gidan na hajiya dai babu yara balle ta aiki wani daga cikin su,
Sai dai kuma tana shiga dakin kira ya shigo wayar ta koda ta duba kuma sai taga malam ne ya dawo mata da kiran da tayi mishi d'azun bai dauka ba dan tunda ta dawo gidan kullum ne zai kirata dan ya tambayi ya take da fatan hajiya bata matsa mata kamar wata wacce hajiyar zata dafa ta cinye,
To anyi rashin sa'a yau din gaba daya basuyi yawa ba dan tayi sammakon zuwa makaranta wanda hakan yaja harta mance da wayarta data kashe tasa a caji,
Sun dade suna hira bayan sunyi gaisuwa kafin ya mata saida safe ya kashe wayar,
Gyalen dake kanta kwai ta gyara ta d'auko kudin ta sauko, babu kowa a falon sai Sadeeq dake waya, AK da Musty duk bata san ina sukayi ba garama hajiya taji motsin bude kofar dakin ta d'azun da alama ciki ta shige,
"Ah ah an matan Hajiya sai ina kuma?"
Sadeeq ya tambaya yana dan kauda wayar daga bakin shi,
"Kofar gida zani zan d'an siyo abu a shagone yanzun zan dawo"
"Kawo in amso miki Kiyi zaman ki dare ya farayi"
Kai😳" ta furta tana zaro ido, ina ita ina aiken Sadeeq siyo pad fisabilillahi,
"Ya akayi ?"ya tambaya
"Ah ah ka barshi dan Allah wallahi yanzun zan dawo kaga ai waya kakeyi"
"Kawarkice ko in baki ku gaisa ne?"
Bata tsaya ba tana ficewa daga falon take cewa "ah ah kace ina gaisheta"
Koda ta fito babu kowa a harabar gidan sai hasken wutar lantarkin daya haska ko ina ya fito fes kamar ba dare ba, daga can bakin gate kuma masu gadine zaune suna hira a tsakanin su,
Karasawan da tayi kusan sune kuma hakan yasa daya daga cikin su mai suna Isah tasowa,
"Zakiyi aike ne Hajiya?"
"Ah ah ya Isah ba bu wani abu jeka zauna kawai zan amso da kaina"
"Haba Hajiya gamu zaune ba wani abun mukeyi ba ai da nauyi mu barki kije siyan wani abu da kanki da girman kujeran ki ranki ya dade"
Da murmushi a fuskanta ta amsa mishi da cewa,
"Allah kuwa ka koma ni da kaina zanje ai ba zama zanyi ba kafin ka sani na siyo na dawo"
"To shi kenan ranki ya dade tunda kince haka a dawo lafiya"
Ya k'arasa ya bude mata kofar ita kuma ta fice a gidan,
Duk da cewa a wasu unguwan nin za'a iya cewa dare ya farayi ta yanda zirga zirgan mutane zakaga ya ragu su nan ba haka abun yake ba domin yawancin darare a cike wajen yake kasancewa da mutane sakamakon wadannan shagunan da suke raya unguwar akoda yaushe baya rabo da jama'a inba tsakiyar dare ba,
Bata tsaya bata lokaci ba taje chemist din dake nan ta siyo pad din guda d'aya kafin idan taje asibiti gobe zata dibo wasu,
Tana siya din kuma ta dawo gida, wannan karan ma Isah ne ya bude mata domin tana tsaye harta je ta dawo,
AK ta hango zaune a cikin motar shi ya kunna fitilar cikin motar sautin kid'a na tashi kadan kadan shi kuma yana zaune a mazaunin driver sai dai bai kulle kofar motar ba domin kafar duka biyun ma ata wajen motar suke yana danna waya,
Murmushi tayi, kasa kasa take cewa,
"Mutum bashi da aiki sai na cire manyan kudade yana siyan manyan motoci to muma dai baza'a mana Kuri ba atoh,"
