dama shi kanshi Sufyaan ɗin ba dan haka Malam ya kara yima Sufyaan nasiha akan ya rike Teemah da amana kodan Albarkacin iyayen ta.
Basu bar gidan ba sai da ya damka mishi duk takardun gidan sannan ya mishi jagora suka zagaya gidan sak yanda Teemah ke fatan gidan ta ya kasance haka uban nata yasa aka tsara mishi gidan saboda ya faranta mata.
Kar a manta aci gaba da sharing please.
#Ummiee~Zaria
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱 FAMILY HOUSE ⚜️🔱
~{{ȶֆɨռȶֆɨʏǟ ʍǟƊǟʊʀɨռӄɨ Ɗǟʏǟ}}~
*©®UZ-2023.*
*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne ga gidaje biyu masu albarka,BENEFICIAL WRITERS ASSO,tare da gidanmu na gado abun alfahari FAMILY HOUSE,Allah ya ƙara haɗin kai ameen._
*Ga masu tambayar littafin daga farko zaku iya tuntuɓata kai tsaye da wannan number ɗin 08061358462,*
Karku manta littafina kyauta ne banyi shi dan in siyar ba dan haka karkuji ɗar kuba duk wanda kuke so.
Free book ne yan bati a dage da karatu a daure a dunga comment atoh.
```Page12
Anyi auren Sufyaan da Amaryar shi Rabin ran shi Teemah lafiya, kasancewar auren na soyayya yasa suke dage wajen cinye soyayyar nasu ba kama hannun yaro kamar su mai da juna cikin cikin su haka sukeji dan tun bayan auren da sati ɗaya suka ketare kasa zuwa honey moon,
Sai dai kuma ba anan gizo ke sakar ba domin tun daga dawowar su chakwakiyar ya fara. dafarko yawan zuwan gidan da kawayen ta sukeyi shine abu na farko daya fara ɓata mishi rai sai dai baiyi saurin yin magana ba a zaton shi ai dama in amarya tana sabuwa mutane kanyi zaryar zuwa kawo mata ziyara,Sai dai kawayen ta maida gidan sukayi kamar wani joint na jin daɗin su nan zasu zo ko wacce taci abunda take so tayi abinda take so,har ya zamana tun abun bai ɗaɗashi da kasa ba har ranshi ya fara ɓaci da hakan,dan basujin ɗar ko shakkar yin ma gidan nashi zuwan duku² sau da yawa inya dawo daga masallaci yakan wuce wajen training idan ya dawo kuma yakan so ya kusanci iyalin shi ta bashi energy yanda zai samu karfin fita,sai dai abun haushi sai sanda wasa yayi wasa yan wasu sun dau harama duka kan duka kowa nakai naushi kawai sai su farajin karar karar rawa inko Allah yasa yayi mantuwa bai kulle kofar falon ba haka zasu shigo kai tsaye in basu samu kowa a falon ba babu wani dogon tunani kawai tafiya zasuyi zuwa ɗakin ta,hakan yasha faruwa ba sau ɗaya ko sau biyu ba sannan abun haushin da zarar taji motsin su tofa shike nan wasa ya kare dan bazata bari ya sauke tashin hankalin daya ɗibo ba in yayi magana kuma sai tace,wai ita kunya take karsu gane yayi wasan danbe da ita. da abun yakai mishi ko ina yayi magana ba karamin rikici suka so suyi ba,domin dai ita Teemah tun tashin ta a gidan su bame takura mata abunda take so shi akeyi mata sai gashi daga aure zai fara tsiro mata da wani tsirfa.
