amana.! Is it a crime to trust someone.? Ta ya haka zai kasance.?! Yaci gaba da girgiza Kai yana ganin abun tamkar dai a mafarki ne. Not his Hisham. His best friend. Mutumin da ya aminta dashi sama da kowa a duniya ciki harda iyayensa kafin alak’arsa dasu ta gyaru. Ya lumshe idanunsa yana mai kuma Waresu tar a daidai lokacin da ya shigo Company. Securities na gaishesa ko zarafin amsa su bai ba ya tambayesu ko Hisham yazo Company. Nan suke sanar dashi bai shigo ba gaba d’aya ranan. Haidar ya jinjina Kai kafin yasa kai ya nufi cikin building d’in kaman zai kifa k’asa. Duk Wanda ya gansa basa hanya kawai yake. Yanayi ne da zasuce Sun jima basu gansa cikin irinta ba. Ko a zamanin baya da yake samun sab’ani da mahaifinsa bai shiga cikin irin yanayin da suka gansa. Kai tsaye Office d’in Hisham ya nufa. Ya soma takowa cikin Office d’in yana tuno farkon had’uwarsu da Hisham. Motarsa ce ta tsaya masa a wajen gari Hisham helped him out daga nan suka k’ulla zumunci nan Hisham yake sanar dashi Neman aiki ya kawosa Abuja and he’s an architect. Haidar yace ai kuwa he’s in the right place, because his Dad owns a Construction Company dan haka yasa ma ransa tamkar ya Sami gurbin aiki k’ark’ashin Kampanin mahaifinsa mai suna Maitama Builders. Nan take yai going through takardun Hisham ya kuma ga ya cancanta hakan yasa babu b’ata lokaci Hisham ya Sami gurbin aiki a kampanin. Hisham yai ta murna harda hawayen murna yana fad’in Allah ne ya amsa kokensu shida mahaifyarsa ya turo Haidar cikin rayuwarsa dan ya jima yana neman aiki bai samu ba. Shi maraya ne mahaifinsa ya rasu tun yana k’aramin yaro. Mahaifyarsa ta sha wahala sosai sann tayi d’awainiya dashi tun yana k’aramin yaro. Ya gode Allah yanzu zai share mata hawayenta da izinin Allah. Tabbas bazai tab’a mance halaccin Haidar gareshi ba. Ire iren kalaman Hisham kenan Wanda yasa a ko Yaushe yake ma Haidar nasiha gameda bin iyaye. Hisham tolerates Haidar a cewarsa bayan Hajjarsa baida Wanda ya fiye masa Haidar. Wanda hakan yasa suka k’ulla abota sosai har ta zarce ta koma amintaka. Haidar ya yarda dashi dan hardly ka gansa da wani aboki idan ba Hisham d’in ba.
Haidar ya numfasa had’ida d’aukan wani k’aramin hotonsu da aka saka cikin k’aramin frame suna tsaye a wani construction site aka musu hoton ba tareda saninsu ba. Cikin shiga irinta k’wararrun magina. Idan ka gansu gwanin ban sha’awa. Hisham yaji dad’in hoton ya k’aunaci hoton wanda hakan yasa ya aje hoton cikin frame ya jera shi a Office d’insa. Idanunsa Sun kuma rine sosai yake duban hoton yana tuno duk rayuwarsu tare daki daki da tsawon lokacin da Hisham ya kwashe yana munafurtansa.
Wayar salulansa Ya Ciro yakai kan number d’in Hisham yana kallo. Yana ji kaman ya daki wayar lambar ta tarwatse. Lokaci guda yai dialing zuciyarsa naci gaba da tafarfasa.
Bugu biyu a na uku Hisham Ya d’aga duk a birkice yake tambayar Haidar yaushe ya dawo k’asan.
Haidar yace “I just landed. Ya naji muryarka haka.? Is everything all right.? Nazo company baka nan..?”
