasa kike yakice kanki daga gareni, ba don mu biyun da kika haifa duk ta dattin hanya kika samar damu ba, da sai na ce ba kya ƙaunata ne saboda kin haifeni a shegiya, amma tsakani da Allah meye banbancina da Alhassan da ni ba za ki iya bani soyayyarki da kulawarki ba?, ko kuma dan shi ya taso a cikin gata da daula ne, ni kuma na rayu cikin karkara, na rayu a ƙazantaccen wurin da kike ganin ba za ki iya tarayya dani ba, to bari kiji, wallahi summa tallahi ƙauyen bichi ya fiye min wannan daular masarautar taku sau dubu miliyan, ina ƙaunar bichi fiye da wannan ƙasar taku, nafi ganin kyanta akan wannan wajen da rashin rayuwata acikinsa ya hanani samun soyayyar uwata...ba komai Mami, na gode da iya amsawar ma da ki kai na cewar kin haifeni, Allah sarki Gwaggona, Allah ya jiƙanki da rahma ya haskaka ƙabarinki, na tabbata ko babu soyayyar wata uwa a gareni a duniyar nan, tunawa da iyaka tata da na samu ma kaɗai ta isheni nayi farin ciki muddin rayuwata, ballantana ina da Ummi, wacce ta sadaukar da jin daɗin rayuwarta dan ganin na rayu, ta hana kanta jin daɗi da walwalar duniya duk saboda kada na shiga damuwa ko da na sakan ɗaya".
sai kawai ita ma naga ta shiga zubar da hawaye daga idonta, kuma ta ke hankalina ya kai ƙololuwar tashi, hakan yasa na tsayar da maganganuna, na shiga kaɗa mata kaina da sauri ina kama fuskarta ina goge hawayen, sai ta kuma rungumeni muka shiga kukan tare, kukan da bana komai bane sai na huce takaicin da zuciyoyinmu ke ciki.
"ki yafe min Maryam". muryan Mamin ta fito a hankali, a hankalin da ya haifar da tsargawar jin wani tsananin tausayi da jinƙai na mahaifiyata. "ni ba ki min komai ba Mami, dan haka ki daina neman yafiyata, ni ce dai zan nemi yafiyarki, na kuma roƙeki da Allah nima ki sammin soyayyarki da kulawarki, ko da ace bai kai kwatankwacin yanda kike nunawa Alhassan ba". "Maryam kenan, ba ki san cewar nafi ƙaunarki akansa ba. ba za ki gane bane, you are still a baby, shi yasa gaba ɗaya kika kasa fahimtata, Maryam ina kunyarki ne idan na tuna ta irin hanyar da na samar da ke, amma kiyi haƙuri ki yafe min, nima bana jin daɗin yanda na ke mu'amalantarki, kuma daga yau na daina, insha'Allahu, zan nuna miki dukkan so da ƙauna da kulawa muddin rayuwata, ƙila ma har kice Mami wannan soyayyar ta fara isata, domin za ki dinga ganinki ne kamar jaririyar da ke shan nono...kin yafe min ɗin?".
ban san lokacin da wani murmushi ya suɓuce min ba, na kaɗa mata kai, sai ta ɗago da fuskata sama ta sumbace ni a goshina da kumatuna, kamin ta furta,"ina sonki Maryam, ina tsananin sonki". nima nace da ita,"nima ina sonki Mamina". ta kamo hannuna ta riƙe acikin nata, sannan murya a hankali tace,"idan kina cikin fushi ki daina magana kinji, ki dinga bari sai kin sauko, dan na lura ba kya iya controlling harshenki a duk san da kike cikin yanayi na ɓacin rai, kinga aure za ki yi, idan ni na ɗauka ba lallai mijin rufin asirinki ya ɗauka ba". sai na kaɗa kai nace,"zan kula insha'Allah". "yauwa Allah yay maki albarka".
