ce da yake jarabtar bayinsa dashi.
Ba’a yarda ka d’auki ‘yarka ka bada aurenta ma ko wane irin mutum ne yazo Neman auren nata ba dan kawai kana hanzarin ka kauda ita gabanka. Shiyasa addini ya bada tsare tsare cikin Neman auren Kansa kafin aje ga auren. Uwa uba a nemi zab’in Allah cikin duk abinda ake nema. Allah ya shirya mana zuri’a ya azurtamu da yaranmu da samun abokan rayuwa na gari. Ameen.
Umma naku fah kan kace me ta ware. Har wani cakarewa tai cikin tsaddan leshi da Hajja Asshe ta kawo mata a d’inke. Kayan da Ummul zatai fitan biki ma Hajja Asshe ta kawosu a d’inke masu d’an karen kyau da tsada. Dik wani buk’ata da amarya zatai amfani dasu Asshe da k’awayenta Sun kawo.
Hajiya Hadiza k’awarta ta dubeta bayan Sun keb’e “Amma fah kawata kin bani mamaki, ko a mafarki ban tab’a hasashoki tsakankanin talakawa ana damawa dake ba. Wai fisabilillahi ya akai kuka amince da wann aure tinda nasan duk yanda tsiya yake ba’a ganinku wajen.”
Murmusawa Asshe tai tana duban Umma yanda taketa shige da fice cikeda farin ciki. Ta kuma duban k’awarta Hadiza “Hadiza kenan, kin fad’a daidai. Duk yanda tsiya da talauci yake bana zuwa wajen. Toh amma babu yanda muka iya ne. Dole ce ta Kama sai anyi auren.”
Hadiza ta girgiza Kai kad’an “Toh amma gida bai k’oshi ba yaya za’a kawo waje. Ina nufin ga Anisa ‘yarki dan me baki had’a auren da ita ba tinda tana zaune itama ba mijin har yanzu.?”
Asshe ta kuma murmusawa “Tinda kikaji na Miki amfani da kalmar dole ki amince kawai dolen ne. Ni fah kaza ce Hadiza bani k’wai na saida zakara. Ke kinfi kowa sanin haka. Yanzu dai ki bari a gama hidiman nan idan mun natsu na sanar dake komai.”
Hadiza ta jinjina Kai a hankali har lokacin mamaki bai saketa ba ganin yanda Asshe ta shiga cikin talakawan nan ana damawa da ita. K’awarta ce tun secondary school ta Santa farin sani. Asshe da zuri’arta worshiping money suke inji su Hadiza. Mutane ne da zasuyi komai Akan duniya da abinda ke cikinsa. Shiyasa ta sha mamakin ganin wann al’amari. Kaman yanda Asshe tace da ita akwai dalili ta tabbata akwai dalilin.
**
A can police station kuwa motar ‘yan sanda na shigewa na Hilal ma ya sako kai.
Sauri sauri Hilal ya take mata baya ganin ta nufi hanyar da aka shige da Mama sai kururuwa Maman take tana fad’in wllhi bata ci kud’ad’en ba.
Mama taci gaba da fad’in “Wayyo Khulsum ‘Yata ki cece ni ki ceci Mamanki kar a rufeni. Idan aka rufeni babu mai kula da Abbanku dake kwance gadon asibiti Khulsum.”
Khulsum ta samu zarafin dakatar da ‘yansandan ga bak’auye a gefe yana fad’in kwarankwatsa sai an karb’ar masa hakkinsa. Baici nanin ba nanin bazata cisa ba. Takardun bogi suka kawo masa ya saka hannun. Sarkin kasuwa yace baisan da zancensa ba. Idan sama da k’asa zasu had’e sai an fitar masa hakkinsa.
Police ya dubi Khulsum yace “Ke kuma fah.?”
Mama tai saurin bud’e murya tace “‘Yata ce. “
Tsananin mamaki sai ya hana Khulsum furta koda kalma. Wai yau Mama ce ke kiranta da ‘yarta. Ikon Allah, Ashe har akwai ranan da Mama zata danganta kanta da jinin Ummanta. Bata kaiga furta kalma ba ta hango Habib mijin Azeema da police woman d’in da kwanaki suka kawota nan police station d’in. Sai wani mannewa take jikinsa. Mama ganin Khulsum tayi shiru ya sanyata duban yanda Khulsum d’in ke duba.
