nata tunanin damuwar halinda Ummul ke ciki ne ke d’awainiya da Haidar d’in tsaban abinda ta raya ma ranta kenan. Zuciyarta sai wani irin k’una yake mata tana ci gaba da addu’an Allah yasa a fito masu da gawan Ummul kowa ya huta.
A can gidan Haidar d’in kuwa hankalin Dareen yayi dubu Ya tashi. Haidar d’inta ne ke ignoring calls dinta yau. Mutumin da ko important meeting yake zai excusing kansa ya d’aga kiranta musamamn da taga an d’auki lokaci bai returning call din ba. Ita kad’ai sai safa da Marwa take tana jin zuciyarta na mata d’aci. Tana a haka taga wayan Shadow na shigo mata.
SameenaAleeyou📚*AUREN WATA UKU..!*
*31*
*©️Sameena Aleeyou…✍🏽*
Tana d’aga kiran ta sinkayo muryarsa daga d’aya b’angaren “I heard that you’re back in the country.. Ya akai banji hakan daga bakinki ba..?”
Shiru batace dashi komai ba sai hucin da take dan gaba d’aya zuciyarta a cunkushe take tinda ta kasa samun Haidar a waya. Muryar Shadow ya kuma dakan dodon kunnenta “Dareen are you sure you are not hiding something from me.?”
“Toh mai zan b’oye maka. Yes mun dawo amma ban samu chance na sanar dakai hakan ba. After all, jiya ne kawai muka dawo k’asar. Is not as if na shafe kwanaki ne da dawowa bakaji daga gareni ba.”
Katseta yai “Don’t you dare take me for a fool. I know you so well. Na sani idan kina shirya wani abun.. Let me warn you Dareen. Idan kika shirya wani abu a bayan ido na believe me zaki d’and’ani kud’arki.”
Tai murmushin takaici “Is that a threat.?”
Murmushin shima yai “You know me so well. I don’t keep people around with threats. Idan har zanyi abu lokaci d’aya nakeyi ke kinfi kowa sanin hakan.”
Yai gyaran murya kafin yaci gaba “Ina Haidar..?”
Ta kuma furzar da huci “How would I know.? Ya fita bai sanar Dani ba.”
“You should know Dareen. Because that’s what you are there for. Ban ajiyeki tareda dashi ba just for you to have fun with him kin fahimta.”
“Oh excuse me! You don’t own me.. And you are not the one calling the shots here. Ni ce nake rayuwa da Haidar a halin yanzu… Barazana kawai kake da kake cewa tulun da aka d’aure kurwar Haidar aka shata layin k’iyayya tsakaninsa da iyayensa na wajenka.. Kuma bari kaji from now henceforth bazan bari ka cutar da Haidar ba. Babban kuskuren da ka tapka shine da ka min sanadin shiga rayuwarsa. A halin yanzu Haidar dani are one.. He’s my husband da nake sonsa da duka zuciyata.. Bazan bari kai ko wani ya cutar dashi ba. So if I were you zan maida makaman yak’ina.”
Murmushi yai daga d’aya b’angaren “Haka kika ce.?!”
Bata bashi amsa ba sai sakin huci da take.
Ya kuma murmusawa “Fine. Zamu gani tsakanin mu biyun Who owns Haidar..!” Yana Ida fad’in haka ya katse kiran.
Dareen taci gaba da kallon wayar tana sakin huci.
**
A can asibiti kaw suna nan zaune jiran tsammani Mommy ta dubi Anisa wacce dama saura su biyu ne zaune wajen “Idan likitocin Sun fito kimin magana.”
Jinjina mata kai Anisa tai had’ida amsawa. Tabi bayan Mommy da kallo wacce hankalinta ke ga wayar salularta. Mommy tana ficewa wani corridor d’in ta soma waya da ‘yaruwarta Asshe. Nan take sanar da Asshe abinda ke faruwa.
Baki har na rawa Asshe ke tambayarta “Haidar..? Haidar fah..? Ina Haidar Haidar yana lafiya.?” Dan ita duk a tunaninta aikin gama ne Ya riga Ya gama tsakanin Haidar da Ummul.
