amma su gwanayen sukak'i.
"Ke dallah can kyaleni inace ke mu ke ma duk wannan gatan!
Kwana nawa ya rage miki ki rasa yancin da kike dashi a matsayinki na budurwa zuwa matar auren da zamu kai gidan miji mu baro,
daga nan kuma keda yawo sai dai na zuwa unguwa shima sai da izinin isasshe baki ba damar fita kai tsaye a duk sanda ta raya miki dan kin riga kin zama d'aurarra, ke inya so nuna isan shi a kanki ma sai ya bari kin shirya fitan ya murza kambum iko yace miki bai san wannan, dan haka yarinya wannan shine damar ki na k'arshe dan haka karki wani damu da fad'an da zaiyi, dan ko gobe ma sai mun fita wallahi ko yana so ko baya so,
to haka kawai dan mutum ya fita bai gama abinda yakeyi ba za'a wani matsa mishi da kira, bari kigani yanzun muna fita zai rufemu da fad'a kalli fuskar shi ki ga yanda ya d'aureta Allah ni ban fiye son takura ba wallahi, shi kuma babu abunda yafi kwarewa irin yaga ya takura ma mutum"
Maryam ce ta fara bud'e gaban motar ta fito sai Meelat dake gefen mai zaman banza kafin Sultana dake baya tare da Meenal itama ta sauko daga cikin motar ita ko oganniyar gyara zama ma tayi abunta bayan ta d'aga kiran da Salman ya mata dan dama tun da yamma da suka had'u a gidan gaisuwa yace mata zai kawo mata yawo inta koma masaukin ta, to d'azun daya kira ta fad'a mishi cewa bata gida sun fita dasu Sultana shine yanzun ya k'ara kira yaji ko sun koma gidan, inda haka banza ne ba lallai ta d'auki wayar nashi ba zatace dare yayi bata son damuwa dan ta lura dashi kwanan nan baya tashi kiranta sai dare yayi inta tambaye shi dalilin kiran kuma sai yace mata wai kawai ya kirane dan yaji ya take,
Ita kuma bata tab'a daukar hakan a bakin komai ba,
domin dai tun kafin ta auri Sarki dama shida ita suna shiri sosai,
Bayan auren ta da Sarki kuma sai shirin nasu ya k'aru dan Sarki da kanshi ya bata damar komai take buk'ata tayi magana da Salman d'in kai tsaye, sai ya zamana duk cikin K'annin Sarki tafi shiri da Salman d'in.
kowaccen su idan ta fito simi simi sai dai ta nemi waje ta rab'a a gefen yar uwarta ta tsaya haka nan suka jeru a gefe guda uwa wasu wad'anda ke tsayuwar assembly babu wacce ta iya cewa dashi komai a cikin su kamar yanda shima bai tanka musu ba,
sai ma takawa da yayi gefen da ita oganniyar ke hakince tana amsa waya ko alamun damuwa babu a tare da ita, yana bud'e gefen da take zaunen abu na farko daya farayi shine zare wayar dake cikin hannun ta wanda ta k'ara a kunne tana maganar da tsabar munafunci koshi dake kusa da ita bayajin me take cewa,
Latse kiran yayi ya kuma kashe wayar gaba d'aya, bai tsaya b'ata ma kanshi lokaci ba ya janyo hannunta ya fito da ita daga cikin motar itama ya jerata a kusa dasu Meelat wadanda suka wani duk'ar da kai k'asa, uwa wad'anda aka tsare a gaban alkali,
k'asa k'asa suke satar kallon shi ko waccen su ta kasa d'ago kai ta kalleshi balle kuma su samu damar furta wani abun har zuwa lokacin saboda tsabar kwarjinin daya musu,
K'ara daure fuskar shi yayi sosai kafin ya bud'e baki a kame sosai yace,
"Daga ina kuke?"
Bai tsaya jiran amsa daga kowaccen suba yaci gaba da jero wasu tambayoyin kamar haka,
"Ina kuka je? Nace
Kuma da izinin wa kuka fita gidan nan?
Mai kuma ya hana ku dawowa dawuri tun tuni sai yanzun k'arfe 11 da wani abun, shin kun manta cewa ku matane da har zaku fita kukai irin wannan lokacin a waje?
