Share this page
the charges against me..? Zaki janye k’aran dake kaina..?” Saurin girgiza Kai Ummul tai “A’a Mommy dama babu wani k’ara.. Dan Allah kar ki fad’i haka.. Ina Jin kaman laifi na ne da aka ajeki nan… Kiyi hak’uri banzo da wuri na fiddake ba Mommy..!” Ta k’arashe cikin rawar murya. Murmushi Mommy ta kuma yi tana mai rik’e hannayen Ummul cikin nata sosai “Baki mun komai ba Ummul face alkhairi… Just like your name.. Ke d’in alKhairi ce.!” A hankali Ummul ta sadda idanunta k’asa. Allah sarki sai ta soma tuna kalaman da Mama da yaranta harma da mutanen unguwa ke jifanta dashi wani sa’in harda nata mahaifiyar cewa sunan bai kamaceta ba babu wani alheri tattare da ita sai akasin sa. Mommy takai dubanta ga b’angaren Haidar Wanda ke tareda ‘yansanda ga lawyer d’in Mommy ya iso suna kula da al’amarin. Ko kallo Mommy bata ishesa ba. Sanda ya k’araso yanda suke Ummul kawai ya duba fuska a matuk’ar tsare “Let’s go..” Har ya juya zai soma tafiya sai ya kuma juyowa ya dubi Mommy “Your driver will be here to pick you.” Ya maida dubansa ga Ummul “Don’t waste my time.!” Yana ida fad’in haka yasa kai yai shugewarsa cikin sassarfa. Ummul ta bisa da kallo jiki a sanyaye sai kuma ta juyo ta dubi Mommy. Jinjina mata Kai Mommy tai murmushin k’arfin hali saman fuskarta “Just go. Go with your husband.. Don’t worry about me I’ll be fine.. Ya k’ira driver zai zo ya d’auke ni. Tashi kije kinji. Allah ya tsareku yayi maku albarka.” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta. Jiki a sanyaye Ummul ta mik’e. Mommy ta bita da kallo zuciyarta na mata sanyi. Ficewar su Ummul da kad’an ta hangi Daddy na shigowa. Sosai mamaki ya cika Mommy ganin Daddy yana shigowa. Toh mai ya kawosa.? Ta zaci zai rabu da ita kaman yanda ta basa zab’i. Ta zaci zai zab’i Kasuwancinsa da reputation d’insa sama da ita da D’anta da a kullum yake ikirarin basuda wani amfani cikin rayuwarsa. Take kuma zuciyarta ta soma raya mata toh kodai zuwa yai ya tabbata ya yanke sauran alak’arsa dake na har abada.? Kodai zuwa yai ya tabbata bazaki koma gidansa ba daga nan.? Dukda bugun zuciya da tunanin ya haifar mata hakan bai hanata kauda fuska tai kaman bataga zuwan Daddy ba. Ya k’araso yana mai gyaran murya. Dan ya tabbata taga zuwansa amma tai biris dashi. “Barrister called….. and told me you are free now.” Ya fad’i daga nan yanda yake tsaye. Ta kaiakito da kyar tana dubansa, bata ce komai ba sai ta kuma kauda fuska. Daddy ya had’iyi abinda ya tsaya masa “Shall we go now.?” Ya fad’i a hankali. Bata tashi ba sai ta girgiza kai “Haidar ya kirawo driver na zaizo ya d’auke ni..” Da mamaki Daddy ke girgiza Kai “Kwaise did you hear yourself.? Ya inace miki ki tashi mu tafi kina ce min Haidar ya kira driver..” Mommy ta kaikaito sosai suna fuskantar juna daga nan yanda take zaune “You shouldn’t be here in the first place.. Kai babban mutum ne dake jagorancin babban kampani.. Bai kamata a ganka a waje irin nan ba. It won’t be good for business and your reputation.” “Enough Kwaise. Nasan ina kalamanki suka dosa.. But this is not the right place to talk about that.. Ki tashi mu tafi gida then we talk..” “Kai hakuri kaje kawai Engr. I don’t want to go with you..” Mommy tace cikin Shan k’amshi. Mamaki ya mugun cika Daddy. Shine Kwaise take turning