Share this page
amma har yanzun yarinta ne cike da kanki ai dai na fada miki ba bacci koh? Wallahi in baki sauko ba daukarki zanyi Dan allah sai kinje" ya fada yana dauko mata hijab din da tayi sallah dazun, haka nan dai ta sauko tana tura baki rikota yayi yadan rungumota ta gefen kafadar shi, Kallonta yayi da gafen idon shi "waike nima zaki rufema kofa Dan kin gama raina nikoh?" Tura baki tayi ba tareda ta bashi amsa ba, "Da kyau"ya fada shima yana kauda kai, "to kayi hakuri" ita kuma tace, shareta yayi bai amsa taba, "Kayi hakuri Dan allah," ta k'ara fada "ki rike hakurin ki dan ke zanba hakurin anjima kad'an dan kinsan dai yau dagani saike koh ?"ya fada yana dage mata giraren shi biyu da wani munafukin murmushi a fuskar shi, "ko bazaki sha sweet ba? halshen shi ya fidda daga cikin bakin shi yana dan karkada shi, "zaki sha koh?" Ya kara tambaya yana tsareta da idanuwan shi da suka fara kankancewa, Kauda kai tayi tana murmushi " Yauwa yar kanwata ai nasan bazaki ki shaba koh? " Ya kara fada yana mai k'ara rungumota sosai zuwa cikin jikin shi ya sunbace ta a goshi "ina fa sonki da yawa yarinyar nan kinga yau ko bugun da zuciyata keyi in kina kusa dani ya ragu," ya fada yana mata hararar wasa, Kara langwabewa tayi a jikin shi domin wallahi duk wata gaba dake jikinta saida ta mace a wannan lokacin. "Yarinya Ai kema kin san nayi shekaru ina taraki dan haka yauce ranar kwasan adashe ki gode Allah yau din babbar ranace a gareni dan haka zan dan sassauta miki kad'an nasan kema zakiyi farin ciki ko Matataa... ? Itadai bata k'ara samun zarafin magana ba domin ko idan dai har mai Jama'a yace zaiyi Abu tofa ko za'a mutu sai yayi, Dan haka yau dai ta sadakar sai yanda allah yayi da ita kuma........ Karku manta tuzuru nefa,,,,, Koda suka k'arasa falon mikewa tsaye su sadeeq sukayi, Barka da fitowa amaryar mu suka fada a tare, rufe fuskata tayi da tafukan hannunta tana k'ok'arin janyewa daga jikin AK Amma gayen nan sai ma kara chachume ta yayi da gayya, ina ruwan ba saban ba ko kuma ince Dan kauye yayi agogo, Kujeran dake daura dasu 2 sitter ya masu masauki akak, Yusuf ne ya bude taron da addu'a, Sannan suka masu yan nasihohi bayan doguwar addu'ar da ko wannen su ya masu sannan suka kuma gabatar mata da wata jakar briefcase a matsayin kyauta daga abokanan su a gurguje dai sukayi masu sallama suka wuce, " Ki jirani anan " yace yana maiyi musu rakiya, gyara kwanciya tayi a kujeran dan wallahi har yanzun baccine cike da idonta baiji maba ya dawo bayan ya kulle kofa ya kashe fitulun dake kasan sannan ya hauro sama bai kulata ba ya jawo ledojin nan ya bubbudesu, kayan ciye² ne a cikin su sai kayan sha a wata ledar daban " tashi ki zauna muci abinci yunwa nikeji" ya fada yana zama a kasa saman kafet din dake malale a wajen, saukowa itama tayi ledar da kaji ke ciki ya tura mata gabanta, Waiyo Allah hajiya kaza tun kan ta sauko kamshin su ya tadomata da duk wata tsohuwar yunwar dake boye cikin hanjinta, Kajin nan fa sunsha hadi sannan sun samu lafiyayyar gashi gasu luka² ko ina tsokace kwance sai kyalli suke, mukut fa hadiye miyau, itadai allah ya sani tana matukar so da kaunar Aunty kaza soyayya mai danko ne a tsakaninta da kaza Dan haka batajin zata iya wuce tayin ta. Amma dai duk da haka batayi saurin bada kai ba saida ta latsa shi, Duk wannan sakar zucin da take shi hankalin shi yana kan cin chips din shi da yikeyi, mika hannu tayi zan