Mommy ta girgiza Kai kad’an “Asshe Haidar lafiya yake. Hasalima shi yai driving namu to hospital. Amma meyasa kike tambayar lafiyar sa.?”
Sauk’e ajiyan zuciya Asshe tai tana jin gumi da ya tsartsafo mata na bin jikinta yana sauk’a. Lokaci guda tai k’ok’arin saita kanta “Toh amma Aunty Kwaise is possible asirin ne yai aiki. Is possibile amfanin yarinyar ya kare ne. Tinda ita d’in makarin asiri ce.”
Kaman Asshe na ganinta haka Mommy ta girgiza kai “Ta ya hakan zai kasance bayan Haidar shigowarsa gidan kenan. Babu wata alak’a data shiga tsakaninsa da yarinyar. Ko kin mance mai Malam Ya sanar damu. Har sai wata alak’a ta auratayya ta gifta tsakaninsu kafin ta karya asirin.”
Daga d’aya b’angaren Zuciyar Asshe yaci gaba da tsinkewa. Toh ko dai Anisa tayi shashashancinta ne ta bama yarinyar turaren bata zubar ba kaman yanda ta umarceta. Kodai har mai aukuwa ya auku ne ba tareda Kwaise tayi la’akari ba. Wann abu da d’aure kai yake. Toh amma idan Har illan dake jikin yarinyar bai shafi Haidar ba kaman yanda Dije ta sanar da ita. Ta iya yuwa da gaskiyar Suwaiba Dije fansarta kawai take son d’auka kan yarinyar da uwarta tinda gashi yarinyar ce ke kan gargarar mutuwa kaman yanda bokansu Ya sanar dasu ba Haidar ba. Idan Har hakan ta kasance zatafi kowa farin ciki.
Muryar Mommy ya kuma katseta “Kaina Ya k’ulle gaba d’aya Asshe. Shin idan yarinyar nan ta mutu a haka wann na nufin asirin dake jikin D’ana Ya karye ne kokuwa dai Har yanzu da asirin jikinsa.?”
Asshe ta sauk’e ajiyan zuciya tace “Aunty Kwaise bakida tabbacin idan Haidar bai shiga b’angaren yarinyar nan ba a tsakanin shigowarsa gidan. Kinsan abu ne da aka had’a da asiri kuma wann turaren da Malam Ya bamu ya tabbatar mana shi d’in tamkar magnet ne Wanda zai janyo Haidar zuwa gareta..”
Mommy tai Shiru kaman mai nazari sai kuma ta girgiza kai “Asshe al’amarin nada rikitarwa amma inada tabbacin a lokacin da muka tsinceta kwance k’asa kaman gawa a wann lokacin Haidar ya soma sanyata a idonsa.. Tabbas tayi amfani da turaren inada tabbacin hakan amma bana tunanin amfani da turaren kawai zaisa ta Mutu kafin Haidar ya samu kusanci da ita.”
Haidar da isowarsa wajen kenan yai tsaye Cak yana sauraren kalaman Mommy na k’arshe. ‘Turare.? Mutuwa kafin shi Haidar ya samu kusanci da yarinyar.?’ Ya nanata kalaman da yaji Mommy tace cikin zuciyarsa.?
A razane Mommy ta juyo tana dubansa duk a birkice. Kana ganinta kaga maras gaskiya. Tai saurin canza maganar da take cikin wayar tana mai katse kiran. Ta k’ak’aro murmushin da yafi kama da yak’e ta sakar masa “Em.. Em.. Haidar ashe kana nan baka tafi ba..? Na zata ai ka tafi..?”
Ya girgiza mata kai kad’an alamun a’a “Ina nan Mommy.. Naje sallah ne. Why.? Is there something I should know.?” Yai tambayar yana tsareta da idonsa.
Tai saurin girgiza masa kai alamun a’a.
Ya jinjina Kansa a hankali ba tareda ya nuna mata yaji koda word d’aya daga wayan da ta gama ba. Ya d’an ci gaba da takowa kusanta har lokacin Mommy a tsarge take. Haidar na hankalce da ita.
“Any news about the girl’s condition.?” Ya tambaya yana tsare Mommy da ido.