d’insa down. Ya baro tulin ayyuka tinda Lawyer d’inta ya kirasa ya sanar dashi halin da ake ciki cewa Haidar yazo da matarsa kuma an janye k’ara Akan Mommyn. Yai mugun tsarewa “Haka kika ce.? Fine, ki sani duk direban da yazo ya d’aukeki a bakin aikin shi.” Ta dubesa da mamaki “Zaka koreshi aiki dan yazo d’aukata.?” “Of course I’ll have him fired.” Ya bata amsa Kai tsaye. Mik’ewa tai “Shikenan ni zanje na shiga motan haya..” Ta k’arashe tana mai mik’ewa. Yai saurin dakatar da ita “Umarni nake baki a matsayina na mijinki.. Idan har zaki bawa matar D’anki umarni da tabi mijinta Ashe ke ya kamata ki fara bin umarnin naki mijin.” Yanzu kuma ta nan ya b’ullo.? Kenan ya jima da zuwa station din Akan idonsa tace ma Ummul tabi Haidar. Ba don taso ba sai dan babu yanda ta iya haka tabi bayansa kaman rak’umi da alkala. Har suka iso gida daga ita har Daddy fuskokinsu babu walwala babu mai cewa da kowa komai. Abun sai mamaki yake ba ma Daddy wai Kwaise ke banza dashi irin haka. Matar da tsawon zamanta a gidan tin bayan abinda ya faru batada buri face taga itada D’anta sun samu attention d’insa. Koda suka isa gida basu tadda motan Haidar can ba. Addu’an mommy d’aya Allah yasa ba wani wajen Haidar ya kuma kai Ummul ba. Suna isa Mommy ta bud’e k’ofa ta fice. Daddy yai saurin fitowa had’ida dakatar da ita. “Kwaise what’s with the attitude.? This is not like you..? Ya kike Abu kaman wata yarinya. Abinda bakiyi ba a k’uruciya.. Akan Haidar kike duka wad’ann abubuwan.? Ina Haidar d’in.. Ina yake a nan..? I can’t believe you are risking everything… And even our relationship for him.. D’an da bai damu dake ba.” Juyowa tai tana dubansa, sai tai murmushi wann karon “Did you say our relationship.?” Ta dan kuma girgiza Kai “I thought all you care about is your business.” Cikeda mamaki ya girgiza Kai “Kwaise, amma kinji yanda kike mun magana.?” A hankali ta sadda kanta k’asa “Tuba nake. Allah ya huci zuciyarka Engr…. Idan akwai abinda kake buk’ata kafin ka koma company.. I’ll have it prepared for you..” Dakatar da ita yai da fad’in “No, bani buk’atar komai.!” Yanda yai maganar zaka fahimci ya gama tunzura amma sai Mommy ta murmusa ta dubesa. “Thank you… for driving me home..” Ta k’arashe murmushi saman fuskarta tana mai shigewa. Daddy ya bi bayanta da kallo. Maiyasa ya d’auki shawarin Alhaji Gimba da yace yaje ya dawo da Kwaise gida.. Dan lokacin da Lawyer d’insa ya sanar dashi halin da ake ciki gameda batun case din Mommy suna tare a company da Alhaji Gimba kuma shi ya basa shawarin da yaje ya d’auki iyalinsa ya maidata gida, ya tafi da Kansa shi kad’ansa ko driver bai bashi shawarin d’auka ba. Gashi nan ya baro abinda yake dik irin mahimmanci da yake ba ma aikinsa yazo kwaise tana masa abinda batayi da ba. Ko shiga gidan baiba yai komawarsa company. Anisa duniya sabuwa, tana zaune parlorn Mommy ta mimmik’e k’afafu tana bawa ma’aikatan gida umarni da order Kai kace itace Madam din gidan Mommy tai Sallama. K’iris ya rage Anisa bata saki glass cup d’in dake rik’e ciki hannunta ba. SameenaAleeyou📚*AUREN WATA UKU..!