shiru ya gimla a tsakaninmu na wasu ƴan sakanni, kafin tayi min tambayar da na iya amsa mata da ƙyar saboda kunya. "ba muyi maganar da Umminki ba, ai na Ahmad ɗin yace za ku zauna?, lagos ɗin ko kuma a kano?". "Lagos ɗin yace, idan ya sami hutu kuma sai muke zuwa kano". "hakanma yayi, to ya batun tsarin gidan ya faɗa miki?". na ƙara yin ƙasa da kaina cike da kunya nace,"ehh hoton yana wayata". "to sai ki turawa Daddynki, ɗazu yace yanata kiran wayarki zai tambayeki. duk da Umminki tace ita zata yi sayayyar komai. kin san Mai Martaba ya baku gida ma anan?". nayi saurin ɗago da kaina ina kallonta, kafin na girgiza kai nace,"a'a Mami". "ɗazu ya bawa Yayanki Almustapha key ɗin gidan, yace ya bawa Ahmad ɗin idan sun haɗu". na shafa gefen fuskata a hankali kamin nace,"Allah sarki Abi an gode Allah saka da alkhairi, Mami ki masa godiya". ta ɗan harareni da wasa kan tace,"tun da ni ce bakinki ko". sai kuma ta ƙara cewa,"me za kiyi yanzu?". na ɗaga kaina sama na kalla agogo sannan na sauke nace mata,"mu na da test har uku gobe, zan duba littafaina". ta gyaɗa kai,"to yayi, ai karatu da yawa. bari na ƙyaleki idan kin gama sai ki sameni a ɗakina, dama saboda ke na fasa komawa gida, dan haka daga yau har zuwa ranar da Umminki zata miƙa ki ɗakinki lokacina gaba ɗaya naki ne". murmushi kawai nake yi, na sakko akan gadon na dakatar da ita taga fitar da za tayi. "Mami ba ki sa sarƙar ba". da murmushin da bai bar fuskarta ba tace,"yanzun kuma za'a ara min kenan?". nasa hannu a fuskata cike da kunya sannan na kamo hannunta ta tsaya a gaban madubin, na ɗaura mata sarƙar sannan na ɗora haɓata saman kafaɗarta muna kallon juna ta cikin madubin, muna sakarwa juna ƙayataccen murmushi, tare da haskawar tsantsar soyayyar da muke yiwa juna a cikin ƙwayar idonmu. "kin yi kyau Mamina, kin haska sarƙar".
Alhassan ya turo ƙofar ɗakin ya shigo, ya tsaya daga bakin ƙofar yana kallonmu cike da burgewa, ba mu juya gareshi ba, shi ma kuma bai yi magana ba sai da ya gama kallon namu sannan yace,"gwara dai ma kiyi auren ki tafi ki ƙyalemin Uwa". baki kawai na murguɗa masa bance komai ba, ya ƙwalo min biron da ke hannunsa na kauce ya sauka akan wuyan Mami, Mami tace da shi,"ya maka kyau Alhassan". "yi haƙuri Mami". tace,"ai ba wani abu bane, indai ƙwalowa mutum abu ne kar ka daina kaci gaba, zanyi maganinka wataran tun da kai baka san alkunya ba". yay dariya yana cewa,"yi haƙuri Hajiya Mami". "ka dai ci gaba kaji, garin jifan mutum da abu ka jefa ka sami Ubana, to nima kuwa da izinin Allah zan rama akan ubanka Major, ko da yake Allah ba azzalumin bawansa bane gashi yau da kanka ka rama min akaina, amma duk da haka ka sani sai dai idan ban sami abin jifa ba, sai na jefi goshin Major da shi yayi ƙwalele". ya rufe bakinsa yana dariya yana faɗin,"wa yaga goshin Dad yayi tsini". ta girgiza kai tana faɗin,"Allah ya gyara min kai, yanzu ya akai?". sai ya dubeni yana faɗin,"wai ke me ya sami wayarki?". nace,"me ka gani hala?". "Dad ne yace yanata kiranki tun ɗazu a kashe". sai na sa hannu na rufe baki na nufi wayar ina faɗin,"laaa wallah na manta na kashe sim ɗin, Na Yaya ne kawai a kunne". yaja tsaki kamin ya taɓe baki ya haɗa da faɗin,"to dai yace ki kira Ya Ahmad ɗin ki faɗa masa ya kawo masa result ɗin genotype ɗinsa". ban san dalili ba haka kawai naji allon ƙirjina ya girgiza, na ɗago na dube shi da sauyin yanayin da fuskata ya samu nace,"me za'ai da shi?". yace,"ki kira Dad ɗin ki tambaye shi tun da bani nake nema ba". daga haka yasa kai ya fita a ɗakin. Mami kuma tace,"dama tuntuni ba'ai wannan gwajin ba?". nayi shiru ban iya cewa komai ba, dan yanda naji jikina yay sanyi a lokaci ɗaya. sai ta fita tana faɗin,"to ki kira shi da sauri ki sanar masa kin san halin Daddynki sarai ba ya son delay". na ɗauke idona daga bayan ficewarta, na haɗiye wani abu a maƙogorona da ban san mene shi ba, kamin na iya neman wuri na zauna.