Zuciyarta Ya kuma tsinkewa tana tuhumar kanta mai hakan yake nufi.? Kenan Haidar Ya damu ne da Ummul.?
Bata kai ga samo amsa ba suka hango wani Dr ya fito daga ER d’in. Mommy ce ta nufe shi cikin sauri tana tambayarsa Ya jikin Ummul. Yayinda Anisa ma ta taso daga yanda take zaune ta nufo su.
Haidar kaw daga can yanda yake tsaye yana karantar yanayin Mommy. Meyasa take nuna damuwa gameda yarinyar bayan ga abinda yaji a waya kaman mutuwa take nema ma yarinyar.? Meye nufin Mommy akan yarinyar.? Mecece manufarta na aura masa yarinyar.? Tunani daban daban cikin zucjuarsa. Muryar Dr ya sinkayo yana fad’in “She’s still not out of danger. A halin yanzu bazamu iya bada shaida akan komai ba. Anything can happen.” Ya numfasa kafin ya dubi Mommy “Is she your Daughter.?”
Kafin Mommy ta bada amsa Anisa tai tsulum ta bud’i baki tace “No she’s not her daughter.”
Mommy ta k’ara da “She’s my Son’s wife.. Dr meke faruwa da ita ne.?”
Dr ya d’anyi Jim sai yace “Where’s her husband then.? I’d like to speak with him.”
Mommy ta juyo a d’arare tana duban direction din da Haidar yake. Anisa ma shi take duba tana jira taji yayi rejecting hakan amma sai taji akasin hakan. Abun mamaki muryar Haidar suka sinkaya yana fad’in “I’m here. I am her husband.”
Daga Anisa Har Mommy cikin tsananin shock suke duban Haidar Wanda tuni ya soma takowa kusansu.
Dr yace “May I have a word with you.?”
Haidar ya jinjina masa kai alamun eh “Sure.. After you.” Ya k’arashe yana alama ma likitan da hannu.
Dr ya jinjina masa kai kafin yasa kai ya nufi ofishinsa Haidar na take masa baya. Daga Mommy har Anisa mamaki ya hanasu rufe baki. Babu Wanda ya tasammaci haka daga Haidar. Ko ita kanta Mommy da takeda yak’inin maganin bokansu ka iya tasiri akan Haidar tinda ya sanar dasu turaren da suka ba ma Ummul ta dinga amfani dashi zai janyo Haidar gareta batai zaton abun zaizo da sauk’i haka ba. Kenan Watak’ila d’aukanta da yai cikin hannunta har ya shak’i turaren.? Gaba d’aya kan Mommy ya k’ulle ta rasa fahimtar tunanin da take. Gaba d’aya duk abubuwan dake wakana Sun k’ulle mata kai.
Anisa ta sauk’e ajiyan zuciya a hankali tana tinanin kiran k’awarta Leenah dan sanar da ita halinda ake ciki.
**
Dr ya dubi Haidar kafin yace “Amma kana ina har ake barazanar d’aukar rayuwar matarka..?”
Haidar ya jinjina kai lamun nuna rashin fahimta “Ban fahimceka ba Dr. Barazanar d’aukar rayuwarta kaman yaya.?”
Dr ya jinjina kai yace “Sakamakon gwaje gwajen da mukai mata na gaggawa ya tabbatar cewa she’s being poisoned… Guba ne da ta shak’esa ta numfashi Wanda ya harba huhunta. Most likely cikin turare aka saka guban.”
Haidar yai shiru yana had’a maganganun Likitan da wayan da yaji Mommy nayi. Sai girgiza kai kad’an yace “Turare.?”
Dr ya jinjina kai alamun eh kafin yaci gaba “Irin wann guban akan sanya shi ne cikin wani scent da mutum ke amfani dashi slowly yake lalata lungs d’in mutum ba tareda an ankara ba. Shi irin wann guban anfi amfani dashi ne idan ana so mutum ya samu slow and painful death. Fortunately guban baiyi wani tasiri jikin matarka ba. But we can’t say she’s completely out of danger har sai mun mata minor aiki a lungs d’insa munyi flushing sauran wann guban to prevent it from spreading. Muna buk’atan saka hannunka Shiyasa na buk’aci ganinka a sirrance. Sann abu ne da Ya danganci criminal act kaga dole ai taka tsantsan tinda ba’a tantance waye perpetrator din ba. Koda tana k’ark’ashin kulawarmu a asibiti rayuwarta na cikin had’ari Har sai an kama mutumin dake k’ok’arin ganin bayan rayuwarta.”
