a wannan lokacin ba"
"Oh soyayyar ce tasa ka fara tunanin tsame ni a cikin *DANGINA* zuwa wata duniyar ta daban?
Kasan abinda yasa naji zan soka harma in rayu tareda kai a wancan lokacin?
Saboda tsubin nutsuwar da Allah ya maka na kuma yaba da kyawun halayyan ka,
Amma a yanzun daka fara fitomin da ainihin ka hakan yasa na gano rashin dacewar mu,
Abdul bazan aureka ba zan koma gida wajen Yayan babana wannan karon ma zan bashi dama ya k'ara zab'ar min miji a karo na biyu"
Tana gama fad'a mishi hakan ita kuma ta juya mishi baya ta fashe da kuka,
Allah ma ya sani kalaman AK sun bata haushi sun kuma kona mata rai,
Domin ko bai fito fili ya furta ba a cikin zancen shi ta shinshino rashin son da yake ma wanda ta d'auka a matsayin gatan ta, taya zata yarda so ya rufe mata ido harta tsaya a gaban shi yana neman zagin uban ta bata d'auki mata ki ba indai har itace so zaici amana irin haka to taci uwar son tasha ruwan kanwa maganin kwarnafin ciki,
Sanyi jikin shi yayi sosai shi kuma,
Shifa duk abinda ya fad'a bada mugun nufi ya furta suba yadai fad'ane kawai saboda ranshi da yake b'ace,
Ya ita kuma take neman juya zancen haka daga d'an magana kuma shine zatace wai ta dena son shi ta fasa auren shi,
Da sanyin jiki ya koma inda ta juya,
"Meenal "
ya kira sunan ta a sanyaye ita kuma sai ta k'ara juya mishi baya tana cigaba dayin kuka,
"Meenal Ina son ki karkice zaki juyamin baya a daidai lokacin da nike sa ran na kusa mallakar ki"
"Ni kuma nace bana sonka kuma ban auren ka tunda ka raina min uban da bani da kamar shi" ta karasa fad'a tana kara sautin kukan ta,
Wallahi jiri yaji yana neman maka shi da kansa,
"Ki rufa min asiri meenal bazan iya rasaki a wannan lokacin ba Ina sonki,
Kuma ni bada wata manufa nayi magana ba tsoro dai nikeji kar a maimaita abinda ya faru a baya kiyi hakuri ki fahimta"
Kara juyawa tayi ganin ya k'ara binta inda ta juya,
Haka sukaci gaba dayi duk inda ta juya shi kuma zai bita yana faman son ya fahimtar da ita cewa shifa bawai ya raina baban ta bane, kawai dai tsoro yakeji,
"Bana son..... " bai bari takai k'arsher kalmar ba da karfin tsiya ya jawota zuwa cikin k'irjin shi ya rungume a cikin jikin shi tsamtsam ya ta bude baki zataciga da masifa karaf ya had'e bakin ta da nashi ya fara aika mata da wasu irin mahaukatan zafafan kissing masu juya kwakwalen mata irinta wadanda basu saba keb'ewa da namiji ba,
Duka da yakushi ta dunga kai mishi a k'okarin ta na ganin ta kwace amma ko gezau baiyi ba,
Baya tayi da jikinta da karfi shi kuma ya biyota suka fad'a kan gadon dake kusa dasu yako k'ara danneta gaba d'aya batareda ya sarara daga aikin daya sa kanshi ba,
Astagfirullah astagfirullah
Astagfirullah yau dai duk yanda AK yake kai zuciyar shi nesa sai da bakin Yarinyar nan tasa hege shed'an ya kusa cin galaba akan shi domin dai rufe ido yayi ya tumurmushe ta saida ya murtsuke bakin rashin kunyar nan tsaf, itama dai tun tana ciccijewa tana tureshi har dan dole ta hakura ta nemi biye mishi dan jiki da jini atoh kuma itama dai a shekarun ta ai takai matakin da idan namiji yace mata kule zata maida mishi Cass ai wacce za'ayi wallahi, ๐