nasa finger print na buɗe wayar, kuma ta ke fuskata ta washe da annuri sakamakon cin karo da saƙon Ya Ahmad da nayi, wani taraddadi dann ji yana neman mazauni acikin zuciyata ya washe, na shiga karanta text ɗin nasa da haskawar hoton fuskarsa acikin idona.
_"I am in you and you in me, mutual in divine love. Saying it a thousand times won’t be enough to express my feelings towards you, but I’m going to keep saying it nevertheless- I love you! I will keep loving you till the end of my days, no matter what lays ahead of us Cutie nah, waiting and eager of the day, wannan ranar, a wannan daren da Ummi zata damƙa hannunki a nawa tace Diman Da'iman Ahmad..."._
sai na rungume wayar a saman ƙirjina na kifa kan gadon, na haɗe murfayen idona waje guda na lumshe, sannan naja leɓena na ƙasa na shigar da shi cikin bakina ina tsotsa da tarin murmushin da ya ƙi barin fuskata, ji nake ajikina tamkar Yaya nah na rungume ba wayar da ke ɗauke da saƙonsa ba. kuma ta ke hoton wannan ranar ya shiga haska min acikin idona, wannan daren ranar da Ya Ahmad ya buɗe min zuciyarsa, ya tona min sirrin da ke shimfiɗe a cikinta a game dani da soyayyata.
wannan daren da ya sameni da Al'ameen a parlo muna hira, saurayina da ya min proving soyayyansa a computer school ɗin da na shiga kafin na baro bichi, kuma a wannan daren ne zuwansa na farko gida da izinin Baba da Yagana, amma zuwan Ya Ahmad ya wurin ya tarwatsa zaman fahimtar junan da muke shirin yi ni da Al'ameen.
a gaban Yagana, gaban Ya Kabir, gaban Basma da Inna Zulai, gaban Ya Aminu da Baba, gaban Ummina, gaban kusan kowa na gidan. ya jawoni daga kan kujerar da na ke zaune gefen Al'ameen, ya tsayar da duga-dugaina a gabansa, dab da shi sosai, ya kama dukkan hannayena biyu ya ɗora saman ƙirjinsa, saitin zuciyarsa, wani abu da ya haifar da tasirin da na ji kamar zanyi fiffike na tashi sama.
wannan lokacin da nake a dab da gabansa, hannayena saman ƙirjinsa, sai nake jin zuciyata a lokacin kamar fayau ta ke babu komai acikinta, na kasa haɗa ido da kowa na kuma kasa kallon gefen da kowa yake, sai haɗiyar wani yawu nake a maƙogarona da ke wucewa da ƙyar, kafin daga bisani naji ƙafafuna na neman gaza ci gaba da ɗaukata, dalilin wannan harufa biyar da Ya Ahmad ya furta min.
_"Maryam za ki Aure ni?."_
*Plss Comment,Share&Vote.*
[7/17, 08:47] Halimahz(Anyway): *SIRRIN ƁOYE*
*©️Halimahz*
*Anyway@arewabooks*
*HalimaAnyway@Wattpad*
*Halimahz@Bakandamiyahikaya*
_Ina ƴan kasuwan da ke da buƙatar a tallata masu kasuwancinsu cikin littafinmu domin ƙara samun customers?, a sanka a san sana'arka, zamu tallata maku hajarku cikin farashi mai rahusa, ku dai ku tuntuɓi wannan number 08024976578(whatsapp only) kai tsaye, mai talla a ko da yaushe shi ke da riba._
*(44)*
"Maryam za ki aure ni?". tambayar ta ƙara fitowa kamin rufewar idanuwana da buɗesu.