Shiru Haidar yai Zuciyarsa Ya kasa aminta da abinda Likitan nan ke fad’i da maganar da yaji Mommy tayi cikin waya. Idan ya had’a maganan Mommy da maganan Likitan nan. The whole thing yanada alak’a da turare kaman yanda yaji Mommy tace sann ta ambaci mutuwa a ciki. Ga turare ga mutuwa. Ga kuma abinda Dr ya sanar dashi cewa anyi poisoning yarinyar ne ta cikin turare. Toh idan Har Mommy kashen yarinyar takeda niyya meyasa ta aura masa ita.? Meyasa zatai poisoning d’inta.? Shin kodai Mommy shi take so tai poisoning shine ta b’ullo ta wann hanyar ta aura masa wann yarinyar ta saka poison din cikin turarenta dan shima ya shak’a su hadu su Mutu gaba d’aya tinda gashi ta matsa sai yazo ya zauna da yarinyar. Shin wann shine shirin Mommy na k’arshe akan shi ta kashe shi ba tareda kowa ya zargeta ba.? Shin har haka Mommy ke masa k’iyayya.? Shin Anya Mommy ita ta haifeshi.? Anya shi d’aya ne daga cikin wann ahalin.? Muryar Likitan ne Ya dawo dashi daga duniyar tunanin da Ya tafi yanda Likitan Ya d’an murmusa dan dik shi a tunaninsa Haidar tunanin aikin da za’ai ma matarsa a lungs yake kar aje a tab’a mata lungs dinta sabida sanin Had’arin irin aiki da Ya danganci organs.
“Look Engr. It’s just a minor surgery. We call it Minimally invasive thoracic surgery.” Ya d’an numfasa kafin yaci gaba “Is a way of performing surgery in the chest through small incisions, without making large cuts in the body, and it does not require spreading apart of the ribs. We use camera and instruments to get to the lung through small incisions in between the ribs. Kaman ma ba’ayi wani aiki ba haka jikin matarka zai zauna. But it’s necessary a dakatar da guban daga yad’uwa cikin jikinta.” Ya k’arashe yana mik’a ma Haidar pen da form.
Haidar ya jinjina kai a hankali kafin ya karba yai signing a yanda aka buk’aci Ya saka hannu. Har lokacin ya kasa yarda da abinda ke faruwa. Ya dubi Dr yace “Dr I want this to stay between us please. Ban jima da dawowa k’asar ba so bansan waye ke farautar rayuwar matata ba da kuma dalilinsa. I need to investigate first.”
Dr ya jinjina masa kai “Bakada matsala Engr. If you excuse me. Zan koma bakin aiki.”
Haidar ya jinjina masa kai kafin suka mik’e a tare suna masabaha cikin mutunta juna.
Sanda Haidar Ya fito ya iske Mommy da Anisa duk sunyi tsuru tsuru alamun suna jiran ba’asi. Babu ya Mommy. Kallo d’aya zaka mata ka fahimci a hargitse take. Ta k’araso da sauri tana tambayarsa Ya jikin Ummul mai Drs suka ce.?
Haidar bai kaiga bata amsa ba dan har lokacin mamakin matar yake Wanda Ya girma ya sani matsayin mahaifiyarsa.
Wayar Mommy ne yai ruri Daddy ke kiranta nan ta matsa gefe tana amsawa dan ita Har ta mance ranan Daddy ke dawowa Nigeria.
Bayan ta Ida wayar ta dawo garesu tana duban Haidar Wanda ya tsareta sosai da ido kaman mai tuhumar ta.
A d’an daburce tace “That was your Dad. Gaba d’aya na mance yana hanya sabida tashin hankalin nan da muka tsinci kanmu ciki. Driver yana hanya zaizo Ya tafi dani.. Yanzu yarinyar ce bansan da waye zamu barta ba.”
Anisa tai karaf tace “I’ll stay here with her.”
