lura da cewa AK yana da damuwa, na kumayi iya bincike na ban gane miye silar damuwar nashi ba sai daga baya na lura da cewa yawancin lokuta yakan shiga damuwan ne idan yazo garin nan,
Wanda idan kun lura a lokacin zakuga cewa sam koda wani abun ya taso anan bazai zoba sai dai cikin ni daku wani ya wakilce shi,
Daga baya kuma sai abun yayi kamar yayi sauk'i duk da ni na tabbatar da cewa yana kokarin boyewa ne kawai a duk lokacin da muke tare saboda gudun amsa tambayoyin da yasan zamu mishi,
Sai dai duk yanda ya boye ni na san damuwar nashi tabbas tana da alaqa da soyayya sai dai nima ban matsa mishi ba amma ina dai ta binshi da addu'a,"
"Wai kana nufin tsawon lokacin nan dama son wata ya mace ne yake faman wahal dashi? "
Musty ya tambaya.
"Kwarai kuwa ina da tabbacin hakan domin da farko daya fara sonta shima kanshi bai gane son ta yake ba,
A lokuta da dama idan naga yanda yake mata nakan tsaya inyi ta kallon shi dan na gane cewa yar tsamar dake gudana a tsakanin su sosai yake sashi nishad'i,
Amma ban ce mishi komai ba dan nasan da zarar nayi magana musamin zaiyi ko kuma yama fita a sabgar ita yarinyar,
Dan haka a boye wani lokacin nakan aika a kirata dan tazo inda yake dan nasan baza'a kwashe lafiya ba dan ita ma bata da hakuri kuma ita ce kadai macen da naga tana da zarar tsayawa a gaban shi ta mishi maganar da taga dama amma kuma sai ya kasa d'aukar ko wani mataki a kanta sab'anin hakan ma sai dai kawai yayi ta binta da kallo idan kuma ta tafi sai yayi ta murmushin da ba halin shi bane,"
"Ikon Allah"
Sadeeq ya fad'a yana rike baki,
"Kana mamaki koh?"
Cewar Yusuf.
"Ci gaba please Yusuf so nike in san ina aka kwana"
Musty ya Fad'i hakan yana dungure ma Sadeeq hannun daya dafe hab'ar shi dashi,
"A dai dai lokacin da shi yake rainon soyayyar ta, a lokacin da canji ya shigo rayuwar shi kawai sai rana d'aya muka tsinci mummunar labarin cewa Baban yarinyar ya fidda mata mijin aure, wanda a lokacin shi kuma a boye AK yake ta yak'i da samarin yarinyar dan ya rabata dasu,
Kun san me?"
"Ah ah sai ka fad'a"
"Wallahi lokacin har k'aramin ciwo sai da yayi ninayi jinyar shi a asibiti na kwana biyu ko Hajiya bata sani ba balle ku, duk da kuwa cewa ko a wancan lokacin yaki yarda ya fad'amin dalilin ciwon nima kuma ban iyace mishi komai ba, dan ban san ta inda zan fara rarrashin shiba, bayan yaji sauk'i ne kuma ya tattara yabar kasar gaba da goyon bayana dan nasan idan baya kasar yawan tunata da yakeyi zai ragu sab'anin idan yana nan da zaici gaba da ganin ta ciwon sonta yana taso mishi alhalin ita d'in kuma matar wani ne"
"Innalillahi wa'innah ilairir raju'un"
Suka tsinci bakunan su da maimaitawa,
Musty ne yayi k'arfin halin bude baki ya jefama Yusuf tambayar dake cikin zuciyar shi cewa,
"Kenan matar aure yako so?"
"Ah ah ba matar aure bane domin kuwa a yanzun dai auren nata ya mutu sun rabu da mijin nata"
"Alhamdulillah kenan dai akwai hope dake nufin cewa Abokin mu zai iya samunta a matsayin mata?"
Sadeeq ya tambaya yana kallon Yusuf.
