Allah ya dawomin dake lafiya" karasawa kan kujerar shi dake gefe yayi ya zauna "kinci abincin kuwa? dan kinga yau mun ɗan kara lokacin tashin karatun namu nasan kila kinji yunwa",
eh gashi na ɗiba ina kanci nema" karasowa tayi kusa dashi ta zauna a kasa gabda kafafun shi bayan ta adana littafan data amsa a cikin ma'ajiyar su,
Ina wuni Baba, ka dawo lafiya, ya gajiyar hanya ya mutanen Zuntun? Kun ɗaura auren lafiya? Ubangiji Allah ya basu zaman lafiya!.
Lafiya kalau na wuni uwata, kuma na dawo lafiya dan harda tsaraba ma nayi miki, mutanen zuntu suna nan kalau duk sunce suna gaisheda Uwar Malam, Alhamdulillah kuma mun ɗaura aure lafiya dan har an wuce da Amarya gidan ta tuni sai fatan zaman lafiya kamar yanda kikayi.
In kawo maka abincin nan ne ko saika huta zakaci?
To da yake ma dai bani da wani yunwa sosai inaga kiɗan ɗibomin kaɗan dai haka a faranti sai in gani ko zai shiga" to ta amsa dashi tana mikewa zuwa inda abincin yake saida ta tsatsatsakuri duk wani abunda tasan zaiso sannan ta haɗo da ruwa da zoɓo drink ta kawo,
Saukowa kasa yayi ya zauna da kyau sannan ya fara cin abincin,
Baba ashe karnukan Ƴa Sufyan suna cin naman mutum? ta jefo mishi tambaya dan abinda yake ta cizon ranta kenan tun ɗazun,
Tofa uwata ke waya faɗa miki?
"Toba wannan da yasa ya rakomu bane yace wai yau da mun kara lokaci har aka saki karnukan da sunci nama, wai karnukan ne zasuci naman mu, kaji shifa.
"Ah³ babbar magana to kinji koh ai shi yasa bana son kuna fitar daren nan yanzun da sun cizamin uwa yake nan? Kai lallai to uwata ki kiyaye fitan nan kin san ance hanyar lafiya a bita da shekara kinsan dai ko banza sojoji ba kirki ke garesu ba balle kuma karnukan su da suka sha training suka koshi,
To Baba haka za'a bar karen su dunga cizon mutane baza'ace su mai dasu can inda suka ɗauko suba? "
Ina Za'ayi haka uwata bakiga su karnukan sunayi mana gadi a unguwa bane? Aisu waɗan nan karnukan sune maganin yaran nan marasa kunya yan sara suka masu sa babba zabgawa da gudu ko bai shirya ba inya gansu, ko kin manta yanda kwanan baya suka so su fara shigo mana unguwa da sunan shara, kai ubangiji Allah dai ya shirya mana zuri'a kana nan yara su dunga ɗaukar makami suna shiga unguwan ni haka kawai duk wanda suka gani yaro ko babba tsoho ko tsohuwa mace ko namiji sai subi su sassare sai dai in ka hango su kafarka ta kwace ka, dan rashin hankali da sharrin kwayoyin da suke sha in an kamasu sai kaji suna cewa wai ai su sunje shara ne,
To saboda sune yasa ai Malam Sufyan yayi Magana a kawo mana sojijin da zasu dunga mana gadi su kuma waɗan nan karnukan ai nashi ne in yazo unguwar ne yakan sallami waɗancan sojojin suje su huta nashi yaran sojojin da karnukan suke kwana gadin mu ai mu muna cikin gidajen mu muna bacci, kinga ko ai abun a yaba mishi ne koh? Allah dai ya saka mishi da Alkhairi, "
Ciki² ta iya daurewa ta amsa mashi da ameen badan taso ba, dan ita bata san me yasa Malam yake son mutumin nan ba ko kaɗan baya son laifi ko tace Ƴa Sufyan yayi kaza sai ya nemo wani abunda zai wanke shi dashi, ita dai Allah ya sani ta tsani karnukan can masu shigen kama da zakuna, shegun karnuka dako gefen gidan kaje wucewa indai sunji motsin ka sai kukan su ya firgita ka, kawai su dai ana ɗaukar alhakin su duk sonta da zuwa tsinko mangwaro da gwaiba a gidan na Malam Ladan ɗin yanzun ba hali sabida sheggun karnukan nan insha Allah sai ta nemo poison ta basu sunci sun mutu.