Ganin tadau zafi yasa ya koma rarrashin ta dan baya ƙaunar abinda zai taɓa mishi ran gimbiyar tashi dan haka a daren maganar ta wuce,ya akayi ya ba'ayi ba dai oho domin a lokacin kawayen nata sun ɗan rage zuwa gidan dan ya zuba ido yaga ko zata musu magana akan zuwan mishi gida da sassafe amma baiga tayi hakan ba dan haka yama mai gadin gidan kashedi akan karya kara barin su suna zuwa mishi gida da sassafe,
Rashin zuwan kawayen nata yasa ta tsiro da yawan fita unguwa naba gaira babu dalili domin ko a kullum ba fashi sai ta fita ko yana gari ko baya gari ko yana gida ko bashi haka zatasa kafa ta tsallake shi tayi tafiyar ta wajen yawo dan har lokacin bata fara aiki ba,wani lokacin ma ko yana gidan bazai san ta ficeba sai in ya nemeta bai sameta ba,ga kuma wani hali data tsiro na rashin gyaran muhalli abinda bai sani ba shine dama kawayen nata sune ke ɗan kan kanta mata gidan in sunzo dan ita kam shegen san jikin ta bai barin ta ko tsinke ta ɗage to yanzun sun dena zuwa dan haka a hankali gidan ya fara sukurkucewa, kullum Kafin ya tafi aiki shike kimtsa gidan fess tun daga kan shara wanke² ita gimbiyar nacan kwance tana bacci sai dai inta gaji da baccin inta tashi ta fesa wanka ta feffesa turare a kuma fente fuska da kwalliya wannan kam ba fashi indai batun gyaran jikine amma ɗakin ta in ka shiga Sam bashi da daɗin kallo dan yanda take watsa kaya ko ina,shine ma inya shigo yake daurewa ya gyara mata ya ware na wanki ya fitar sannan ya gyara mata ɗaki duk abunda yake mata bai ɗauke shi a matsayin komai ba sai kyauta tawa tsabar son da yake mata yasa ya kasa gane cewa hakan bai dace ba domin shidai a rayuwar shi bai ƙaunar abinda zai mata ta ɓata rai harta raba shimfiɗa dashi dan ba karamin daɗin ta yakeji ta wannan fannin ba gashi kuma Allah yasa itama ɗin jaruma ce,
Kun san mu mata bamu iya samun waje ba haka nan ma mukan tsula tsiya muyita wulakanci balle kuma in an bamu dama,
Dan haka gaba ɗaya ganin cewa ai mijinta yana son ta dan gashi ko laifi ta aikata mishi da zarar ta ɓata rai dole yake neman sulhu yasanya tasa kafa ta fara kwallo da duk wasu hakkoki daya kamata macen aure ta kiyaye su akanta,suko kawayenta dama ba ƙaramin bakin cikin auren data rigasu yi sukeyi ba dan haka ko sunga tayi ba dai² ba babu mai kwaɓa mata a cikin su,
Abunda ta sani kawai in gari ya waye tayi wanka ta ɓata lokaci wajen shiryawa inta gama ta fito in Sarki yayi girki kafin ya fita taci in bai girka ba kuma zayi order ɗin abinda take muraɗi taci sannan itama ta kama gaban ta,domin dai a dole Sarki ya koyi girke² dan shi Allah yayishi mutum ne shi mai tsagina gini bako ina yake iyacin abinci ba,yanzun kuma da yake auren Teemah bazai yuwu yaje gidan brig gen cin abinci ba dan haka ya dage da koyan girke² kala² a kokarin shi na ganin ya faranta ma Rabin ran shi dan su zauna lafiya,to ita kuma hakan data gani yasa ta ƙara sakan kancewa da irin son da yake mata dan gaba ɗaya bata shiga kitchen bawai kuma dan bata iya girkin bane NO tsabar gayune a ganin ta tafi karfin shiga kitchen sannan bata yarda da batun ɗaukar mai aiki ba saboda kishin mijin ta da takeyi,in Sarki baya gari kannin ta take daukowa su dawo gidan da zama har ya dawo kuma su zasuci gaba da kula da gidan da duk wani abu daya kamata.sun share shekaru biyu da aure amma babu wani alama na bullowar ciki daga jikin ta sannan har zuwa wannan lokacin a halayyar ta babu abunda ya canza sai ma wadanda suka ƙaru domin ta fara aiki dan haka ta kara haɗuwa da kawaye yan gayun da sukayi dai² da ra'ayin ta saukin ɗaya dai yasamu yanzun shine ɗaya daga cikin yaran shi mai suna Ibrahim kwaro shine yake kula da tsaftar cikin gidan dama girkin abincin da zasuci abinda ya shafi tsakar gidan kuma sauran yaran nashi suke kula dashi amma har kwanan gobe shike gyara ɗakin shi ya kuma gyara mata nata a matsayin ta na ƴar gaban goshi,har zuwa wannan lokacin kuma ko sau ɗaya bata taɓa taka kafarta a Zaria da sunan taje taga asalin shiba duk sanda bukatar hakan ta taso to saita kirkiri wani babban dalilin dazai katangeta da zuwa sai dai yaje shi kaɗai ya dawo,sannan koda yan uwan shine suka zo Mahaifiyar shi ko cikin kanne ko yayyen shi babu ruwan ta dasu sha'anin gaban ta shi zatayi in mutum yaji yunwa ne dole ya nemi hanyar kitchen macen da bata dafama mijinta bane zata dafa dan wani baƙo.