* *38* *©️Sameena Aleeyou…✍🏽* Zumbur Anisa ta mik’e tana duban Mommy cikin tsananin shock. Gaba d’aya sai ma ta daburce ta rasa mai zatai… Kaman wacce aka sinkara ta tafi a guje sai kuma taja ta tsaya gaban Mommy murmushin da yafi Kama da yak’e saman fuskarta “Mommy.. Are you free now… Omg! I’m so happy you are free.. Thank goodness you are free Mommy..!” Ta d’anyi rau rau da ido tana duban Mommyn “Can I.. Please hug you..?” Tai maganar kaman zatai kuka. Sosai Mommy ta tsare tana dubanta Wanda har saida yasa Anisa Shan jinin jikinta. Zuciyarta ya cika da tsoro da fargaba. Gani take kaman asirinta ne ya tonu… Kar dai Mommy ta gane gaskiya ne cewa ita ta zuba ma Ummul guba cikin turare ta kumayi incriminating d’inta.. Tsoro da fargaba suka hanata motsawa.. Mommy ta juye mata Kwaise matamar ta wacce bata d’aukan wani shit. Har ta gama saduda kwatsam ta hangi Mommy na sakar mata murmushi. Bugun Zuciyar Anisa ya soma yin k’asa. Mommy ta bud’e mata hannaye “Silly girl.. Come here.” Tai maganar murmushi irinta manya saman fuskarta. Anisa ta k’araso da murmushi ta rungume Mommy a d’an d’arare tana fad’in tayi kewarta.. Gaba d’aya gidan ba dad’i sabida bata nan.. Mommy ta harareta “Ke tafi can rufe mun baki.. Ai Shiyasa na ganki zaune kin nad’e k’afa bak’e bak’e kina cin Duniyarki da tsinke.” Tai maganar tana mai shigewa lokaci guda tana ceda Anisar tai mata kiran d’aya daga cikin ma’aikatan ta. Har Mommy ta shige Anisa bata dawo daidai ba. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un.! Meke faruwa.? Waye ya fitar da Mommy.. Toh kodai Haidar ya fito da Ummul ne daga yanda ya b’oye ta.? Tunani daban daban cikin kanta.. Wayar Hisham ne taga ma shigo mata. Tai saurin d’agawa tana barin wajen. Daga d’aya b’angaren Hisham yace “Tell me what’s going on there..? Is Haidar there..?” Anisa ta rausayar da ido had’ida furzar da huci “No, Haidar is not here but My Aunt Hajiya Kwaise is here.. She’s free now..” Tsaki yai yana fad’in “Well I don’t give a damn about your Aunt, and much less about her freedom. Tell me is Ummul there..? Do you know her whereabouts..?” Anisa ta murmusa tana kuma rausayar da ido “I don’t care about Ummul or whatever.. And much less her whereabouts.. All I care about is Haidar.. I don’t care if she never shows up.. I don’t care if she dies matuk’a Haidar zai dawo gareni..” “Shut up.!” Hisham ya katseta kafin yaci gaba “Kina ji.. Idan har Hajiya Kwaise is free that only means Haidar ne ya fitar da ita ko Ummul.. Kuma jikina na bani idan har ba Ummul bace tai escaping daga fursunan da Haidar ya b’oye ta toh kuwa Tabbas Haidar zai bayyana a gidan anytime soon.. Use your brain and do something useful ki gano mana ina yaje ya b’oye Ummul.. Idan kikayi wann kin gama naki.. Leave the rest to me.. Zan kula da komai.. Na Miki alk’awari zan d’auke Ummul daga rayuwar Haidar.. And Haidar is all yours..” Anisa sai ta fara dariya dan murna tana fad’in “Seriously, are you for real.. Zan mallaki Haidar.” Furzar da huci Hisham yai cikeda takaicin Anisa dan ya kula shashasha ce lamba d’aya. Bai tsaya sauraron sakarcin Anisa ba ya katseta da fad’in kar tai gigi b’ata masa shiri.. Muryarsa ne ya sark’e sakamakon hango motar Haidar da yai k’ofar gidan Haidar d’in yanda suka zauna da Dareen dan dama Hisham bai bar area din ba sabida zuciyarsa bata daina raya masa Haidar ko Dareen d’ayansu ka iya waiwayan gidan ba. “He’s here..” Anisa ta girgiza Kai cikin rashin fahimta “Who’s there..?” “Haidar.. Haidar