Uwata ya dai tunanin me kike kuma? Malam ya katse mata tunanin ta, kafin ta bashi amsa uwar gidan shi ta shigo da sallama.
Bayan ta shigo tun kafin takai zaune tal farama Meenal ɗin tsiya da cewa " gaskiya fa gidan nan karara ake nunamin ban²ci ashe kin dawo tun dazun wato Baban ki kaɗai kika nema niko oho, to ai ba komai bari lokacin aure yayi mugani ko shi Malam ɗin binki zaiyi ku tare acan, "
Taran numfashin ta tayi da cewa
" barka da dare Innan mu, so nike fa in natashi daga nan dama in shigo, ai kinsan ban iya bacci saina ganki ko Baba"
"Kwarai kuwa uwata"cewar malam.
Ah² Malam ai kai daman kullum goyon bayan mai sunan manya kakeyi to barka da dawowa ya kika baro kakar naku da sauran mutanen gidan? "
Dukan su suna lafiya kuma sunce a gaishe ku tare muka dawo dasu Aisha ma," ta karasa fada a yayinda take mikewa bayan ta gama cin abincin datake ci,
"Badai har kingama yima Baban naki hirar ba? Naga kin mike alamun tafiya! "
Eh Innan mu akwai saƙon da zanba Momi ne kinsan ita da wuri take bacci shi yasa"
Malam ne yayi gyaran murya hakan ya maida hankalin su a kanshi Kayataccen murmushine kwance a fuskar shi a yayin da yake cewa "Innan su inaga fa maganar ki keson ya zama gaskiya, yau wacce rana kinga fa uwata ta shigo har tana shirin wucewa batayi tambaya akan tsarabar ta kamar yanda ta saba ba"
Dariya tayi tana mai amsa mishi da cewa aina faɗa maka ƴata ta girma,
Tsumewa Meenal tayi a tsaye ita kanta mamakin kanta takeyi,
"Allah Baba karnukan can na Ya Sufyaan ne duk suka firgitani" ta fadi hakan a yayin da take komawa ta zauna a kusa da Malam tana leke²n inda zata hango ledar tsarabar nata, "ina yake tsarabar nawa?"
Gefen shi ya mika hannu ya yawo wata leda bag "gashi ta nan asha lafiya jeki huta kuma sai da safe"
Haba malam ka mika mata kuma duka baka bani na ɗibi kasona a ciki ba shi yasa fa nace kuna wareni gashi kuwa! " ta faɗa tana juyar dakai gefe alamar tayi fushi,
Dariya Meenal takeyi tana mai cewa "Allah innan mu ke wai sai kice muna wani wareki, nidai ba ruwa na inma duka kike so gashi in kuma ɗiba zakiyi duka dai" mika mata ledar tayi ita kuma Innar tasa hannu ta ɗauki apple guda ɗaya a cikin ledan "nagode wannan ma ya isa yi maza kije nasan suna nan suna jiran ki"
Ficewa tayi tana musu saida safe.
A wannan rana dai kusan kwanan zaune su Meenal sukayi suna hira, domin koda ta koma ta samu Ya Sa'ad ya siyo musu kazar har biyu dakwa² ya kawo musu harda su ice cream kamar yanda yayi alkawari, basu suka rintsa ba har saida Momi Hauwa ta gaji dajin motsin su tazo ta sanya su baccin dole.
**washe gari ma da wuri Momi Hauwa tabar gidan dan ta samu kira na gaggawa daga asibity dan haka ta wuce bayan ta rarraba ma su Meelat ɗin aiki sannan ta doka musu warning cewar karsu yarda ta dawo ta cimma sun mata ɓarna a kitchen dan tana sane da abunda ya faru tsakanin su da hajiya,
To suma dai basu damu ba domin tun jiyan sun gama tsara cewa yau ɗin gidan Ya Mashkur zasu in sungama da can kuma zasu wuce gidan su Maryam dan ta kirasu da safen akan tana kan hanyar dawowa daga KD.