diba chips din ya janye " haba Amarya ai yau ranar cin kazace Bari ki gani" ya fada yana janyo ledar kajin gaban shi, "gashi ko kamar sun sanki da maitar kaza suka kwaso miki kici ki gaji," bata rai tayi "ni bazanci kazar ba," " Iyeee" yace da dan karfi yana kallon ta "me naji kince? " " Cewa nayi bancin kazar" dariya ya fashe dashi " karya kikeyi wallahi haba An mata ni zaki layance mawa nine fa! ko kin manta bayane da kike hadani Allah annabi in siya miki kaza? "To ai baya kace yanzun kuma na girma,kuma ni ban tab'a cewa ka siya min kaza ba" " Allah wasa kikeyi ke tsaya ko kema kawayen ki sun zugeki karkici kazar ne? " Wallahi dariya sosai ya bata "kai Ya Abdul" tace tana dariya " Eh mana ba haka kukeyi ba to garama kici dan ko bakici ba ni inajin yunwa kuma sai nacii... " ya fada sai naciiiiin a iskance, Hararar shi tayi "to ai kasan wannan kajin na kawayen Amarya ne" ta fada cikin subutar baki, "zakumayi bayani to ci ki rage musu nasan ai bazai ciwu miki dukaba ni kuma kinga kifi zanci," " to "tace ciccire mata tsokokin yayi yana ajiye kasusuwan a gefe, "Yau wata rana wai kaza bata ciyuwa a wajen wata, kawai yarinya kice biyan bashi zakiyi kinci nasu suma suci wannan kai wallahi yaran nan sai a barku" ya fada yana dariya, "To ashe da nayi gangancin zuwa ba kaza da batun Musty ya tabbata da amarya ta rufema ango kofa, kai ai dole ma in ma gayun nan godiya sun cetoni daga kwana ni daya, kinsan nifa nama manta ana shiga dakin amarya da kaza kiji wani ganganci dukan mace da magariba," A baki yayita bata saida ya tabbatar cewa ta koshi sannan ya kyaleta tissue ya jawo ya goge mata baki "to zoki kwanta anan kafin in gama sai mu shiga daga ciki " ya fada yana kwantar da ita a cinyar shi, Wallahi duk baccin da takeji neman shi tayi ta rasa ya gudu ya barta sai faduwar gaba data dungajin yana kamata, shiko bai karabi ta Kanta ba maida hankali yayi ga abincin shi bayan ya gama, zame kanta yayi ya maida mata pillow din kujera a makwafin cinyar shi sannan ya tashi tattara ledojin abuncin yayi ya shige dasu cikin madaidaicin kitchen din dake saman saida ya ajiye ko wanne a inda ya dace sannan ya wanko hannun shi ya fito daga kitchen din, tanajin motsin fitowar shi ta tashi zaune tana mutsitsika ido, hannun shi ya miko mata ita kuma ta Kama ya dagota daga zaunen da take, wayoyin shi ya zuba cikin aljihu sannan yayi amfani da dayan hannun wajen daukar briefcase din nan, bata ankara ba taji yamata daukar cak, "Kai😳" tace tana zaro ido cike da mamaki "nidai ka sauke ni karka yarda ni," " ke yarinya irin ku guda goma in aka dauramin ku sai in zagaye gari ba tareda na gajiyaba," " to sannu iliya Dan mai karfi" Kai tsaye dakin shi ya masu masauki bai sauketa a ko ina ba sai kan gadon shi, kunna fitilun dakin yayi "masha allah" ta fada dan gaskiya ba hassada dakin yayi kyau, Dakin mai Jama'a nefa Ai dole asha kallo....... Kurukus kuje kuyi bacci🤣 *UMMIEE CE*✍🏼[10/14, 10:53 PM] Ummiee Zaria: ⚜️🔱👨‍👩‍👧‍👦 *DANGINA*👨‍👩‍👧‍👦🔱⚜️ *BOOK 2* *PAGE 49* Wayoyin shi ya kashe ya sasu a caji waiwaya wa gefeta yayi giran shi guda ya dag " ke yarinya tashi muje muyi wanka nima bacci nikeji" " Nayi wanka" ta fad'a tana turo baki a shagwab'e, "Eh aina gani amma wannan nina bukata," "to" tace dan tasan musu dashi bashi da wani amfani zaman lafiya kawai idan yace ayi to ayin, akasin hakan kuma asan me zai biyo baya, ita hauka takeyi ma da zata tsaya tana