tashe da iyayen nashi nasu Baba Usman suka rankaya asibiti,
Hajiya ko a wannan rana tayi ma Malam Almu allah ya isa yafi cikin carbi dubu, a cewarta ga wani yana shirin sheqe nashi rayuwar akan jikanta amma mugun Yayan uba ya d'auki auren yar kanin shi da kullum yake ikirarin cewa yana sonta ya aura ma d'an d'an uwan shi wanda kowa yasan cewa ba lallai bane tayi daraja a wajen mijin ba tunda dai tuni tun Ana rade radi har kowa ya tabbatar da cewa matar Sarki ce Sarkin shi kuma bafade,
Gaskiya Hajiya taji bak'in cikin wannan aure sosai sai dai kuma bata da yanda zatayi ta hana ko tasa a d'aura da Bash da yake can kwance s asibiti dan koda Allah yasa ya farfado rikicewa jikin shi yayi dole iyayen shi sai da sukayi jinyar shi mai tsayi,
Bayan ya dawo hayyacin shi taso ganin Meenal kwarai sai dai kuma babu hali saboda dai tuni aka kaita d'akin Mijinta, gaskiya Bash yasha wahala sosai duk wanda ya ganshi a lokacin nan sai ya tausaya mishi domin sam ya kasa jure rashin Meenal,
Wannan dalilin shi yasa Maman shi ta matsama Master akan gara Bash d'in ya tafi k'asar waje ko sa samu ya mance da Meenal badan yaso ba haka ya shirya suka bar k'asar,
Shekara uku yayi a London ya matsa akan shi dai zai dawo Nigeria ganin da iyayen sukayi cewa zuwa lokacin ya cire batun Meenal sai suka yarje mishi dawowar, sai dai kuma tunda ya dawo Mahaifiyar shi ta fara matsa mishi akan maganar aure a cewar ta tunda Meenal tayi auren ta ai gara shima yayi, duk ta inda ta bullo mishi shi kuma sai ya kucce daga k'arshe daya gane cewa indai fa zaici gaba da zama a k'asar tofa bazata barshi ba ko auren dole ne sai ta mishi dan haka a sirrance ya had'a nashi ya nashi ya gudu yabar k'asa, Malesia ya koma wannan karan sai da yayi kusan shekara kafin iyayen shi suka gano inda yake, dan haka da suka tashi tafiya inda yake ita Maman tashi ita tayi tsaye saida aka d'aura auren shi da yarinyar yayan ta ikram sannan suka wuce mishi da amaryar shi can kasan,
Wannan abubuwa da suka faru na doguwar jinyar da yayi da kuma yanda ya gudu yabar gida ba tareda sanin kowa ba sune dalilan da suka sa ita uwar shi ta tsani Meenal dan ita a ganin ta ai kawai Meenal din ce ta yaudareshi dan da ace tana son shi tun farko da bazata hana shi zuwa wajen iyayen ta ya gabatar da kanshi ba,
Gashi yanzun ita tana gidan Mijinta hankali kwance ta manta dashi shi kuma har yanzun ya kasa cireta a ranshi balle ya maye gurbin ta da wata a cikin rayuwar shi,
Todai a dole a babu yanda zanyi dole haka nan ya amshi auren iklima bayan iyayen ta sun kaita da sati d'aya suka tattaro suka dawo gida Nigeria,
Zamane wani iri yake gudana a tsakanin ma'auratan domin dai shi tunda aka kai mishi ita gidan shi ko sau d'aya bai tab'a kallon ta a matsayin mata ba yanda ya saba gudanar da rayuwar shi tun farko haka yaci gaba babu abinda ya canja sai dai kuma yana dawowa gida da dare yake kulle k'ofar d'akin shi saboda yanda take ta faman kai mishi far maki abin ya isheshi, ace a kawo maka Amarya kuma wai budurwa amma tun baka nuna bukatar ka akanta ba ita ta fara kawo maka farmaki, dan haka sai ya d'auki matak'in k'in zaman gidan daya dawo kuma yake rufe k'ofa haka zatazo tayi ta bugu yayi mata banza,
Ita ko baiwar allah dama tun tuni ta dad'e tana renon soyayyar shi sai dai kuma a sanda ta bayyana mishi lafiyayyen mari ya wanke mata fuska dashi da kuma gingimemen gargadi kan cewa koda wasa idan harta bari wani yaji zancen sai yaci mata uwa,