Ta zaro ido waje tana kuma mutsukesu. Waye take gani haka.? Habibu ne mijin Azeema Sun fito daga wani ofishi yana faman gyara kwalan rigarsa sai washe baki yake ga wata ‘yarsanda gefe sai kashesa da kallo take kaman zata shige cikinsa. Ta dafe k’irji tana furtawa da k’arfin gaske “Na shiga uku mai nake gani.! Habibu..!”
Hankalin Habibu da ‘yarsandarsa ya dawo kansu.
Mama ta soma nunasa da yatsa “Habibu mai zan gani mai kake a nan..? Amanan Azeema kake ci da wann ‘yarsandan.?”
“Madam ki iya bakinki police station kike ba Tasha ba.” ‘Yarsandan ta fad’a cikin dakatar da Mama wacce tai sokoko tana kallonta.
Habibu ya wayance “Haba Mama ya kike magana haka.? Nan fah police station ne. Zuwa nai inata fafutuka ina fad’i tashin yanda za’a samu a kamo mana Tasi’u mana Mama..”
Ya dubi mutanen dake wajen ya kuma dubi ‘yansandan da suka kamota “Meke faruwa a nan.. ya na ganki da ankwa.?”
Sai Mama ta soma kuka “Habibu ka ceceni.. Kamo ni sukai.. Ka fad’a masu waye yaci kud’in shagon Malam. Kai shaida ne wllhi banci ba. Habibu kar ka bari a rufe ni.”
Kaman daga sama suka sinkayo muryar Khulsum “Ni kuma zan bada shaidan kece kika sayar da shagon koda kuwa Kotu za’a je na shirya zuwa.!”
Mama ta kaikaito tana duban Khulsum “Fitsara zaki min a nan Khulsum.? Inji kin biyo ni ne dan ki taimakeni ki bada shaida kaina.”
“K’warai kuwa Mama. Zuwa nai dan na bada shaida akanki na kuma tabbata kin biya abinda kika aikata wa mahaifina Wanda yake kwance baida ikon kare kansa balle dukiyarsa.”
Mamaki ya cika Hilal. Ya dubi wann ya dubi wancan “Wait. D’an dakata, wai dama ba zuwa nan kikai dan ki taimaki matar nan ba.. I thought I heard you call her Mama or something.. Is she not your Mom.? Ba naji ta kiraki ‘yarta ba. Ta ya kike bada shaida mai muni kan mahaifiyarki.. Are you going to let them arrest your mother just like that..? Don’t tell me we came all the way here just for you to make sure anyi arresting Mamanki..”
“Malam kar ka sake kiran wann matar Mamata. Ni ba uwata bace. Kuma ka fad’i daidai zuwa nan nai na bada shaidan abinda ta aikata kafin wancan surkin nata yayi amfani da damarsa ya fiddata.” Ta k’arashe tana nuni da Habib dake tsaye gefen budurwarsa ‘yarsanda wacce ya kawo ta kama Khulsum d’in lokacin da ta mari Azeema.
“Amma nafi uwarki da ta saida ‘yar Malam Isubu yana kwance. Gwara ni shago kawai na saida.” Mama tace tana huci.
Hilal ya kuma duban Khulsum da mamaki Wanda kalaman Mama ya haifar mata da sanyin jiki.
Bakauye ya kafe sai an rufe Mama idan ba kud’ad’ensa aka lalo aka basa na. Haka dole aka jefata cikin cell Habib na kwantar mata da hankali da fad’in zai iya k’ok’arinsa yaga ta fita.
Khulsum kaw bata kuma fahimtar komai ba tun bayan maganan da Mama ta fad’a mata. Take taji wani irin kuka na zuwa mata. Tabbas Mama ta fad’i gaskiya gwara ita Akan Umma. Ita abun duniya kawai ta saida amma Umma fah mutum ta saida. ‘Yarta da ya kamata ace ta zamto tamkar lu’ulu’u a hannunta. Abu mafi daraja fiyeda shago da abinda ke cikinsa Umma ta sayar. Ko kusa baza’a had’a laifin Mama da Umma ba. Bata San yanda take jefa k’afafunta ba tafiya kawai take tana kuka. Tana Jin wani abu mai kama da k’iyayya Wanda shine zata iya cewa iyakacin alak’arta kenan da mahaifiyarta.