Hisham ya kuma Shafa goshinsa yana furzar da huci. Bai sani ba sai ji yai bakinsa na furta “Ina Teaching hospital can Bauchi.. Na kawo ‘Yaruwata”
‘Traitor.!’ Haidar ya furta a zuciyarsa yana fidda huci. A fili kuwa karfin hali yai Yace “ ‘Yaruwarka kuma.. Dama kanada ‘yaruwa.? I thought Hajja ka kai..?” Yana maganar yana k’ok’arin dannar kansa dan bazai ba ma Hisham wani k’ofa da zai gane yasan meke faruwa ba har sai ya isa yanda yake Ya cafkesa da hannayensa. Sai dunk’ule hannunsa guda yake yana murzawa sabida yanda zuciyarsa ke masa zafi.
Hisham Ya rintse ido yana tuhumar kansa meyasa zaice ma Haidar ‘yaruwarsa Ya kawo. Tsaban a birkice yake baisan yayi sub’utan baki ya furta haka ba. Ya rintse idanunsa da k’arfi ya soma kame kame “Eh.. Eh.. ‘Yaruwa ta nesa ce.. Sun rabu da mijinta tana zaune gaban Hajja toh ga haihuwa yazo mata.. Tin safe muke asibiti Har yanzu bata sauk’a ba..”
“Haihuwa.?!” Haidar yace zuciyarsa na tsnanta bugu yana tuna cewa da Anisa Tai Ummul na wajen Mahaifiyar Hisham kuma ta shiga watan haihuwarta.
Haidar bai k’arasa sauraren Hisham ba ya fice yana huci idanunsa suna kuma rinewa kaman zai kifa k’asa.. Mota Ya shige Ya nufi hanyar airport. Yana tafe hanya wayan Sadis ya shigo masa. Nan Sadis d’in ke sanar dashi jirgin Bauchi ta riga ta cika kuma gab take da tashi.
“I don’t care Sadis.! Just make sure a space is created for me in that plane. I must fly to Bauchi right this instant.” Yana ida fad’in haka Ya katse kiran yana ji kaman bazai isa ba.
**
Bauchi,
A can TH kuwa b’angaren masu haihuwa hannayen Ummul rik’e cikin na Hajja ta gama galabaita sosai. Hawaye take tana girgiza kai take duban Hajja “Ki kira min Umma dan Allah.. Dan Allah Ki kaini wajensu.. Ki kaini naga Abba na.. Ki kaini na nemi yafiyarsu Hajja.. Mutuwa zanyi.. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un.. Dan Allah kar ki barni na Mutu a nan ban nemi yafiyar iyayena ba.. Hajja ki kaini wajen Umma da Abba.. Bazan iya ba mutuwa zanyi.. Abba na tuba.. Umma dan Allah ku yafe mun.. Nayi kuskuren kaurace muku.. Na tapka kuskure ku yafe mun dan Allah.!” Ta kuma kankame hannun Hajja. Cikin rarrabewar kalamai take furta “Dan.. Allah.. Kice.. Su yafe mun.. Ki sanar dasu ina k’aunarsu.. Ki rok’ar min iyaye na gafara Hajja ko zan samu sassauci da rahamar Ubangiji..” Ta kuma rintse idanunta “Bayana.. Hajja.. Wayyo Umma na ki yafe min.. Bayana.!” Jikinta ya kuma sakewa nishin ma ya daina fita. Hajja nata k’ok’arin kwantar mata da hankali tana fad’in “Bazaki Mutu ba in sha Allah Ummul.. Zaki haihu lafiya da izinin Allah.. Zaki rok’i Umma da Abba yafiya da bakinki. Ta kuma ficewa a kid’ime kiran likitocin dan sun sanar da ita basuga wani complication da zai iya hana Ummul din haihuwa da kanta ba Shiyasa basuyi yunk’urin yin cs ba.
Hisham Ya nufo Hajja a birkice yana tambayarta ko Ummul ta haihu. Hajja ta girgiza kai tana fad’in Likitocin zata kira dan ita kanta lamarin Ya soma bata tsoro. Gwara kawai suzo idan ma aiki zasu mata sai su mata amma ta riga ta galabaita.
Hisham Ya shafe fuskarsa yana girgiza kai yake fad’in “No.. No Hajja.. Please tell me Ummul is going to make it alive.. I can’t lose Ummul.. I lost her once bazan bari ta sake kufce min ba..!” Ya kuma dafe Kansa a kidime kaman sabon kamun hauka yake fad’in “Wai ina Doctors din suke ne…! Which kind of incompetency is this.. Meyasa tuntuni ma basu cire cikin ba.. I don’t give a damn wether the child survives or not matuk’a Ummul zata kasance cikin k’oshin lafiya ban damu a rasa wann jaririn ba.!”