Dan dole tayi hakuri ta kama kanta dashi badan taso ba sai gashi kwatsam daga baya suka samu labarin wai jaririyar yarinyar dashi bash din keso iyayen ta sun mata auren dole, ita Ikram ta girme ma Meenal nesa ba kusa ba sannan tana da waye da budewar ido dan kwata kwata bata da kunya, wannan halin nata shi yasa shi kuma Bash baya shiri da ita tun farko dan shi baya son auren macen da idanun ta suka riga suka bud'e irin haka yafi son karamar yarinyar da shine zai reneta da kanshi ya tafiyar da ita yanda yake so,
Watanni aka share Ikram tana ta faman son ganin ta shawo kanshi kodan saboda bala'in dake cin jikin ta na kayan mata na bala'i da ta d'ud'dura ma cikin ta tunda aka fara zancen auren ta dashi sai gashi an kawota amma har lokacin ba'a samu cigaba ba,
Ganin idan ta zauna a gida tofa wata rana sha'awa na iya sheqeta sai kawai ta dena zaman gidan, domin da zarar ya fice itama take yin nata shirin ta fice a binta,
A haka sukaci gaba da rayuwa bai rageta da komai ba illah harqallah na kwanciyar aure, itama kuma tunda ta zama yar gari ta samu masu d'ebe mata kewa ga kuma kud'ad'en da yake tura mata na kula da komai na gidan duk wata sai kawai ta tattara shi da auren shi ta watsar, da auren ta idan taga dama zatabi saurayi suyi tafiyar kwanaki bata gida, har taje ta dawo kuma ba sani yakeyi ba kamar yanda shima har yabar k'asar yaje wani wajen ya dawo bata sani, sai dai in tayi katarin ji a bakin uwar shi ko kannin shi,
Haka sukayi ta zama cikin wannan rayuwa har sai da suka shekara biyu da watanni da aure kafin ranar bacin rana ya risketa, domin dai tsautsayi ne yasa ranar ta gayyato d'aya daga cikin samarin ta har cikin gidan bata damu da cewa Bash yana nan ko baya nan ba tunda tasan ko yana gari idan ya riga ya fita gida da safe to sai tsakiyar dare zai dawo,
Abinda bata sani ba shine a wannan satin shi gaba d'aya ma baya k'asar Nigeria yazo saboda rashin lafiyan daya kama Master dole ya ajiye komai ya wuce Nigerian bai saba sallaman ta idan zaiyi tafiya ba dan haka koda zai tafi bai shaida mata ba, sai dai kuma zuwan shi gida a wannan lokacin nasihan dashi Master ya mishi na cewa ya rik'e matar shi da kyau kar yace wai dan ya rasa Meenal hakan zaisa ya wulakanta Ikram domin koba komai ita din yar uwar shice, koda Master ya mishi wannan nasihar yana cikin Zafin ciwo shi kuma Bash ya ma Baban nashi alqawarin dai daitawa da itane saboda bazaiso ace ya kasa bin nasihar da mahaifin shi ya mishi a cikin halin rayuwa ko mutuwa ba domin sosai Master yake jin jiki babu wanda yayi zaton zai tashi a wannan ciwon hatta da iyalan shi sun cire rai,
Sai dai kuma da yike ran bawa a hannun Allah yake sai gashi ya samu lafiya, a dawowar shi yaso ya fuskance ta su gyara zaman su dan ya shirya amsarta zai kuma gudanar da rayuwar auren su kamar na sauran ma'aurata sai gashi yana dawowa yayi mummunar gani,
Domin dai ita Ikram tunda tasan cewa gidan ta bawai gidan da bak'i ke yawan zuwa bane dan haka bata wani damuwa da kulle kofa saboda unguwar da suke akwai tsaro sosai kuma su can ba kamar mu nan Nigeria bane da zakaji tsoron barin kofa a bude,
Mummunar gani idanuwan shi sukayi mishi ganin da saida yayi silar yankewar numfashi daga k'irjin shi, a sanda ya farfado ko tuni kwarton daya tarar tare da matar auren shi ya cika ma wandon shi iska ya gudu ita k'adaice zaune a falon tana faman rusa mishi kukan munafunci da rokon shi akan ya taimaka ya rufa mata asiri shairin shed'an ne,
Duk hakurin da take bashi bai iya ce mata komai ba yadai samu ya lallab'a duk da duhun da jirin da yake d'ibar shi haka yakai kanshi d'aki,