Ina kuka sani da har zaku fita, Ah ah ko dai salon ku fita wani abu ya sameku kusa mutane a shiga uku, idan da ace kun b'ace kuka kasa gane hanyar dawowa gida kuma fa? Ke kuma Jameela saboda kema ba hankalin kika fisu ba shi yasa kema da kike shirin zama macen aure kika biye musu kuka kai har wannan lokacin a waje, baki san cewa Amarya tsautsayi ne yake binta a duk inda ta taka k'afarta ba"
Bai sarara ba yana nuna Meenal da yatsa yaci gaba da cewa,
"Ke kuma saboda tsabar kin riga kin gama raina ni shine nake ta kiran wayar ki kika gagara d'auka saboda baki d'aukeni a bakin komai ba,
shin kin san irin tashin hankalin da kika nemi jefa zuciya ta a ciki kuwa?
In kuna son zaku fita mai yasa ba zaki nemi izini na ba? A ganin ki bazan iya barin duk uzurin dake gabana in dawo gida dan in kaiki inda kike buk'atar zuwa bane? Yanzun fisabilillahi ya kike zaton zanji inda ace wani abu ya sameku a fitar nan da kukayi, kun kama kun fice ni bana gida ita kuma Hajiya tana bacci hakan da kuka aikata dai daine kenan?"
Ya k'arasa jero tarin tambayoyin shi a kansu yana mai kai hannuwan shi duka biyun ya yamutsa gashin kanshi,
"Ya'ya!
Ya'ya please dan Allah ka tsaya kaji, muma fa Allah bamu san zamu dad'e haka ba, kuma ai ba b'ata mukayi ba,
Ba gashi mun dawo da kanmu gidan ba, kawai fa mun d'an fita zuwa wajen siyar da ice cream d'in daka siyo mana jiya ne, kuma ni ban san ranka zai b'aci ba amma kayi hak'uri kaji,
abunda ma duka duka daga gobe dai shi kenan zamuyi komawar mu muma, kuma ai mun so dawowa gida da wuri a hanya nefa muka lura da wata mota dake ta bin mu a baya shine mukayi ta yawo da kyar fa muka samu muka b'acema mai motar"
"Wata mota ta biyo ku a baya kuma?"
Meelat ce ta amsa mishi da cewa
"eh wallahi Ya'ya tun fa a wani shago da muka tsaya zan siya charger wayata dan na manta ban taho da nawa ba shine suka biyomu to mudai bamu kulasu ba, d'ayan yace wai yana son magana da Meenal ita kuma tak'i tsayawa ta saurare shi, kuma wallahi mu bamu hanata tsayawa dasu ba itace dai tak'i ko Sultana?"
"Eh wallahi Yaya sai da mukace mata ta tsaya taji me zaice mata amma tak'i nasan shi kuma yana ta bin mu ne dan yaga inda zamu shi yasa ya biyo mu a baya"
Cewar Sultana,
"Oh wato ma so kukayi ta tsaya ta saurare shi!
Ashe rashin wayan naku yakai har namiji ya tsare ku a titi ku tsaya dashi, ashe kenan data saurare shin kamar yanda kuka so da yanzun kuna can a titi su suna hira ku kuma kuna jiran su gama ku dawo gida, to ai ba laifi gobe ma in kun fita sai ku tsaya da duk wanda ya tare ku a titin tunda haka kuke so, ku shige kuje ku kwanta in kunga dama, in kuma baku tashi kwanciyar ba kuna iya kwana a nan ma in ya muku"
Girgiza kanshi kawai yayi, sai kuma yayi gaba ya shige cikin falon ya barsu nan a tsaye, dan in yaci gaba da tsayuwa a wajen to dukan su sai sunji ba dad'.
Kallon kallo suka farayi a tsakanin su bayan shigewar su ciki,
Kafin Maryam ta d'aura hannun ta d'aya a kirji bayan ta sauke doguwar ajiyar zuciya ne tace
"oh Allah mun sha da kyar, Allah nayi zaton zai d'an faffalla miki mari koda biyu ne a yanda naga ya d'aure fuskar nan, to dai anyi na farko anyi na k'arshe gobe kam ko ceton rai zakujeyi a wani wajen sai dai ince muku Allah ya bada sa'a a dawo lafiya"
"Ke wai kin tsorata da fad'an da yayi ne? Tab ai wallahi ko gobe sai mun fita koh Bebs?"
