ciresa da tai yana tsaka da shan nono.
Haidar ya amshesa ya izasa bisa kafad’a “Ki same mu a mota.. Kar ki bata lokaci.!” Daga haka ficewa yai cikin sassarfa.
Mamaki da tsoro suka cikata. Haidar ya juye mata tashi daya. Tasan bai iya fushi ba amma mai ya bata masa rai irin haka. Toh kodai ta masa laifi ne.? Bata ida tunanin ba ta sinkayo sautin horn kaman zai daga gidan alamun ita yake jira.
Kuka ta fashe dashi tana mai zira mayafinta.
Koda ta nufo k’asa hankulan su Khulsum bai ta b’angaren da take. Hakan yasa ta nufi k’ofa tana danne kukanta.
Khulsum da ta hangeta tai saurin mik’ewa ta nufeta tana ambaton sunanta.
Bata iya amsa ta ba sai kawai tasa Kai ta shige cikin sauri wani kukan na kuma zuwa mata.
Hakan ya janyo hankulan sauran ‘yanuwan . Wann ta kalli wann wancan ta kalli wann gidan dai da alama ba lafiya. Aunty Asshe ta fice tana kuka.. Su Mommy sun fice hankula tashe yanzu ga Ummul ta fito tana kuka.
Badia ta rapka tagumi tana fad’in “Oh ni Badi’atu yau meke faruwa ne a gidan nan.?”
Salima tace “Gaskiya ba lafiya.. Toh amma meke faruwa ne.?”
Badia ta tsaida wata ma’aikaciyar gidan tana tambayarta meke faruwa a gidan.
Matar ta girgiza kai tace “Naji securities da suke gate suna cewa yaron Alhaji da zai dawo daga SouthAfrica aka kidnapping together with his wife Anisa.”
Azeema ta saki baki tace “Anisa dai.?” Sai ta rangad’a guda tana fad’in Alhamdulillah an gama taro lafiya ba Anisa dan ta iso kafin a gama taron da ta wargaza komai.
Salima ta girgiza Kai tace “Kedai bazakiyi hankali ba Azeema. An ce Miki an sace mutane kina shewa. Toh gashi bata zo d’in ba amma taro ya tashi ba dad’i. Ki gaya min hankalin waye ke kwance.?”
Azeema ta tabe baki tace “Wllhi Anty Salima dan dai baki zo bane lokacin bikin tariyar Ummul da ke kanki sai kin tsani wann anisar.”
Salima ta girgiza Kai “Toh yanzu dai duk ba wann ba. Mu had’a hannaye mu tayasu da addu’a Ubangiji ya bayyanasu cikin aminci.”
Suka amsa da Ameena gaba d’aya.
**
Koda suka isa gida a d’aki ta k’ule tana share share hawayenta bata bi takansa ba. Har saida ta soma sinkayo kaman muryoyi daga parlorn.
Hilal yaci gaba da girgiza Kai yana duban Haidar “I just don’t get you Haidar.. Kasan bazan iya abinda kake fad’i ba. Anisa ‘Yaruwata ce and she’s been kidnapped.. I can’t just sit back and do nothing.!”
A zafafe Haidar ya katsesa “Well Anisa ita ta jefa kanta cikin mess d’in nan.. I warned her not let that maniac use her.. but what did she do.?She went ahead and married him.. Now she’s trapped. Dama na fad’a amfani kawai zai da ita. Ni na tabbata ba kidnapping dinsu akai ba. Hisham zai iya shirya komai ta yanda Zai looking kaman sace su akai dan ya cimma wani manufa nasa.!”
Hilal yaci gaba da girgiza Kai yana duban Haidar “Ya kake magana kaman ba Nigeria muke ba. Yanda satan mutum ya zama ruwan dare.? Mai zai faru idan real kidnappers ne suka d’auke su.?”
“Tell me akwai abinda zaka iya yi ne idan ma sacesu d’in akai.? Ka fad’a mun zaka iya tracking motar da suka shiga..? Tell me, Did the kidnappers call.? Did they ask for ransom.?” Yaci gaba da girgiza Kai yana duban Hilal “ Babu ko d’aya Wanda hakan yake tabbatar da wasan Hisham ne kawai.! That imbecile is using Anisa as a bait.! I warned her from the very start amma tak’i taji. She thought she could outsmart him.!”