Yayi kuka sosai domin yasan shima yana da laifi saboda da ace bai wofantar da itaba da babu yanda za'ayi tayi tunanin bin wasu mazan balle harta kawo mishi su gidan shi, shekaru kusan uku fa ake magana da auren su amma ko sau d'aya bai tab'a zama shida ita sukayi magana na fahimtar juna a tsakanin suba sosai yayi dana sanin irin rik'on sakainar kashin da yayi ma auren nasu lallai ya cutar da ita,
Kwana biyu yayi a cikin d'akin ba tareda ya fito ba ita kuma tsoron shi da kuma abinda take tunanin zai aikata akanta sune suka sa ta tattara duk wani abunda ta mallaka tsayin zaman da tayi a k'asar ta tattaro komai tabi jirgi ta dawo Nigeria, sai dai kuma koda ta dawo bata fad'ama kowa ainihin dalilin dawowar nata ba, tadai ce musu shine yace tazo gida dan dama tun auren ko sau d'aya bataje gida ba sai sukayi zaton kawai ko ta kawo ziyara ne,
Bayanda ya gama jinyar nashi ya fito domin yana son yin magana da ita ne ya tadda bata a gidan ganin babu kayanta a d'akin ta komai nata ta kwashe ne kuma hakan ya tabbatar mishi da cewa gida ta koma,
Bai tab'a zaton cewa zata koma gidan ba dan yaso ne kawai tunda komai ya riga ya faru shi yaji ya gani zai rungumi kaddara abinda yaso suyi shine suje asibiti a fara duba mishi lafiyar ta,
Idan har an tabbatar mishi da lafiyarta kalau to zai sa tayi istibra'i ne idan ta gama sai ya nemi wani Malamin da zai d'aura musu wani auren anan tunda bai san ko tun yaushe take mu'amala da wasu mazan ba, sai gashi kuma hauka da rashin hankalin ta yasa ta kwashi jiki ta koma gida,
Ya kuduri aniyar bazai bita ba tukun zai zauna yasa mata Idone tukun har zuwa sanda zata dawo, idan kuma iyayen su sun neme shi to yasan cewa ta tona ma kanta asiri kenan, dan haka sai kawai yaci gaba da harkokin shi,
Sai da tayi kusan wata biyu da tafiya kafin ya samu kira daga wajen Mahaifiyar shi akan cewa me ya hanashi zuwa bayan Ikram ta shaida musu cewa shine yace ta zauna har sai yazo sannan zasu koma tare,
To bai zoba kuma yan gulma sun fara yad'a surutai akan zaman da takeyi har yanzun bata koma ba ko dai akwai wani abun a k'asa ne?
Shiru yayi bai iya bata amsa ba data matsa sai kawai yace mata zaiyi kokari ya shigo k'asar zuwa karshen wata, karshen watan nayi ya shiryo ya dawo gida sai dai kuma abinda ya tarar bayan dawowar nashi har sai yafi na baya tashin hankali domin dai ashe ita Ikram tun dawowar ta mutane da yawa sun ankare da cikin data dawo dashi wasu da yawa sunyi zaton ko rainon cikin nema ya dawo da ita tunda acan k'asar basu da kowa sai su biyu,
Sai dai duk wanda ya mata maganar cikin saita basar dan ta gaji dace musu bata da ciki ita a zaton ta hutun data samu a can kasar shi yasa mutane ke ganin kamar ko cikin take dashi,
Ranar da yaje gidan su ikram d'in saboda kafin yayi magana da kowa zaiso ya farajin ta bakin ta idan babu wanda yasan abinda ya faru kenan komai zaizo mishi da sauk'i zai tambayeta ne idan tana ra'ayin zama dashi in kuma tace tafi son su rabu zai saketa ne kawai batareda ya tona mata asiri ba,
Sai gashi daga zuwa uwarta ta tare da cewa ai tayi zaton ko sai watan haihuwar ikram din ya kama ne zai dawo,
Da fari yayi zaton zolaya ne kawai sai da ta k'ara mai maita mishi cewa,
"Ai tunda ta dawo nace to kunyi kyan kai dan dama rainon cikin fari ai sai gida, kodan saboda abubuwan kwadayi da ita zata buk'ata wadanda ba lallai ku same su a can k'asar ba,"
Yanke ta yayi a yayinda yake bin ikram din da kallo da cewa,
"Ai bata d'auke da komai"