Cikin tsananin shock Hajja ke dubansa. Ta sani Ya tab’a son Ummul kafin tayi aure amma maganganun da ke fita daga bakinsa ya haifar mata da tsoro da rud’ani.. Gani Tai kaman na Hisham dinta ba.. Kaman wani ne daban take gani tsaye gabanta. Kasancewar halinda ta baro Ummul din yasa ta janye jiki ta shige bata bi ta kansa ba. Amma tsoron da mamakin bai bar jikinta ba.
Bayan shud’ewan wani lokaci Hajja da likitoci guda biyu suka nufi kan Ummul yayinda Hisham yaci gaba da safa da marwa daga waje yakai Mari Ya Kai gauro yana fad’in bazai rasata ba. Yana tsaka da safa da marwansa yaji wata murya daga bayansa ta ambaci “SHADOW.!”
Zuciyar Hisham Tai wani irin tsinkewa. Yaji kaman an aje masa guduma. Jinin jinka kaw tamkar Ya tsaya Cak Ya daina circulating. Da kyar ya soma k’ok’arin karkato jikinsa. Juyowan da Hisham zai yayi ido hud’u da Haidar cikin yanayin da bazai iya fasaltawa ba.!
*Toh fah.! Yau dai ga Shadow ga Haidar ga kuma Ummul akan gwiwa. Ko Ya za’a wanye.?*
SameenaAleeyou📚*AUREN WATA UKU..!*
*54*
*©️Sameena Aleeyou…✍🏽*
Girgiza Kai Hisham yake a hankali ganin yanda Haidar ke fidda wani irin huci yana dubansa da rinannun idanunsa. Yasan duk yanda akai Anisa must have screwed up kaman dai ko yaushe. A hankali Hisham ya soma takowa ga Haidar Wanda har lokacin dubansa kurum yake without uttering a word. Hisham ya soma ware hannayensa a hankali tamkar mai shirin yin surrender “Whatever it is that’s in your mind, I hope you listen to me first.. I know by now your cousin Anisa ta gama b’ata sunana a idonka.. Haidar nasan matarka Ummulkhair even before you met her.. Saidai bansan itace matar taka ba har sai bayan da kuka rabu a lokacin da na fahimci ‘Yaruwarka Anisa na neman rayuwarta..!” Ya dan numfasa yayinda Haidar ke dubansa fuskarsa na kuma rinewa. Yana kuma dunkule hannuwansa zuciyarsa naci gaba da zogi had’ida tafarfasa.
Hisham yaci gaba “Haidar ko mai Anisa ta sanar dakai ka sani nayi ne to protect you, your wife and your child of course.. Anisa zata kashesu kaman yanda ta kashe Dareen.. Anisa is a maniac Haidar.. Zata iya aiwatar da komai dan cikan burinta.. Dan ta mallakeka she can go to any extent… She ran Dareen over while pregnant with your child.. I fear the same would happen to Ummulkhair da abinda ke cikinta Shiyasa na barta wajen da zata zama safe from any danger.. Yanda Anisa bazata cimmata cikin sauk’i ta kashesu ita da abinda ke cikinta kaman yanda ta kashe Dareen da abinda ke cikinta..!” Bai Kai aya ba yaji sauk’an naushi a bakinsa Wanda saida ya kaisa k’asa. Haidar ya saka duka hannayensa biyu ya cakumosa yana fidda huci fad’in “The nerve of you.. Bastard.! Are you that shameless.! Tell me.. Tell me who are you..?! Ka fad’a mun waye Kai waye Kai..? Mai ya kawoka cikin rayuwana..? Answer me.!!!” Ya k’arashe yana kuma shak’e Hisham kaman zai aikasa lahira. Huci Haidar yaci gaba da yi idanunsa suna kuma rinewa, yaci gaba da jinjina Kai yana duban Hisham “I couldn’t care less if it’s about business. All the scandals.. Alla the damages and losses..!” Yaci gaba da jinjina Kai yana fitar da huci “But you’ve crossed the line The moment you involved my wife you Bastard.!” Ya k’arashe yana kuma kaima Hisham naushi a hanci. Ya kuma cakumo wuyan Hisham d’in yana wani irin huci “How dare you look at my wife.! How dare you hear her voice.! How dare you go near my wife you Bastard.!” Ya k’arashe yana gwaran hancin Hisham da goshinsa saida ya kaisa k’asa.