Da wurwuri suka gama gyaran gidan tsaf sannan sukayi wanka suka shirya da niyyar ficewa, saida suka fara shiga sashen Anty Murja suka gaisheta ita da Baba Adamu kafin suka wuce sasan Matan Malam suma suka miƙa musu nasu gaisuwar haka sauran sassan sirikan gidan saida suka zaga ko ina kafin suka yada zangon su a falon Baba Malam, to anan ɗin ma basu wani daɗe ba Meenat ɗin ta nemi izinin fita a wajen Malam kamar yanda ta saba akoda yaushe indai yana gida, to shima tunda yasan bawai yawon fitan ta cika ba shi yasa duk sanda ta nemi izinin fitan bai fiye hanata ba, dan haka yaudin ma fatan dawowa lafiya yayi musu da kuma gargaɗin su kula da kansu #2k ya cire ya basu da sunan ko zasuga wani abin a hanya.
***
Kira Anty kiji ko Ya Mashkur yazo gida"
cewar Meenat tana kallon Meelat, "kuma fa haka ne Allah yasa ma ya fita dan wallahi bana son muje gidan nan mu sameshi, dan wallahi yau duk abinda Nafi tamin ramawa zanyi" ta faɗa tana ciro wayar ta a jaka ta danna ma Aunty kira, wayar bata daɗe tana ringin ba Auntyn ta ɗauka, "Autar Aunty badai har kinyi kowata ba? ta fada muryarta cike da kewar ɗiyar tata, dariya Meelat ɗin tayi "Anty ina kwana"
Lafiya lau, ya kwanan mutanen gidan?
"Kowa lafiya lau Aunty dama na kirane in tambaya ko Ya mashkur ya shigo dan kinsan Meenat tace zamuje gidan yau"
To bai dai riga ya zo nan ɗinba, kardai kuje gidan ku zauna kinji koh Auta dakun gaisheta kubar mata gidan ta, ni dan ma kunki jin ta nawane da bazakuje ba"
Allah kuwa Anty bazamu daɗe ba zamu dawo bye" ta faɗa tana kashe wayar, hahaha tayi dariya tana kallon Meenat kinji Anty Allah bata son muje gidan nan kuma yau dai saidai tayi hakuri in mun dawo ma bata labarin yanda ta kaya.
"Ai wallahi Nafisan nan munafuka ce inta ganka a cikin mutane sai tayi ta maka fara'a kamar da gaske ta dunga fadin wai bama son zuwa gidanta bayan daka taka kafarka a gidan take canza fuska to yau dai gamu nan tafe gareki uwar Aslam kuma wallahi yau sai munci mun ture koya kukace? "
Ah kwarai kuwa Rabin rai fadi ki kara muda gidan Ya'yan mu ai dole mu sarara, duk wannan hirar da sukeyi suna kan tafiya ne sukeyin shi.
Wow tubarkhallah masha Allah gaskiya gidan nan ya wuce da kwatar zuciyata," Moon ta fada tana ɗaura hannun ta a kirji idanuwan ta a waje tana mai karema gidan kallo,
Gaskiya ba hassada nidai gidan nan yamin kyau ko a kasar waje sai haka,
Gaskiya indai irin gidan nan za'a kaini wallahi na shirya ayimini aure na hakura da karatun bokon"
Ta fada tana rungume Meenat cike da shauƙi, sororo Aishat ta tsaya tana kallon ikon Allah "ke Maimoon yaushe kika zama yar iska bani da labari dan ubanki daga ganin gida tun baki san meshi ba zaki wani ce kin shirya a miki aure! To shi mai gidan zaki aura kowa! "
Tafaɗa cike da takaicin Moon ɗin,
Inda kasan Meenat ta rufeta da duka haka takeji dan haka tayi kicin² da fuska dan abun yakai mata ko ina, ita ko Meelat inta kalli Moon saita koma ta maida kallon ta ga Moon sai kuma ta kyalkyale da dariya,
"Ke wai wani dariyar iskanci ne wannan kikeyi kamar wata taɓaɓɓiya ke kuma in baki rufemin baki da batun gidan nan ba kuka wuce muka tafi duk sai na muku rashin mutunci wallahi mtws koba gida ba kawai daga ganin gida dan hauka sai ki fara warwarewa kina sambatu"
Katseta Moon ɗin tayi da cewa "ke Meenat kiji tsoron Allah wallahi komin hassadar mutum yasan gidan nan ya gama haɗuwa, kinga fa yasin ko rantsuwa bazanyi ba nasan ginin mace gudane wannan gidan oh allah Allahumma Arzugni ya Allah" ta karasa addu'ar tana shafawa a fuskarta.