musu dashi bayan tasan daga ita sai shine a cikin sashen gaba d'aya! Ah ah wallahi zaman lafiya ai yafi zama sarki ma balle ita d'iyar Malam. Miko hannun shi yayi ya Kama nata hannun ya mikar da ita tsaye, kyakyawar runguma yamata tsam² a jikin shi yana mai sauke wadansu irin ajiyar zuciya masu kashe gabban jikin mace, Oh Allah wata dai aure rahamar shi daban ne, adacan idan ya matse mata waje har karkarwa takejin hanjin cikin ta suna mata saboda tsabar tsoro, amma yau daya rumgumeta sai takejin wani irin sanyin dad'i da nutsuwa na lullub'eta, Dan Allah inba aure ba wane mutum yasa mace a cikin d'aki daga shi sai ita su kulle kofa gida cike da mutane ciki harda iyayen shi dama wasu idon kunya, dan haka itama dai a wannan lokacin Bushe fitilar idonta tayi tak'ara rungumeshi tsam ta yanda takejin kamar ya bude mata cikin jikin shi ta shige dan wani kalar nutsuwar zuciya data gangar jiki takejin yana ratsata, Hijab din dake jikinta ya yaye yayi jifa dashi, Kwantar da kanshi yayi a saman kafadarta yana hura mata iska mai zafi dake fita daga cikin bakin shi zuwa cikin kunnen ta da wuyan ta a yayinda yake amfani da halshen shi yana d'an lasar bayan kunne da gefen wuyan ta, hakan da yake yi ita kuma shike k'ara kashe mata jiki dan haka sai ta k'ara kankame shi a cikin jikin ta saboda yanda tsigar jikin ta suke ta tashi tana jin yanda jinin jikinta ya k'ara gudu, Yanda ita kuma takeyin ne yasa shi kuma notikan shi suka fara warwara dan haka da zafi² ya dunga sakin mata numfashin shi mai kama da sheshekar kuka akan fatar wuyanta sai da ya taabbatar sakon da yake aikawa ya kai madakatar da yake bukata sannan yabi fatar wuyar nata da kisses din shi masu zafi tun daga cikin kunne kan wuya kafin ya dawo kan bakinta, Wallahi ita dai a lokacin nan allah ne kadai yasan yanayin data shiga dan wasu tsutsotsi taji sunamata yawo a gabobin jikinta sai dai cike da k'arfin hali ta fara k'ok'arin raba jikinta da nashi jin abun yana neman wuce waje kuma, Shi kuma ganin tana neman kwacewa saiya cusa duka tafin hannuna shi a bayanta ta cikin riga ya fara shafa gadon bayan nata kamar dai yana mata susar bayan, bata fara jin saukin kaikayin ba har saida yaci gaba amfani da hannuwan shi wajen shafo wasu daga cikin sassan jikin nata, domin daga susar baya sai taji yana neman juyar da ita dan haka dam ta kara rungume shi zuwa wannan lokacin itama kanta hannuwanta kaikayi sukemara dan haka bata kwaresu ba da gwarin gwuiwar ta itama na fara aikin lada, irin abubuwan da yakemata itama ta fara kwatan tawa ita dai bata san ya akayi ba kafin ta ankara ta sama rigar jikinta ta fita ko ta kasa oho dan bata san ya akayi da rigar ba domin jin saukar hannun shi kan nipple's dinta ne ya ankarar da ita cewar an fara shiga sabon babi, Karfi tasa wajen kwace jikinta daga gareshi tana waro idanuwa waje cike da mamaki kai wallahi maza dai bata ido fisabilillah da Wannan hasken tar a cikin d'akin ne ya wani kama ya cire mata riga, yaufa aka kawota shiko duk saurin da yakeyi ai dai in yana tsoron Allah kamata yayi ya d'aga mata k'afa har bak'in dake gidan su gama watsewa zuwa nasu garuruwan amma shine yake wani tab'ata. fisabilillah yanzun ya gama cin abinci fa bare tace yunwa yikeji, to in ma yunwar ne ai taga dai ita sunan ta Meenal ne ba tuwon daya saba narka kullum ba, Waiyo Allah ta fada a bayyane yayinda taji ya k'ara fusgota zuwa cikin jikin sha kai tsaye kuma ya