Tana tafe gefen kwalta Hilal na biyeda ita cikin mota. Yaci gaba da fad’in “You know you are unbelievable.. Da nasan Akan wann dalilin kika taho all the way to police station da ban b’ata lokaci na na kawoki nan ba. Because of you na rasa d’aurin auren d’an uwana.”
“Malam idan baka Kama gabanka ba duk abinda na maka Kai ka saya da kud’inka.. Da ace baka b’ata min jiki ba Watak’ila da ban tsaya na b’ata lokacina wajen ji da kai ba balle har nayi gamo da Mama. Watak’ila da na samu damar dakatar da auren zalunci da ake yunk’urin yima ‘Yaruwata..”Ta fad’i tana ci gaba da sakin huci ga hawaye dake ci gaba da gangaro mata.
“Blame your step mother then.” Hilal ya bata amsa Kai tsaye.
Khulsum taci gaba da tafiya tana hawaye.
Hilal yai parking ya fito ya tare gabanta “No I can’t just leave you here. After all, Ni na kawoki nan. Idan wani abu ya sameki I’ll blame myself for the rest of my life. Please get in the car. Ki bari na maida ke yanda na d’aukoki. At least.”
Bata amsa shi ba sai kukan da take ci gaba da yi dan mugun takaicinsa take.
Ya d’an waiga yana duban mutane masu giftawa sai kallonsu suke.
Ya d’an kuma gyaran murya “Look, I don’t want people to think that I hurt a girl. Dan Allah ki shiga.. At least ki bani dama na fitar dake daga nan.. Dare ya soma yi duba ki gani.. And is not safe for you to walk alone a babban kwalta irin haka.”
Cikin kuka Khulsum ke dubansa “Na tsaneka.! Na tsani mugayen ahalinka da sukai amfani da raunin mahaifiyata suka sayi ‘Yaruwata da sunan aure.!”
Hilal ya zuba mata ido “Look, bansan meke faruwa tsakanin ahalinmu ba. But the only abu da zan fad’a Miki shine my cousin is a good person.. He has his faults as human. But I can assure you he’s a good person.” Ya d’an tab’e baki “Idan yar uwarki ta kasance matarsa abun kiyi mata murna ne.”
Takaici ya hanata furta koda kalma tasa kai tana ci gaba da tafiya. Hilal ya kuma tareta “Yamma yayi sosai ki shiga na kaiki gida. That’s idan Kinaso ki cimma ‘yaruwarki kuyi Sallama kafin a tafi da ita. Dan na tabbata kawo wann lokacin an d’aura auren. Tinda bakiyi nasaran dakatar da auren ba. Watak’ila zakiyi nasaran samun dama kuyi Sallama idan har kika shiga mota ta.” Ya k’arashe yana nuni da motar.
Bata k’aunan abinda zai kuma had’ata da d’aya daga cikin wann ahalin. Toh amma gaskiya ya fad’a idan batai saurin cimma Addanta ba Watak’ila bazata samu suyi Sallama ba za’a tafi da ita. Saida ta rakasa da harara kafin ta nufi motar.
Hilal ya d’an tab’e baki yana bud’e mata marfin motar “Sorry to say a daidai yanda na d’aukeki zan ajiyeki. Kinga ko ba komai na rage Miki hanya.”
Ta kula nema yake ya dad’a tunzurata hakan yasa bata kuma bi takanshi ba balle ta amsa shi.
Saidai suna isowa bakin babban kwalta da zai shigar da kai layinsu suka hango motocin amarya na ficewa. Alamun Sun makara amarya ta riga ta hau hanya.
Hilal ya tab’e baki kad’an “Looks like someone didn’t make it on time. Unless zaki bi bayansu.”
“Ajiyeni a nan.” Ta fad’i tana k’ok’arin bud’e motar.
“Are you serious.?” Hilal ya fad’i yana k’ok’arin juya kan motar cikin k’ok’arin bin bayan motocin.
Da mamaki Khulsum ke dubansa ta kuma jan marfin motar ta jita a rufe alamun ya rufe daga wajensa.