Ganin haukar na Moon da Meelat ba karewa zaiyi ba yasa fuuuu tayi gaba cike da takaici karo taci da mutum shi ya fito daga gidan cikin hanzari ita kuma adai dai lokacin burinta shine taga tabar kofar gidan, kanta ne ya bugi kirjin shi a take wayar hannun shi ta faɗi sai akan kafarta, "waiyi Allah Baba Malam za'a fasa maka kaina ta faɗa tana dafe goshin ta daya daki kirjin shi tana shirin yin kuka chak yayi tsaye yana binta da kallo dan gaba daya gabban jikin shi yaji sun sake.
"Ke karki sake kimin kuka a wajen nan" ya faɗa cikin muryar shi mai amo sosai ganin yanda tasa hannu tana mutsutsuka ido alamar gab take da fashewa da kuka.
"To bakai bane kawai ina tafiya na kashiga gabana ba waya sani ma ko goshina ya fashe"ta fada tana turo baki, "ai da yike kinsan da dutse kikayi karo dazai fasa miki goshin koh, come on duƙa ki mikomin wayata da kika yar min kuma tana fashewa sai kin biyani"
Dukawa tayi badan taso ba ta dauko wayar dake gefen kafarta ta mika mishi ba tareda ta ɗaga kai ta kalle shiba, karbar wayar yayi ya dudduba ta cikin sa'a dai wayar bata fashe ba, "Allah yasoki da sai kin koma gida kin faso asusunki kin gyaramin wayata, ba tareda tace komai ba ta ɗaga kafarta da niyyar tafiya cikin zuciyarta koh ba kalar kunkunin da batayi ba, daga kafarta yayi dai² da buɗe makeken gate ɗin gidan da akayi wata motar hilux ta fito daga cikin gidan ashe ba iya motar bane kadai harda waɗan nan sheggun karnukan nashi masu kama da zakuna a bayan motar fit haka karnukan nan da gudu kamar an korosu suna haushin su na rashin dalili,
Lura da fitowar karnukan da yayi yasa shi juyawa cikin zafin nama da niyyar ya kamota dan yasan yanda take jin tsoron su, aiko juyawar da zaiyi sai jinta yayi a cikin jikin shi ta wani irin rukun kume shi kamar wacce ke shirin komawa cikin jikin shi tama kasa ihun data saba na neman ceto duk sanda ta gansu sai ma numfashin ta da take wani irin jan shi da kyar, jikin ta ko babu inda baya rawa sai faman kara kankame shi take, ga kuma karnukan da suka kewaye su sukayi tsaitaye suna dararo harshen su ganin uban gidan su tsaye a kofar gidan,
Zuwan da tayi ta faɗa cikin jikin shi ba tareda tsammani ba yasa harta da fatar bakin shi yaji sun mishi wani irin nauyin daya kasa motsa su,
Sai ma runtse idon shi da yayi yana jin yanda take kara shigewa jikin shi tana gogga mishi abubuwan dake kirjin ta waɗanda suke karasa jinin shi yana kara daskarewa, duk yanda yaso ya cireta a cikin jikin shi abun ya faskara dan gani take da zarar ya cireta a jikin shin to karnukan shi zai mikama ita suyi kalacin hantsi dan haka taki yarda ta fita a jikin shi,
Da kyar ya samu ya buɗe bakin shi "ki nutsu mana baki ganin suma sun nutsu, sakeni ki gani bazasu miki komai ba"
Girgiza kanta tayi alamun bazata sake shi ɗin ba karamin murmushi yayi "oh dadin kwanciyar kikeji a jikin nawa kenan da kike ta wani kara kankame ni"
Dan ɗago kanta kaɗan tayi domin ta tantance shin wai a jikin nashi taken kamar yanda yace ɗin?