Hilal ya furzar da huci yana girgiza Kai “Kai hakuri brother, a wann b’angaren Nima ban yarda da kai ba.!” Yana ida fad’in haka yasa kai ya fice cikin sauri.
Juyowan da Haidar zai ya hangi Ummul tsaye bayansa tana hawaye. Lokaci guda itama take girgiza kai “Da gaske ne.? Da gaske ne an sace Yaya na Hisham da Anisa.?”
Cikin huci yake furta “Kar ki sake kiran wann D’aniskan Yayanki. He’s nothing to you.!”
Taci gaba da zuban hawaye “Meyasa kake nuna masa k’iyayya irin haka.? Meye ya maka da tsanani.? Shid’in fah D’anuwanka ne.. Kan wani dalili kake masa irin wann kiyayyar.?”
Cikin huci ya juyo yana dubanta “Do you want to know the reason.? Kece Khairy.. That maniac is obsessed with you.! Do you know that.!”
Ta soma girgiza Kai tana dubansa “Baka fahimta bane.. Na san shi tun kafin na aureka amma babu komai tsakaninmu.. Ya taimaka min a wajaje da dama taimakon da bazan tab’a mancewa ba. Shi d’in mutumin kirki ne bai kamata ka masa irin wann mummunar fahimtar ba.!” Cikin kuka take maganar.
Yaci gaba da jinjina kai yana dubanta da idanunsa da suka rine “Ya aikata duka abinda ya aikata Miki ne for a reason. And that’s to win your heart. And he’s doing what he’s doing now for a reason. To separate us.!”
Taci gaba da zuban hawaye tana girgiza Kai “Meyasa kake fad’in haka.?! Meyasa kake furta wani yana sona.! Of all people D’anuwanka.! Ni fah matarka ce.!”
“You too don’t believe me. Do you.?” Ya tambaya yana dubanta cikin sanyin jiki idanunsa na kuma rinewa.
K’arasowa tai kusansa ta kamo hannayensa “My love.. Please don’t misunderstand me.. You are being paranoid for no reason. You are being jealous for no reason.. Hisham is your Brother.. And he’s married to your cousin now.. Hisham bazai taba irin tunanin da Kai kake ba. Shed’an ne kawai yake raya maka haka dan baiso ku samu daidaiton fahimta da D’anuwanka.!”
Murza hannayensa yake yana huci “Kema baki yarda dani ba Khairy..! Kin zab’i ki yarda da wancan banzan sama dani.! Haka ne.?!” Ya k’arashe yana dubanta.
Ta dan furzar da huci zata kuma kamo hannayensa ya dakatar da ita “Get out Khairy..!”
“Amma..!”
“I said get the hell out of my sight.!”
Ummul taci gaba da girgiza Kai tana hawaye “Why do I feel like I don’t know you.! Meyasa bazamu samu daidaiton fahimta ba.?”
“Idan Akan wann banzan ne ni da ke bazamu tab’a samun fahimta ba.!”
Izuwa wann lokacin sosai take hawaye tana dubansa. Cikin murya irinta mai kuka taci gaba “Idan duk abinda kake zargin Hisham dasu gaskiya ne maiyasa bai ida nufinsa akaina ba lokacin da ya samu dama.?! Ya taimaka min a lokacin da ka cika wa’adin AUREN WATA UKU...! Ya bani shelter a lokacin da na fice daga gidanka bansan wajen zuwa ba.! Ya kaini ga mahaifiyarsa a lokacin da na kasa tunk’aran nawa mahaifiyar.!”
“Khairyyy.!” Haidar ya dakatar da ita da fad’in haka har ruwa na fita daga idonsa. Yaci gaba da nunata da yatsa “Kar ki sake maimaita min kalmar AUREN WATA UKU..! Kar ki sake jingina abinda ya faru tsakaninmu da wann D’aniskan.!” Yana ida fad’in haka yasa kai ya fice daga gidan a fusace.
Duk’awa Ummul tai wajen sabon kuka na zuwa mata.
*
Yana ficewa bai zarce ko ina ba sai wajen Sadis.
Sadis ya dan shafi fuskarsa da tafukan hannayensa “Kai ma Daddy uzuri Haidar, Shi har yanzu gani yake yayi failing Hisham as a father. Har yanzu gani yake bai biya Hisham ba.”