To dai ansha baki an kuma tsotsi kunne an lashe wuya kafin dai ayi batun kaima yan biyu da sauran sassan jiki hari Allah ya kwato mana gogan a hannun shed'an kila dai ya tuna cewa har yanzun ba'a d'aura auren bane dan haka a sanda jikinta ya amsa ta fara neman kai naushi itama shi kuma sai ya murgina gefe ya sauka a jikin ta yana faman maida numfashin dake neman d'auke mishi tun d'azun hakan ne kuma yabata damar jin kunyar kanta dan haka sai kawai ta dunkule itama taja bargo ta kudun dune a ciki dan bata da bakin magana,
To me zatace jama'a bayan saura kad'an ta mance kanta,
sai da yaji numfashin shi ya koma mishi dai dai kafin ya yunkura ya sauka a gadon,
"Tashi ki fita min a cikin d'aki tunda kin samu abida kike so, ban hanaki ba kuma in kinga dama anjima idan muka k'ara had'uwa shima ki k'ara fad'amin cewa bakya sona ni kuma bazan gaji da kawo ki nan inci gaba da ladafta bakin rashin kunya ba badai ni kika ce bakya soba?"
Yaye bargon tayi ta mik'e zaune,
"Ka daiji kunya wallahi mugu mai shan bakin mata kawai kuma nidai ban yafe tab'amin jiki da shan bakina da kayi ba"
"Ai saboda a iya bakin na tsaya shi yasa kika samu damar magana, duk ranar da hauka yasa kika kara cewa zaki rabu dani ko kuma bakya sona gonar ki zan shiga inyi b'arna wallahi an dad'e ba'a kaini kotun musulunci ba k'aramar yarinya kawai har nine ma zaki kalli idona kice bakya so dan kawai na fad'a miki gaskiya"
Kuka ta fashe dashi,
"eh din ba'a sonka kuma bana yin auren na fasa ko ko a k'afa aka daura min kai saina kwance na gudu inda bazaka k'ara ganina ba mai farin jinin mata kawai"
"Oh kice min dama kullum ashe target dina kikeyi shi yasa da nace idan kika k'ara cewa baki sona zanyi noma yanzun kika furta,
To bismillah inkin shirya nima na shirya k'aryar rashin kunya kikeyi"
Juyowa yayi ya nufo inda take, da wani irin zafin nama ita kuma tayi kifiya ta sauka a gadon kafin ya ankara harta bud'e kofa ta fice da shegen gudu ko d'an kwalin ta bata tsaya d'auka ba,
"Ke dawo ki d'auki d'an kwalin ki karkisa a fara yimin kallon d'an iska dan duk wanda ya ganki a haka ko nace ban tab'a kiba bazasu yarda ba mara kunyar karya dake kawai"
Ina itafa tuni ta haye sama abinta shi yasa ko jiyo shi batayi ba,
Su kuma su Sultana tun d'azun suka wuce sashen su Moon wajen Umma dan ita da kanta ta leko tayi kiran su Bayan da Hajiya ta bada sallahun a d'aura abinci kafin su dawo gidan acan ne kuma sukaji labarin d'aurin auren AK da Meenal din da akayi, dan haka Sultana ta sato jiki ta dawo falon dan ta fesa ma AK labari sai dai kuma tana shigowa ta hango Meenal ta haye sama da gudu bata gama tunanin dalilin gudun da Meenal keyi ba sai kuma ta hango AK kuma duk maganganun da yayi taji su rass dan haka sai zuciyar ta ya bata ko shima ya samu labarin d'aurin auren ne, shi yasa ya fara celebrating
D'aga murya tayi ta kira sunan shi
"Ya AK"
Bai amsa ba sai dai ya juyo yana kallon ta har ta isa gareshi,
"Congrats angon Meenal Ubangiji Allah yasa ace gara da akayi, muma yan baya Allah ya aurar damu" ta fad'a da fara'a sosai a murya da fuskar ta,
"Wai Yaya dama ashe ana d'aura aure ko ango baije wajen ba? Ni wallahi ban tab'a jin daga zuwa tambaya ace an d'aura aure ba sai yau, dan Allah kaje kayi wanka kasa manya kaya kaima kafin su Hajiya su dawo inba haka ba ai baza'a wani gane cewa kaine angon ba"
"Me kike cewa ne Sultana auren wa aka d'aura ne?"