wani irin kunya neya kamata dayasa fita daga cikin jikin nashi babu shiri tana duddukar dakai gefen shi ta koma bayan ta kama hannun shi ta rike gam,
To kace musu su koma ciki nidai tsoron su nikeji ance suna cin naman mutane"
Kur yama fuskarta yana kallon yanda take motsa labban ta tana magana a shagwaban ce,
"Kaji" tace ganin yayi shiru kuma bai kora karnukan nashi zuwa gidan kamar yanda ta bukata ba sai ma zagaye su da karnukan sukeyi suna kaɗa bindi, kara manne wa da jikin shi tayi a sanda wata karya tazo dab da kafarta tayi kwance, "waiyo Allah dan Allah ka koreta ai kaga dai wallahi bada gangan nayi karo dakai har wayar ka ta faɗi ba Allah da nasan ma kana gidan nan da bance mu biyo tanan ba"
Alama yayi ma karnukan dasu wuce cikin gidan ganin yanda har yanzun jikinta bai daina rawa ba, "ki natsu nace wai me yasa kin cika tsoro ne Ameenatu"
Dago kanta tayi cike da mamaki take kallon shi dan tsawon rayuwarta bata taɓa sanin wai yasan sunan ta ba dan koda wasa bata taɓa jin ya kira sunan taba sai yau,
"Kibar kallo na Malama"
"To kaima ba tun ɗazun kaketa kallona kuma bance komai ba ta faɗa tana juyar da kanta gefe "ina su Moon? Ta fada a bayyane tana juyawa dan sai yanzun take tuna cewa ba ita kadai ta fito gida ba, can ta hango su a baya sunyi carko² duk da halin tsoron itama ba gama sakin ta yayi ba amma wallahi sun bata dariyar yanda sukayi tsamo² kamar waɗanda ruwa ya daka aiko sai ta kyalkyale da dariya, daga kai yayi shima yabi inda take kallo da ido dan yaga dalilin dariyar nata, ɗan murmushi yayi dan shima sun bashi dariyar saima girziza kai da yayi yana ci gaba da binta da kallon "Ya Sufyaan kalle su kagani dan Allah matsorata dasu kawai"
"Ai garasu tunda nasu tsoron baisa sun rungume wani sun tada mishi tarxoma ba"
Na'am tace tana kallon shi, shareta yayi "ina zaku ne ma wai?
Ku me yasa bakwa gajiya da yawo ne? "
Bafa yawo zamu ba gidan Ya Mashkur ɗin su Meelat zamuje'
Kara sowa su Maimoon sukayi "Ina kwana" suka hada baki wajen mika gaisuwar su gareshi "lafiya" yace a takaice juyawa cikin gidan yayi ya fasa fitar da yayi niyya dan yarinyar nan ta rusa mishi tsari kuma.
#karku manta dan Allah kusa Sister ɗina a addu'a, Allah ya baki lafiya Fauzy
#Share and Comment
#Ummiee~Zaria[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱 FAMILY HOUSE ⚜️🔱
~{{ȶֆɨռȶֆɨʏǟ ʍǟƊǟʊʀɨռӄɨ Ɗǟʏǟ}}~
*©®UZ-2023.*
*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne gareku mutanen gidan uwata Mai Dambu, most especially Oum Khadija💙, NAgode sosai da comment
*Surayyahms*
*Binta Umar Abbale*
Nagode da kulawa.
```Page11
Ba ita ta dena binshi da kallo ba har sai sanda ya kulle ta dena ganin shi tukun,doguwar ajiyar zuciya ta sauke tana mai maida dubanta zuwaga su Moon katuwar hararar tabi dukan su dashi tana mai cewa "ai wallahi kulli yaci amanar koko daga yau daga yanzun ɗin nan nasan zamana daku, shine dan cin amana kuka barni a gaba wato ashe ma tsayuwa kukaci gaba dayi kuna gulma,yanzun fisabilillah da Ya Sarki baya wajen nan fa haka karnukan nan zasuyi partyn kalacin hantsi da nama a wajen nan,gaskiya dai Allah ya isana,"
Meelat na danne dariyar da takeyi kasa² gudun kar Meenal ta gani ta dangwalo ma kanta wani jangwal ɗin tace "haba kawata kema kinsan bazamu miki haka ba,kuma ma waye a cikin mu yayi zaton karnukan suna gidan nan tunda mun san ba anan ake ajiye suba,kuma karon ki da Sarki ai naga laifin kine tunda ke kika kai mishi karo kika gaure shi koh? ta karasa faɗa tana kallon su Aisha "eh wallahi mu bamu san kinyi nisa bama",
" Yauwa kinji koh kuma ba gashi yauma Sarki ya kara cecenki a hannun karnukan shiba".