Kasancewar wajen Amenity ward ne yasa ba zirga zirgan mutane sosai.
Da kyar Hisham ke nishi daga nan yanda yake duk’e k’asa . Haidar ta kuma cakumosa Ya mik’ar sa tsaye. Ruwa ne ke tsartsafowa ta ko wani mahudan gashi dake jikin Haidar. “How could you..! I gave you everything..My trust..! My friendship… I gave you job.. I even called you brother..!”
Da kyar Hisham ke iya furta “Ha.. Haidar wllhi ka yarda dani.. Ka yarda dani this is all part of Anisa’s plan. The moment da naji shirinta akanka sai na fahimci kaida ahalinka kuna cikin had’ari sabida ita… Ita da bakinta ta fad’a tayi attempting kashe Ummul lokacin da ta zuba mata guba cikin turare.. Nasan baka mance wancan lokacin ba.. Kaga idan Har tayi attempting kasheta tun a fari ashe rayuwar Ummulkhair harma da jaririnka dake cikinta kusan ‘Yaruwarka Anisa na cikin grave danger.. Anisa ita ta aikata maka komai kuma I’m very sure bakinta d’aya Dareen and that’s why she killed Dareen.. Because sunyi tarayya itada Dareen wajen son abu guda. And that’s you.! “
Cikin d’acin rai Haidar ya kuma Kai ma bakinsa naushi hawaye har tsartsafowa daga idonsa yake. Ya shak’e Hisham sosai yana fad’in sai ya kashesa tinda yaje kusan matarsa. Dariya Hisham Ya soma yana girgiza kai “But she’s no longer your wife Haidar..! Saurara Kaji da kunnuwanka..!”
Daidai nan yaji sautin kukan jariri ya daki dodon kunnensa ya karad’e wajen gaba d’aya. Cak Haidar ya dakata da abinda yake.. Yayinda Hisham yaci gaba da murmusawa jini na bin bakinsa da hancinsa “That must be your newborn baby, Haidar.. You ended that marriage yourself nine months back.. Haihuwar D’anka ya tabbatar da cewa Ummulkhair ta gama Aurenka Haidar.!”
Duban Hisham Haidar yake kaman mutum mutumi.. A hankali ya sake wuyan rigar Hisham Ya d’ago yana duban matar dake tunk’aro yanda suke ga jariri sabon haihuwa rungume cikin hannunta.. Idonta naga jaririn dake hannunta.. Murmushi saman fuskarta take furta “Hisham.. Ummul ta sauk’a lafiya.. Alhamdulillahi..!” Birki tai ma kalamanta sakamakon hango fuskar Hisham da tai jina jina.. Sam bata kula da matashin dake tsaye gefen Hisham yana kallon jaririn dake rungume cikin hannunta cikin wane irin yanayi ba. A yayinda Hajja ke nufo D’anta dake duk’e wajen fuskarsa na d’igar da jini a daidai wann lokacin Haidar ke nufota yana duban nasa D’an dake rik’e cikin hannunta..
K’arasowar da Hajja zatai sai ganin hannun wani matashi tai yana k’ok’arin amsar jaririn dake hannunta. Hannayen kawai ta kalla zuciyarta yai wani irin yankewa. Zuciyarta na bugawa take duban hannayen Har zuwa fuskarsa yayinda Haidar ke duban jaririn. Cikin rawar murya yake ke furta “My child..!”
Cak Hajja ta d’ago tana duban matashin. Take zuciyarta yai wani irin yankewa dan ba kowa ta hango ba face Aliyu Maitama da kuma matarsa Kwaise. Tai tsaye Cak ba tareda ta iya wani katab’us ba har saida Haidar ya amshi jaririn cikin hannunsa.
Ya k’ura ma jaririn ido yanajin k’walla na ciko idonsa. Kyakkyawan yaro mai kamanninsa sak kaman an tsaga kara. Ya sumbaci yaron yana lumshe idanunsa. Har lokacin ko motsi Hajja ta kasa yayinda Haidar ya nufi k’ofan da yaga matar ta fito rungume da yaron ba tareda ya kuma bi takan Hisham da mahaifiyarsa ba.