"Eh kusan hakan ne if we act quickly, idan kuma muka tsaya sanya tofa tabbas zamuji a salan sane dan ita yarinyar baban ta shike zab'ar ma yaran shi mata miji a yanda wanda nasa shi yamin bincike ya tabbatar min da hakan,
Sannan kuma shima din adai yanda ni daku muka sani ba lallai bane ya iya tunkaranta kai tsaye ya furta mata cewa yana son ta ba,
Wannan nema dalilin da yasa nace kuzo mu tattauna dan musan ta yanda zamu bullo ma al'amarin, jiya naso inyi maganar da Hajiya sai kuma dai nace bari in farayin magana daku biyun tukun, ya kuke ganin zamuyi?"
"Wai kenan kana nufin har yanzun bai gayama yarinyar cewa yana sonta ba?"
Sadeeq ya k'ara tambaya da mamaki,
"Eh bai fad'aba"
Shiko musty cewa yayi
"Ikon Allah lallai AK son gaskiya yake ma yarinyar nan inba haka ba mace taje tayi aure a wani wajen harta fito amma ka kasa cireta a cikin zuciyar ka yanzun data riga ta zama bazawara, wai ma wacece yarinyar nan ne?"
Dariya Yusuf yayi yana kallon musty yace "mamaki kakeyi kenan, to ai soyyaya tafi gaban nan kuma ita yarinyar inda zaka ganta yanzun a gaban ka na tabbatar da cewa kana iya d'aura alwallah ka dafa qur'ani akan cewa budurwa ce, dan yarinya ce k'arama har yanzun dan tana da yarinta sosai akayi mata auren ba kuma son juna suke ita da mijin ba dan haka nema shi sakaran ya sakota ba tareda ko sanin ta a matsayin mace yayi ba, wannan labarin kuma duka a safiyar yau na same shi a wajen wanda nasa ya bincikamin, duk da kuwa ita yarinyar yar uwar AK ce ta kusa"
"Kai tsaya dan Allah Yusuf wai badai akan Meenal kake magana ba? "
Cewar Musty a yayinda ya mik'e tsaye ya fara kaida kawo a cikin falon.
"Ita fa jikar hajiya yarinyar aunty Jidda wacce yanzun haka take zaune tareda Hajiya"
Yusuf ya bashi amsa.
"Ikon Allah wai meenal ce dama AK keso?"
Sadeeq ya fada cike da tarin mamaki,
"Babu wai a cikin maganar nan" Yusuf ya bashi amsa.
"To amma me yasa mu bamu gane hakan ba tuntuni? "
"Saboda baku sa kanku zaku gane ba amma ni tuni na harbo jirgin shi"
Dariya sosai suka fashe dashi,
Musty ne mai cewa
"Shegen gora mutumin dake cewa allah ya kyauta yayi soyayya da karamar yarinya,
Wai kum ma san da sunan da yake kiranta?
Jaririya fa yake ce mata saboda tana da sunan maman shi shi kuma yafi karfin ya kirata da meenal,"
Ya k'arasa fada yana dariya sosai,
"Aiko sai naci uban shi wallahi yanda ya dunga mana maganar banza muma gashi alhaki ya kamashi zai kare a karamar yarinya bazawara ma"
Inji musty
"Kai wallahi in kana ce maka bazawara matsala zaku samu,
Dan jiya cemin yayi ba zawara ba ko duniya ta haifa shi dai yana sonta a haka balle kuma itama din budurwa ce,"
"Kai gaskiya naji dadin labarin nan sosai gaskiya koba komai shima ya samu abunda zuciyar shi keso zanso kuma ace wannan karan ya mallaketa a matsayin mata karta k'ara kucce mishi kuma mu shiga uku dan yasin AK yana iya haukacewa idan ya rasa ta"
"Kwarai kuwa, amma dai yanzun muyi hakuri zuwa gaba kadan duk da dai bawai zatayi iddah bane amma mud'an jinkirta har abun ya saketa tukun,
Hajiya kuma ni zan mata bayani da kaina, shi kuma na mishi bayani akan yayi kokari ya dunga jan yarinyar a jiki bawai irin yanda ya saba d'aurema yan matan shi fuska zai mata ba, kuma muma zamu taya shi wannan yak'in a bayan fage dan Wallahi wannan yarinyar yanda take nasan da zarar maza suka gane bata da aure tofa bashi kadai ba muma mun shiga ukun mu dan ba matar yara bace wallahi"
"Wai shi yana ina ma?"