"Dallah yimin shiru ai wallahi nasan dake ce sai kinyi fitsari a wando da shegen tsoron kin nan,"
cigaba da tafiya sukayi ba tareda wata a cikin su ta kara cewa komai ba dan sunga alamar mutuniyar nasu fa ta shaƙa da yawa.
can dai Moon ta kasa daurewa tace "Bebs tsakanin ku da Allah gayen nan bai burgeku ba? kuma fa kamar mutumin da yasa aka rakamu gida jiya koh? duk da dai jiyan ba wani ƙare mishi kallo nayi ba dan Allah shike da gidan nan koh? Oh ya rabbi yau dai inga a sa'a na tashi shi yasa nike ta gane² nidai wallahi ya burgeni,ku baku gani ba duk tsayin Meenal fa wallahi nidai gani nayi kamar a iya kugun shi ta tsaya,oh Allah yau she za'a aurar damu ne kar maza masu kyau su gama karewa a barmu da kwarababbu masu kama da mata"
Takalmin dake kafar Meenal ta cire ta fara bin Moon ɗin dashi tana son lallai saita bugeta,faɗi take cewa "badai kin zama yar iskaba zaman lagos ya lalata ki kema kin iskance,to yasin duk ki gama iskancin ki ki ɗauka cewa kinyi shuka a idon makarwa ne domin kamar a kunnen Hajiya maganar nan"
ta karasa faɗa tana dafa Aisha da yau mamakin Moon itama yake ta neman kasheta wai Moon ce take ta maganganu haka kamar wata wacce tasha kwaya, so take tajawo musu bala'in daba iya kanta zai tsayaba dan dukan su zai shafa in yayyen su maza sukaji batun nan karma Iliya ɗan mai karfi yaji labari tasan shi kenan su kuma sun tashi aiki.
Cike da nishaɗi Moon tace" wai ke ƴar Malam miye matsalar ki shikenan mutum inyaga abu ya burgeshi bazai faɗa ba,to wallahi nikam na fada na kara gidan damai gidan duk sun burgeni,Allah da ace na isa aurema cewa zanyi ina son shi to miye a ciki".
Itafa tsakanin ta da Allah bata ɗauki hakan a bakin komai ba.
"Innalillahi wa'ainnah ilaihir'raju'un kai jama'a yau kuma boyayyun aljannu ne ke shirin bayyana a jikin yarinyar nan ne koya?
" Ke yana da mata fa" cewar Meelat dan ita Meenal ai nihin yau ne taga abunda ya isheta dan haka da ido kawai take bin Moon ɗin,.
"And so sai me dan yana da mata sai inƙi son shi kome?ko akwai inda aka rubuta kar aso mai mata ne?
Na rantse da Allah in bazaku zo mu tafi ba zanyi komawa ta gida ban son iskanci,ke dan makiyin ubanki har kike wani cewa miye dan kince kina son shi,to ai baida damuwa ko yanzun kina iya shiga ki faɗa mishi cewa kina son nashi,ai da nasan cewa iskancin Lagos jinin mutane yake bi dako ke bazan dunga sakar miki fuska ba iskancin banza mutumin dako dariya baya yi kullum fuskar shi a ɗaure shine zaki wani ce kina so tirr wallahi kin dai faɗi kasa ba nauyi wallahi,duk inda zai shiga fa haka zakiga yaran shi na binshi shine zaki wani ce kina so to sai kije kiyi ta kaya ai,shin zakuzo ku wuce ne ko tsayawa zakuci gaba dayi kuna kallon bakina".
Easy mana Meenal wannan zafin da kika ɗauka ai yayi yawa miye laifin ta dan ta faɗi abunda ke cikin zuciyar ta,ke shike nan dan baya burgeki sai kice kar wata ta
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 9 Chapter of 92