Maitama of course..” Anisa ta zaro ido kaman yana ganinta “You mean Haidar my cousin.. Toh kasan mi.? Do something to distract him..” Hisham yace “What do you mean..?” Anisa tace “I don’t know.. Just do whatever is necessary.. Think of something.. Something that will lead you to yanda ya b’oye Ummul.. And hey, don’t think of following him.. Kasan zai iya gane ana binsa, you know how he’s.. Just ka gane.. Ka samu chance ka lalata motarsa kodai Kai wani abin. Yanda dai zaka samu yai leading dinka zuwaga mab’oyar Ummul.” Shiru Hisham yai yana sauraron shawarin Anisa. A hankali ya soma jinina Kai “Seems like k’wak’walwarki na aiki.. I know exactly what to do.” Ya k’arashe yana katse kiran murmushi saman fuskarsa. Anisa ma murmushin tai tana kallon kanta jikin mirror haida ziga kan nata “You are genius Neesah.. Kedin akwai kwanya.” Ta k’arashe tana kuma murmusawa tana duban kanta. A b’angaren Hisham kawa tsaye yai daga nan mab’oyarsa yanda yake iya hangar motar Haidar dake lullub’e da bakin glass. Sam bai iya hangar cikin motar. A cikin motar kaw juyowa Haidar yai yana dubanta bayan ya ida parking. Nan yaga ta kwantar da kanta jikin seat had’ida lumshe ido kaman na mai bacci. Ya d’an d’auki lokaci yana dubanta kafin yai unlocking motar. Har zai fice sai ya kuma juyowa yana dubanta. Yai gajeren tsaki kafin ta soma k’ok’arin kwantar mata da kujeran yanda zataji dadin kwanciya.. Yanda ya kwanto da fuskarsa harma da jikinta kusan nasa cikin k’ok’arin kwantar mata da kujeran yasa numfashinsu sark’ewa waje guda. Yai tsaye cak da abinda yake yana kallon fuskarta wanda yai kusa dab da nashi. A daidai lokacin Ummul ta bud’e lumsassun idonta ai kaw sai cikin na Haidar. Su duka biyun fuskokinsu kaman zasu had’e. Bugun Zuciyar Ummul ya k’aro.. Tsoro ya bayyana cikin idonta masu yalwan haske a cikin nasa idon. Ta zaro idon sosai tana k’ok’arin mik’ewa amma sai taji ya d’aureta da Seat belt ya hanata mik’ewa. Kwanto da fuskarsa ya kuma yi kaman mai shirin sunbatarta yayinda zuciyar Ummul yaci gaba da bugawa. A hankali ya zame fuskarsa. Saitin kunnenta yakai bakin nasa, murya can k’asa yace “Relax, I’m not kidnapping you.. And I’m not going to lock you away again.. Just wait for me here….I’ll be back in a bit.” Yana ida fad’in haka ya matsa baya yana mai daidaita zamansa cikin kujera had’ida yin gyaran murya kad’an. Idonsa na kallon ta yake fad’in “Bansan daga ina Mommy ta d’aukoki ta kawo ki cikin rayuwata ba. At first I was angry at you.. Sabida Mommy ta sayeki da kudi ta kawo ki cikin rayuwata.. Watak’ila dan ta cimma wani manufar ta akaina dake…” Ya d’anyi fasali still yana dubanta “My life is a complete chaos.. I know I’m a monster.. And maybe that’s what she raised me to be.. But believe me, I don’t want to hurt you..” Yaci gaba da kallon ta yana jinjina Kai “Kin amince da aurena ne sabida mahaifinki dake jinya.. Haka ne..?” Ta jinjina masa Kai a hankali cikin sanyin jiki. Haidar yai shiru kaman mai nazari yana dubanta. Sai ya kauda fuskarsa kadan yana jinjina Kai a hankali “Even though I have an unhealthy relationship with my parents.. I know parents are important.. And they play a pivotal role in their children’s life.. Koda ace ni ban samu haka ba..!” Yaci gaba da jinjina Kai yana duban