Sadeeq ya tambaya,
"Ina zaka ganshi yana can falon Hajiya tun safe daya d'auki wanka can yaje ya kasa ya tsare yana kallon rabin ran shi"
Fashewa sukayi da dariya, lallai aiki ya samu ga masuyi,
To Allah ya sanya alkhairi, sun dade suna tattaunawa....
Yayinda suke nan suna tattaunawa shi kuma gogan yau tunda safe ya k'ara d'aukar wani wankan cikin wasu fararen kayan wani yadi mai d'an karan taushi uwa auduga idanun ka kad'ai sun isa sheda wajen fada maka cewan tsadadden yadine, kasancewar shi mara nauyin shi da kasancewar shi mara kaurine yasa ake iya hango best din daya saka a ciki, kamar koda yaushe kuma sai da ya tabbatar da cewa ya feshe jikin shi da turare kafin ya doshi sashin Hajjaju to dai tunda ya shiga dama yake ta faman ware idon dan son ganin ta inda gwanar nashi zata fito sai dai kuma harya share kusan minti Biyar baiji motsin saukowar taba,
Dan haka ya tashi kai tsaye ya nufi kitchen sai dai koda ya lek'a Larai ce kadai a kitchen din,
Bayan sun gaisa yake tambayar ta "mutanen gidan basu tashi bacci bane?
Ita kuma ta bashi amsa da cewar sun tashi basu dai sauko bane duk da dai ita Meenal bata jima data sauko ta had'a tea ta koma saman ba,
Komawa da baya yayi kafin ya haye saman, d'akin Hajiya ya shiga da sallama sai dai ita kuma a gado ya hangota lullub'e da bargo tana bacci,
Gudun karya tashe tane kuma hakan yasa ya koma da baya ya fita daga d'akin ya rufe mata kofa,
Har yayi gaba da niyar sauka sai kuma zuciyar shi ta kasa bashi had'in kai dan haka sai kawai ya koma da baya ya murd'a kofar d'in nata da sallama d'auke a bakin shi, sai da yayi sallama sau uku kafin a amsa mishi ana hud'u shi kuma jin ta amsa hakan ya bashi damar Sakai cikin dakin ba tareda jiran izinin shiga daga mai d'akin ba,
Shigar da sai da yayi dana sani kwando dubu cewar daya sani da baima shigo Sashen ba balle har ya hauro saman........
*Allah kuwa idan banga comment ba babu na dare*๐คท๐ปโโ๏ธ.
Kuma banyi editing ba๐
*UMMIEE ZARIA*โ๐ผ
#Mai Jama'a
#Sheikh Naseer
#Meenal
#Hajiya
#Malam
[8/21, 9:44 PM] Ummiee Zaria: ๐ฑโ๏ธ๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆ *DANGINA!*๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆโ๏ธ๐ฑ
*~{{MY FAMILY}}~BOOK 2
ยฉยฎ *UZ-2023.*
*RUBUTAWA*
*ZAINAB USMAN*
*~{Ummiee Zaria}~*โ๐ผ
----- *Page 5*
Da wani irin sauri mai cike da zafin nama irin na zaratan maza ya juya ya fito daga d'akin nata idanuwan shi a rufe ruf, bayan ya runtse idanuwan shima sai da yayi amfani da hannun shi ya k'ara rufe fuskar shi da tafukan hannun nashi,
Sai dai kuma har zuwa lokacin bai daina ganin hoton abunda yaci karo dashi a cikin kwayar idanun shiba, to wai shi me zai kira wannan ganin? Farin gani ko bak'in gani,
"Subhanallah Masha Allah lallai Allah yayi halitta a wajen can wai wai wai dank'ari",
Gaba daya fa ya rud'e dan bai tab'a zato ko tsammanin cewar gamon da zaiyi kenan a cikin d'akin ba, rawan da jikin shi keyi ne kuma hakan yasa dole ya kasa tsayuwa har saida lalube yasamu ya lalubo jikin bango ya jingina kafin ya sulale zuwa k'asa yana mai had'e jikin shi waje d'aya,
Kafin ya wani k'ara cusa fuskar shi cikin tafin hannun yana mai matse cinyoyin shi waje d'aya,kamar wani wanda yake cikin matsanan cin tsoro.