“Malam ka ajiyeni a nan nace ko na maka ihun b’arawo.!”
“You and I both know this is what you want. Kiyi Sallama da ‘yaruwarki. Just admit it.” Ya d’an dubeta sai yai murmushi da gefen bakinsa “Don’t worry, I’ll do you a favor and take you to your sister. After all, Nima can na nufa..” Ya maida idanunsa ga kwalta “Kar ki damu ba sai kin biya kud’in abun hawa ba. A simple thank you will be okay.”
Bai kuma cewa komai ba yaci gaba da tuk’a motan.
Izuwa lokacin ta rasa ma mai zatce ma wann d’an rainin hankali. Shiru tai tana duban titi yanda Hilal taketa fifila gudu da ita.
**
Abuja..
Zaune yai gaban mahaifinsa yana sauraronsa yanda Daddy yaci gaba da fad’in “I will be meeting with our international clients in Nairobi.. Daga can zan wuce Cape Town, southAfrica gameda business alliance da muka fara a can months back.” Ya gyara zaman glasses d’in dake mak’ale idonsa kafin yaci gaba “Maybe it will take me two to three weeks before I return..” Ya k’arashe yana ci gaba da duba documents d’in dake gabansa.
Haidar ya jinjina Kai yana duban mahaifinsa “So why are you telling me all these Daddy.? Are you.. Do you want to hear from my own perspective.? I mean regarding the alliance.?”
D’agowa yai had’ida d’an zame glasses d’insa yana duban Haidar d’in sosai. “I did not send you to those expensive schools dan kawai ka dawo na saka ka a gaba naita kallonka. But unfortunately it is unfolding.. Watak’ila ba kai bane wann D’an da zanyi alfahari dashi. By now ya kamata ace na huta. Ya kamata ace Kai ke wakiltana a tafiye tafiye irin wann. Saidai Kai d’in banida k’warin gwiwa akanka. It is enough da na amince ka jagoranci project d’in cikin gida..!” Ya kuma dubansa sosai kafin ya k’arada “You are a complete failure to my name Aliyu!” Ya k’arashe yana maida glasses d’insa.
Haidar yai murmushi mai ciwo yana jinjina Kai “Is this the kind of legacy you wish to leave behind for your Son.?” Ya jinjina Kansa zuciyarsa na kuma masa d’aci kafin yaci gaba “I wouldn’t be surprised of course. But You know what Daddy. No matter how insignificant you keep insisting I’m to you.. You can’t deny the fact that your company needs me.. And you need me too.. Kuma shine dalilin da yasa ka kirani kake sanar Dani duka shirye shiryenka.. So Daddy, deny it all you want. But the truth is that I’m very much important to you.. And your company is nothing.! Absolutely nothing without me.!” Yana ida fad’in haka ya mik’e zuciyarsa na masa zafi.
A daidai k’ofan fita daga sashen ya had’u da Alhaji Gimba na shigowa. Alhaji Gimba na ganinsa ya fad’ad’a murmushinsa. Bai damu ba idan Haidar bai gaishesa ba. Shi dai bazai tab’a cire hope Akan Haidar d’in ba. Alhaji Gimba yaci gaba da fad’in “Congratulations to you and your team. Naji dadin wann al’amari kuma inada yak’inin company bazatayi danasanin zab’en gwarazan da zasu jagoranci wann aiki irinku ba..I trust you and your team.” Ya d’anyi fasali kafin yaci gaba “Wann aikin kampani ne so ina shawartanka kar ka bari wani matsala da kake dashi tsakaninka da mahaifinka yasa kai ma aikin rik’on sakainan kashi ko ka yanke hukunci cikin fushi. Na yarda da Kai amma tunasarwa yanada kyau. The company’s future relies on your hand Aliyu. And we have high expectations of you.. Let’s set our differences aside so we can reach our common goal. Ko dan mu ba ma abokan Adawa kunya.” Ya k’arashe murmushi saman fuskarsa.
Tinda ya soma magana Haidar da hannayensa ke sakale cikin aljihu yake dubansa lokaci guda yana nazarinsa “Trust me, it’s just a matter of time before we find out who the real traitor is.”