Ta fad'a tana mai da kallon ta kan Meelat,
"Eh kekam zaki fita amma wallahi nidai babu ruwa na, dan nasan yanzun haka sai ya fad'ama mijina cewa munje yawo kina ganin saboda kar ya kira wayata yaji a alamar muna wani wajen ne ba gida ba shi yasa na kashe wayar gaba d'aya, to tsakani da Allah muna shiga ki k'ara bashi hakuri a toh"
"Ai kuma sai kuyi"
Cewar Meenal
"Amma Sister mai yasa kikayi mishi k'aryar cewa wani ne ya biyo mu? kunga duk yanda ya damu kuwa😕?"
Cewar Sultana,
"Zauna a wajen to yasin da bamu ce mishi haka ba da har yanzun muna nan muna jero mishi dalilan da yasa mukayi daren, amma ba gashi yanzun harya gama fadar nashi ya wuce ciki ya barmu ba ku muje ciki please kafin mu k'arayin wani laifin kuma,"
"Tsaya Sister wai wannan d'in shima yayanki ne? Gaskiya dai yana da kulawa wallahi duba kuga duk ya damu kar wani abu ya same mu" Sultana ta k'ara tambaya.
"Yayana kuma?😒" Itama Meenal ta tambaya,
"To ba gashi naga kuna kama dashi ba, ai naga sauran Yayyinki da Baba Adamu ya nuna min d'azun bakya wani kama dasu sosai amma shi da ganin shi an san d'an uwan kine"
"Ke bafa yayan ta wanda suka fito ciki d'aya bane taubashin tane! ba d'azun kinji muna maganar mota ba, to shine wanda yayi kyautar motar da muke magana ai"
Maryam taba Sultana amsa tana dariya,
"Miye *taubashi* kuma?"
Sultana ta k'ara tambaya.
"Cousin dinta ko ince miki abokin wasa kamar yanda kuke keda ita, kinga kamar yanda Maman ki take dasu Baba Auta haka shima baban shi yake da Mommy Hauwa shi yasa kikaga suna kama in kin lura ai zakiga dukan su fuskar kakar su Hajiya suka d'auko wacce muka dawo da ita d'azun kinga kuma ai ko ita Maman Meenal din da Hajiya take kama itama"
"Wai dan Allah da gaske shine kuke hirar shi d'azun wanda ya bata wannan motar yau d'in nan?"
"Shifa! Kin ganshi zazzafa koh,Mai Jama'a ake ce mishi saboda tsabar farin jinin da Allah ya mishi sai ma kinga yanda yan mata ke suma a kanshi kuma wai a hakan yar uwar ki ke kushe shi, kema da kikazo yau kika fara ganin dramar su tsakanin ki da Allah zaki cemin baki fahimci komai ba🤔 tsakani da Allah ko abun da ya aikata yanzun ai ya tona asirin abinda ke cikin zuciyar shi amma ita yar uwar ki babu abunda take ganewa sai karatun likitanci🤨" Meelat ta fad'a tana matsawa gefe, dan a kusa da Meenal take ta kuma san halin mutuniyar,
"La'ilah ha'ilallahu muhammadur Rasoulullahi Sallallahu Alaihi Wasallam yanzun nan Meenal wai dama duk zakalkalewar da kikayi d'azun wannan kyakyawan halittar kike kushewa? Kai amma dai da badun kar kiga zakewa taba da nace rashin rabo ne ke bibiyar ki, ina laifin wannan yace ma mace yana son ta ai da gudu zaki amsa shine ke kike wani jan aji! Zo Abuja kiga yanda yan mata ke neman irin su da kud'in su da kyau da ilimi ga kuma gata amma basa samu,"
Tunda Meelat ta fara soki burutsun zancen ta dama Meenal tayi gaba, bayan ta suka bi bayan su kwaso ledojin da suka bari a cikin Motar,
Itace ta fara shiga falon, dan haka tana shiga sai ta nemi waje ta zauna a gefen kujerar da yake zaune,
D'aya d'aya suka shigo duk wacce ta shigo kuma sai ta mishi gaisuwar da basu samu damar yi mishi ita a d'azun ba,
Shiko a takaice yake amsa musu da cewa "lafiya lau,"
Sad'af sad'af suka sulale suka wuce ciki suka barta dashi a falon,
Tunda ta zauna ko gefen da take zaune bai yarda ya kalla ba, hannu wanshi dai duka biyun suna saman kanshi wanda ya duk'ar yana kallon k'asa,
"Ya'ya dan Allah kayi hakuri, kaga dai d'azun nace ma Hajiya mun dena fad'a yanzun kuma in taji ai dariya zata mana wallahi, nidai tunda kace baka son muna fitan ma to gobe zamu jira har sai ka dawo sai mu fita tare kaji?"