Yasan bazai taba iya kai kanshi d'aki a hakan da yake ba hakan nema yasa koda wasa baiyi gigin sauka matakalar da sunan sauka k'asa ba dan yasan wallahi yana iya missing step ya mulmula zuwa k'asan yaji ma kanshi ciwo a banza, ya dad'e zaune a wajen a kallah dai sai da yayi zama na wajen mintuna goma yana k'ok'arin ganin ya samar ma kanshi nutsuwar daya rasa a lokacin,
sai dai kuma hoton dake cikin kwalwalwar shifa sam ya kasa gogeshi dan har yanzun hoton yawo miki mishi a cikin kwayar ido kamar dai har yanzun d'in itace dai a gaban nashi a yanda ya ganta,
Tafin hannun shi daya rufe fuskar shi dashi yad'an fara warewa kad'an kad'an yana lek'o idon shi ta tsakanin yatsun dan yagani ko ta fito ne ko tana ciki sakamakon motsin da kofar dakin nata yayi,
ganin cewar ba itace ta fito ba hakan yasa ya dafa dakyar ya samu ya mik'e a dudduke ya samu ya shige d'akin da yake gefen nata wanda shine yafi kusa dashi,
"Wannan yarinyar in banyi wasa ba saita sa zuciyata ta buga na mace tun lokacin mutuwar nawa baiyi ba"
Ya samu damar furtawa a bayyane a yayinda ya samu yakai kanshi zuwa ga gadon dake cikin d'akin ya kwanta a wahalce.
Ita ko mutuniyar a gefen ta tun bayan data had'o tea dinta a kitchen a gurguje tasha tea d'in dan so take ta fita da wuri dan tama hajiya k'aryar cewa tana da lecture din safe ne alhalin su kuma kasuwa suka shirya zuwa yau d'in ita dasu Meelat dan Wallahi bata zama gida haka kawai Hajiya sai faman wani kimeta takeyi a cikin gida ita ba matar aure ba alhalin koda take da auren shi mijin ba kulle yake mata ba,
Yanzun kuma da take ganin ta samu free ta zama sakakkiyar tsuntsuwa shine kawai Hajiya zata wani k'irk'iro mata da wani zaman idan ganin ido wanda kowa yasan babu ta inda iddan ya kamata, haba ina ma dalili ai in hajiya tasan wata tofa bata san wata ba dan Wallahi babu abun da zai mata sha maki da shirin bikin da sukeyi na Meelat,
Bayan ta gama shan shayin d'akin Hajiya ta lek'a, ganin ta kwance rashe rashe a gado hakan yasa ta dawo da baya ta fad'a daki da gudu ta shek'o wanka a gurguje,
Tofa ta fito ne tana shafa mai ta farajin sallama tsakani da Allah kuma ita bata d'auki ko muryar waye bane, dalilin kin amsawarta da wuri kuma ita tayi zaton cewa ko Hajiyar ne shi yasa da farko ta shareta duk da tana jin sallamar tak'i amsawa har sai a sallamar k'arshe,
Bata tab'a zaton cewa wai idan AK ya hauro saman zai iya yunkurin shigowa d'akin ta ba dan bai tab'a kwatanta aikata mata hakan ba, domin ko zaman da tayi a gidan shekarun baya ko saman baya haurowa, hakan nema yasa koda taji motsin bud'e kofar d'akin bata wani damu da son d'ago kai dan ganin ko waye mai shigowan ba dan sau da yawa Hajiyar kan biyota d'akin su sha hirar su,
Sai gashi yau saboda rashin sa'a wani k'aton ya fad'o mata cikin d'aki a d'ai dai lokacin da take kok'arin sa riga alhalin yau ko bra bata saba,