Ga mamakinsu muryar Haidar suka sinkayo “No, I’ll stay with her. Kuna iya tafiya Mommy. After all, abinda kike so kenan na dawo na zauna da ita. Right.?” Ya k’arashe yana tsare Mommy da ido.
K’ak’aro murmushi Mommy tai tana jinjina masa kai alamun eh. Yayinda Anisa tai mutuwar tsaye tana kallon abun mamaki wai Haidar zai zauna a asibiti da wann bagidajiyar.? Ikon Allah. Wai meke shirin faruwa ne.? Anya Haidar bai kamu da son bagidajiyar nan a kallon farko ba.? Sai tai saurin girgiza kai alamun a’a tana mai kwaban zuciyarta da irin wann tunani maras kan gado. Abu ne da bazai tab’a faruwa ba ko a mafarki. Haidar would never ever fall for someone like her. Muryar Mommy taji tana fad’in suje driver yana close Daddy na gida na jira. Anisa tabi Mommy jiki duk a mace sai waigowa take tana duban Haidar da Ya tsaya kaida fata wai shi zai zauna wajen Ummul. Gaba d’aya mamaki ya kasa sakin Anisa.
Suna isa gida ta shige d’aki tana faman safa da marwa tana tunanin kiran Leenah dan ta sanar da ita halinda ake ciki. Bata Ida tunanin ba taga wayar Haidar na shigo mata. Zuciyarta yai wani irin tsinkewa sai tana ganin kaman Haidar Ya fahimci cewa ita tai poisoning Ummul. Da kyar ta iya d’aga kiran zuciyarta sai harbawa yake dan tsoro.
Daga d’aya b’angaren Haidar yace “Kina jina. Kije d’akin yarinyar nan ki tattaro mun duk wani perfume dake d’akin ki kawo mun shi asibitin right this instant. Ina jiranki..” Ya k’arada Kar ki bari Mommy ta ganki ko ta fahimci wani abu. Understood.?”
Anisa da zuciyarta bai daina tsinkewa ba a d’an daburce take jinjina kai “Oh ok.. Zanyi yanda kace.”
Jinjina kansa yai kaman tana ganinsa kafin ya k’ara tabbatar mata da yana jiranta yanzu yanzu. Daga haka katse kiran yai Anisa kaw gijif ta zauna cikin kujera shikenan asirinta Ya tonu Dr ya sanar da Haidar guba aka saka ma Ummul cikin turare. Yanzu mai zatai..? Taje ta fasa turaren ne ko ta kai masa ne.? Amma idan ta kai masa ta kama kanta ne.. A fili ta furta “Oh no Neesa.. This is not happening. You screwed up again.!” Ta kuma rintse idonta tana tunanin abin yi. Cikin sauri ta d’ago wayarta . Jikinta har na wani irin kyarma ta shiga neman layin Leenah dan samun mafita.
Leenah tana zaune taga kiran Anisa na shigo mata. Ta saki murmushi a hankali kafin ta furta “My stupid friend is calling again.” Ta kuma sakin murmushi kafin ta d’aga wayar.
A birkice Anisa ta soma fad’in “Leenah komai Ya lalace.. Our plan didn’t succeed.. I’m afraid I messed up everything again..!”
“Girl calm down..! Just… What are you trying to tell me..?” Leenah tace cikin dakatar da Anisa.
A tak’aice Anisa ta bama Leenah labarin duk abinda ke faruwa Har kawo yanzu da Haidar Ya bata tax na kawo masa duka turaren da suke d’akin Ummul. Anisa ta k’arada “Leenah what if he he suspects me.. What if he finds out about the truth cewa ni ce nan na zuba poison din..?”
Leenah ta rausayar da idonta “Here you are being paranoid again Neesa. Ta ya zai zargeki idan ba kece kika basa k’ofa ba. Base on abinda kika ce. Idan har Haidar ya baki tax na kai masa turaren hakan na nufin Ya yarda dake ne.”
Anisa ta katseta “Nifa Leenah mafita na kiraki ki bani ba wai kimin narrating abinda na gama baki labari ba. What if I destroy the perfume..?”