"Lah wai basu kiraka sunce maka an d'aura ba? Tsaya ka gani"
Shifa shirme ya d'auki zancen ta ko kuma dai kila tana mishi wasa ne, dan haka sai kawai ya tsaya yana kallon ta harta d'aga wayarta ta d'anna kira, Number din ya Sheikh ta kira yana d'auka ko bayan tayi sallama ya amsa ta jefa mishi tambaya kamar haka,
"Ya Sheikh da gaskene wai an an d'aura auren ka da Fauxieyerh ita kuma Meenal da Mai Jama'a?"
"Ke kina Ina ne da kike kirana a yanzun? Bakya gida kenan"
"Nidai dan Allah ka amsa min tabbaci nike son samu kuma nasan kai baka k'arya"
"Eh Sultana Allah yayi a yau nasamu k'aruwar aure nima na zama ma gidanci"
Kit ta yanke wayar,
"Kaji koh Wallahi da gaske an d'aura dan ya Sheikh baya k'arya"
Kofar d'akin AK ya bud'e ya fito a tsakiyar falon ya yi sujudur shakur bayan ya d'ago sai da ya d'aga hannuwa sama yayi addu'o'i harda hawaye yana shafawa kuma baibi takan Sultana ba ya fice da gudu
Sashen Abba Ahmad ya shiga,
Akwai mata a falon amma bai damu daya tsaya gaishe su ba ya wuce da sauri yana kwala kiran Ummi,
"Kai lafiyar ka zaka fad'omin cikin gida kana wani kwala kiran sunana uwa dai sabon makaho"
Maman su Bilkisu daya wuce su a falon ne tace "bashshi Amina ke koh ango nefa"
"Da gaske ne an d'aura aurena da mai sunan ki ummi?"
"Da gaske ne mana ba abinda kake buri kenan ba dama?"
Rungume ta yayi yana dariya,
Dan haka sai itama ta rungume shi tana cewa "na tayaka murna Ina fatan kuma zaka riketa amana, Allah ya baku zaman lafiya da zuria masu albarka"
"Ameen Matan falon suka amsa shi kuma sai ya saketa daga rungumar daya mata ya juya ya fice daga sashen gaba d'aya tsabar farin cikin da yake cikine yasa bai tuna da wayar shiba tun d'azun sai yanzun, aljihunan shi ya fara lalube sai dai kuma baiji wayar ba, kenan dai a kaduna ya barta, komawa cikin sashen Ummi ya karayi da gud'a, Wayarta ya amso ya k'ara fitowa number din musty ya fara kira,
"Kana ina? "Ya tambaya bayan musty ya d'auka,
"Kai kana Ina yanzun haka?" Shima musty ya tambaya,
"Ina gidan Hajiya kazo yanzun please"
"Fito kofar gida ka jirani"
Yanke wayar yayi shi kuma AK mai makon ya fita wajen sai ya koma sashen Hajiya gaskiya fa Sultana ta fad'a mishi gara yaje yayi sabon wanka yasa manyan kaya shima ya fito a matsayin ango sak,
Kafin ya shiga d'akin shi har ya fara tunanin haurawa sama yaje yama Yarinyar nan albishir amma sai ya fasa,
Zaiyi lokacin tane anjima badai shi tayi ma rashin kunya ba hummm,
Bayan ya fito daga wanka cikin sabbin manyan kayan daya d'in ka da bikin Musty ya zab'o wata lafiyayyar farar shadda mai had'e da malum malum wacce akayi ma aiki blue din zare ya sanya, tsaf ya shirya ya fito a angon kafin ya fito daga d'akin hula a hannu sai zabgaga kamshin turaren dayayi ma jikin shi wanka yakeyi,