Key din motar ta na wajen Sarki dake rike a hannun ta wanda dama ta fito dashi ne da niyyar idan zaka koma ciki ta bud'e kofar motar akwai sakon da Meelat ta bata d'azun a makaranta shi take son dauka a cikin motar,
Sai da ta jinjina mukullin da kyau sannan ta matsa luck daga inda take tayi unlucky din motar, har wani canza tafiya take a yayin da take k'arasa wa zuwa wajen motar,
Shi kuma AK dake zaune yana amsa waya ta Bluetooth din dake kunnen shi daya wayar dake hannun shi kuma yana duba sakon ni karar da motar tayi ne yaja hankalin shi zuwa gareta dan sam bai san da wanzuwar ta a wajen ba,
Kallo yake binta dashi cike da burgewa domin shi dai a yanzun kam allah ya sani babu wani abun halittan da baya gajiya da kallo wanda kullum yake fatan ya dauwama yana kallo kodan samuwar farin cikin zuciyar shi irin yarinyar nan,
Shi dai yasan bai taba jin son wata yarinya irin yanda yake jin sonta a cikin ko wani fitar numfashin shi,
Ji yakeyi kamar inbai sameta yana iya rasa numfashin shi,
Wallahi ko nawa za'a nema a wajen shi zai bada koda ko kafatanin dukiyar shine dan dai kawai ta zama mallakin shi.
Dan haka da kallo yaci gaba da binta yana jin wani yanayi mafi kololuwar dadi na lullube shi, har zuwa sanda ta isa wajen motar ta wani bude ta da still,
Murmushi yayi a bayyane ya furta cewa "da alama dai yar kauye tayi agogo shine ake mana kaud'i"
Kallon ta yaci gaba dayi yayin da ita kuma ta shiga cikin motar ta zauna, saida tayi warming motar da kyau kafin ta fito daga ciki ba tareda ta kashe motar ba ta zagaya ta bud'e bayan motar ta cire sakon da take son d'auka sannan ta maida booth din ta rufe ta Kara komawa cikin motar ta zauna itama kafafuwan duka guda biyun suna waje kamar yanda ya zauna,
"I will call you back John please excuse me"
Ya furta cikin harshen turanci bai kuma jira amsar John din ba ya yanke wayar,
Takowa yayi zuwa inda nata motar yake bayan ya tura murfin nashi kofar motar ba tareda ya kashe ba har ya iso inda take,
Tun tasowar shi idanuwan ta ke kanshi tana mishi kallon kasan ido ba tareda tayi yanda zai gane cewa kallon nashi takeyi ba, har ya iso inda take, yana karasawo kuwa kamshin turaren shi gaba d'aya ya lullube wajen, wanda dole saida ta runtse ido tana mai bude kofofin hancin ta dan taba turaren nashi damar isa cikin kwalwarta da kyau......
*UMMIEE ZARIA*✍🏼
[8/20, 8:48 PM] Ummiee Zaria: 🔱⚜️👨👩👧👦 *DANGINA!*👨👩👧👦⚜️🔱
*~{{MY FAMILY}}~ BOOK 2.*
©® *UZ-2023.*
*RUBUTAWA*
*ZAINAB USMAN*
*~{Ummiee Zaria}~*
*Page 5.*
Ke farar kura wai me yasa kika raina nine?"
"Ni kuma fisabilillahi to me kuma nayi maka yau daga dawowar ka?"
Itama ta maida mishi da tambaya.
"Oh baki ma san me kikayi min ba kike cewa?"
"Eh"
ta bashi amsa a takaice.
"Da kyau amma kin san dai tunda na shigo ko gaisuwa bai had'ani dake ba koh?
Ko shima gaisuwar ban kai darajar da zan same shi daga gareki bane?"
Ya k'ara tambaya yana kureta da kallo.