Saboda dama ita idan tana period to bata babu bra dan nonuwan ta kan cicciko ne su kama mata ciwo na rashin dalili ko rigar da zai matseta bata sawa balle kuma bra,
Allah ma ya taimaketa ta riga ta zura dogon wandon skin tight a jikin ta aida yaci amanar ta da yawa wallahi kuma ko yanzun saita Allah kawai amma fa wallahi bata yafe ba,
Domin yafa shammace ta da yawa shigowar nashi d'akin yayi dai dai ne da sanda ta d'aga hannun ta sama da niyyar zura rigar ta, motsin shigowar ne kuma yasata juyowa a zaton ta Hajiya ce, wanda motsin juyin nata ne kuma yaba albarkatun k'irjinta daman juyawan da k'arfi suma, hakan kuma duka akan idon bawan Allah ya faru, karon farko a rayuwar shi da yaga halittar mace a waje b'aro b'aro bawai a tv ko kuma hoto ba,
Ita kuma ta juyo da zummar ganin Hajiya kawai sai tayi gamo da wani bak'on halittan yau a cikin d'akin nata wanda ya fad'o mata ba tareda gayyata ba ko neman izinin shiga ba,
Zaku sha dariya in kuka hango yanda ta buga wani uban tsalle gaba d'aya uwa wacce taga dodon da zai iya cinyeta a take, wanda tsallen nata shi kuma ya k'ara haifar mishi da wani sabon tashin hankali a cikin ruhi da jiki, dan haka babu shiri shima ya juya,
Ita kuma jikin ta ya shiga mazari kamar wata wacce ta kwana a waje a lokacin hunturu,
Da gudu ta k'arasa wajen kofar ta tura shi da k'arfi ta murza mishi key kafin ta sulale a jikin kofar itama ta zauna,
Ajiyar zuciya kawai take faman saukewa, kafin ta fara bori anan wajen daga zaune ta fara watsa k'afafuwa tana buga hannayenta a k'asa,
"Wallahi Allah sai ya saka min kawai shi kenan mutum sai ya wani shigomin d'aki babu izini duk ya gama ganina babu kaya"
Kukan tab'ara taci gaba da yi tana cigaba da fad'in,
"Allah dai ya isana wallahi shi kenan ya gama kalle min Mamaa,"
Mai da duban ta kan k'irjin nata tayi, kamar kuma wacce aka tsikara sai ta k'ara fashewa da kuka yayinda tasa hannuwan ta ta kare su dashi domin dai tuni dama tayi watsi da rigarta a can gefe,
"Nidai wallahi ban yafema ganina da babu riga da akayi ba kuma Allah ma sai ya sakamin"
Ta fad'a tana share tsilli tsillin hawayen da suka taru a idon ta,
Ta dad'e zaune a wajen kafin ta rarrafa ta d'auko rigar sai da ta kakkab'e shi tana cigaba da mitar cewa bata yafeba kafin ta zura rigar sai kuma ta nemi waje ta zauna domin dai duk saurin da take wallahi bazata tab'a yarda ta sauka k'asa ba a yanzun balle kuma tsautsayi yasa su had'u dan bata san da idon da zata kalle shiba, dan tasan yana ganin ta yanzun Maman ta kawai zai dunga hangowa koda ko daga nesa ne,
Wannan hasashen nata kad'ai ba k'aramin kunya da bak'in ciki ya k'ara mata ba, dan haka sai kawai ta koma ta kwanta ta janyo wayarta ta kira Maryam akan subar tafiyar sai zuwa anjima, domin tasan ba zaman gidan sosai yafiye yiba in yana gari, a nata nufin wai in ya fita itama sai ta fice kunga kenan bazasu had'u ba.