Murmushin da yafi Kama da takaici Haidar yai “Growing up as a Maitama has never been easy.. Idan akan wann sunan ne naso ace shi ya girma as Maitama ba ni ba.!”
Sadis ya dan furzar da huci “Amma Maganarka zai iya zama da k’amshin gaskiya Haidar. Hisham zai iya sakawa a sacesu shida Anisa idan duk ya aikata abubuwan da suka faru a company ba tareda an ganosa ba”
Haidar ya jinjina Kai “My point exactly amma cikinsu ba Wanda ya fahimta. Meyasa Hisham ya dage zai cire Anisa daga mess d’in da shi ya jefata ciki.? Idan ba yanada wani babban shiri ba bazai tab’a amincewa ya auri Anisa ba. Ya wuce duk yanda mutum yake tunani.. Amma koma menene shirinsa ka yarda dani Sadis sai na kawo k’arshen k’aryarsa.”
Sadis ya dan furzar da huci “How do you plan to do it.. Ina nufin har yanzu babu wani call ko wani abu mai Kama da haka.”
Jinjina Kai Haidar yake “I don’t know how.. But I’ll surely bring hm down.. ka yarda dani Sadis. Zanyi unmasking Hisham.!” Ya k’arashe yana jinjina Kai alamun tabbatar da kalamansa.
Wayar Sadis ne ya soma ringing. Sai ya d’anyi excusing Kansa ya matsa yana amsa kiran.
Bayan ya gama amsa kiran ya dawo ga Haidar. Ya d’an furzar da huci kad’an yace “That was Azeema. Tambaya take gameda case d’in.. Duk hankulansu a tashe yake.”
Jinjina Kai Haidar yai “Could you do me a favor.”
Sadis ya jinjina Kai “Ina sauraronka.”
Haidar yaci gaba “I’ll stay here tonight.. Ka Kai mata sisters dinta gidan..Tana buk’atar su kusa da ita.”
Jinjina Kai Sadis yai yana fad’in zai k’ira Azeema ya sanar da ita.
**
Washe gari Sadis ke sanar da Haidar ba wani developments gameda case d’in bacewar su Hisham. Har yanzu ba wani k’ira ko wani abu mai Kama da haka daga kidnappers d’in.
Jinjin Kai Haidar yai kad’an “I wonder what that maniac is planning.” Bai Kai aya ba wayarsa ta soma ringing.
Ganin ba suna yasa shi juya wayar cikin hannunsa. Har ta kusa tsinkewa sann ya d’aga.
Cikin wane irin murya mai gauraye da tashin hankali ya sinkayo muryar Hisham yana fad’in “Haidar you need to help me.! Help my wife.. And my unborn child..! Zasu kashe mu.. Dan girman Allah ka basu duk abinda sukai demanding brother.. Please.!”
Girgiza Kai Haidar yake cikeda mamaki dan tuni an katse wayar d’if. Ya soma dialing layin amma bata zuwa.
Sadis ya dubesa “Lafiya.?”
Haidar ya d’ago yana duban Sadis “It was.. Hisham.. I clearly heard his voice Sadis.”
Sadis ya girgiza Kai kad’an “Did he say something.. Maybe abind ya samesu ko yanda suke.?”
Girgiza Kai Haidar yai yana duban Sadis d’in “Cewa yake zasu kashe shi.. Zasu kashe Anisa da unborn child dinsu..”
Sai ya girgiza Kai had’ida sakin murmushin takaici “I knew I was right.. Ba wani abu mai Kama da kidnapping a nan. D’aya ne daga cikin wasannin Hisham. Cewa yake na bama kidnappers d’in whatever they demand.!” Ya mike yana huci “I told you Sadis.. Hisham is playing a game here.! Idan da gaske sacesu akayi meyasa ba’a kira Daddy ba aka kirani.? How does this make sense.?”
Sadis ya girgiza kai “Amma meye demand d’in nasu.?”
Haidar ya girgiza Kai “Ya kashe wayar bai fad’i wani demand ba.”
Kaman jira kaw suke nan wayar Haidar ta kuma ringing da wani layi.