A yayinda ita kuma kunya ya rufeta, dan sosai taji rashin kyautawar hakan,
"Kayi hakuri na manta ne ban gaisheka ba,Ina wuni ya hanya dafatan ka dawo lafiya?"
"Lafiya kalau alhamdulillah, ko kefa!"
"kuma ma ai laifin Kane tunda kaine ka shigo ta kofar baya ka bani tsoro yasin nayi zaton aljanine!"
"Oh shi yasa kika kirani da suna fatalwa dan kawai na biyo ta kofar kitchen? Kuma ai nayi sallama keda kakarki da kuke ta surutu ne bakuji ba"
Sai da ta maida kanta k'asa saboda abunda take son fadi tasan bazata iya fadar shi a yayinda take kallon cikin idon shiba kafin tace.
"To ai manyan kaya naga kasa kuma fa sai faman murmushi kake tayi shi yasa kawai nayi zaton ba kai bane, amma da kayi magana aina gane cewa kai din ne dai da gaske,"
"Manyan kaya!
Murmushi?"
Ya tambaya yana dage mata giran shi guda daya a yayinda ta d'an d'ago nata kan tana kallon shi kad'an kad'an,
Sai da tayi yar karamar murmushin ta dake bala'in burgeshi kafin ta amsa mishi da cewa...
"Eh mana Allah kuwa nidai banfa tab'a ganin kasa manyan kaya harda hula irin yauba, ko lokacin bikin su Aunty Sas da Anty Fati duk kana nan kaya kasa, kuma kai ai kullum fuskarka a murd'e take"
"Kamar fuskar shanu ko?"
Ya tambaya yana tsare ta da ido,
Sai da ta kauda kai kafin ta amsa da cewa,
"Eh mana sai yau kawai naga kanata murmushi harda dariya da kyakyatawa ka dunga yifa,shi yasa ni kuma nace fatalwa.
Dan ma ba kaga yanda manyan kayan da murmushin fuskar ka suka sa ka k'ara kyau kamar wani ango bane, allah da kullum bazaka yarda ka dunga d'aure fuska ba,"
"Ango dai!"
Ya tambaya da mamaki,
Ita kuma ta amsa da cewa
"Allah kuwa koda yike kuma gara dai ka dunga d'aure fuskan naka saboda yan matan dake nacin binka kamar wani namar kasuwa"
Ta k'ara furucin ta da d'aure fuska sab'anin farkon zancen data d'auko shi da murmushi a fuskar nata,
Murmushi yaci gaba dayi, yana jin wani irin farin ciki da dad'i mara musaltuwa, domin dama ai shi abunda yake muradine wato ta yaba kwalliyar kuma gashi ta yaba d'in duk da dai cewa ita bata san manufar shi nayin kwalliyar ba, in ko haka ne ai shi abubuwa zasu zo mishi da sauk'i koba komai ai gashi yanzun ma ta bashi wani k'arin haske, akan yanda zai samu damar kwamushe zuciyar ta a saukake,
Dan haka a can kasan zuciyar shi ya tsinci kanshi da furta cewa,
"Anything for you my ❤️ love "
Dan haka fuska cike da murmushi kana kuma yana girgiza kanshi ya nunata da yatsar shi manuniya duk a lokaci d'aya.
"Ke wallahi yarinyar nan fitinan niyace, oh kice k'aremin kallo kawai kikayi a d'azun din bawai tsoron fatalwa ba, to tunda har kika samu damar kallona a arha sai kin biya farashin kallon,
Toma wai waye yace miki nid'in bana dariya neh? Inda bana dariya zakiga mutane na bina ne? Ko kin manta in kiyata ne *MAI JAMA'A*? "
K'ara matsar da jikin shi zuwa kofar motar yayi ya wani jingina kafadar shi da kofar motar ta inda take zaune yayi tsayuwar a karkace gamida d'an rage tsayin shi ta yanda tsayin nashi zai dai da ita da ita dake zaune, hannun shi duka biyun kuma goye suke a kirjin shi, ya kuma karkato gaba daya ya rufe ta kafin yace..