Dariya tayi ita kuma a nata zaton tayi tsammanin ko kunya ne yasa shi fad'in hakan dan haka sai tace "to ai tunda gaka kazo sai ka d'auketa kuje asibiti dan a tabbatar mana da wata nawa ne cikin nata, dan gaskiya in cikin baiyi kwari ba bazan yarda ka d'auketa ku koma can wata k'asar ba dan ku yaran nan ba hakuri kuka cika ba kuna iya kuje can wajen rashin hakurin ku ku zunguro cikin ya fita"
Bashi da yake cikin kwankwanto ba ita Ikram da ake zancen ciki a jikin ta itace take cikin tashin hankali mad'aukaki,
Domin a iya sanin ta dai tasan cewa kafin ta fara yawace yawacen ta sai da tayi planing na shekaru uku saboda gudun b'acin rana,
To ta ina kuma zatayi ciki, kenan planning din ne baiyi ba ko kuma dai wannan bala'in ne daban ake kira mata, zufa ke shatata tako ina a jikin ta, ciki fa ake magana bayan kowa yasan tana da aure amma ai babu wanda yasan cewa cikin bana aure bane,
Yanzun idan shi kuma ya bud'e baki ya fad'ama duniya gaskiyar cewa bai tab'a kwanciya da ita ba da wani idon zata kalli iyayen ta bayan babu wanda yasan tana biye biye,
Ita dai ta shiga ukun ta ta lalace da ace tasan da batun cikin nan da tun dawowar ta zata zubar da shege ko kuma tabi malamai a kulle mata bakin shi ruf ta yanda bai isa ya musa cewa cikin ba nashi bane,
Ta ina ma zata yarda ta haifi cikin da uban nin shi suka kasu sama da biyar dan ita tsabar jarabarta bai barta ta rayu da namiji d'aya ba, indai kana da kud'i kana kuma sake mata su babu ruwan ta zata barka ne kayi ido iya iyawarka to yau ga ranar bacin rana,
Dauriya sosai Bash ya aro ma ranshi koda Maman ikram din tace suje asibiti baiyi musu ba dan shima yana so a tantance din domin dai yanzun kam an yanka ta tashi,
Allah ya gani yaso ya rufama ikram asiri kodan saboda kasancewar ta yar uwar shi amma hakan zai yuwune kawai in babu cikin a jikin ta idan kuma akwai to babu ubanda zaisa shi amsar cikin da bai san inda ta samo shiba wallahi,
Uwar da kanta taja ikram din d'aki ta shirya badan taso ba haka ta fito ta same shi a mota suka wuce asibitin,
Wani private hospital sukaje inda acan ne aka k'ara tabbatar musu da batun cikin,
Tunda suka fito a asibitin ikram ke kuka shi dai bai kulata ba, to me zaice mata bayan inda yana da hali shima kamata yayi ya daura hannu akai yayi ta kwarara ihun har sai ya gamsu dan kanshi,
Gajiya da kukan tayi dan kanta ta nemi ya faka dan tana son su nemi mafita tun yanzun,
Bai musa ba haka ya faka motar a gefen titi yana binta da kallo da son jin abinda zatace,
"Yaya ni dakai dukan mu munsan cikin nan ba naka bane,
Kayi hakuri bansan da wani idon zan kalleka ba shi yasa na dawo gida, saboda in baka sararin da zaka yanke hukunci ba a cikin fushi ba,
Wallahi tunda Nazo ban iya fadama kowa laifin dana aikata maka ba saboda bansan da wani idon zan kalli iyayena ba, Yaya ka yafe min nasan na cutar dakai wajen cin amanar auren ka gashi kuma tun ba'aje ko ina ba Allah ya saka maka nayo cikin daba na aure ba, nayi laifi kana da damar da zaka hukunta ni nasan ban cancanci cigaba da zama a matsayin matar kaba, sai dai kuma ina so in rok'eka alfarma d'aya dan Allah ka rufa min asiri kamar yanda baka fadama kowa dalilin dawowa na gida ba bana son iyayen mu su san abunda na aikata maka ka rufamin asiri dan Allah, ko baka fadaba nasan cewa ni yanzun ba matar auren ka bane sai dai kuma duk da haka zanso ka rubuta min takardar saki wanda zai zama shaidar dazan gabatar bayan ka koma a matsayin ka sakeni,"
Katseta yayi da cewa shi kuma cikin jikin naki ya zakiyi dashi?