k'ara maida hannuwan shi yama dukiyar nata wani irin matsa kamar mangwaro a hannun yaro, "Ya Abdul da zafi wallahi dan Allah ka bari"ta fad'a muryar ta na k'aryewa alamun dake nuna gab take da fashe mishi da kuka,shiko ina ma yasan tana magana mugun.... Abun nema ya samu ai nasan dama yau ba kanta, " Ya akayine yarinya?" ya tambaya da shakakkiyar murya ba tareda ya cire hannun a wajen ba, "Kaya nane fa in ban fara sauke hakki da wuri ba aiko Allah bazaiyi farin ciki da hakan ba karma Brothers din da suka had'a kudi suka biya min sadaki suji labari ai kema kin san idan na kyaleki naci amanar su, dan allah ki rufamin asiri karki hadani da Allah ki cuceni kar kuma kimin rowa ki kwareni, Baby idan kika hanani hakkina ayau zan hanu Amma ki sani kinci zalina kuma kin dauki alhakina kin san dai niba yaro bane sannan da lafiya ta ba karamar wahaltuwa nayiba tsayin shekarun nan, nasan allah ne yamin gata ya tsareni ban fada zinace² ba, Dan haka ina mai baki hakuri kiyi hakuri ki daure ki jajirce wajen kula dani ata ko wani fanni ina sonki da yawa shi yasa na kasa ba ko wacce mace matsayin ki a cikin zuciyata domin ko sau daya tsayin shekarun nan sonki bai tab'a barina na huta ba, Alhmadulillahi yanzun dai komai ya zama labari tunda kin zama tawa". ya fada a yayin da ya dagata sama yana jujjuyawa da ita kamar yanda akema yara, dukan su dariya sukeyi cike da nishadi, "Ni ina hauka ne zan yarda ink'i sauke hakkin ki in kwana cikin tsinuwar mala'iku ai hakan ma zunubin gangancine,ke baki san cewa gari na wayewa sunturin nan da akeyi na zuwa ganin amarya wasu da yawa gulma ne kawai yake kawo su dan suzo su gani ko ango yaci nasarar doke yan wasa a filin dambe ba, amma in bakya son ladan daren farkon ai sai inyi hakuri kuma har gafara ma sai na tayaki nema a wajen Allah dan nasan k'ila dai tsoro kikeji koh?" Ya k'arasa kalaman shi da tambaya yana d'age mata giraren shi kai mai Jama'a da shegen wayau yake wai ita yakema hannunka mai sanda, Saukota yayi k'asa ita kuma ta kara rungume shi tana rufe kirjinta da jikin shi, yana dariya yace "ya akayi ne? tubewa zanyi muje wankan ai saurin me kikeyi Baby?" Kunya sosai maganar shi ta bata dan haka sai ta saki jikin shi ta juya baya da hannuwan ta tayi amfani wajen kare kirjinta duk da sunfi hannun nata girma amma dai yafi ta sake su a haka tsirara, Baiji kunyar taba haka ya kama kayan jikin shi ya cire ya rage daga shi sai gajeren wandon shi na ciki, ta baya ya lallab'o ya rungumenta bayanta daba komai ya mannu da faffadar kirjin shi da ba komai sai kwantaccen gashi, da hannun shi yayi amfani wajen zagaye cikinta, kwanto da kanshi yayi dai² kunne ta ya furta mata, 'yane kin shirya"ya k'arasa fada yana huramata iskan bakin shi cikin kunne "nidai sanyi nikeji bazanyi wanka da daren nan ba," Ta amsa dashi tana lak'e kafad'a, "Haba Baby karki damu sai muyi amfani da ruwan zafi" " A'ah nidai bacci nikeji kaje kayi wankan ka fito zan jiraka anan" "Bashi yuwuwa yarinya kafata kafarki" ya fada a yayin da yake juyo da ita gaban shi baiyi wata² ba wajen hade bakin shi da nata bakin shi na cikin nata yaci gaba da magana " kin san bana son musu koh?" kadan² ya cigaba da shan bakinta tun yanayi a hankali har ya fara warwarewa yana kara kaimi, wallahi kasa bujirewa tayi duk da yanda taso ta kame kanta abun da takeji yak'i rik'uwa dan haka bata san ya akayi ta biye mishi sukaci gaba da murza totur ba, bai