A hankali Haidar ya tura k’ofan D’akin. Can ya hangota tana kwance saman gadon asibiti, idanunta a lumshe suke tamkar na mai bacci.
A hankali ya furta “Khairy..!” Sann ya soma takowa gareta jaririn na mak’ale cikin hannunsa.
Ya k’araso har gaban gadon da take kwance. Ya k’ura mata ido sosai yana dubanta. Fuskarta yayi fayau dukda d’an jiki da ta k’ara Wanda bai wuce yanada nasaba da haihuwan da tai ba. It’s been nine good months rabonsa da ita.. Ji yai k’afafunsa na barazanar gaza d’aukarsa. Ya zauna saman kujeran dake gefen gadon. Har lokacin rungume yake da jaririn idanunsa naga Ummul wacce ke kwance tamkar mai bacci. Siririn hawaye Ya gangaro masa. Ashe da ciki ya saketa.. Ta tafi tayi rainon cikin ita kad’ai Har ta haifi jaririnsu ba tareda shi ba.. He wasn’t there for her.. She did it all alone by herself.. Bazai tab’a yafe ma Hisham ba da Ya b’oye Khairy tsawon lokacin nan. He denied him the right to know Khairy was carrying his child koda ace Ya saketa. Bazai taba gajiyawa ba har sai Hisham Ya biya abubuwan da Ya aikata masa. Ya sauk’e idanunsa kan jaririn dake cikin hannunsa. Ya k’ura masa ido sosai idon yaron a bude suke yana iya kallon cikin k’wayan idon yaron. A fili ya furta “My Son… Dad is here.. I won’t allow that Maniac to go near you or your Mom. Dad is here to protect you both.” Ya k’arashe yana sumbatan goshin yaron. Lokaci guda Ya maida dubansa ga Ummul dake kwance har lokacin idanunta a lumshe suke.
Cikin wane irin yanayi ya soma furta “I’m sorry.. I’m sorry I wasn’t there for you.. I’m sorry you had to go through all this alone..” Yaci gaba da jinjina Kai yana dubanta “I should never have.. divorced you.. I should never have gave that maniac a chance to go near you. This is all my fault.. Amma, ina so ki sani… I.. I never stopped loving you Khairy.. Ko lokacin da na furta Miki kalmar saki ban daina sonki ba.. You are always right here.. In my heart.!” Ya k’arashe yana nuni da b’angaren k’irjinsa.
**
A can waje kuwa gaba d’aya hankalin Hajja a tashe yake. Ganin Haidar ya haifar mata da shiga wani irin yanayi Wanda yasa har ta kasa tambayan Hisham mai ya samu fuskarsa.
Abinka da gogagge sai ya nufo Hajja yana fad’in “Hajja akwai abubuwa da dama da ya kamata ku sani daga ke har Ummul. Na b’oye muku ne to save Ummulkhair.. Sabida Rayuwarta dake cikin had’ari.”
Dubansa kurum Hajja take ba tareda ta iya furta koda kalma ba.
Hisham yaci gaba “Ummul abokin aiki na ne tsohon mijinta Hajja.!”
Kaman sauk’an aradu haka taji maganar. Ta d’ago a daskare tana duban Hisham cikin tsananin shock. Jiri Ya kusan kaita k’asa.. Ta girgiza kai kad’an “Ka.. Ka ka ce.. Wann wann mutumin abokin aikinka ne..?” Ta k’arashe hannunta na tsananin rawa kaman yanda muryarta ke rawa. Ta ci gana da nuni da hanyar da Haidar yabi.
Hisham yaci gaba da jinjina Kai “He’s not only my colleague Hajja.. He’s my Friend.. Haidar is my friend.. Sann Haidar shine mijin Ummul.. Ban jima da sanin hakan ba. Haidar Ya tareni da fad’a Hajja kafin ya saurara yaji daga gareni.. Akwai abubuwa da dama da Ya kamata Haidar Ya fahimcesu. Wasu mata sunyi tarayya wajen soyayyarsa sann Sun tarwatsa rayuwarsa.. Ni taimakon Abokina kawai nake Hajja amma bai fahimta ba… Hajja Haidar is a good person.. I can’t let those two women ruin him..” Ya k’arashe cikeda nuna tsantsan damuwa.