Ummul “Kuma mutane masu kyakkyawan alak’a irinki da iyayensu would do the same.. So I won’t judge you for doing what you did… The only person who’s to blame here is my Mom for taking advantage of the situation… Ta duba halinda kike ciki na buk’ata tai amfani da damarta akanki da family d’inki..” Saurin d’agowa tai tana dubansa zuciyarta na bugawa.. Ba Mommy bace Kai tsaye ta buk’aci haka daga wajenta.. Ummanta ne da Aunty Asshe k’anwar mahaifyarsa.. Shin ta yaya zata sanar dashi idan akwai mai laifi a nan ba kowa nace face nata mahaifiyar, wacce take tsananin son taga tayi aure ta bar gabanta koda Aunty Asshe bata buk’aci wani abu daga wajensu ba. Kafin ta samu wani k’warin gwiwar magana ta sinkayo muryarsa yana fad’in “I’ll set you free and go far away from here..!” Daga haka bud’e motar ya fice ya nufi cikin gidan. Yayinda Ummul tai mutuwar zaune maganganun Haidar na dukan dodon Kunnuwarta.. Haidar zai sawak’e mata yai tafiyarsa.. Zai fice daga rayuwar Mommy.. Innalillahi wa inna’ilaihi raji’un… Mommy bata cancanci haka ba.. Iayakacin abinda take fata da buri shine alak’arsa da Mommy ya inganta ba wai yai nesa da ita ba. Ya zatai..? Mai zatai ta dakatar da Haidar kar ta tafi ya k’yale Mommy..? Sai tai lamo cikin kujera had’ida lumshe idanunta hawaye na ziraro mata. A b’angaren Hisham kaw yana ganin Haidar ya fice ya shige gidan sai ya lab’ab’o a hankali cikin sand’a. ‘Yar k’aramar wuk’a ya ciro cikin aljihun sa. Ya rarrafa jikin motar yanda babu mai iya ganinsa. A hankali ya isa jikin birki ta k’asar motar ya b’allata da wuk’ar hannunsa. Yana gama abinda zai ya kuma lab’abawa ya fice daga wajen ya koma mab’oyarsa yana jiran fitowar Haidar. Muguwar murmushi saman fuskarsa yake duban motar daga nan yanda yake lab’e. A fili yake furta “Let’s see Haidar.. Bari dai muga ina ka Kai Ummul ka b’oye.. Kaida kanka zaka kaini yanda ka b’oye Ummul sabida motarka ta buga..!” Ya k’arashe murmushin bai bar fuskarsa ba. Jim kad’an Haidar ya fito daga cikin gidan hannunsa rik’eda suitcases harda laptop bag alamun dai abubuwan amfanin sa ya d’auka. Hisham na huci yake duban Haidar sanda ya isa jikin motan. Akan idonsa Haidar ya zuba stuff d’insa bayan motar ya bud’e mazaunin driver zai shige a nan Hisham ya hango kaman mutum cikin motar.. Daidai lokacin kuma Ummul ta soma k’ok’arin mik’ewa zaune nan Hisham ya hangota cikin motar. Zuciyarsa tai wani irin tsinkewa. A fili ya furta “Ummul.? No.. No no this can’t be.. She can’t get hurt..!” Yana maganar cikin tsananin daburcewa har bai san sanda Haidar yaja motar ya bar wajen ba. Cikin rikicewa Hisham ya shige nashi motar daga can yanda ya ajeta. Yana driving yake dialing layin Anisa. Tana d’agawa Hisham ya fara cikin sakin huci “I know where Ummul is.. Tana cikin motar.. Tana tareda Haidar.!” Anisa tace “So, come up with something.. Kidnap her and runaway.” A hasale yace “Shut up. Just shut up.! Kece kika bani shawarin na shirya ma Haidar accident ta haka ne zai leading dina to where he hides Ummul.. Na d’auki shawarinki and tempered with his brakes. And now.. Komai ka iya faruwa da Ummul.. Damn you..! I shouldn’t have listened to your advice..!” Cikin daburcewa Anisa ke fad’in “Idiot..! I didn’t say you should temper with his brakes.. Kawai cewa nai Kai