sassauta ba saida yaga alamar tafiyar tana so tayi tsayi dan gab yake da idasa warwarewa sannan yamata daukar cak zuwa cikin makewayin, Itadai bata gama dawowa daga sararin samaniya ba sai da taji zubar ruwan sanyi a jikinta dan a k'arkashin shower ya tsaidasu dan haka sanyin yana ratsa ta ita kuma saita kankameshi tana b'ata fuska "Ya akwai sanyi fa" "na sani"ya fada yana mai taran ruwan a tafukan hannun shi ya watsamata a kirji, Dukewa tayi shi kuma ya kama dariya, atakaice dai badan taso ba haka Mai Jama'a ya wanke mu tas itadai mai sauran kunya bata yarda ta bud'e idoba har akaci aka sid'e, towel ya jawo ya daura mata bayan shima yasa rigar wanka a jikin shi sannan yamata nuni da tayi alwallah, bayan sun fito shi ya jasu sallar nan mai falala ta ma'aurata kamar yanda sunnah ta koyar to yau suma munbi sahu kuma yayi masu doguwar addu'ar samun zaman lafiya da zuria masu albarkha, bayan sun idar itadai bata tsaya wani iyayin shafe²n mai ba turare kawai ta feffesa sai Vaseline data murza a baki dan bata son lebenta suna bushewa, Da towel din jikinta ta haye gado ta lume cikin bargo tana mai addu'ar Allah ya kawo bacci ya yi gaba da ita kafin lokacin da zai hawo gadon, Shiko dan gayun sai da yayi zama na musamman a gaban mirror yayi shafe² bayan ya gama yabi sassan jikin shi da turaruka masu dadin shaka saida ya gamsu cewa komai yaji sannan ya iso kai tsaye zuwa gadon ya haye da bismillah yana neman sa'a wajen ubangiji, cikin bargon ya shige ba tareda jiran iso ba, Wallahi AK tantagaryar mara kunya ne a tuben shi yake fa tuf bata san hakan ba sai da ya hada jikin shi da nata, Itadai tsit tayi kamar mai baccin gaske taso taci gaba da pretending amma ina jikinta yak'i bata had'in kai dan haka nan jikinta ya Kama rawa to fisabilillahi ai dole jikin mace ya kwashi rawa kukoh abunda baka saba dashi ba kwana fa da k'ato a gado d'aya kuma dan tsabar son ya nuna ma duniya cewa shi din digirgirarren tuzuru ne kawai ya wani shige mata bargo a tub'e🤔 to dai Allah ya shirya mutum kawai mu dai zamuce..... Da wayau ta samu tad'an k'ara jan jikinta gefe kamar irin a magagin bacci, Sai da ya bud'e idon shi ya k'are mata kallo da kyau dan har lokacin jikinta bai daina rawa ba duk yanda ta dunkule kuwa, Bai damu ba sai ma jan nashi jikin shima da yayi yabita ya k'ara matse tazarar data bayar tsakanin su, Kafar d'aya ya d'aura a saman cinyarta hannun shi d'aya akan konkoson ta sannan yakai fuskar shi wajen gashinta da hak'orin shi yayi amfani wajen janye ribom din data d'aure gashin dashi kafin ya maida hancin shi cikin gashin yana shakar kamshin da gashin keyi, "Muah"ya sauke mata kiss mai k'ara a saman kai yana k'ara matseta a cikin jikin shi gefen kunne ta yakai bakin shi yana huramata iskan bakina shi a cikin kunne yayinda k'afar shi da hannu basu iya tsayawa waje d'aya ba dan haka tuni jikinta yaci gaba da rawa ba kak kautawa kamar wacce zazzabi ke shirin rufewa, Da karfi ya juyo da ita jin tana son yi mishi gardama dan ta wani kama towel din ta cukuikuye shi a jikin ta to shi har itace ma zata wani gwada mishi k'arfi, dan haka yana juyo da ita baiyi wata² ba ya haye saman jikinta dan tsabar mugunta kuma haka nan ya sakemata nauyin shi kafafuwan shi yasa ya raba nata kafafun da karfin tsiya, dan hadesu tayi gam, hannuwan shi kuma basu tsaya waje daya ba duk inda hannun shi ka iya zuwa saida ya sadashi dashi da wayau ya dunga murza