Shiko jikan innah can ya mak'ale a d'aki sai faman burgima yake a gado,
Pillow biyu ya rungume d'aya a tsakanin cinyoyin shi d'ayan kuma ya rungume shi a k'irji, da kyar ya samu bacci b'arawo ya silalo ya yi wuf dashi.
*CIKIN MAFARKI*
A cikin mota suke tafe shida ita sai dai kuma yanda yake tuk'in motar kamar mai shirin shiga rami ne abunda zai baka mamaki, domin kowa yasan yanda baya d'aga k'afa wajen bama mota wuta a duk sanda ya zama na shine matuk'in motar,
Da wannan tukin nashi suka samu suka k'araso cikin gidan na Hajiya har zuwa lokacin kuma tana ankare da yanda hankalin shi ya rabu biyu rabi a kanta rabi kuma akan tuk'in da yakeyi,
Can cikin lungu a wajen da ake parking motocin gidan ya k'arasa da motar duk da yanda wajen yake da d'an duhuwa saboda bishiyoyin dake wajen sab'anin ainihin wajen parking d'in da yake da haske sosai,
Koda ta yaka motar batayi yunkurin fita daga cikin motar ba, haka shima daya gyara zaman shi yana mai binta da kallo kamar ya lasheta haka yake ji a lokacin kuma ya kasa furta mata koda kalma d'aya ne,
Har sai da suka shafe a kalla tsayin mintuna 10 suna bin juna da mayen kallo, kafin ta bud'e baki tana ci gaba da kallon nashi tace,
"Me yasa kayi parking anan sab'anin bayan mu inda kowa ke ajiye nashi motar?"
"Bana son kowa ya ganin min ke shi yasa na yanke hukuncin tsayawa anan har sai kowa ya shige ciki"
Ya bata amsa.
"Saboda me to yasa hakan?"
Ta k'ara tambaya tana mai cigaba da binshi da ido, wani irin kallo take mishi mai sa mutuwar gab'ob'i,
"Saboda ina kishin abunda nike so mana bakiga wad'ancan masu gadin yanda sukayi tsai-tsaye kamar wasu masu gadin fada bane!"
Ya fad'i hakan a yayinda yake mata nuni da glass din gaban driver na cikin motar wanda ta ciki yake iya kallon abunda akeyi a cikin gidan.
Murmushi tayi tana kauda fuska gefe bayan ta rufe fuskar da tafukan hannayen ta alamun jin kunya,
"Kin san me?"
Girgiza kanta tayi alamun Ah ah ba tareda ta bashi amsa da baki ba.
"A kullum fatana shine in dauwama tare dake har zuwa karshen numfashi na" sai kuma yayi shiru,
Dan haka itama sai tayi shiru bata iya cewa bata iya cewa komai ba,
Shirun da motar yayi ga kuma sanyin ac da kamshin turaren jikin sune suka had'u suka bada wani irin daddad'an yanayi,
Wanda hakan ne kuma ya haifar da mutuwar gabb'an jikin kowannen su, ji yake ina ma zai iya daya jawota cikin jikin shi ya k'ank'ame kozai samu sa'idah akan yanda yake jin jinin jikin shi yana yamutsawa,
"Shshshshuuuu"
Taja dogon iska ta bakinta sakamakon sanyin data kejin yana huda tsigar jikinta yana ratsa tsokarta yana shiga mata cikin k'ashi,
Sai dai kuma fitar iskar bakin ta zama yayi kamar wani d'an sak'o ko kuma ince abunda akayi shi da gayya domin kuwa kai tsaye ya wuce cikin kunnen AK ya ratsa har zuwa cikin zuciyar dake bugawa a cikin k'irjin shi,
Jikin shi a mace ya jefa mata tambaya da cewa.