"Fad'amin yarinya kenan dai na miki kyau, koda yike ai kin riga kin fad'ama miye nawa na tambaya kuma"
Dariya ta fashe dashi irin dariyar ban haushin nan tana nuna shi tace.
"To sai me dan nace kayi kyau ko bakayi kyau ba,halan baka yarda da kanka bane? ai dai kasan ni ba abokiyar adawar ka bace ba kuma zanyi maka hassada ba koba komai ai nima mai kyan ce ba kuma fina kyau d'in kayi ba,balle inyi kishi dan kawai nace manyan kaya da murmushi na maka kyau bawai yana nufin na yaba bane, kawai dai ka d'auki hakan a matsayin shawara ina ganin idan ka rike hakan a gaba zaiyi tasiri ga matar da zaka nema kasan wasu matan sun iya jefa kansu a had'ari wajen auren abu mai kyau"
Katseta yayi da cewa
"Kefa? Ke baki son abu mai kyau d'in ne?"
"Tab aini matsala na da namiji mai kyau bai tab'a zama mijin mace d'aya, domin ko bai nemi mace ba su matan zasu neme shi kaga kuma ni mijina nike da burin aure bawai mijin wata ba dan haka babu maza masu kyau a lissafina sai wanda na tabbatar da cewa shi d'in zai kasance nawa ne bana kowa ba🤷🏻♀️ ina nufin bazan tab'a rabashi da wata macen ba zai dauwama ne a matsayin mijina ni kadai"
"Hummm" ya sauke ajiyar zuciya mai nauyi,
"Kenan in irina ya nuna yana sonki ba zaki amince ba?"
"Zan amince idan na tabbatar da gasken gaske yake son nawa kuma bashi bayi min kishiya"
ta k'arasa fad'a tana karkata kai,
Dariya ma ta bashi wallahi dan haka yako kama dariyar abunshi dan ya tabbatar har yanzun da yarinta sosai akan yarinyar nan, a cikin dariyar nashi ne yake cewa.
"Ashema karamar kwalwa gareki yarinya tunda har zaki yarda idan namiji ya miki dadin bakin cewa dake kadai zai dauwama har karshen rayuwar shi, to ma idan ya miki alkawarin kuma zuwa gaba allah ya kaddara cewa dole saiya k'ara auren ya kenan zakiyi?"
"Sai ince ya sakeni" ta fad'a tana bata fuska da turo baki.
"Ai kaji matsalar yarintar ba, to idan kin fito kina da tabbacin samun wani mijin single wanda bai da mata kuma shima kina da tabbacin zai iya zama bai miki kishiya ba? Ko koh haka zakiyi ta aure kina fitowa da zarar miji yace zai k'ara aure?
Koda yike muma bar hirar nan dan bazaki gane me nike nufi ba, yanzun fad'amin ya zaman gidan ina fatan kina jin dadin shi tunda kika zab'i dawowa cikin shi ki zauna? "
"To wai kai dan Allah laifina kake gani?" Ta tambaya muryar ta cike da rauni,
"Ah ah ni bance ba, nasan dai zama da Hajiya ne kamar yanda zuwa yanzun nasan kin fara tantancewa"
Dariya tayi sannan ta daura da cewa
"Hajiya hooo wannan matar Allah dai ya yafe mata yanda duk tabi tasa min ido bani da katabus harta abincin da zanci so take tace sai wanda ta zab'amin zanci kamar a cikinta zansa abincin, nama gode Allah daba uni nikeyi a gidan ba, kasan Allah da naga ta fara sababin ta nike sulalewa inyi makaranta koda ko bani da lecture"
Dariya suka sa dukan su ita dashi din,
"Hajiyar ce yar sa ido koh? Aiko sai na fad'a mata,"
"Amma aini dai kaine ka tambayeni ni kuma na baka amsa"
Ta fada tana tab'e baki a shagwabe,
"Wai akwai bak'in da akayi a cikin gidan nan ne?"