Kawayen Hajiya data kira ta shaida ma batun auren ya tarar a zaune a falon cikin su kuma harda Dadah turai,
Su kuma kamar masu jiran fitowar shi haka suka lullubeshi suna gud'a,
Gidan hajiya fa ya cika da makota mata suna cikin gida suna aikin abinci suna kuma jiran dawowar yan d'aurin aure,
Tunda su Musty suka dawo tudun wada suke wasa da motoci a majalisar su dan haka wajen ya cika dam da mata sa harda wad'anda basu samu zuwa can wajen d'aurin auren ba shagali kawai sukeyi abin su, dan haka sai shi kuma ya janye jikin shi yayi cikin gida,
Sasan AK din ya fara zuwa ganin kofar ya kulle yasan baya wajen dan haka sai ya wuce sashen Hajiya kai tsaye, a falon nata ya sameshi mata sun dabaibaye shi suna mishi gud'a yana Karasawa shi kuma ya ciro kud'i daga cikin aljihun shi ya farayima Ak manni dasu dariya.
*Ummiee ce*
[10/10, 8:51 AM] Ummiee Zaria: โ๏ธ๐ฑ๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆ *DANGINA *๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆ๐ฑโ๏ธ
*BOOK 2*
*PAGE 46*
*My Aleesah where are you? Ki sani tundaga kan wannan page din har zuw karshen labarin na sadaukar dashi a gareki domin kin cancanta na yaba kwarai da kokorin ki*๐....
Da kyal suka samu suka fice daga cikin falon suna dariyar Dadah wacce ta d'age akan cewa sam bata yarda da shigo shigo ba zurfin da aka mata kishiya da yamma sakaliya ba,
Haka kawai tana zaune daga zuwa tambaya sai taji tashin zancen wai an rangad'a mata kishiya ba notice,
Su kuma k'awayen Hajiya suna taya ta da cewa tabbas suma suna tayata kishi,
A harabar gidan sukaci burki bayan fitowar s daga falon suka nufi inda su Baba Usman suke, domin su Musty sun rigasu barin can gidan Malam shi yasa su sai yanzun suke isowa tareda uwar garken wato Hajiya.
"Kai ku matsa ku bani hanya in isaga mijin Aminatu Abdul Khareem d'ina haba jama'a haka akeyi duk kunbi dai kun yanyame min jika kamar wani naman kasuwa bazaku barshi ya iso gareni mu taya juna murna bayan kowa yasan cewa nice kashin bayan arzikin daya samu na auren jikata,
Nice nan fa k'ashin bayan nasarar shi wai a hakan ma dan auren yazo ne babu zato amma ji yanda aka cika min gidan dama unguwar kamar dai wad'anda akayo ma shela,
Zonan kaji mai Babban suna zo wajena kaji yau dai Alhamdulillah alkawarin Allah ya cika masu murna suyi akasin haka kuma mutum sai ya rufe kanshi a daki inyaso karya fito sai ranar kiyama"
Janye jikin shi yayi daga cikin abokan shi da suka baibaye shi suna mishi mishi murna da fatan alkhairi ya k'arasa wajen Hajiya da iyayen shi yana isa baiyi wata wataba yabata kyakyawan runguma,
"Hajiyata da gaske kun amso min auren ta? " ya tambaya cike da mad'aukakin fara'a a fuska da muryar shi,
Itama da fara'a sosai ta amsa da cewa..