Muryar Anisa ya sinkayo wann karon “Haidar..! Dan Allah kazo ka ceceni.. Zasu kashe ni wllhi.. I’m bleeding already.. Haidar I’m pregnant.!”
“What.!” Ya furta a hankali kafin yace “Anisa don’t let him use you. Just tell me what’s going on.? Ina Hisham ya kaiki..? Meke faruwa.?”
Muryar wani Mutumi ya sinkayo wann karon “Don’t act foolish Engr.! Do not involve anyone in this matter.! Ba ‘yansanda ba ba ahalinka ba. Ba kudin mahaifinka muke nema ba.! Kai kawai muke so ka kawo kanka.! Mun baka less than 24hrs idan baka kawo kanka zuwa adireshin da zamu tura maka ba komai zai iya faruwa da ‘Yaruwarka harma da abinda ke cikinta.!”
Wani irin huci Haidar yake zufa na tsartsafo masa “Ta nan ka b’ullo Hisham.! Haw could you use Anisa as a bait.! Why can’t you confront me coward.! You don’t need to use anyone.!”
“You have less than 24hrs.. Lokacinka ya fara kirgawa daga yanzu.!” Cewar mutumin.
D’if yaji an katse kiran.
“I’m going to end this once and for all.” Cewar Haidar yana mai mik’ewa a zafafe.
Sadis ya taresa “Haidar wait.! Ka dakata. Ya kamata a fara sanar da gida sann ayi reporting ma yansanda. Bazai yuwu ka kai kanka ba dan kawai sun buk’aci haka. For all we know zai iya zama dakwai muggan makamai tareda su.”
Murmushi yai yana jinjina Kai “This is my chance Sadis. Wann shine damata Akan Hisham.!” Ya k’arashe yana mai nufan k’ofa.
Sadis ya kuma taresa “Toh idan kaje sukai trapping d’inka fah.? Burin Hisham ya cika na ganin bayanka. You need to think first Haidar. Kar Kai abu cikin gaggawa.”
Jinjina Kai Haidar yake yana dubansa “I have a plan Sadis. And you will help me in carrying out my plan.! Bazaka sanar da kowa ba musamman ahalina. Idan na buk’aci backup kaida yansandan kunsan yanda zaku sameni.!” Ya k’arashe yana jinjina Kai.
Sadis ma jinjina masa Kai yai kafin suka soma tsara yanda zasu tunk’ari lamarin.
*
Yinin ranan Haidar bai dawo gida ba bai kuma kira ba. Cikin zuban hawaye take duban Addarta Salima bayan Sun keb’e a d’aki. Yayinda Aunty Salima taci gaba “Duka laifin naki ne Ummul. Akan wani dalili zakiyi jayayya da mijinki kan wani daban. Ummul sufah maza ba son jayayya balle ma Akan wani namijin.”
Cikin zuban hawaye Ummul ke girgiza Kai “Aunty Salima ni fah ba jayyaya nake dashi ba. Hisham fah D’anuwansa ne kuma yana auren ‘yaruwarsa Anisa.. Akan wani dalili zai dage Hisham sona yake.? Idan ma fushin ne ni ya kamata nayi. Maimakon yai tunanin yanda zai ceto ‘yanuwansa hannun azzaluman da sukai garkuwa dasu amma zuciyarsa sai ingizasa take Akan Hisham. Mutumin da babu wani abu na sharri da ya tab’a shiga tsakaninsu tun suna a matsayin abokai kafin su fahimci su d’in ‘yanuwan juna ne.”
Sauk’e ajiyan zuciya Salima tai “Yanzu dai addu’a kawai shi zamuyi Allah a bayyanasu cikin aminci ya kuma warware duk wani abinda ya shige duhu.” Ta janyo mata plate din abinci tana fad’in taci abinci haka nan tin Daren jiya bataci komai ba. Yaronta zai buk’aci abinci idan bataci ba shima bazai samu ba. Da lallama Salima ta tasa Ummul gaba kafin ta samu ta saka abinci cikinta.
*
Bayan la’asar Hidar ya shigo gidan da sallama. Yanda ya tadda Duk yanuwan nata suna parlor idan ka d’auke Salima dake kitchen. Ga Baba Ali hannun Azeema. Suka gaisa da sakin fuska. Sann suka masa jajen bacewar su Anisa da addu’an Allah ya bayyanasu. Haidar ya amsa da Ameen yana amsan Baba Ali dake hannun Azeema. Nan yake tambayarsu Khairy fah.? Azeema ta basa amsa d fad’in tana ciki.