A irin hakan ne wata rana kanwar Sufyaan ɗin mai suna Hindatu sukazo garin ita da mijin ta kasancewar aikine ya kawo mijin nata garin hakan yasa ta rokeshi arzikin ya barta taje gidan ɗan uwan ta taɗan kwana biyu maimakon zaman dazata dungayi koda yaushe a cikin ɗakin hotel ɗin da sukayi masauki,hakika kam tayi zuwa a sa'a kuma tayi kyawawan ganin da in a labarine tuni zatayi watsi dasu wajen cewa karya ne domin zaman auren da ake gudanarwa tsakanin Sarki da matar shi ko gidan turawa albarkha domin ita dai a kwana biyu da tayi a gidan sau ɗaya ne sukayi ido biyu da matar gidan tun ranar data iso gidan suka gaisa ta shige ciki ta barta da ɗan uwanta suna gaisawa bata karajin motsin taba sai dai in taji yunwa ta shiga kitchen ta dafa abunda take muradi taci dan Ibrahim kwaro sau ɗaya yake musu girki a rana,ta dai naɗi abubuwa ma'ishi waɗanda Allah² take ta koma Arewa dan taje ta fesama Uwar gida labarin halin da gidan Sarki yake ciki,wannan irin kwamacala har ina.
Bayan mijinta ya gama abunda ya kawo shi sun koma bata tsaya ɓata lokaci ba taje ta zayyana ma uwar su irin mulkin da Teemah keyi a gidan ɗanta harma da ƙari (lol su dangin miji an iya sharri),
Hankalin Uwar gida ya tashi matuka tsoron ta shine Allah yasa bawai ɗanta ya faɗa komar mata marasa tsoron Allah bane dan haka a satin ta kirashi akan duk abinda yakeyi ya bari ya tattaro shida mai ɗakin shi su taho Zaria karshen wata dan akwai bikin da za'ayi dama a nan cikin gidan ta kara da cewa bata bukatar jin wani uzuri umarni ta bashi dole yazo.
A sanda ya samu kiran ba karamin tashin hankali ya shiga ba domin yana kan shirye²n fita kasar wajene zuwa hutawa shida rabin ranshi wacce ita Teemah ce ta bukaci fitar a cewar ta ta gaji da zaman 9ja tana so su fita su ɗan sarara,aiko ba karamin tashin hankali sukayi ba a lokacin da yazo mata da batun tafiyar nasu,dan amsa na farko data bashi shine cewa ai yana sane da batun fitan su dan haka ba wani Zaria da zata kokari take ta rarrage wasu aiyuka a office kafin su tafi yayi zaton zai shawo kanta da sauki sai dai ina a kullum kawayen ta cikin zugata suke akan ba itaba koshi ta nemi yanda zata hanashi shigema yan uwan shi da yakeyi dan idan yana zuwa gunsu tabbas wata rana bashi daya zai dawo ba sai dai ta ga sun haɗoshi da wata matar ita bata san halin mazan Arewa bane dason tara mata barin ma shi da Baban shi yake da mata 4 dan haka ta kiyaye.