"Da gaske ne mana Abdul ana wasa da igiyoyin aure ne dama?
Kai dai yau Allah ya nufa cewa rana bazata fito harta fad'i batareda igiyar auren ka ya hau kan mai suna naba,
Ka daiga ikon Allah koh!
Inda ace ayau din nan wani zai tareni yace min ke Amina ki shirya yau za'a daura auren jikokin ki tofa ina fad'a maka da sai na kalli kwayar idon mutum kafin in kirashi da suna mugun makaryaci,
Eh mana kaikoh tunda mudai nan mun saba komai sai an bishi daki daki kafin a kaiga batun daurin aure, kaga dai ayi tambaya na angani Ana so,
Idan an amince aba saurayi dama ayi zancen baiko dasa rana amma mu babu d'aya da muka gabatar tun bayan dai da iyayen ka suka ma wancan d'ayan uban nata batun shi kuma da yafi kowa iya shiririta yaje yayi ta sha'anin gaban shi bai tada zancen ba,
ai dole kowa yayi mamaki dajin batun auren nan tunda dukan mufa saida muka sallaci sallan azahar kafin mu fita zuwa can gidan,
To da Allah dai ya kaddara cewa yaune ranar kamar yanda yan magana ke cewa mutuwa,
Aure da haihuwa dukan su lokaci garesu to kaima dai yau naka ranar yazo amma kaga kai da yike Allah yana sonka shi yasama ya baka ni a matsayin kakarka gashi munje da batun sa rana amma mai makon hakan mun amso maka auren gaba d'aya"
Kara rungume ta yayi tsam tsam hawayen farin ciki na cika mishi idanu dan kamar yanda Hajiya tace ne koshi yau kam ya jinjina ma girmar kudurar ubangiji lallai Allah ne kad'ai keyi inyaso kuma babu mai hanawa tunda gashi yau allah ya mallaka mishi Meenal a dai dai sanda take cikin tutsu, dazun nan fa ta gama mishi rikicin cewa bata auren shi ashe daga shi har ita basu san cewa aure ya tabbata akan su a daidai lokacin ba, to kodai shaukin auren nema ya kwashe shi yau yakusa sab'a lamba?, murmushi mai fad'i yayi hawaye na zirarowa daga cikin idon shi,
"Nagode Hajiya,
Nagode kwarai ubangiji Allah ya bada lada,
Allah ya kara miki lafiya ya kuma raya manake kiyi jinkiri mai amfani da albarka ameen nagode kwarai kuma nayi miki alkawari insha Allah zan rike mai sunan ki da amana bazan taba yin abunda zaisa tayi kuka dani ba zan cigaba da sonta har zuwa sanda zanja numfashina na karshe a doron k'asa "
*Ameen!
Ameen
Ameen Abdul Khareem ubangiji Allah yasa albarka a cikin auren ku Allah ya zaunar daku lafiya Allah kuma ya baku ikon sauke hakkin juna hakika nafi kowa murna da faruwar wannan al'amari, Allah ya baka ikon rike Amina kamar yanda mai sunan ka ya rikeni har zuwa sanda mutuwa ce ta rabamu"
Ta k'arasa fad'a da muryar kuka idanuwan ta na zubda hawayen itama kamar dai shi,
Ameen jama'ar dake wajen suka amsa,
Bayan ya raba jikin shi dana Hajiya wajen su Baba Usman ya koma suma kuma saida ya bisu d'aya bayan d'aya ya rungume su yana musu godiya akan jajircewar su na ganin sun samar mishi abinda yake so Hajiya dai sashen ta tawuce bayan itama ta gama amsa gaisuwar jama'ar dake harabar gidan,
Shi kuma Musty da sauran abokan su sai suka janye AK zuwa kofar gidan cikin sauran matasan da suka cika unguwar suna taya shi murna,