Ya tambaya
"Babu kowa fa daga ni sai Hajiya dan Hajiya Jummai ma ta tafi Abuja jiya, me kagani ne kake tambaya hala?"
"Ok nayi zaton ko anyi bak'ine danaga wannan motar ai"
"Wannan motar wai? Mota tace fa bayan tafiyar ka aka kawo min!"
"Motar ki😳?" Ya tambaya da mamaki a cikin muryar shi zuwa kan fuskar shi duba da yanda yayi tambayar yana k'ara ma idanuwan shi girma.
"Eh tawa kuwa ko ance maka dama kaine kad'ai aka yarjema hawa manyan motoci ka dunga yawo a gari,"
Ta fadi hakan kasa kasa sosai ta yanda a zatonta bazaiji maita furta ba sai dai kuma cikin rashin sa'a tsaf yaji me tace d'in.
"Waya siya miki mota?"
"Lallai ma kenan da kai kallon talaka kake min bani da kudin siyan mota kome?"
"Ki dai bani amsa tukun, eh kuma nasan baki da kudin siyan motar tunda kika kasa iya siyan turare da kudin ki uwar mak'o dake ne zaki cire kud'i masu nauyin da zasu siya motar nan?"
"Nagode tunda gorin turaren da kake siyamin ina fesawa yau kake min, kuma tunda abun ya zama haka ka fad'amin kud'in turaren naka dana fesa ni kuma zanyi lissafin adadin kwalaben daka siyamin in biyaka kudin ka, dan in tabbatar maka da cewa nima mai arziki ce,"
Ta fad'a fuska a daure, kana kuma sai ta gyara zaman ta ta maida duka kafafuwan ta duka biyun cikin motar ta mik'a hannu ta kwaso sakon data ciro a booth d'in motar da pad d'in data ajiye duka a kujerar mai zaman banza,
Key d'in motar ta cire bayan ta kashe motar, tana kokarin fita sai dai kuma shid'in da a yanzun ya mik'e daga kishingid'ar da yayi a jikin motar a d'azun yanzun saiya zamana gaba d'aya ya babbake bakin kofar,
"Kabani hanya zan shige ciki dare yayi"
"To ya muna hira zaki shige ciki kuma ko kinyi fushine dan na tambayi wanda ya siya miki mota?"
"Eh nayi fushin ai wannan ma tambayar rainin wayau ne, wato ni gidan mu babu mai arzikin da zai iya siyamin mota ya bani kenan kake nufi, naga dai kafin wannan motar na hau wasu wancan ma in baka manta ba motatace"
Ta fad'a tana nuna d'ayar motar ta.
"Kuma kafin ita nahau wata, in kuma son sanin wanda ya siya min kake to mai sona ne ya siyamin dan wanda keson Kane kadai yake maka kyautar da har abada bazai maka gori ba"
"Ke wai ya kike wasu maganganu kamar wacce dama take jirana ne, nifa kawai tambaya nayi, laifine dan nayi tambaya akan motar da ban san da zaman ta a inda nike da iko ba? Shine zaki kalli idona kice min wani wai mai sonki ne ya siya miki motar to kenan ni kallon mak'iyi kike min, kawai daga tambaya duk kin wani bi kin b'ata rai,
To kiyi hakuri ni banyi tambayar dan ranki ya baci ba"
Bata hanya yayi ta fito,
Tana shirin tura kofar motar da niyyar rufewa ne kuma kayan dake hannun ta suka watse a kasa ciki harda ledan pad din da take ta b'oyo dan kar ya gani,
Duk'awar shi da niyyar ya kwaso mata kayan yayi dai dai da sanda itama ta duka dan haka a bazata goshin su ya had'u dana juna ji kake kummm,
"Waiyo Allah goshi na,"
Ta fad'a dan haka shima babu shiri ya d'ago,
Kamo kanta yayi da hannun shi guda,
d'ayan hannun kuma ya fara amfani dashi da niyyar ya murza mata goshin nata data bugu,
Kici kicin kwacewa takeyi tana bori take cewa.