To dai haka da kyar da siɗin goshi ya samu ya lallasheta suka tafi kasancewar a lokacin bai mallaki muhallin shiba sai ɗakin shi na samar taka daya gyara wanda yakan sauka a cikin shi lokaci lokaci yasa koda suka isa dole sai sashin uwar gida aka sauketa duk da gidan ya kasance ginin zamani kuma an kawata shi domin dai kaf matan gidan babu wacce side ɗinta yakai na uwar gida tsaruwa,amma hakan bai burge ƴar gaban goshi ba,sai ma fargaban ta daya ƙaru a sanda aka dunga gabatar mata da jama'ar gidan bata ƙara tantance zancen kawayenta da suke faɗa mata cewar mazan Arewa na tara mata ba sai zuwan ta Zaria domin bayan nan gidan su Sufyaan ɗin da aka dunga nun nuna mata wacce kishiyar wacce sauran gidajen ma dai duk kanwar ja ce dan haka ta tsorata sosai dan haka taci alwashin dakushe mijinta daga zuwa garin sauran yan uwan shi dake mata jele a gidanta ma duk zatayi maganin su ne,tun fitan da tayi na ranar da uwar gida tasa a mata jagora zuwa gaishe² bata yarda ta kara zuwa ko ina ba koda yaushe tana cikin ɗakin da aka sauke ta dan harta uwar mijin nata sai dai inta so ganin ta ko magana da ita ta leko ɗakin ko tasa a kira mata ita sai ta gama Jan aji kafin ta fito taji dalilin kiranta da akayi bata komai sai dai taci tayi bacci domin abincin gidan ma bata sakin jikinta taci sai dai ta kira Sarki ta faɗa mishi abunda take so shi kuma jikina rawa yaka zai kawo mata.
A wannan kwanaki kam Uwar gida tayi ganin abubuwa kala² a kuma lokacin ne ta kuduri aniyar dole ne Sarki ya kara aure dan bazata yarda Teemah taci gaba da juya mata yaro sai abinda taso zaiyi ba dan taga alamar a yanzun in ta matsa tace ya saketa tofa kunya zai bata dan bazai saketa ɗin ba dan haka zatabi komai a hankali.
To dai kamar Teemah tasan abinda uwar gida take shiryawa dan suna komawa itama bata samu sa'ida ba saida ta zayyane ma kawayen ta abinda ta tarar a Zaria su kuma suka ƙara ɗaurata a hanya dan haka tun daga wannan zuwan gaba ɗaya Sufyaan ya dauke kafa da zuwa Zaria koda aiki ya kaishi Arewa baya iya zuwa kullum in yayi waya dasu zaiyi ta cewa yana tafe amma shiru kakeji.a cikin shekaru 3 da watanni da auren sune Teemah ta samu ciki bisaga shawarar kawayen ta domin dama tun farko su suka ɗaurata akan karta yarda tayi ciki da wuri dan da zarar ta samu ciki tofa tsufa ne zai fara ƙonƙosa mata ƙofa kuma son da Sarki yake mata raguwa zaiyi,ita kuma a duniya tana taƙama da kuma alfahari da irin son da Sarki ke mata bazata so wani abu yasa wannan soyayyar raguwa ko kuma ace son ya gushe ba,a yanzun data tabbatar ma kanta da cewa Sarki nata ne ita kaɗai ga kuma matsayi da tarin arzikin daya tara shine suka bata shawara akan ta haihu yanda komai zai mata daga ita sai ya'yan ta.