Murmushi Leenah tai “Idan kikai destroying turaren shine kin basa room na suspecting d’inki… You know what Neesa, You always call me a moron. But you are the one acting foolish here. Idan har kika lalata turaren nan no doubt Haidar zai zargeki. Idan kuma ya zargeki ki tabbata sunana bai fito ba. Sabida nida kike gani inada burin aure da samun family of my own bana mafarkin karasa rayuwata a jail.” Ta numfasa “But wait.. A yanda kika bani labari Haidar yace kar ki bari mahaifiyarsa yasan kin kai masa turaren.”
Anisa ta jinina kai alamun eh kaman Leenah na ganinta kafin Leenah taci gaba “Then let him suspect his mother.. Incriminate her. After all, kin sanar dani turaren da kika zuba poison din ma Ummul ciki turaren da Mommy ta baki ki bata ne kika canza da wani. Ya zo gidan sauk’I Anisa. Mahaifiyarsa itace ta bada wann turaren mai guba aka zuba ma matarsa ciki.!”
Dummm.! Haka k’irjin Anisa ya buga. Leenah fah cewa take tai incriminating Mommy. Mahaifiyar Haidar..?
A hankali Anisa ta soma girgiza kai…
SameenaAleeyou📚*AUREN WATA UKU..!*
*32*
*©️Sameena Aleeyou…✍🏽*
Anisa taci gaba da girgiza Kai tana duban wayan. Mommy fah.? Ta ya zata soma d’aura ma Mommy laifi.? Bayan kasancewar ta mahaifiyar Haidar ita d’in fah ‘yaruwa take ga mahaifiyarta. Idan Abu ya lalace ba rasa Haidar kawai zatayi ba harda zumuntar iyayenta zata b’ata. Amma mai zatayi..? Ita kad’ai tana sak’awa da warwarewa ta kuma kiran Leenah dan ta gaza samun mafita.
Leenah ta rausayar da ido tace “Haba Neesa ya kike abu kaman wata bagidajiya.”
“Ban kiraki just for you to insult the hell out of me ba Leenah. Na fad’a Miki hujjojina if things go wrong. It will definitely be the end of me Leenah..!”
Leenah ta kuma rausayar da ido irin yanda Anisa take kaman dai Anisa na kallon ta “Toh banda abinki Anisa. Abun nan fah a bayyane take turaren da mahaifiyarsa ta ba ma matarsa akwai poison ciki ke meye naki a ciki.? Idan akwai wacce za’a zarga bazai wuce Hajiya Kwaise Maitama ba. Unless kuma zaki b’ullo ta wani hanyar kisan yanda zakiyi ki kutsa cikin d’akin da Ummul take ki k’arasata amma fah wann yafi had’ari Anisa because you would easily get caught. Hanya d’aya shine ki kyale mahaifyarsa ta d’auki laifin nan because he already grows suspicious of her idan har zaice ki aiwatar da Abu ba tareda saninta ba. Kuma kinsan me matar nan fah mahaifyarsa ce he would forgive her, definitely. Even if she’s convicted sabida ita d’in mahaifiyarsa ce amma ke fah kika kuskura kika bari ya kamaki kashinki ya bushe Neesa ba hannun Haidar kawai ba harda hannun uwarsa.”
Anisa ta jinjina Kai idanunta na kuma k’ek’ashewa “You are absolutely right Girl. After all, Haidar baya son wann auren tai masa. Akwai tarin tanbayoyi da ya kamata yai ma mahaifyarsa.” Ta k’arashe tana sakin murmushin cin nasara. Lokaci guda ta katse kiranta da Leenah ta soma shirin fita. Nan taga wayar Amminta na shigo mata.
Ta rausayar da ido kafin ta d’aga kiran mahaifiyarta “Yes Ammi. I guess labari ya isa miki.” Tace tana kuma juya ido.
Daga d’aya b’angaren Asshe tace “Da uban wa kiketa waya ina nemanki..?”
Anisa ta kuma juya ido “Abinda kika kirani kice kenan kawai Ammi.?”
“Ke bani son shashanci.. Wai meke faruwa ne a gidan Aunt d’inki da banji daga gareki ba. Ko kin mance na barki a can ne matsayin ido na. Ki sanar Dani meke faruwa tsakanin Haidar da yarinyar can. Shin kin bata wann turaren ne da nace ki zubar.?”