"Nidai ka sakar min kaina ai kaine kaja mukayi karo, waiyo Allah nidai ka kyaleni wallahi akwai zafi idan na shiga zan goga mishi Robb,"
"Oh so kike in bar miki kan yayi tsini uwa goshin jirgi? Salon in gari ya waye hajiya ta nemi ba'asi"
"Eh nidai bana so ka bari zanyi da kaina"
Bai yarda ya saketa ba duk da yanda take harbin shi da kafarta tana dukan shi da hannayen ta sai da ya murza mata goshin ita ko harda kwalla sai da tayi, kafin ya saketa,
Dafe goshin tayi da hannu guda d'ayan hannun kuma tana murza idon ta dashi a dole nan wai ita kuka takeyi,
Shi kuma ganin hakan sai ya duk'a kasa ya tattaro mata kayan.
"Ke wai ma ina kikaje ne da kika fito? "
"Shago"
ta bashi amsa da shagwababbiyar muryarta,
Ledan dake hannun shi ya bud'e wanda pad d'in ke ciki kafin yace
"bari muga mai aka siyo nasan bazai wuce kayan kwadayi ba," budewar ko yayi ba tareda ya jira amsar taba,
"Wallahi Allah nidai karka bud'emin abuna, aiba kai ka aikeni ba ina ruwan ka da abunda na siyo, ka bani abunna karka budemin bana so"
Sai dai duk har gaginta a banza danya riga ya bud'e, dan son ya k'ara kular da itama sai kawai ya wani cire pad d'in daga cikin ledan, ya d'aga pad d'in sama zuwa wajen fuskar shi yana k'are mishi kallo da kyau,
"Miye wannan d'in wai naji shi da taushi ko buredi ne, bakya son inci ne kike wani b'oyewa ba akwai buredi a cikin gidanba shine kikaje kika siyo wani"
"Koba buredi ba nidai kaban kayana bacci nike ji inba haka ba saina had'a ka da Hajiya"
"Allah ya baki hakuri ga kayan ki, karki manta kuma idan kin shiga ki kulle kofar,"
Mika mata yayi, harya juya da niyyar tafiya kuma sai ya juyo.
"Ke..."
Bata amsa ba duk da kuwa tasan da ita yakeyi.
"Kina jina fa"
"Ni ai suna na Ameenatu in ya maka nauyin fad'a ka kirani da Meenal ko Meenat"
"Ai na fad'a miki sunan Mamana ne kike da dan haka bazan iya kiraba, kuma dole duk sunan dana kiraka dashi ki amsa,
Duk bama wannan ba, karki yarda in k'ara ganin ki da yan iskan kayan dana sameki dasu a jikin ki d'azun, bazan hanaki zama tsirara in kina cikin d'akinki ba amma koda wasa karkice zakici gaba da fitowa da wannan shigar zuwa falon Hajiya dan bake kad'ai bane a gidan, ke ko kunya ma bakyaji bayan kinsan bak'i na iya zuwama Hajiya ko wani lokaci"
"To aikai ka shigo mana babu sallama tunda kafin in zauna sai da na kulle kofar falon"
"Na dai fad'a miki kar in kara gani,"
Yana gama fad'in hakan yayi gaba ita kuma ta take mishi baya babu wanda ya k'ara cewa komai a cikin su har suka kai kofar falon yana tsaye harta shige ciki ta kulle kofar falon da key kafin shima ya juya zuwa nashi sashen.