jikin shi a nata har yayi nasarar zame towel din tana daura towel din ya koma gefe shi kuma yana ganin hakan ya fincike shi ya watsar a k'asa, Ita kuma hakan ne yasa ta kwalla k'ara, "Waiyo Allah dan Allah kayi hakuri wallahi ni bacci nikeji kuma ma bani da lafiya yasin kuwa" Sai da kifa kanshi a tsakiyar k'irjin ta yana murzawa kafin yakai hannun shi kan cikinta yana shafawa a hankali sannan ya iya amsa mata da wata iriyar murya wacce bata fita da kyau yace, "Nima bana da lafiya kuma ke k'adaice maganin damuwa ta ki d'aure ki tsaya in samu nutsuwar da nike nema a tareda ke nayi alkawarin bazan baki wahalar da kike guduba, nima ai bazan yarda gari ya waye azo aga amarya ta kasa tafiya dai dai a tafi dani a baki ba d'an kad'an kawai zaki sammin," Yana gama surutan shi ya maida bakin shi akan abubuwan da suke ta zagin mishi k'aniya tun d'azun, Hannunta duka biyun ta d'aura a kanshi a kokarin ta na ganin ta tureshi daga aikin da yake sai dai kamar mayen k'arfe haka ya kafe kanshi a wajen ko gezau, Daga tana neman rage mishi lagwada ma sai ya had'e hannayen nata duka biyu bayan ya mai dasu ta saman kanta ya rikesu da hannun shi d'aya Dagowa yayi yana bin fuskarta da kallo kafin yakai bakin shi kan nata bakin ya lasa ita dai runtse idonta gam tayi dan bazata iya kallon shi a wannan yanayin da yike ciki ba, "Ammina ina rokon allah yanda ya cikamin burina na mallakeki ayau daya kara cikamin wani burin nawa ya bani ikon yin ajiya anan" ya fada dai² sanda ya maida hannun shi kan mararta yana shafa marar a hankali wanda ita kuma yasata yin wani irin bank'ara babu shiri dan sosai shafar ya shigeta, "Ameen ya Allah"ya amsa ma kanshi muryar shi cike da farin ciki, nima dai na tayashi da Ameen a cikin zuciyata. Cigaba da wasa da hannun shi yayi daga kan mararta zuwa saman yen tagwayenta yana kuma bi yana lasar wuyarta, Ajiyar zuciya mai nauyi ya dunga saukewa a bayyane sanda ya maida duka hannayen shi akan su, "kin san batun yau ba nike da fushin su! Ina son su sosai kici gaba da kulamin dasu kinji? Kuma banajin dadi ina magana kina min shiru ki dunga bani amsa da baki," Shirun tayi yanzun ma bata amsa ba, Dan haka sai k'ara matse ta da k'arfi a jikin shi "to zan gyara" ta amsa a wahale jin numfashin ta na shirin guduwa ya barta, "Yauwa yar kanwata" bakin shi ya daura akan guda yana mai tsotsa cikin sigar tsokano zance bawai ya turbutsa shi a bakin bane a'a yayi amfani da hannun shine wajen tumbulo su sannan yakai bakin shi kan nipple's din yana wasa da halshen shi akai sannan sai ya dan rike su da labban shi yana massaging kansu. Tayi zaton ko abin na wasa ne dan tun d'azun take rik'e kanta dan kar yaga lagonta ya rainata amma yanzun kam tabbas tasan ta fad'a rijiya dan bata san wani tsautsayin yakai hannu ta saman kanshi ba , Itafa burita ta tureshi ne dan taji yana neman ballo mata ruwa dan sosai gab'obinta suka bud'e suna amsar sak'on nin shi Ashe takai Kainta makasa ne, To kafin dai ta ankara gaba daya ya riga ya fice a saiti kamar ba mai jama'an data sani ba, Dan da gudu ya saki abin duniyar ya dawo kan bakinta dake mishi magiya akan yayi hakuri ita bacci takeji, Hannu ya mik'a gefe ya kashe hasken d'akin yayi duhu gaba d'aya a hankali ya karanto addu'a kafin a tsanake ya fara neman hanyar shi bada garaje ba dan baya son yayi abinda zai tona ma kanshi asiri, Kan kameshi tayi a sanda yake goga jikin shi a nata

Chapter 88 of 92