Zan zubar dashi saboda idan na haifeshi duk daren dadewa dole wata rana asirina zai tonu duniya zata gane cewa dan dana haifa da auren ka ba naka bane ni kuma bani da amsar da zan bashi idan ya tambayeni wanene uban shi, dan haka gara in zubar dashi tun cikin bai gama yin kwari ba,"
"Bakyajin tsoron wani abu ya sameki a yayin cire cikin? Ko baki san cewa har mutuwa anayi ba"
"Na sani amma hakan shi yafi min,"
"Ok tunda hakan kika zab'a ni bazan tilasta kiba rayuwar kine sai dai ina fatan hakan daya faru ya zama silar da zaki canza rayuwar ki"
A takaice dai a wannan ranar ikram bata yarda ta koma gida ba dan a hanya tasa ya sauketa bayan ya rubuta mata takardar saki d'aya ya damka mata ita kuma tayi cikin sabon gari ba ita ta koma gida ba saida aka kwalkwale cikin nan tsaf ta tabbatar da cewa ta rabu dashi koda ta koma gida kuma dauri ya ta aro sai ta sheda ma Mahaifiyar nata cewa ba ciki bane al'adarta ne yayi gardama amma an bata magani tayi amfani dashi har period din nata yazo,
Shiko daya tashi komawa koda iyayen sukayi magana ce musu yayi ba can Malesia zai koma ba South Africa zashi ta zauna har sai ya koma kafin ta dawo,
Sai da ya tafi da kusan wata biyu ita kuma lokacin tana da kusan wata HUDU kenan a gida kafin ta gabatar da takardar daya bar mata,
Ganin abin yana shirin tab'a zumunci ne kuma yasa ta fadama iyayen nasu cewa suyi hakuri itace ta mishi laifi kuma itace ta nemi Sakin,
Sunyi sunyi da ita ta fada musu maiya faru amma tak'i, shima kuma da aka tambaye shi sai cewa yayi su tambayeta,
A haka dai maganar saki ya tabbata aure ya lalace ba tareda kowa yasan mai ya faru ba,
Tun wancan lokacin kuma bai dawo k'asar ba sai wannan dawowar da yayi ya had'u da Maryam a k'ofar doka gashi kuma yau ya had'u da Meenal,
Meenal din da rashin ta ne duk yayi sanadiyar fadawar halin daya tsinci kanshi a ciki tsayin shekarun nan,
Taya kuma yanzun data dawo wata zatace mishi wai wani auren zata karayi, kenan suna nufin cewa zai kara rasata a karo na biyu?
Koda ya isa unguwar malamai so yayi ya wuce gidan su meenal din kai tsaye sai kuma wata zuciyar ta hana shi dan haka sai yaci burki a k'ofar gidan su Meelat kasancewar shi zaka fara isa kafin gidan Malam,
Cikin masu gadin gidan yayi magana da wani akan yayi mishi kiran Meelat d'in babu dadewa ko sai gata ta fito saboda basu dad'e da magana da musty ba yace mata zai bada sak'o a kawo mata amma sai gashi bayan fitar ta taci karo da bash,
Bash dai tsohon saurayin Meenal wanda yayi d'awainiya dasu a shekarun baya,
Lallai Maryam batayi karya ba da tace ya canza domin kuwa da gaske ne ya canza din ya k'ara girma da cikar kamala ga kuma arzikin da yaci uwar na baya,
Fara'ar dole ta aro ta yafa ma fuskarta a sanda ta k'arasa inda yake,
"Wa nake gani yau a k'ofar gidan mu kamar Bash din mu?"
"Ni ne dai Bash din Meenal ba gizo idanuwan ki sukai miki ba, Jamila ya gida ya kwana da yawa?"
"Ah ah aini bai kamata ma in tsaya ko gaisuwa muyi ba ace kana raye sai yau zaka nemeni tsayin shekarun nan ina ka shige Bash?"