Jinjina Kai yai kafin yasa kai ya shige sai wasa yake ma yaron. Saida ya tsaya a k’ofan kitchen suka gaisa da Salima da sakin fuska harda ‘yar zolaya yake mata yau Addar tasu ce da kanta a kitchen. Salima kaw ta d’an murmusa kafin itama ta masa jaje. Da haka ya nufi upstairs wajen Ummul rungume da D’ansa.
Sanda Haidar ya tura k’ofan d’akinta ya tadda tana saman darduma alamun tana sallah.
Ya zauna daga gefe har ta sallame.
Bata juyo ta dubesa ba sann bata ko motsa daga yanda tai sallan ba. Yasan za’a rina.. Ya kwantar da Baba Ali saman gado kafin ya k’araso gareta. Rungumarta yai ta baya yana mai lumshe idanunsa. Itama d’in lumshe idanunta tai hawaye suka gangaro mata.
“Take care of our Son Khairy.. Take care of yourself for me.. I love you both so much.!” Yana ida fad’in haka ya manna mata kiss a cheek dinta kafin ya isa ga Baba Ali daketa cilla k’afafu daga nan saman gado yanda yake kwance. Ya saki murmushi yana duban yaron “Maybe I named you Aliyu for a reason.! Allah ya maka albarka. Son.” Ya k’arashe yana mai sunbatan yaron.
Yai tsaye yana duban Ummul da har lokacin hawaye take “Sadis zaizo ya kaiku gidan Daddy.. Ki kula min da Mommy.. Tell her that I love her.. Kuma ina neman yafiyarta..!”
Ummul tai saurin waigowa tana dubansa ga hawaye na kuma ziraro mata. Shid’in ma ita yake duba. Bata san dalili ba sai taji illahirin jikinta yayi mugun sanyi. Ta nemi kalma d’aya a bakinta ta rasa. Sai taji kaman an d’aure harshenta.. Tanaji tana gani Haidar ya fice ba tareda ta iya furta koda kalma ba. Aiko yana ficewa ta rungumi D’anta ta fashe da wani irin kuka mai ban tausayi.
**
Bayan sun had’u gaba d’aya parlorn Daddy. Mommy, Hajja, Aunty Asshe, Ummul, Hilal.. Harma da Daddyn Kansa.
Daddy ya dubi Sadis da shgowarsa parlorn kenan. Jikin Sadis d’in duk a sanyaye.
“Sadis what’s the meaning of this.? Meye manufarka na tara mu a nan..? Ka fad’a mun kidnappers d’in Sun kira ne.? Did they ask for ransom.? Tell me.. Nawa suka nema.?”
Sadis ya jinjina kansa a hankali “Eh Daddy sun kira.”
Daddy ya juyo ya dubi su Mommy Wanda suma gaba d’aya tashin hankali ya kuma bayyana saman fuskokinsu.
“Ai sai ai gaggawan sanar da jami’an tsaro.. Nawa suka nema.?” Cewar Daddy muryarsa har na hadewa.
Sadis ya girgiza Kai daga nan yanda yake tsaye “Ba kudi suka nema ba Daddy.”
Da mamaki Daddy yace “Ba kudi suka nema ba.. Toh me suka nema.?”
“Haidar..! Haidar suka nema.. Sun kirasa Sun buk’aci kodai yakai musu Kansa kodai su kashe Hisham da Anisa harma da jaririn cikin Anisar. Sann sunce kar ayi gangancin involving jami’an tsaro.”
Girgiza Kai Mommy take zuciyarta na wani irin harbawa yayinda Ummul ta soma ganin parlorn na juya mata.