Lokacin data samu ciki ba ƙaramin murna Sarki yayi ba a ranar duk wani makusan cinshi ya shaida hakan lokacin da watar haihuwar ta kama kasar suka bari dan acewar ta bazata iya haihuwa a 9ja ba duk da cewa tun kafin cikin nata ya tsafa Uwar gida tamishi magana akan ya dawo da ita Zaria inta haihu ayi suna a can amma ƴar gaban goshi ta kekashe kasa cewa bata zuwa dole sai hakuri yaba uwar gida,ɗiya mace ta haifa suka sanya mata sunan uwar Teemah Ramlat,a jejjere dai sai da tayi aihuwa uku duka kuma Allah ya bata duk da batayi farin ciki da hakan ba dan Allah ya sani ita yara maza taso samu ta yanda zata samu kwanciyar hankali cewa zuwa gaba komai na Sarki ita zatayi iko dashi ba yan uwan shi ba,dan zuwa lokacin a babu yanda zatayi dole tanaji tana gani Sarki ke tafiya Zaria yaje yayi kwanaki duk da tayi yanda tayi ta hana yan uwan shi zuwa gidan Amma hankalin ta bai kwanta ba kullum tsoron ta karsu haɗashi da wata a can ɗin duk da tasan mijin ta tana son ta da wuya ya iya kula wata amma ai ance har maza ma ana musu auren dole a Arewa,
Ana hakane kuma ya samu canjin wajen aiki zuwa KD wanda kafin faruwar hakan ne ya siya fili anan cikin unguwan su ya ɗauko masu aiki tafiyayya tun daga wata kasa sukazo suka ɗanɗasa mishi ginin nan da kowa ke maganar shi saboda kuɗaɗen da ginin yaci,ya kashe manyan kuɗi a tunanin shi in taga ginin zata yarda ta dawo gidan ba tareda anyi tashin hankali ba,sai dai ina a banza wai an tsikari kakkausa dan a lokacin da yake nuna mata pic da vid ɗin gidan ta yaba kwarai harma take ce mishi irin gidan zai gina musu in zai canza musu gidan zama,ganin yanda ya yaba da tsaruwar gidan yasa bai ɓata lokaci ba wajen faɗa mata cewa gidan nashi ne kuma yasan zata so gidan shi yasa yayi amfani da komai bisa ra'ayin ta dan yana son wannan karon dasu zai wuce,saboda duk sanda ya samu canji na wajen aiki shi kaɗai yake tafiya bata yarda tabishi har gara² takan kai mishi ziyara in taso.
Aiko tamkar dukar guduma haka taji zancen wai itace zata koma Zaria da zama ita da yaran ta,to ai ito ko abuja sai dai ta zauna aba yanda ta iya Zaria fa tab.
#kuyi hakuri ba yawa naso in kai karshen labarin sarki a page ɗin nan amma na kasa wallahi kaina ke ciwo,zanyi kokari mu gama dashi a page na gaba dan mu koma kansu Ameenatu, kafin na uban gayya jikan Hajiya ya biyo baya*Mai Jama'a*
#Team Sarki
#Team Mai Jama'a
#Sheikh Naseer🥳
#Ummiee~Zaria
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱 FAMILY HOUSE ⚜️🔱
~{{ȶֆɨռȶֆɨʏǟ ʍǟƊǟʊʀɨռӄɨ Ɗǟʏǟ}}~
*©®UZ-2023.*
*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne ga gidaje biyu masu albarka,BENEFICIAL WRITERS ASSO,tare da gidanmu na gado abun alfahari FAMILY HOUSE,Allah ya ƙara haɗin kai ameen._
# Free Book ne
```Page13
Duk yanda Sarki ya hasaso abin ya zarce tunanin shi domin tun sunayi iyasu sai da maganar ta koma gidan Brig domin Teemah ta samu ɗaurin gindi daga wajen uwarta,domin a lokacin Brig baya kasa shi kuma Sarki gudun kar in maganar yaje kunnen Brig gimbiyar tashi ta karayin fushi fiye da wanda take kai a yanzun yasa bai iya kiran Baban nata ya faɗa mishi ba,to dai koda maganar ya koma wajen Hajiya Ramlat itama bin bayan yarta tayi suka kafa hujja da cewa karatun yaran zai dakushe ga kuma aikin da Teemah ɗin keyi a lagos ɗin.
Haka nan yanaji yana kallo dai dole ya tattara yabaro su a Lagos shi kuma ya dawo Kaduna inda yaci gaba da aikin shi,sabida ya nuna mata rashin jin dadin shi akan abinda tayi yasa a lokacin sai da ya kwashe wata 5 bai koma Lagos ɗin ba sai dai duk karshen wata a Zaria take mishi.