Anisa ta murmusa “Of course ban bata ba Ammi..Kuma na canza turaren kaman yanda kika umarceni.. Amma saidai..”
Zuciyar Asshe yaci gaba da tsinkewa tinda tasan kalan shashancin ‘yar tata “Amma me Anisa..? Meye kika aiwatar ba tareda sanina ba. C’mon tell me.. Meye kika aiwatar.?”
Juya ido Anisa ta kumayi a hasale ta katseta “Nayi poisoning turaren da na canza mata dashi..” Ta juya ido tana jan tsaki “She’s like a cockroach Ammi. Duk irin tuggun da nake k’ulla mata taki mutuwa kaman dai kyankyaso.!”
K’iris ya rage Asshe bata saki wayarta ba. Baki na rawa take furta “Anisa kece kika zuba guba ma mutum..?Anisa waye ya aikeki.. Are you that dumb.? Bance Miki ki bar min komai ba zan kula da komai..? Bance miki kar ki yanke wani hukunci on your own ba.? Anisa kanki Kalau zakiyi kisan Kai kan namijin da baisan kinayi ba.?”
Tsaki Anisa tai “There you go again Ammi. Very soon nida Haidar zamuyi aure as soon as wann makirar is out of the picture. And please do me a favour Ammi. Duk abinda zaki ji ko ki gani naki ido.” Tana Ida fad’in haka ta katse wayan. Asshe na k’ok’arin dakatar da ita amma inaa tuni ta kashe.
Tuni Anisa tayi kaman yanda Haidar ya umarceta. Sanda ta kawo masa turarukan asibiti sai ta dubesa da mamaki “Amma me zakayi da turare a asibiti.? Kodai Ummul d’in ce ke so.. Amma idan itace ke son a kawo mata definitely zai kasance wann ne.” Ta k’arashe tana juya kwalban turaren cikin hannunta ga damuwa saman fuskarta kai kace zallan tausayin Ummul din ke d’awainiya da ita.
Haidar ya tsareta sosai da ido sai ya girgiza Kai kad’an “Meyasa kikace haka.?”
“Because it’s her favourite.” Ta dan murmusa cikeda makirci tana nuni da tausayi sann taci gaba “Mommy ce musamman ta bata turaren nan. Ummul tana son turaren sosai. Allah sarki Allah ya bata lafiya. At first bama wani jituwa amma daga baya I have become fond of her sabida tanada zuciya mai kyau. Kowa yana sonta a gidan especially Mommy.” Ta k’arashe tana share guntun hawaye da ya gangaro mata.
Ba wai yana sauraron surutan da Anisa ke masa bane tinda yaji key points din da yake son ji ya daina gane mai take cewa sabida ta cika masa kunnuwa.
Dakatar da ita yai da fad’in “You can go now. And don’t say a word to Mommy. Are we clear.?”
Anisa ta jinjina masa Kai tana mai tabbatar masa bazata sanar da Mommy komai ba. Bai kuma bi ta kanta ba yasa Kai yai shigewarsa. Anisa tabi bayansa da kallo yanda ya shige hannunsa rik’eda turarukan cikin dan jaka.
Murmushi ta saki dan ta tabbata ko gwaji akai aka gano turare mai d’auke da guba ciki Mommy ce zata rufta. Sann ne zata b’ata sunan Ummul a wajen Mommy dan ta tabbata idan har aka d’aura ma Mommy laifi zata tsani Ummul ne taji ta fita akanta. Zatai amfani da wann daman ta cire ma Mommy son Ummul cikin zuciyarta tinda dama ita kad’ai ke son wann jarababben aure. Zuciyarta wasai ta dauki hanyar gida.
**
Tsaye Haidar yai gaban gadon da Ummul ke kwance bayan an fito da ita daga surgery. Yai mata k’uri yana dubanta. Tanbayoyi da dama cikin zuciyarsa. Cikin zuciyarsa yake jero tanbayoyin da baida amsoshinsu ‘Who are you..? Maiyasa Mommy zata farauci rayuwarki.? Shin Mommy ta kawoki ne dan ki zame
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 27 Chapter of 64