causing masa minor accident ka dan bigi bayan motarsa or something.. Amma ni bance Kai causing babban accident ba.. Do you even realize they can both die in that car..!” Sai ta fara kuka tana fad’in “Wayyo Haidar.. If something bad happens to Haidar wllhi bazan tab’a yafe maka ba.. And you will answer to me..!” Hisham ya daka mata tsawa da fad’in “Shut up. Shut your trap..! I can’t lose Ummul. Bazan rasata ba.. Kuma idan wani abu ya sameta you’ll be the one to pay the price.!” Bai kuma tsayawa sauraron Anisa ba ya Katse kiran yana mai dukan steering wheel da iyaka k’arfinsa yana tsaki. ** A b’angaren Daddy kuwa tinda ya koma Office tunanin abinda Mommy ke masa ne ya sha masa Kai. Da fari ta basa zab’i cewa zai iya datse aurensu Idan yaso.. And now tana nuna masa kaman dai zaman D’anta kawai take a gidan. Kaman dai shid’in baida wani mahimmanci wajenta. Ya sani yaso Kwaise da duka zuciyarsa, hasalima bai tab’a son wata mace kaman yanda yaso Kwaise ba.. Amma bayan abinda ta masa.. Bayan rabasa da matarsa da sheganta cikin D’ansa da tasa yai yaji ta fita masa a rai. Ba ita kad’ai ba ko wace mace ma ta fice masa.. Yaji baya mararin wani abu mai suna soyayya because he was betrayed by macen da ya nuna mata zallan soyayya. Wanda hakan yasa ya d’ibi kwaise ya watsar sann bai kuma yunk’urin sake wani aure ba. Kaman yanda tace Kasuwancinsa shine kawai a gabansa shine rayuwarsa shine komai nashi.. Bai kuma damu ba idan Kwaise bata nuna damuwarta akansa ba. Hasalima yanda taketa Neman attention d’insa zuwa gareta da kuma D’anta tun bayan abinda ya faru sai hakan yake kuma tunzura shi yake nuna mata da ita da d’an nata basu gabansa hasalima babu abinda ya baiwa rashin mahimmanci irin su… But why’s he feeling this way now..? Meyasa yake ji yanzu da Kwaise ta fara nuna masa baya gabanta abun ke masa zafi sosai..? Meye dalili.. Meyasa yake Jin ciwon hakan bayan abinda yai buri kenan tsawon shekarun nan. Ya d’an furzar da huci yana aje pen d’in dake hannunsa. Alhaji Gimba daketa Sallama Daddy baisan da zuwansa ba sabida nisa da yai cikin duniyar tunani k’arasowa yai ya zauna kujera mai kallon na abokin nasa. Daddy ya d’anyi gajeren tsaki “Yi hakuri Gimba banji shigowarka ba..” Alhaji Gimba ya murmusa “Ina kuwa zakaji shigowata Madam ta caza maka Kai..” Yai maganar cikin barkwanci irinta abokai. Daddy ya kuma yin gajeren tsaki “Don’t please.. Don’t bring her up here.. Let’s talk business..” Girgiza Kai Alhaji Gimba yai yana juyi cikin kujeran “Abokina kenan. Kana nan a Aliyun ka da na sani.. You know your son Haidar takes after you.. Bai bar maka komai ba.” Daddy ya kuma yin gajeren tsaki “Are we going to talk about this issue again..?” “K’warai bazaka iya guje ma hakan ba.. Sabida sud’in ahalinka ne.” Daddy ya kuma lumshe idonsa cikeda k’osawa “Gimba please, my day is bad enough coming to add to it.. Kar ka min maganan D’aya cikin biyun nan..” “Abinda nake fad’a maka a kullum shi zan sake tunasar dakai. Bakada Wanda ya fi maka su.. Sud’in ahalinka ne..” Daddy ya kuma yin tsaki “Gimba, please get out before I ask my secretary to escort you out.!” Ya k’arashe yana nuna masa k’ofa. Murmushi Alhaji Gimba ya kuma yi “Seems like your pride is speaking for you again Abokina.” Ya kuma gyara zamansa “Shi rayuwar nan