Dago kanshi dake duk'e yayi yana binta da kallo idanuwan shi a k'an k'ance,
"Oh kun ma shirya wani fitan a gobe kenan?"
"Eh mana amma ai bazamu wani dad'e sosai ba zamu dawo da wuri I promise"
"Meenal "
Ya kira sunan ta,
"Na'am" ta amsa dashi tana wasa da zoben dake yatsar ta,
"Meenal kina jin tausayina kuwa?"
"Eh wallahi sosai ma nikejin tausayin ka"
"Karya kikeyi!"
"Allah kuwa da gaske"
"To me yasa kika fita bayan kin san dole zan dawo da wuri saboda ke?, amma kuka fita harma wani sakarai ke bin ku"
"To aini ban san zaka dawo ba, kuma mu bamu san cewa dare yayi haka ba"
"Meenal"
"Uhumm" ta k'ara amsawa,
"Meenal Zuciyata zafi take mun"ya fad'a bayan yakai hannun shi saitin da zuciyar take ya danneta da d'an karfi,
"Baka da lafiya ne dama?"
"Nima ban san ko wani irin ciwon ke damuna ba amma dai naji ba dad'i da naji cewa wani yaso tsaidake dan yayi magana dake, bai hak'ura ba kuma shine har saida ya k'ara bin bayan ku, to idan da mugune ya samu damar da zai cutar dake kuma fa ya kike tunanin zanji,"
Shek'ek'e take binshi da kallo dan ba wani gane abunda yake cewa takeyi ba,
Rik'o hannun ta suna kallon juna ido cikin ido, kafin dakyar ya fizgo maganar dake cikin bakin shi,
"Meenal ban san me yake faruwa dani ba, amma tabbas inajin babu dad'i aduk sanda na nesan ta kaina dake,
Zuciyata takan kasance a kuntace idan na ganki a cikin damuwa komai k'ank'an tanta kuwa,
Ina jin matsanan cin farin ciki aduk sanda naga murmushi kwance akan wannan kyakyawar fuskar taki, ki fad'amin me yake faruwa dani Meena.
*Ummiee ce*✍🏼
[9/4, 6:16 PM] Ummiee Zaria: ⚜️🔱👨👩👧👦 *DANGINA*👨👩👧👦🔱⚜️
*BOOK 2*
*PAGE 20*
Cigaba da kallon shi tayi ba tareda tace komai ba,
"Tashi kije ki kwanta dare yayi!"
Ya fad'a hakan a yayinda ya saki hannun ta daya rik'e tun d'azun,
Mik'ewa yayi ya wuce wajen kofar falon ya rufe da makulli ya kuma kashe TV dake aiki dama sauran kayan wutan dake falon,
Bai yarda ya kalli inda take ba ya wuce d'akin shi yana shiga ya kullo kofar,
Ita ko da kallo kawai taci gaba da binshi tun tashin shi a wajen har saida ya k'ule ma ganin ta sannan ta d'age kafad'un ta, alamun ko a jikin ta itama ta tashi ta nufi d'akin dasu Meelat ke ciki, a zuciyar ta take cewa k'ila da gaske dai Hajiya keyi da tace yana da aljanu wallahi🤔.
Suko iyayen gulma tun bayan barin su falon suna shiga cikin d'akin ledojin hannun su kawai suka ajiye suka dawo bakin k'ofar suke jeru uwa kujerar roba da ake d'aurawa d'aya dan d'aya domin duka ukun haka suka jera Maryam ce a k'asa ta lek'o kai sai Meelat sai Sultana a saman su sun kasa kunne da zuba idanuwa suna kallon abunda ke faruwa a cikin falon duk da ba wani jin abunda shi AK yake cewa sukeyi ba,
Suna ganin shi ya shige itama kuma ta nufo d'akin sai sukayi hanzarin barin bakin k'ofar kowaccen su ta samu waje ta zauna suka kama bud'e ledojin da suka shigo dashi suka wani basar kamar basu ne suka gama lek'e yanzun ba,
Da Sallama Meenal ta shigo itama ta nemi waje ta zauna,
Maryam ce ta mik'a mata leda guda d'aya.
"Ga nashi ki mik'a mishi waya sani ma ko k'ila baici komai ba tunda ya dawo yana gadin dawowar mu"
Babu musu Meenal ta amshi ledar ta juya ta fice daga d'akin,
Kofar d'akin shi ta tsaya sai da takai hannun ta tayi nocking kafin ta had'a da sallama tana jiran ya bata izinin shiga,
"Bud'e ki shigo!"