Wannan nisa da juna da sukayi yasa a hankali saboda yawan ziyara da yakan kaima abokan shi yake ganin yanda suke tafiyar da al'amuran su na zaman takewar aure tsakani su da matan su da kuma yanda matan ke kaffa² da komai daya shafi mazajen nasu hakan yasa duk sai ya fara tsarguwa domin idan ya ɗauko nashi zaman auren ya kara dana abokan shi sai yaga ina ko kusa basu dai² taba, wanda ada shi bai taɓa ɗaukar cewa sakewa da damam makin da yaba Teemah take yin abinda ranta keso a matsayin wani abuba sai tsabar soyayya,bai san cewa wuka ya ɗauka ya daɓa ma cikinshi ba sai yanzun domin gashi dai har ankai matakin da yanaji yana gani bai isa yace ga abinda yake buƙata tayishi cikin daɗin rai ba,ko kuma yace yau ya kafa doka akan wani abu.
duk bashi da waɗannan daman ta yanda sai abinda taso taga dama takeyi,
kula dashi da adacan baya takeyi a filin wasan dambe shima tuni ta tattara ta watsar a cewar ta wai yawan dambacewa na tsofar da mace dan haka inba ita tayi ra'ayin kawo mishi kanta ba koya nema bata bashi shi kuma ya kuduri aniyar bazai taɓa yi mata dole ba dan haka ya koma koda yaushe cikin azumi yake sannan kuma yana matukar kauracema duk wani abu dazai danganta shi da hurɗa da duk wata mace a tsoron shi na faɗawa harkar neman mata duk kuwa da yanda yake fama da ciwon mara lokaci lokaci.
Ganin tsayin watan nin daya ɗauka ba tareda ya dawo ba yasa taɗan fara damuwa,domin dai ita babban tashin hankalin ta shine kar yaje can iyayen shi su sanya shi ya kara aure, sai dai duk sanda tayi maganar da kawayen ta suke kwantar mata da hankali akan cewa ta tsaya akan bakin ta in kuma ya matsa to ta faɗa mishi ya saida wannan gidan ya siya mata wani a Abuja ko anan KD ɗin,
Koda ta tunkare shi da Maganar bata samu yanda take soba,dan kai tsaye shima ya faɗa mata bai amince da hakan ba in bazata zauna a Zaria ba to taci gaba da zaman ta a Lagos .
ɓacin ran rashin samun biyan bukatar ta yasa ta tattara shi ta watsar dan tasan ko giyar wake yake sha bai isa ya mata kishiya ba.
duk wannan rikicin da sukeyi yan uwan shi basu sani ba ciki kuwa harda mahaifiyar shi domin hatta da ginin gidan da akayi har aka gama ba kowa yasani ba daga mahaifin shi sai Malam sai kuma mahaifiyar shi duk yanda ginin gidan yaja hankalin mutane sukayi ta cece kuce a kanshi wasu na yabawa wasu na kushewa babu wanda yasan ko gidan na waye domin aikin ginin company keyin shi sannan kafin a fara ginin saida aka zagaye filin da kwano aka mishi katanga da idon mutane,lokacin da aka kammala ginin ko da aka cire wannan katanga ba irin surutan da mutane basuyi ba dan da yawa ganin su almabazzaranci ne kawai wannan gidan duniya da a kullum zaka iya tafiya ka barta.
ganin har an gama ginin gidan Sarki baiyi magana akan dawowar iyalin nashi gidan bane yasa Uwar gida da kanta ta tareshi da zancen dan koba komai zata so ace da iyalin shi zai tare a cikin gidan,sai dai bai boye mata yanda ta kaya akan batun dawowar su Zarian ba tayi zaton hakan dama dan haka a matsayin ta na uwa taga ya dace ta shiga maganar dan tayi sasanci,dan ko ba komai tasan ɗan nata na ɓukatar iyalan shi a kusa dashi hakan yasa tayi kiran wayar Teemah ɗin a gaban Sarki a zaton ta ko kila in tasa baki taji nauyin ta ta yarda da batun dawowar,
sai da tayi mata kira biyu kafin ta ɗauka a kira na uku wayar tana gab da tsinkewa,
Bayan sun gaisa ta tambayeta yara da kuma mutanen can gidan su ita kuma Teemah ta amsa mata da cewa "lafiya lau suke"
sannan Uwar gida tayi gyaran murya ta ɗaura da cewa "Fatima dama na kirane inji ya maganar tahowar ku Zaria
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 92