SameenaAleeyou📚*AUREN WATA UKU..!*
*63*
*©️Sameena Aleeyou…✍🏽*
Ummul bata sake fahimtar komai ba sai tsintar kanta Tai jikin Hajja tana mata fifita saman fuskarta. Take ta soma tuno abinda ke faruwa. Ta tuna irin sallaman da sukai kafin ya tafi.. Sai tana ganin abin kaman ba a zahiri yake faruwa ba.. Ta kasa furta komai ta kasa motsawa Har lokacin bata ida dawowa hayyacinta ba. Tana jin k’irjinta na mata nauyi kaman an aje mata abu mai nauyi. Muryar Mommy ta da soma sinkayowa daga can b’angaren parlorn kasancewar parlor ne mai girma sosai. Hakan Ya kuma tabbatar mata a zahiri abin ke faruwa. Haidar ya kai kansa ma ‘Yantadda. Mommy fad’i take “Engr dan Allah ka dakatar dashi.. Ka dakatar da Aliyu.. Kar Ya kai kansa ma ‘Yantadda.. Wllhi zan bada nawa rayuwar fansar nasa.. Engr I can’t lose my Son.. Bazan iya rasa Haidar ba.. He’s all I have.. You need to stop him please.. Please Engr do Something.. Not our Son please..!”
Saurin rik’ota Daddy yai ya shigar da ita jikinsa yana fad’in “Haba Kwaise ke fah musulma ce Ya kamata ki natsu ki ambaci Allah… Addu’a zamuyi in sha Allah komai zaizo cikin sauk’i.. Zamu bi komai cikin tsanaki.. Babu abinda zai samesu gaba d’aya kinji.!” Yanda yake maganar zaka fahimci k’arfin hali ne kawai amma ba daidai yake ba.
Hilal ma rik’e yake da mahaifyarsa yana k’ok’arin calming dinta.
Gaba d’aya gidan Ya kuma hargitsewa.
Ganin haka yasa Sadis saurin zamewa daga parlorn. Wayar Haidar Ya soma kira yana ‘yan waige waige.
Haidar dake tsaye jikin motarsa yana gyara zaman kwalar rigarsa nan yaga wayar Sadis na shigo masa. Ya d’aga yana tambayarsa Sadis ya ake ciki.
Sadis Ya dan girgiza Kai yana rage muryarsa kad’an “Haidar are you sure about this..? I mean, things are really getting messy here.”
Daga d’aya b’angaren Haidar ya jinjina Kai “There’s no going back Sadis.. I need to do this.. I need to catch Hisham in the act..”
Sadis ya dan furzar da huci “But you are putting me in a difficult situation.. Idan wani abu ya sameka ahalinka zasuga laifina.. Musamman ma Daddy.”
“This is my decision not yours Sadis.. Sun sani idan nai making mind dina bana canzawa.”
Sadis Ya kuma furzar da huci “But.. Are you aware of the danger of what you are doing..? I mean, this look like a suicide.. You should have let the police handle the matter.”
“No Sadis.. This is something I need to do it alone.. Kar ka nuna musu komai sai na isa wajen. I’m hanging up now.!” Daga haka katse kiran yai yana saita shirt button d’insa dake daga wuyar rigar. Wanda a zahiri button ne kawai. Idan ba ka sani ba Sam bazaka kawo ‘yar k’aramar spy camera bace dake nad’e hoto da murya. A fili Ya furta “It is now or neve.!” Lokaci guda Ya shige motarsa ya d’auki hanya.
*
A can cikin daji kuwa iyaka laushi da buguwa Hisham da Anisa sunyi. Tsananin bugu ya haifar ma Anisa bleeding shi kuwa Hisham Har kaman sumewa yai ga k’afafunsa da suka koma tamkar basu motsi. Ruwan sama da Ya soma sauk’a shi ya dawo da Hisham hayyacinsa. Yaci gaba da tari jini na bin goshinsa hancinsa harma da bakinsa. Ya bud’e bakinsa da kyar yana fito da harshensa yana lasan ruwan dake saukowa dan rabonsa da Ya saka wani abu a cikinsa tin jiya da aka kawo su wann daji da tin shigowarsu ba abinda suke karb’a cikinta sai bugu da nau’uka na azaba. Ga mutanen basu ce dasu komai ba sai azabtar dasu da suke. saiko wayar da sukai ma Haidar.
Cikin tsananin jin jiki Hisham ke furtawa da kyar “Have mercy.. Have mercy.. Su waye ku..? Mai kuke nema wajenmu..! Look, mahaifina attajiri ne.. ku fad’i ko nawa kuke nema.. I.. I mean whatever amount kuke so.. Mahaifina zai baku.. Amma dan Allah ku kyalemu mu tafi haka..!”