Ya fad'a bayan ya amsa Sallamar nata yana daga zaune a gefen gadon shi dan tun bayan shigowar shi d'akin bai iya tab'uka komai ba zama kawai yayi ya rasa ina zaisa kanshi,
Shi baima san meya hau kanshi d'azun ya zaunar da yarinyar nan yana neman tona ma kanshi asiri a gabanta,
Yanzun nan dan Allah daya fad'a mata gaskiyar abunda yajeki akanta kamar yanda kullum su Yusuf ke zugashi akan ya bayyana mata Soyayyar da yake mata ai yasan wani fassarar daban zata mashi,
Wallahi tanama iya cewa dan ya mata kyautar mota ne ko kuma tace dama ba dan Allah ko da zuciya d'aya ya bata motar ba,
dan haka zai jira lokacin daya dace sai ya fitar mata da abunda yake cikin zuciyar shi amma ba dai yauba.
Sai da ta k'arayin wani sabon sallaman bayan ta shigo,
"Ameen Alaikis Salam"
Ya amsa kafin ya d'ago kai yana k'are mata kallo,
"Ya akayi? Ba cewa nayi kije ki kwanta ba me kike nema anan kuma? Wato kin dai rantse sai kin shigo min d'aki sannan hankalin ki zai kwanta, to sai ki d'auki abinda kike buk'ata ki wuce ki bani waje bacci zanyi"
"Ummh Ummh ba komai fa dama abinci na kawo maka dan Allah kaci kasha magani kuma kafin ka kwanta kaji!"
"Kinga alamun yunwa a tareda nine? da zaki kawo min abinci ? Inda da gaske kin damu dani har haka ai da bazaki kwashi kawayen ki ku fice yawo ba, waye ma ya siya muku abincin?"
"Allah kuwa babu wanda ya siya mana da kud'in mu muka siya, kuma kaga ai su bak'i nane kuma idan mutum yayi bak'i kamata yayi ya karrama su shi yasa nima na fita tare dasu muka d'anyo siyayya,
kuma ai na duba kan dinning table banga alaman kaci komai ba, nidai kaci dan Allah kaji, ai dai na baka hak'uri nace maka bazan k'ara zuwa ko ina ba sai da izinin ka"
Ajiye ledar tayi da sauri ta juya ta fice daga cikin d'akin kamar wacce tayi mantuwa, bai motsa daga inda yake ba harta k'ara dawowa d'akin hannun ta d'auke da wani wani faranti madai daici wanda ta d'auro kwalin 5alive sai gorar ruwa mara sanyi sosai da kofi guda d'aya akai,
wani stool d'in data gani a gefen gadon shita jawo ta d'aura farantin akai sannan ta fidda abubuwan dake cikin ledan suma ta jera su a gefe,
"Wai Ya'ya kai baka shan ko wani drink ne sai na yayan itatuwa? Babu coca cola ba fanta ko maltina babu a cikin pridge din gidan nan sai su 5 alive exotic da wadansu daban"
shi dai da kallo kawai yaci gaba da binta ba tareda ya bata amsar tambayar taba,
harta gama ta juya da niyyar barin d'akin ya ruk'o hannun ta,
"Ni dawa zamuci wannan abincin da kika jera ne wai?"
"Kai kadai zakaci shi mana nima zanje muci tareda su Meelat a d'akine"
"Kwashe su ki wuce dasu ku k'ara a naku kuci ni ban saba cin abinci ni kad'aiba, ba kuma zan fara yau ba shi yasa ma jiya na zauna naci tare dake shine zaki kawo ki wani jeramin su a gabana kiyi tafiyar ki"
Da mamaki take kallon shi,
Dan Allah jama'a ina laifin wanda ya kula dakai ya kawo maka abunci kaci? Ita da tayi mishi abun arziki mai makon ya gode mata shine yake kok'arin kushewa! Ita fa duk tana mishi ne saboda ganin da tayi ranshi ya baci da fitar da sukayi inba haka ba fisabilillahi miye had'in ta dashi da zata wani biyoshi da abinci har d'aki tana lallab'a shi kamar wani yaron goye,
Daurewa tayi tana cigaba da kallon shi take cewa.
"To da kafin muzo nan kai dawa kake cin abincin ba kai kad'ai kake ciba?"