"Kiyi hakuri nayi laifi amma bana k'asar ne shi yasa ban neme kuba, nabar k'asar ba'a cikin hayyacina ba a sanda abubuwa suka dai daita kuma bani da kwarin zuciyar da zan iya zuwa unguwar nan shi yasa ban neme kiba sai yau ina fatan za'amin afuwa?"
"Ah haba dai ba komai wallahi komai ya wuce ai, to ya bayan rabuwa ya rayuwa? Duk da dai Alhamdulillah yanda na ganka nasan an samu cigaba sosai, ya madam da yara to dan nasan kila baza'a rasa ba duba da shekarun da aka d'auka"
Guntuwar murmushi yayi kafin ya amsa mata da cewa,
"Alhamdulillah sai dai iyalin da kika tambaya ne har yanzun babu, sai dai muna fatan wannan karan a dace tunda shekarun baya dai an kasani"
Ya karasa fad'a idanuwan shi a kanta,
Murmushi itama tayi bata bashi amsa ba,
Sai ya daura da cewa,
"Dazun naga Meenal tareda wannan yayan nata na tudun wada, mun kuma hadu da maryam da wata kawarta dukan su a cikin ABU,
Sai dai ita k'awar tayi wasu magan ganu wanda ban gane ba shi yasa nazo nan,
Naso in wuce gidan su Meenal ne sai kuma naga ya dace in farajin ta bakin ki duk da ban sani ba ko kina gida ko allah yasa kinyi aure sai da na zo ne mai gadin ku yace min kina gida.
*UMMIEE ce*βπΌ
[9/21, 8:22 PM] Ummiee Zaria: βοΈπ±π¨βπ©βπ§βπ¦ *DANGINA*π¨βπ©βπ§βπ¦π±βοΈ
*BOOK 2*
*PAGE 33*
To mu shiga daga ciki mana nasan bakasan ansa ranar aure na ba wannan satin mai kamawa zanyi aure kaga ba dad'i mutane su ganni tsaye da kai a nan dan haka bismillah mu shiga daga ciki ina ganin hakan zaifi "
Cikin suka wuce suka nemi waje a farfajiyar gidan suka zauna,
"Bari in shiga ciki in kawo maka ruwa,"
"Ba bukata ki barshi kawai nagode"
"Ok tunda kace haka yanzun me kake son ji daga gareni?"
Ta tambaya tana binshi da kallo, tunda har ya wanko kafafun shi yazo har nan tasan gaskiyar yake son ji daga bakin ta dan haka babu amfani ta boye mishi.
"Ina son insan komai, idan nace komai Meelat ina nufin komai karki boyemin akan Meenal ,"
Gyara zama tayi da kyau kafin ta fara da cewa,
"Kamar yanda ka sani a shekarun baya da suka wuce kaida Meenal duka mun shaida kuna son junan ku, nasan kayi bakin k'okarin ka wajen ganin ka shawo kanta akan ta baka daman gabatar da kanka a gaban iyayen ta amma hakan bai faru ba har zuwa sanda komai ya faru,
tasha fad'ama na yanda kukayi da ita akan hakan,nasan a lokacin zakayi zaton ko bata sonka ne shi yasa amma kuma ita a gefen ta ba hakan bane, tak'i yarda ka gabatar da kanka din ne saboda tasan da zarar ka kai maganar ka gidan su to zancen aure za'ayi saboda kaima kasan yaran gidan su ba'a barin sukai har matakin da ita takai a lokacin ba tareda an aurar dasu ba,
WallahiΒ³ Meenal bataci amanar kaba ta kuma soka da dukkan zuciyar ta a wancan lokacin,
In baka sani ba bari in fad'a maka idan kuma ka sani hakan zai zama maimaici ne a gareka, ita kanta bata san cewa itama tana cikin wadanda za'a d'aurama aure a wannan lokacin ba har sai ana gobe daurin auren nata, tayi kuka tayi kuka babu kalar borin da batayi ba akan bata son auren amma kuma bata isa ta canza abinda Allah ya riga ya kaddara zai faru a lokacin ba sai dai kuma duk halin da take ciki bata manta da kaiba, ina da labarin kiran da Aunty Hassana tayi maka domin a wajen Meenal ta amshi number dinka,
Kayi hakuri a lokacin nida Maryam mun kasa zuwa asibitin da aka kwantar da kai duba Kane saboda bamu sanda wani idon zamu kalle ka ba, munyi zaton cewa zuwan namu zai iya zama
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 69 Chapter of 92