Gaba d’aya Hajja a birkice take.. Ta kasa yarda da abinda takeji. Ta Ya haka zai kasance.. Ta Ya ‘yanuwan suka kasance abokan juna.. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un.. K’iris Ya rage bata zube k’asa ba sabida jiri da Ya kusa kada ita. Cikin sauri Hisham Ya tallafota yana tambayarta lafiya meke faruwa da ita. Bata iya amsa Hisham ba. Hasalima bata kuma fahimtar meke wakana ba. Bata san ina take zuwa ba. Ita dai kawai ji take k’afafunta suna motsawa. K’arshen tikatiki tik.. Bata da sauran wajen gudu.. Ya zama wajabi ta dakata ta fuskanci bayanta. Ta Ya zata soma fuskantar Aliyu Maitama da ahalinsa..? Ta Ya zata soma sanar da tilon D’anta ga asalinsa da ta jima tana b’oye masa.? Ta Ya zata iya sanar dashi abokinsa D’anuwansa ne da suka had’a uba d’aya.? Ta Ya zata iya karya alk’awarin da ta d’aukar ma kanta cewa bazata tab’a jingina D’anta da Aliyu Maitama ba.?
Ji Tai Hisham Ya kamo hannunta yana girgiza kai yake tambayarta “Hajja dan Allah meke faruwa ne wai..? Hajja meke damunki..? Gaba d’aya kin sauya lokaci guda. Tin sanda kika ga tsohon mijin Ummul.. Ina nufin Abokina Haidar.? Hajja kin sanshi ne.?”
Ta d’ago ta dubesa cikin wane irin yanayi “Hisham. Kaini gida..!” Ta furta da kyar.
Hisham yai mata duban mamaki “Gida kuma Hajja? Hajja Ummul fah tana asibitin nan ba’a sallameta ba.”
Sai taji kuka na zuwa mata gadan gadan ga shivering da jikinta keyi kaman an saka mata electric shock “Hisham ka tashi ka kaini gida ina so na kasance ni kad’ai.. Ka kaini gida Hisham.!”
Hisham ya jinjina Kai ya kamo hannayenta ya mik’arta tsaye “Shikenan Hajjah.. Zan kaiki gida.. Just calm down.. Breath.! Inhale exhale.!” Ya fad’i cikin k’ok’arinsa na calming dinta. Ya rik’o hannunta suka nufi mota hawaye naci gaba da gangaro mata.
Hisham ya kauda fuska gefe ya saki wata muguwar murmushi a zuciyarsa yace 'I'll never let you win Haidar.! Musamman yanzu da na tabbata Ummul ta gama aurenka. Ka tsaya kaga yanda zan mallaketa cikin sauk’i. Ka tsaya kaga yanda ‘Yaruwarka Anisa zata d’auki nauyin zunubaina.! I know exactly how to cover all my tracks.. You just wait and see.!’ Ya k’arashe yana sakin muguwar murmushin nan nasa.
*
Yaron yana rik'e cikin hannunsa yana jijjigasa waya manne kunnensa na hagu "Yes Sadis, ka shigo asibitin.? Don't let him escape.! Ka tabbata bai kufce maka ba Sadis."
Daga d'aya b'angaren Sadis ya kaste Haidar da fad'in "Ga plate number dinsa ina gani..Positive. I can see his car clearly yana fitowa daga asibitin.. It's him."
Haidar yaci gaba da jinjina Kai yana jijjiga yaron dake cikin hannunsa “Good Sadis.! Make sure that Bastard doesn’t escape. I’ll call the cops now.” Daga haka katse kiran yai.
Daidai lokacin Ummul ta fara motsa jikinta alamun tana yunk’urin farkawa. Still idanunta a lumshe suke.. Cikin wane irin kasaltacciyar murya take furta “Umm.. Umma.. Umma na.. Umma na..!”
Haidar ya k’ura mata ido ba tareda ya furta komai ba. Ga jaririn rungume cikin hannunsa.