Murmushi Alhaji Gimba ya kuma sakar masa kafin yai nuni da parlorn “Baringa mahaifinka. Have a good evening.” Ya fad’i yana mai shigewa cikin parlorn.
Lumshe idanunsa kad’an Haidar yai had’ida furzar da huci “Fake life fake people. Everything around this family is fake nothing is real.” Lokaci guda yasa kai ya shige cikin sassarfa zuciyarsa na masa wani irin k’una.
Ya fito daga sashen mahaifinsa kenan ya hangi k’atuwar mota ta shigo cikin gidan shak’e da kaya ta nufi nasa b’angaren. Yabi motar da kallo kafin ya nufi hanyar sashen nasa. Nan ya hangi Mommy da Anisa sai nuna ma masu interior d’in yanda zasu jera kayayyakin suke. Ga tsaffin Kayan duka an fito dasu.
Yai tsaye yana dubansu da mamaki. Can Anisa ta hangosa. Sai ta matso kusan Mommy tai mata rad’a a kunne “He’s here Mommy.”
Mommy ta d’ago tana tambayan wane kenan. Ganin Haidar ya sanyata fad’ad’a murmushinta. Ta k’arasa da sauri ta kamo hannunsa “Haidar my son, today is the happiest day of my life.. An d’aura aurenka yau Haidar.”
Sai yaji abun banbarakwai. Shi ya ma mance da wani batun aure da yarjejeniya. Wani irin duba yake mata irin na da gaske take.? Da gaske auren suka masa sabida son zuciya irin nasu.
Mommy taci gaba da fad’in “Wann shine Mafarin had’in kan ahalinmu da yardar Ubangiji. Cikin ikon Allah komai zai daidaita.” Bakinta ya gaza rufuwa har mamaki Anisa take yanda Mommy ke matuk’ar d’aukin wann aure. Taci gaba da nuna ma Haidar kayayyakin “Look duba kaga. I know you have high taste so I ordered everything to your taste.” Ta saka hannu ta tallafo fuskarsa “Yau d’in ina Jin na cika wani gurbi na zama uwa a gareka D’ana. Burin ko wata uwa kenan taga D’anta yakaiga cikan kamala.”
K’ok’arin cire hannun Mommy daga fuskarsa yake Jin tana wasu irin sunbatu “Mommy will you please stop.! Enough of this drama.” Ya dakatar da ita kafin yaci gaba “Quit the act already! Stop acting like you care.. Like you are responsible.! Like you are doing your motherly duties wad’anda kika makara bakiyi ba tun a baya. It doesn’t suit you at all Mommy.!” Ya k’arashe jijiyoyinsa har fitowa suke.
“Haidar.” Ta ambaci sunansa kaman mai shirin kuka.
Dakatar da ita ya kumayi “Mommy you and I both know ba auren tsakani da Allah bane. Ba don ci gaban rayuwana matsayina na d’anki kikai ba. You are doing all this for your own advantage.” Ya d’anyi fasali “Mommy my day is bad enough, thanks to my Dad. bazan bari ki k’ara mun wani akai ba.!” Yana ida fad’in haka yasa kai ya fice daga gidan a gaggauce.
Jiki a matuk’ar sanyaye Mommy ta juyo. Anisa ta k’araso ta taddata.
“Mommy seems like ke kad’ai kike son auren nan a gidan nan. Shin bazaki hak’ura da auren nan ba kawai tinda Wanda akayi dominsa baya so. Kawai ki d’aga waya ki kira Ammi ki sanar da ita an fasa tin kafin a kawo matar cikin gidan nan. Dan na tabbata wann auren ba mai d’orewa bane.”
Mommy ta harereta “Ke dalla rufe mun baki. Bansan shashanci, Wann aure da kika gani mutuwa ce kawai zata raba matar da Aliyu. Idan kinga auren ya Mutu ki tabbata matar ta Mutu ne.!” Tana ida fad’in haka tasa kai ta shige tana neman layin Asshe dan Jin mai ake ciki.
Anisa ta tab’e baki tana mamakin wann irin al’amari.