Engr wllhi kyauta ce. Yau dubu nawa basuda daman rayuwa irin namu. Ba wai k’uruciya muka fisu ba.. Ka juya ka duba environment d’inka sosai kaga masu irin shekarun ka guda nawa ne.? A ajiye maganan arziki na kudi da dama na rayuwa, ka duba masu arzikin lafiya irin naka guda nawa ne.? Ka duba masu ahali irin naka guda nawa ne.? Shin kasan wani ya tara arzikin amma baida lafiyan jin dadin arzikin..? Shin kasan wani ya tara dukiyar amma baida Magaji.. Shi da za’a amshe duka dukiyar da ya mallaka dan a mallaka masa irin D’an daka mallaka K’wara d’aya tak da ya fiye masa duk wani arzikin gidan duniyar nan da za’a basa..” Daddy ya girgiza Kai kad’an “So, what are you trying to imply here.. That I’m ungrateful..?” Alhaji Gimba ya katsesa “Because you are stuck in tha past.. And that destroy your present.” Ya dan gyara zamansa “Kuma kasan ina matsalar take.. A naka tunanin bayan abinda ya faru dakai a baya Kasuwancinka shine abinda yai keeping d’inka moving.. Amma ba haka bane.. Wann ahalin da a kullum kake ik’irarin basuda mahimmanci cikin rayuwarka sune sukai keeping d’inka moving forward.. Your wife and your Son.. Amma ba business d’inka ba kaman yanda Kai kake tunani..” Ya d’an numfasa yana jinjina kai “Your company is your distraction not your source of happiness.. Wann ahalin da a kullum kake tashi ka gansu sune sukai healing wann gurbin ciwo dake cikin zuciyarka.” Katsesa wann karon Daddy yai “Quite the contrary… Ganinsu a kullum da nake shi yake tuna mun baya.. And maybe that’s why I feel trapped in the past.. Watak’ila da ace bani ganinsu things would’ve been different..” Alhaji Gimba ya girgiza Kai yana murmushi “So tari zamu so abu amma ba alkhairi bane wajenmu.. Sann so tari zamu k’i abu amma alkhairi ne a tattareda mu. Watak’ila D’anka daka rasa tun kafin yazo duniya ba alkhairi bane cikin rayuwarka, Watak’ila D’anka Haidar da Allah ya bar maka shi Watak’ila shine alkhairi a gareka. Barinyi maka tuni da wani k’issa na Annabi Musa (AS) da malaminsa Khidr Wanda a k’auli mafi rinjaye shima Khidr Annabi ne. A cikin tafiyarsu da sukai Wanda Annabi Musa(AS) ke Neman ilimi wajen Khidr sunga wani yaro a hanyarsu kuma Annabi Khidr ya kashe yaron Wanda har Annabi Musa ya gaza hak’uri ya tambayesa meyasa zai kashe ran da baiji ba bai gani ba. Koda suka zo rabuwa Annabi Khidr ya amsa ma Annabi Musa (AS) amsoshin tambayoyinsa da ya gaza hak’uri akansu. Shi wann yaron da ya kashe Iyayensa mutanen kirki ne shi kuma yaron Allah ya k’addari idan ya girma zai lalace kuma iyayen nasa suna matuk’ar sonsa zasu jarabtu dashi har ya lalatasu dan haka Allah ya masa umarni da ya kashe wann yaron.” Ya dan numfasa yana kallon Daddy da jikinsa yai sanyi sosai “Karatun da zaka d’auka a nan wani sa’in abu ba alkhairi bane wajenka sai Allah ya d’auke maka shi cikin rahamarsa. Watak’ila wann D’an daka rasa tun yana ciki Watak’ila zaka jarabtu dashi sai Allah ya maka sauyi da wani d’an Wanda ka kasa gani ka kuma kasa appreciating d’insa.” Ya dan kuma gyara zamansa “Ina ka bar tawakkali..? Ina ka bar imani da k’addara Abokina.?” Daddy ya dubesa a sanyaye da idanunsa da suka kad’a ba tareda yace komai ba. Alhaji Gimba yaci gaba da jinjina Kai “You need to let go of the past and accept what you have

Chapter 34 of 64