Gardin dake tsaye kusan kan Hisham ya buga masa k’asar bindiga akai nan jini yaci gaba da fita daga sassan jikin Hisham. Ya saki k’aran azaba sanda mutumin ya kuma buga masa wani abu kaman guduma a sangalalin k’afafunsa. Lokaci guda ya manna masa shocking wire gashi dama cikin cakwab’i na ruwa yake kwance shame shame nan Jikin Hisham ya soma vibrating yana sakin wani irin gurnani na azaba.
Anisa kaw cikin jin jiki take fad’in “Ku taimaka min.. Ku taimakeni zan Mutu.. Wayyo Allah na.. Wayyo Ammi.. Na shiga uku.. Mara na ciwo yake mun.. Zan m… Zan mutu..!” Bata Kai aya ba taji an buga mata wani abu kan cikin Wanda Ya sanyata sakin k’aran azaba siririn jini na kuma bin k’afafunta..
Hisham Ya waiga a galabaice yana duban Anisa ga jini dake bin k’afafunta. Cikin wane irin yanayi yake furta “No.. No please.. Not my child.. She’s pregnant.. Please let her go.. Don’t kill my child.. Please spare my child.!”
Wata murya suka sinkayo tana fad’in “You should have thought about this a lokacin da kuka kashe nawa D’an.!”
Zuciyar Hisham Tai wani irin tsinkewa.. A hankali ta furta “DAREEN..!”
Dareen taci gaba da tura wheelchair din da take zaune bisa har ta k’araso yanda Hisham ke kwance tamkar Wanda yai paralyze.
Jikin Anisa Ya d’auki rawa daga nan yanda take kwance shame shame.. Ta soma k’ok’arin jada baya cikin tsananin tsoro tana cije keb’e sabida azaba. Har lokacin jikinta karkarwa yake tamkar wacce taga fatalwa.
Dareen ta dubeta sai ta shek’e da dariya “Ina zakije Anisa..? Tsoro kike kinga fatalwa.? Kun zata Kun kashe Dareen koh..? Kun zata Dareen ta tafi bazata dawo ba ko.? Sabida Kun cika marassa kunya harda zuwa ku aure juna.?!” Sai ta kuma darawa “But you two look perfect together..! Ku biyun Kun dace da juna.!”
Cikin jin jiki Anisa ke tamke ido tana girgiza kai lokaci guda take furta “Dan girman Allah kiyi hakuri Dareen..! Wllhi ba abinda kike tunani bane.. Ban auri Hisham dan ina son kasancewa dashi ba..! Wllhi he tricked me too..! He betrayed me kaman yanda yaci amanarki.. Na amince da Aurensa ne dan na kawo k’arshen yaudararsa da fuska bayinsa.. Cikin da kika gani jikina ma wllhi fyade Ya mun bada son raina bane..!” Bata kai aya ba taji sauk’an Mari maiji da lafiya a fuskarta Wanda Ya k’ara had’a mata jini da majina.
Dareen taci gaba da huci tana duban Anisa “Sa’anki d’aya Anisa ni mace ce da bata yarda aci zarafin wata mace ta hanyar fyade ba.! Because I believe babu macen da ta cancanci aci zarafinta ta hanyar fyade komin munin halinta.. Ba don haka ba da wad’ann k’artan zansa suyita sukuwa akanki sai tsinannen dake cikinki Ya fita fit.! Amma da nau’ukan azaba sai na ciresa kafin Haidar ya iso nan.!” Dareen ta kuma bud’e murya tace “Kelly.!” Take wann k’aton Ya k’araso gabanta yana risinawa. Nan tabasa umarni da Ya zana Anisa da murd’add’iyar bulalar dake hannunsa.
Kan kace me Kelly ya shiga nade bulalar dake hannunsa Ya shiga zuge Anisa dashi tana sakin k’aran azaba dan ko motsawa bata iyayi.
Hisham Ya zaro ido waje daga nan yanda yake karb’an nasa hukuncin. Cikin tsananin rawar murya Hisham ke fad’in “Please don’t Dareen.. Don’t kill my child please..! Anisa is pregnant with my child.. She’s three months pregnant.. Ina son cikin nan fiyeda komai a duniya Dareen..
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 61 Chapter of 64