**
Kano…
Dik maganganun da Hilal keyi cikin motar ba sauraronsa take ba. Hasalima bazata iya tantance mai yake cewa ba da za’a tambayeta. Damuwarta kawai su isa ga ‘yaruwarta tai k’ok’arin shawo kanta su gudu tinda babu idon Umma. K’aran bud’e gate ne ya dawo da ita daga duniyar tunanin da tai nisa ciki. Zuciyarta sai tsinkewa yake tana addu’an Allah ya bata ikon shawo kan Addarta Ummul cikin sauk’i. Tana ji a jikinta wann aure babu wani alheri cikinsa.
Hilal yana Ida parking tai saurin kama handle tana kokawan bud’ewa.
Ya tsareta da idanu “Easy kar ki balla min marfin mota bayan kin b’ata min da tab’o..”
Bata amsa shi ba dan bata da lokacinsa. Tana Jin sanda motar ta fita a lock tai saurin bud’ewa ta fito. Sauri sauri ta nufi cikin gidan har kaman zatai tuntub’e.
Hilal ya bita da kallo had’ida tab’e bakinsa kad’an kafin ya nufi bangarensa.
A daidai mashigar gidan Khulsum taji ance da ita “dakata..!”
Cak taja ta tsaya sakamon muryar taji ya dakatar da ita.
Umma ta gani ta tsaya tayi k’ebebe rik’e da kunkumi tana duban Khulsum d’in.
“Umma..!” Khulsum ta fad’i mamaki kwance saman fuskarta.
Umma ta jinjina kai “K’warai ni ce nan.!” Tai maganar tana kuma k’obarewa bakin k’ofa.
“Umma.. Me kike a nan..?” Khulsum ta tambaya cikeda mamaki.
“Ke zan tambaya mai kike a nan..? Wani munafuncin ne Ya kawoki..? Awho kinzo ne ki kashe mata auren Tun kan ta tare ko..?”
Mamaki Ya hana Khulsum furta koda kalma sai duban Umma da take. Da k’yar ta iya furta “Umma a ina uwar amarya ta tab’a yima ‘yarta rakiya d’akin miji.. Haba Umma fisabilillahi, bayan auren rashin galihu da kikai ma ‘Yaruwata shine saida kikai mata rakiya. Shin baki gudun maganganun mutanen ne Umma..?”
“Allah tsari gatari da saran shuka.. Aure auren gata nai ma d’iyata irin Wanda kaf lungun ku ba’a tab’a samu ba. Ki koma ki tambayi ‘yan lungun naku kiji wani irin aure akaima Ummul. Aure na bajinta auren da na tabbata bazaa daina kambabasa ana labarinsa ba. Ke harta da masu shigewa saida suka shaida.. Kuma ban rako Ummul ba saida zuciyata ta tabbatar min zaki iya zuwa… Gashi kaw kin zo d’in kaman yanda nai tunani.. Zuwanki na sani ba Alheri bane.. Dan na tabbata kaman yanda nai alwashin aurar da Ummulkhairi haka Kikai alwashin lalata mata aure. Tinda ba yau kika saba korar mata maza ba. .Ke ni fah akan auren nan wllhi Khulsum sai mu raba gari dake.!” Ta k’arashe tana sakin huci.
Khulsum ta jinina kai a hankali tana duban mahaifiyar tata “Umma kin kaw ji abinda kike fad’i..?” Tai maganar cikin rawar murya.
“K’waraiii kuwa.. Wllhi sai kiyi yamma nai gabas muddin kikai yunk’urin lalata auren ‘Yaruwarki Wanda Babu kalan fad’i tashi da banyi ba dan ya tabbata. Tsaf zan yafeki Khulsum muddin kika kawo mishkila.”
Hawaye suka gangaro ma Khulsum “A’a Umma. Abun bai tsanani haka ba. Har kullum ke mahaifiyata ce banida tamkar ke.. Bazan b’ata auren Adda Ummul ba.. Na Miki alk’awari Umma.. Amma dan Allah alfarma d’aya nake so kimin..”
Yanda Umma ke dubanta a dak’ile sai ka rantse ma wata tsararta take jifa hararan.
“Umma dan Allah ki bari nai Sallama da Adda.. Na rok’eki..!” Ta k’arashe tana had’e tafukan hannayenta biyu waje guda alamun rok’o.