bai nisa ba ya ƙara cewa,"Dan Allah kice min eh, kice musu kin amince, ki faɗawa kowa kin yarda dan Allah. na gama shirya rayuwata da ke Maryam, duk wani plans nawa na gaba na gama tsarasu da ke, wallah ina sonki, kuma so nake na aureki. i cant imagine this life without you Maryam, tun daga ranar da komai ya bayyana kika samu muhalli a zuciyata, i love you, i love you so much". harufan ƙarshen suka fito tare da ɗauke hannuna da yake daga saman ƙirjinsa ya sarƙe yatsunmu wuri guda ya damƙe hannuwanmu sose, ya kafe ni da idanuwansa da haskawar wani abu da ban taɓa gani ba a ƙwayar idon wani mahaluƙi.
ina iya jiyo yanda ƙafafuwana suka shiga rawa a wannan lokacin, da yanda jikina ya ɗauki kyarma gaba ɗaya, naji wucewar wani dunƙulallan abu ta maƙogwarona da ban san mene shi ba, a lokaci guda murfayen idona suka haɗe, wani duhu kuma ya shiga haskawa cikinsu, sannan a hankali kuma kalaman Ya Ahmad su shiga maimaituwa cikin kaina. _"Maryam za ki Aure ni? aurenki nake so nayi, i love, i love you so much."_ maimaituwa kalaman suke kaman a lokacin ne yake faɗa min su, ƙara shiga suke ta cikin kaina da tunanina da wani irin tasirin da ke ratsa ko'ina a jikina. iyaka abinda na sani a lokacin shi ne Al'ameen kawai nake so, kuma ko a halin da nake ciki kalaman Al'ameen ɗin da na Ya Ahmad ke kamanceceniya suka gauraye su na amsakuwa a kunnena.
sannu a hankali sai naji duka kalaman Ya Ahmad ɗin sun gushe daga tunanina, zuciyata kuma ta shiga harbawan da zan iya rantsewa na kusa da ni su na iya jiyo sautin ƙararta. na buɗe rufaffun idanuwana na ɗorasu akan fuskar Ya Ahmad da har yanzu bai ɗauke idonsa akaina ba, fuskarsa cike da fargaba, kallona yake da irin tasirin shigar wani abu ta babban yatsan ƙafata zuwa tsakiyar ƙoƙon kaina.
_"na rasa da me zamu biya waɗannan bayin Allah'n da suka mana halacci a rayuwa, Maryam na rasa da me zan saka masu."_ maganar Ummi ta haska a cikin kaina, a washe garin ranar da ta dawo daga india. idan ban manta ba abin da laɓɓana suka furta mata a lokacin shi ne,"Ummi ai mun biya su, ko su bana tunanin su na ƙara saka ran wani abu daga garemu, mun saka masu da abin da basu taɓa haskowa kansu ba". kuma tun daga lokacin da na buɗe baki na fara maganar kallona ta ke da murmushi a fuskarta, har san da nayi shiru ta ɗora da cewan,"Maryam gidan nan da muka basu gani na ke kaman bamu basu komai ba har yanzu, gani nake dama can sunfi ƙarfinsa, Maryam so nake ace yau sun bijiro min da wata buƙata tasu a wurina da zan iya basu kai tsaye, su nemi abin da nasan ina da shi, abin da nasan bai fi ƙarfina ba...". kuma a lokacin bata ƙarasa faɗin abin da zata ce ba Alhassan ya tari numfashinta da faɗin,"Ummi ko Maryam suka nema za ki iya ba su?". kuma ina iya tunawa da amsar da na ba shi a lokacin na cewan,"ai dama ni tasu ce, har abada tasu ce ni". yace,"ina nufin fa Baba ya nemawa ɗaya daga cikin yaransa aurenki, za ki amince Maryam?". abin da Alhassan ya furta kenan, kuma a lokacin ido kawai nasan na iya binsa da shi, ba tare da laɓɓana sun motsa ba har na furta masa wata kalma. Aure! Aure! a wancan lokacin ban bawa Alhassan amsa bane saboda nasan maganar da yayi ba magana bace mai yiwuwa, sai kuma gashi a yau ɗin kuma a yanzu ba Baba bane da kansa, ɗansa ne da kansa a gabana, yake neman yardata akan aurensa, a gaban Baba da Yagana, haka zalika a gaban Ummina da ke jiran wannan lokacin.