"Miye wannan?"
Bai jira ta amsa ba yaci gaba da cewa..
"Ko kinajin sanyi ne in kashe ac?"
Shiru tayi bata amsa ba, can kuma sai ta zura hannunta a cikin handbag dinta dake ajiye akan tsinyoyin ta,
Ta ciro jambaki sai da ta kunna hasken gaban motar ta kuma karkato da glass din dake wajen yanda zata iya ganin fuskarta da kyau ta cikin shi sannan ta goga janbakin a saman kyawawan lab'b'anta,
Chocolate ta ciro a cikin Jakar bayan ta maida janbakin, saida ta bud'e shi ta gutsira taci sannan ta mik'a mishi,
Shiko komawa yayi kamar wani sakago wajen kallon ta dan suma ne kad'ai ya rage mishi a yanda dai yake kallon bakin data bi ta shafe tass da jambaki ga kuma yanda take wani taunar chocolate din cike da jan rai,
Dan Allah inba neman fitina ba miye na wani shafa jambaki da daren nan fisabilillahi, binta yaci gaba dayi da kallo yayinda wasu miyagun miyan kwadayi suka cika mishi baki har sai da kyar yake iya had'esu,
Hasasowa kawai yake na yanda zai cinye bakin nan nata idan ya kamata.
Chocolate din ta mik'a mishi,
"Zakaci chocolate din ne kayi shiru?"
Murya a rarrabe cike da ininan daya fara a yanzun yanzun ya amsa mata da cewa.
"Ah ah ah niba chocolate nike soba"
"Mi kake so to?"
"Bakin"
Ya tsinci kanshi da furtawa cikin tuntub'en harshe,
Shiru tayi ba tareda ta kalleshi ba taci gaba dacin chocolate d'inta kamar bataji shiba,
A cikin zuciyar ta kuwa cewa take "haba malam ashe dai baka shigo hannu da kyau ba har yanzun da sauran ka to shi kenan muje zuwa"
Kallonta shima yaci gaba dayi can kuma dai ya kasa daurewa dan haka ya kira sunan ta a sanyaye yanzun din ma dai kamar d'azun muryar tashi da ininan da bata sanshi da ita ba ya kira sunan da yake kiranta dashi.
"๐ Heart"
Hummm ta amsa,
"Zan iya sumbatar ki"
"kwafal kwafal"
Wani munafukin tari ya sark'eta a bazata sakamakon shak'ewar da tayi da chocolate din bakin ta,
"Ki barni please in sumbace ki sau d'aya kawai, sau d'aya kacal"
Ya fad'a cike da rok'o yana marairaice wa,
"Tofa anzo wajen" ta fad'a a cikin zuciyar ta, a bayyane koh cewa tayi.
"Heart amma hakan fa sam sam babu kyau๐
๐ปโโ๏ธ"
Ta furta tana mai duk'ar da kanta cike da kunya,
"To shike nan tunda kin hanani"
Ya fad'a da karyayyen muryar dake nuna alamun sam baiji dad'iba,
Har yayi shiru kamar ya hak'ura sai kuma can ya juyo, "Dan Allah Heart sau d'aya kawai please ๐"
"Ka tabbata sau d'ayan kacal ne?"
"Eh na tabbata" ya fada yana mai matso da jikin shi zuwa kujerar da take sosai,
Yana binta ita kuma tana k'ara zuwa baya gashi kuma ta wani k'ankame jikinta sosai ta cure a waje d'aya,
Duk'owa yayi sosai zuwa jikin ta ba kuma wai ya had'e jikin nasu bane, a rashin sani hannun shi guda 1 daya dafe sitiyari dashi ya danna horn din motar ji kake motar ta bada sautin biiiiieeee da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 48 Chapter of 92