Ta tambaya tana tura baki, dan itafa a k'age take tayi tabar d'akin ta koma wajen su Meelat dan fitan da tayi d'auko mishi ruwa sai da ta lek'a tace musu su jirata ta dawo sai suci abincin tare shine shi kuma yake wani son ya hanata komawa,
"Da baki zoba a restaurant nike cin abincina ko kuma in siyo inzo muci da Mansoor in kuma d'aya daga cikin su Musty na nan tare muke ci yanzun kuma da kike nan jiya munci tare kinga kenan yau da gobe ma duk tare ya dace muci kafin ki koma koh? "
Ya k'arasa fad'a yana d'age mata girar shi guda d'aya.
"To amma Yaya nace masu Maryam fa su jirani har in dawo sai muci tare dasu😒" ta furta hakan a shagwabe,
Jawota yayi ya zaunar a kasan carpet d'in dake d'akin bayan ya mik'e tsaye,
sauke abincin data jera akan stool d'in yayi ya mai dasu kasa kan carpet ,
"Bismillah kici abincin nan inhar kina son barin d'akin nan in kuma ba haka ba tsareki zanyi wallahi"
Ya furta yana kallon ta fuskar shi a daure babu alamun wasa,
Badan taso ba haka tasa cokali da dunga diba tana cusama cikin ta,dan tasan tunda ya fad'a tofa tsaf zai aikata dan haka gara su rabu lafiya, gobe ma ai rana ne da bata d'auko abincin ta biyoshi dashi har cikin dakin ba ai da bazai samu damar yin mata wannan mulkin mallakan ba.
shima gyara zama yayi yaci gaba dacin abincin da kyau yanajin nishad'in hakan a cikin zuciyar shi, ita ta fara tsame hannun ta daga abincin alamun ta k'oshi amma duk da haka bai bata damar tashi ba har saida ya kammala tsaf tukun,
"Muje in rakaki kikai kayan kitchen sai kije ki kwanta"
"Zan iya kaiwa ni d'aya fa!"
"Ai nasan zaki iya din amma kuma na buk'aci yi miki rakiyar"
Shi ya tattara inda sukaci abincin ya rik'o farantin a hannun shi duk da taso ta amsa ya hanata, bai damu da samun su Meelat da yayi zauna a falon sun kunna Tv suma suna cin abincin ba, illah ma d'auke kai da yayi sai da ya rakata har kitchen d'in suka wanko hannu, sannan ya fito ya barta a kitchen din ya koma d'akin shi, yana shiga wanka ya farayi yayi ya kuma d'auro alwallah yana fitowa ko mai bai shafama jikin shiba turare kawai ya d'an feffesa sai kuma ya Sanya kayan bacci ya gabatar da shafa'i da wuturi yana idarwa ya kashe wutar d'akin yabi lafiyar gado,
Asuba ta gari jikar Hajjaju🥰.
Ita ko kasa fitowa da wuri tayi daga kitchen din dan tasan wallahi badan Allah su Maryam suka dawo falon suka zauna ba, ganin tana b'atama kanta lokaci a cikin kitchen din ne yasata fito fuska d'aure bata kalli ko gefen da suka zaunen ba duk da kiran da suke mata na iya shege kin kulasu tayi tayi shigewar ta d'aki to itama dai kamar shi din tana shiga kayan jikin ta ta cire ta fad'a ban d'aki sai da ta gabatar da duk wani al'adar ta na kafin kwanciyar bacci sannan ta koma kan kujerar 3sitter guda d'aya wacce ke cikin d'akin ta kwanta ta rufe kafafuwan ta da dogon hijjabin ta, ganin ta kasa sakewa a kan kujerar dan bata saba kwana a kujera ba sai kawai ta mike ta fito daga d'akin zuwa wanda Hajiya ke ciki,
Duk yanda su Meelat ke kiranta kin kulasu tayi ta shige d'akin ta kulle kofar da key ta k'arasa kan gadon gefen Hajiya ta kwanta,
Ta dade a kwance tana hasaso kalaman AK sai dai kuma ta rasa irin fassarar da zata musu daga k'arshe dai ture tunanin tayi a gefe ta gabatar da addu'ar bacci ta shafe jikin ta dashi sannan ta rufe idon ta tana ci gaba da istigfarin da take gabatar wa aduk sanda tazo kwanciya bacci har zuwa sanda baccin yayi nasarar d'auketa,
Suko su Meelat tun fitar da tayi zuwa kaima AK abinci tana fita Maryam ce ta fara cewa,
"Bebs wallahi AK
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 58 Chapter of 92