Ya Ahmad! Ya Ahmad dai mutumin da shi ya kaini makaranta, da kuɗinsa na fara karatun boko, to shin dama ni wacece da har zanƙi amsar wannan tayin nasa? na girgiza kaina a hankali zuciyata na faɗa min cewar Maryam ke ba butulu bace. ko da baice min ya fara sona ba tun a ranar da ya san haƙiƙanin alaƙar da ke tsakanimu, zan amincewa aurensa ko da a yanzun nanne yaji ya fara sona, ko da za'a min auren dole da Ya Ahmad bana sonsa ba ya sona tabbas zan zauna da shi, tun da har ya kasance shi ɗin jinin Baba da Yagana ne.
na taɓa cewa Alhassan da Mami duk wani abu da zai sa a binciko asalina to ina gudunsa, zan kuma kaucewa duk wata hanya da zata zama sanadin hakan, dalilin bincikar asalina yasa bana sha'awar yin aure kuma na cire ran yinsa har ƙarshen rayuwata. Abin da Umm ta faɗa min a wannan lokacin shi ne,"Maryam idan har za ki ci gaba da dasa wannan abin a ranki to kuwa kina tare da ɓacin rai har ƙarshen rayuwarki, ki manta da komai tun da komai ɗin nan ya rigada ya wuce, ki fuskanci sabuwar rayuwa da kika shiga a yanzu, kiji daɗinki da kwanciyar hankalin da kika samu...kuma abin da nake so na jadddada maki shi ne Aure ko kina so ko ba kya so Maryam sai kinyi, saboda haka ki tsayar da zuciyarki akan Jawad muddin da gaske kina tsoron duk wani abu da zai tono asalinki, dan shi ne wanda ba zai taɓa goranta maki ba, shi yafi dacewa dake a yanda kike, saboda haka ki yarda ki zama tsintsiya maɗaurinki ɗaya ke da shi tun da acikin danginki yake...idan ba ki sa ni ba ma ki sa ni Jawad ba tun yanzu ne yake sonki ba, tun ranar da ya fara ɗora idonsa akanki yaji yana so ya aureki, ba tare da ya duba banbancin da ke tsakaninki da shi ba, abu ɗaya ne kawai ya jinkirtar da shi akanki Maryam, karatunki! kuma a yanzu da komai yazo a gaɓar da ya tsara, ya furta miki ya kuma sanar da Mai Martaba dan haka ki yiwa kanki karatun ta natsu ki tsaida zuciyarki da tunaninki akansa, ina ƙara faɗa maki da Jawad kaɗai za ki kasance ki tserar da kanki daga wani ƙalubale na asalinki".
ofcourse i know rayuwar aurena da Jawad ta dace dan shi ne rufuwar asirina, to amma a yanzu da nake tsaye gaban Ya Ahmad bana tunanin ko wannan mutumin da Ummi ta bani labarinsa ne zai zo wurin nan a yanzu ya furta min da bakinsa cewar zai aureni zan amince masa, wannan mutumin da Ummi tace ya so ni tun kamin na zama cikakkiyar mace, ya ɗau shekaru goma yana ƙaunata duk da yasan wace ni, ya ɓoye hakan a ransa da zuciyarsa ba tare da ya furta min ba, ba wai dan son da yake min yana da tangarɗa ba, a'a sai dan saboda tsananin soyayyar da yake min, gudun kar ya buɗe min zuciyarsa rayuwata ta faɗa cikin garari idan na gane wace ni, Ummi ta faɗa min tun kafin na san asalina na fara zubar da hawaye shi yake zubar min da nasa, hawayen da yake yinsu akan abu biyu, tausayina da kuma tsananin ƙaunata. mutumin da yace mata ko daga sama aka jefoni zai aureni, ba zai gujeni ba, ba zai taɓa ƙyamatata ba, illa ma yayi dukkan mai yiwuwar da zai yi ya gusar da duk wani dattin baƙin ciki daga zuciyata, ya tsaya min tsayin daka wajen ganin banyi kuka ba dai-dai da second 1, burinsa shi ne kawai yaga laɓɓana na talewa da murmushin farin ciki da jin daɗi a kullu yaumin, ya mantar da ni ƙalubalen da ke cikin rayuwata, ya faɗa mata ya ƙara nanata mata rashina zai iya yiwa zuciyarsa illa._
_"son Maryam zai min illa idan har na rasata Ummi"._ waɗannan kalaman kullum
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 42 Chapter of 52