Umma bata amsa ba sai k’ofan waje da ta shiga nuna mata “Fita.. Wuce ki fita.. Wllhi idan ni na haifeki kuma na haifi Ummul bazakiyi Sallama da ita ba.. Shige ki fita nace kar na bud’e idanuna na ganki..”
Khulsum ta dubi mahaifiyarta da mamaki “Umma kin Sallamanin kenan..?”
“Idan haka kika d’auka.. Kije duniya da yawa..”
Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un Khulsum ke nanatawa cikin zuciyarta. Wai mahaifiya ke fad’a ma ‘yarta haka.. Anya Umma ita ta haifesu..? Anya akwai iyaye irin Umma..? Anya mutum zai d’auki D’ah a cikinsa tsawon watanni tara Ya haifosa duniya yaci gaba da rainonsa rana tsaka Ya k’isa sabida wani buri nasa na duniya..? Anya akwai irin wad’ann iyayen..? A iya saninta harta dabba yasan dadin d’ansa. Meyasa tasu mahaifiyar ta zama haka..? Shin dama ana jarabtan bawa da iyayensa..? Ashe ba iyaye bane kawai ake jarabtarsu da yaransu ashe Yaran ma akan jarabcesu da nasu iyayen.. Ta lumshe idanunta hawaye suka gangaro mata. A hankali take ja da baya hawaye na gangaro mata tana duban Umma.
Umma kaw bayan ta tabbata Khulsum ta fice cikin gidan ta koma harda ce ma maigadi idan wann yarinyar ta dawo ya koreta.
Suna zaune parlor itada Asshe bayan k’awayen Asshe Sun watse. Asshe ta dubi Umma tace “Yarinyar nan taki akwai fitina, sam batai halin ‘yaruwarta Ummul ba.”
Umma ta tab’e baki “Ai mutane biyu ne mabanbanta halayya. Fitinanniya ce ga taurin kai tsiya da masifa yacce kikaga k’anwar Ubanta. Bata rage ma Dije komai a d’abi’a ba.”
Asshe tace “Wacece Dije..?”
Kafin Umma ta kaiga bata amsa suka sinkayo wata murya daga k’ofa “Ni ce nan Dije k’anwa d’aya tilo ga Isubu..!”
Daram.! Daram!! Daram.!!!
Haka k’irjin Umma ya bada wann sauti cikin sakan guda.
SameenaAleeyou📚*AUREN WATA UKU.!*
*20*
©️Sameena Aleeyou…✍🏽*
Inna Dije taci gaba da takowa cikin parlorn. Yayinda Umma keta faman k’ifta idanu, zuciyarta bata daina tsinkewa ba.
Daidai saitin Umma Inna Dije ta k’araso ta tsaya. Umma ta kasa d’ago idanu ta dubi Dije.
“Dole ki kasa d’ago idanu ki dubeni Suwaiba. Idan Har kinada sauran kunya bazaki dago ki dubeni ba..”
Umma ta soma girgiza kai hawaye na zubo mata Har lokacin bata d’ago idanunta ba.
Fincikota Dije tai tana fad’in “zo nan.. Yau sai naji uban da ya tsaya miki a garin nan Suwaiba har kike buga wasanki da sunan wauta da shashancin gangan..!”
Ta kuma janyo Umma a zafafe. Hajja Asshe tai saurin raba tsakaninsu “Inaga dai ya kamata ayi komai gaban idona.!” Ta k’arashe tana duban Inna Dije data cakumo Umma.
Umma ta k’walalo idanu waje Jin zaa kwance mata zani gaban Hajiya Asshe. Ta had’e hannu biyu waje guda alamun rok’o “A’a Dije.. Kar kiyi haka.. Wann matsala ne da ya danganci ahali..”
Inna Dije ta murmusa tana duban Umma “Dole kice matsala ce da ya danganci ahali Suwaiba.. Sabida bakiso a bankad’o sirrikanki gaban sirakanki ko..? Kin masu rufa rufa kin aura masu ‘yarki da lak’anin mahaifinki ya fad’a kanta cewa ita d’in bazata tab’a aure ba.. Sabida wani babban Dalili Wanda nida ke muka binne hakan tinda jimawa..!”
Umma ta zaro idanu waje tana duban Inna Dije da Jin wani batu Wanda ta kasa fahimtar ina ya dosa..
Asshe ma idanu waje take duban Umma
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 64