*** *WASHE GARI*
Kamar yanda Sadeeq ya fad'ama Yusuf cewa zai shigo garin na Zaria hakan ce kuwa ta faru,
domin kuwa da duku²n asuba tun gari bai gama waye ba ya baro garin abuja dan tun jiyan dama Musty ya kyankyasa mishi cewar abokin su fa ya fad'a soyyaya dan haka a zak'e ya kwana yana fatan yaga asuba dan ya kama hanya,
Su ukun suke Zaune a Fadar na mai jama'an wanda yake nan kofar gidan wato,
Yusuf
Musty
Da kuma Sadeeq din,
"Wase ka dubi girman Allah ka bamu labarin nan! Kasan cewar daren jiya bacci barawo ne kawai ya saceni amma k'arfe 4 tana bugawa na bud'e ido na fara shirin tahowa, sai yanzun kuma na iso ka wani tsaya kana ja mana rai,
Gaskiya wallahi alhakin mu kawai kake d'auka"
"Ba wani d'aukar alhaki ai na riga na rantse cewa bazan fad'a muku ba sai kun bani tukuici"
"Munji fad'a tukuicin me kake so Allah kuwa zamu baka"
Cewar Musty da yakejin cewa da da hali cikin zuciyar Yusuf din kawai zai shige dan yajiyo ko me nene cikin sauk'i dan Yusuf din tun safe yake mishi iya shege ko satar amsa ma yaki bashi balle ya gane ko wacece abokin nasu yake so,
Paper Yusuf ya dauka da biro ya rubuta musu account number din shi yayi rubutun manya ta yanda dukan su zasu iya hange daga inda suke,
Sannan ya ajiye musu a tsakiyar su,
"Gashi nan in fara ganin saukar alert masu nauyi a account dina tukun ni kuma in fad'e muku biri har wutsiya"
Yana fad'a yana yarfe hannuwa alamun ko a jikin shi dan haka sai ma ya d'auki remote din tv ya fara canza channels,
Tsaki mai kauri dukan su biyun sukaja kamar masu shirin rufe shi da duka,
"Eh kuyi tsakin ku gama na dai fad'a muku sharadina,"
Kusan a jere karar shigowar sakon nin ya sauka a wayar shi dake ajiye akan center table,
Dan haka babu b'ata lokaci ya mika hannu ya d'auko wayar alert din ne kuwa,
"Oh dama kun gama shawara akan nawa zaku siya labarin nawa ne da naga kun turo min amount d'aya a tare?"
"Kai Yusuf idan kud'in basu maka dawo min da kayana d'an fashin tsakar rana kawai inma banda rashin tsoron Allah muda keda hidimar biki a gaban mu mune wai zaka tasa kana mana sata"
Cewar Musty.
"Oh sata nema? To dan uban mutum nine nace mutum yaje ya tattago aure? In kasan baka tara kudin hidima ba ai sai kace su d'aga auren kawai,
Kunga ni bacci ma nike ji bari in koma ciki idan kun shirya jin labarin sai ku tasoni"
"In ka isa shege nike, mune zaka maida wasu yan iska bayan ka danni kud'i a account dinka ne zakace kuma bacci kakeji"
Sadeeq ya fad'a a yayin da ya mike yana huci yaje ya rufo kofar falon harda murza key,
"Allah ya baka hakuri, atoh bawai dan kunga kun fini girman jiki bane zaka wani rufo kofa waton kuci min uwa babu mai kwata na, to zoka zauna in baku labarin komai dan musan ta yanda zamu bullowa abun dan gaskiya nidai bana son muyi sanya gudun samun ko wacce irin tangard'a daka iya tasowa"
Ya k'arasa fad'a yana gyara zaman shi bayan yaci serious sosai,
Kowama Sadeeq din yayi ya zauna suka sa Yusuf din a tsakiyar su,
"Nasan dukan ku kun lura da canjin da AK yayi wanda a lukuta da dama munsha tambayar shi amma sai yace mana wai stress ne?"
"Kwarai anyi haka"
Suka amsa mishi dashi,
"Tun a shekarun baya nina
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 47 Chapter of 92