Taro ne ya had'u na ban mamaki a wajen nan domin shi kanshi AK yayi mamaki da ganin yawan mutanen dake wajen, koda ya shigo gidan fa a d'azun dai dai kun mutane ne a wajen amma yanzun duk inda ka kalla jama'a ne tako ina, lallai AK ya tabbata mai jama'an na gasken gaske wai a hakan ma ba kowa yaji labarin zancen auren ba,
Matasa sunyi kara gaskiya dan duk wanda labarin yaje kunnen shi baya zama sai yazo dan k'ara samun tabbaci dan da farko da yawa wasu sun karyata zancen auren,
Dan haka kafin ka ankara unguwar ta cika mak'il dan ko abincin da Hajiya tasa aka dafa a cikin gidan kafin a fito dashi waje har ya k'are dan ma shi Musty tun dawowar su daga wajen d'aurin auren ya k'ara bada order a wad'ansu gidajen abincin banda na restaurant din dake nan kofar gidan nasu,
Ko kafin ace karfe 8 na dare tuni Yusuf da iyalan shi harma da Sadeeq sun hallara a gidan Hajiya suma kuma tareda nasu mutanen suka taho domin dai duk wanda akace ma an d'aura auren burin shi kawai yazo ya tabbatar ne dan kowa mamaki yakeyi wai AK aka d'aura ma aure babu gayyata to dan uban shi inma sune bai son gani wajen bikin shi sai sunje shagali sosai fa aka gabatar a kofar gidan Hajiya rana suma kuma matan suna ciki suna nasu,
A can gidan Malam ko bayan an gama d'aurin aure Hajiya da gayyarta sun wuce suma dai haka sukaci gaba da k'arbar bak'i yan zuwa Allah sanya alkhairi yan uwa nakusa suma dai tuni suka hallara duk da kuwa yanda abin yazo musu a girshe,
Baba Auta bai samu shigowa gidan ba sai gab magrib dan Baba Adamu ne ya kirashi ya shaida mishi abinda ake ciki,
Bayan an idar da sallah suna shiga gida Malam ya had'a kan Baba Adamu dashi Baba Auta a falon shi,
"Auta nasan ka samu labarin abinda Hajiya tazo tayi min a falon nan koh!
To Alhamdulillah ta gama nata nima zanyi nawa ikon, domin mu dai gidan nan tunda mukayi wayau bamu tab'a ganin inda aka gudanar da neman aure irin wanda ita ta jogoranta a yau ba,
Inda kuma nace zan tsawata a dazun din nasan kowa laifina zai gani to Alhamdulillah na bata dama itama kuma ta dama sai dai kuma tunda suka sa aka d'aura auren a yau tofa bazasu jingine min yarinya taci gaba da zama tana yawo da auren d'an su ba,
Kai Adamu kai da kayi jagora kaine zaka kira su ka shaida musu cewa yau labara ni kuma na tsaida ranar juma'an nan mai zuwa a matsayin ranar yinin biki da tariya dan haka su fad'i inda d'ansu zai zauna da ita gobe za'aje ayi mata jere, shi kuma Sheikh ka tambaye shi idan bashi da inda zai ajiye Raheenat d'in to akwai takardar gidan da Alhaji Mai Kud'i ya bashi jiya ya kawo min takardun tun a daren jiyan sai aje gidan aduba in akwai gyara kunga sai ya hak'ura da tarewa acan su zauna a wancan sashen dake gefen nasu Sa'eed tunda a gyare wajen yake kafin lokacin dazai koma Abuja,yauwa kuma karka manta kasa mai d'akin ka tayi list na duk abubuwan da basu had'o dashi ba na auren budurwa ciki harda lefe dan kar suga an d'aura aure suyi zaton ko sun sha, a kuma je a d'auko min ita Meenal din a can gidan ta dawo nan, sai abu na k'arshe karku manta ku kira sauran mutanen da basuji auren ba dan ranar juma'an dai za'ayi yinin biki dakai amare d'akin su, kuna iya tafiya na gama magana"