A hankali ta soma bud’e idonta da suka matuk’ar nauyi har ta sauk’e su tar akan Haidar. Sosai ta razana da ganinsa, alamun tsoro Ya nuna saman fuskarta.. Bata ma kula da jaririn dake rik’e cikin hannunsa ba. Ta soma k’ok’arin matsawa baya daga nan yanda take kwance saman gadon tana fad’in “Mai.. Mai kake a nan..? Ya akai kasan ina nan..?”
Idanunsa suna kuma rinewa zuwa ja yaci ga a da takowa zuwa gaban gadon nata “How could you..? How could you have done this Khairy..? How could you have kept something so serious like this..? Ta ya zaki b’oye mun abu mai girma irin wann.? What kind of punishment is this..?” Ya numfasa zuciyarsa na kuma masa zogi. Sai ya sassauta murya kad’an still yana iya sauraran tsananin b’acin rai cikin muryar nasa “Khairy.. How could you have trusted that imbecile..? Ki fad’a mun saceki yayi..?! Answer me now.!” Ya k’arashe cikin dacin rai Har hawaye na gangaro masa.
Kuka ta fashe dashi itama. Ta soma k’ok’arin saukowa daga saman gado. Ta nufi k’ofa tana kuka dukda tangadi da take. Haidar yai sauri ya tare k’ofan.
Ta d’ago ta dubeshi cikin kuka. Da kyar ta iya furta “Ni Ka.. Ka k’yaleni na wuce.. Na tsaneka bani son ganinka.. Ka..!” Sai ta duk’a a wajen tana kuka sosai.
Shima duk’awan yai gabanta sirirn hawaye na gangaro mishi ga yaron na kuka cikin hannunsa. Cikin rawar murya mai cikeda sanyi wann karon yake furta “No Khairy.. I can’t… I won’t let you go..! How.. Can I let you go when you are so close to me..? I went insane looking for you, you know.! Ta ya zan bari ki sake guje mun.. Just how Khairy..?!”
Haidar na hawaye Ummu na kuka haka ma jaririnsu kuka yake.
Ta dubeshi ta dubi jaririn ba tareda ta daina kukan ba. Saima sadda idonta k’asa da Tai tana mai ci gaba da kukan.
Har cikin bargo da tsokarsa yake jin rad’ad’in kukan nata. Ji yake kaman Ya janyota cikin jikinsa Ya lallasheta amma baida wann ikon a halin yanzu.. Ya tuna months back batada masauk’i sai cikin jikinsa. He couldn’t believe shi da Kansa ya furta ma Khairy kalman saki. Kalman da gashi Ya haifar masu da barrier tsakaninsu. Ya lumshe idonsa yana jin zuciyarsa na masa ciwo… A hankali Ya Ware idonsa sanda yaji kukanta na k’aruwa “Please don’t cry… Ki daina kukan nan haka..!” Yaci gaba da dubanta yana jinjina kai “I’ll kill for every tear..”
Batace da shi komai ba sann bata dubesa ba bata kuma fasa zubda hawaye ba saima abinda Ya k’aru.. A daidai nan yaron Ya kuma calla k’ara daga nan cikin hannun Haidar. Ya mik’e tsaye yaci gaba da jijjiga yaron yana fad’in “See.. You are making him cry as well..” Yaci gaba da jijjiga yaron yana fad’in “Oh c’mon champ.. hush now.. Don’t cry..” Yaci gaba da jijjiga yaron yana lallashinsa a haka Ummul ke satan kallonsu. Har yaron yai shiru.. Wayar Haidar ta soma ruri.. Yai saurin cirowa daga aljihunsa. mommy ce mai kira.
Ya d’aga kiran cikin sauri yana ci gaba da jijjiga yaron da d’aya hannun.
Ummul tana jinsa yana waya da Mommy yana sanar da ita tayi jika cikin tsananin farin ciki maras misaltuwa.
Haidar yaci gaba “You have a grandson Mommy.. A beautiful Grandson.”
Daga d’aya b’angaren Mommy sai ta fashe da kukan farin ciki. Fad’i take gata nan zata shigo jirgi ta taho Bauchi. Haidar yace ta bari idan Allah yakai rai da safe sai su taho gaba d’aya da Daddy.
Mommy taci gaba da girgiza Kai tana fad’in “No Haidar.. I can’t wait till morning.. I can’t wait to see my grandson..” Cikin muryar kuka mai gauraye da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 51 Chapter of 64