Yana gama fad'in hakan ya mike ya shige cikin bedroom din shi ya barsu da binshi da ido,
Baba Adamu ne ya fara mikewa kafin yace "muje koh auta dan kasan dai dole yanda yace din shi za'ayi muje in zauna da maman nin su inji yanda za'ayi batun kayan d'akin su in yaso sai muyi magana da Hajiyar kano tunda ga yanda abun yazo"
A daren Baba Auta yaja Mommy Hauwa zuwa sashen Baba Adamu basu tashi a zaman nasuba sai da suka kira Hajiyar kano suka gama magana akan kayan d'akin su Meenal din akan duk yanda ake ciki batun wajen zaman su Meenal din zasu kirata a yayin zaman nasu ne kuma suka kira itama Momin Abuja dan suji ko akwai inda Fauziya zata zauna acan din an kuma samu dan ashe tuni shima Sheikh ya tanaji gidan da zai zauna da nashi iyalin batun auren ne dai yaki maida hankali, Baba Usman suka kira akan batun wajen zaman Meenal shi kuma daya tambayi Hajiya sai tace mishi a sashen marigayi zasu zauna kafin ya k'arasa ginin shi su koma Kaduna, a cikin daren komai na shirin biki ya kammala a gidan Malam Sa'eed aka tura can gidan Hajiya ya taho da Meenal da Sultana,
a gefen Meenal tun bayan data haura sama bata k'ara marmarin saukowa ba, a sanda kuma ta fara jiyo hayaniya a cikin gidan ta dauki hakan kawai a matsayin gayyar hajiya ne dan haka sai bata wani damu kanta cewa sai ta sauko ta duba abinda akeyi ba, su kuma daga Moon har Sultana babu wacce ta neme ta har saida Meelat ta iso gidan sune kuma suka kira Maryam suka bata labari saidai koda suka haura saman sunyi bugun kofar d'akin da meenal ke ciki har sun gaji amma haka tayi kunnen uwar shegu dasu tak'i bude musu kofar har suka gaji suka juya,
Bayan anyi sallan ishsha'i har d'akin Hajiya tabi Meenal d'auke da takardar gidan da Sarki ya siya da sunan Aminatun, tana zama Larai ta shigo da abincin da Hajiya tasa ta d'iboma Meenal din tana ajiye mata ta fice ta barsu,
Ita kuma Meenal tun shigar Hajiya d'akin dama ta wani d'aure fuska dan karma Hajiya tace zata wani bata labarin yanda sukayi acan gidan su,
"Kina nan kin kulle kai a d'aki uwa dai wata matar mamaci kinaji ana hayaniya kin kasa fitowa Sarauniya Aminatu to ni dana matsu ai gani na biyo sahu, d'auki takardar nan ki dubamin ko takardar menene?"
Hajiya ta fad'a tana mika mata takardar, amsa tayi ta fara dubawa tun bata kammala ba ta d'ago kanta tana maida kallonta kan Hajiya,
"Hajiya... Tarar numfasjin ta Hajiya tayi da cewa,
"Eh abindai da kika karanta a rubuce haka yake, ba kullum burin ki shine ki siyama Baban ki Malam gida ba? To ga gida nan yau kin mallaka dan haka sai kije ki mallaka mishi sai me kuma kike da muradi yanzun? Iye uwar malam"
"Hajiya gida na?"
"Kwarai kuwa gidan ki yanzun nidai tukuici kawai ya rage ki bani tunda na isar da nawa sak'on"
Rungume takardar Meenal tayi tana dariya sosai cike da jin dadi tace,
"Hajiya kece kika siyamin gidan?"
"To da dai nace bazan fad'a miki gaskiyar wanda ya siya gidan ba saboda shi dai dan Allah yayi kuma yana son hakan ya zama sirri ba tareda kowa ya
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 83 Chapter of 92