*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne ga gidaje biyu masu albarka,BENEFICIAL WRITERS ASSO,tare da gidanmu na gado abun alfahari FAMILY HOUSE,Allah ya ƙara haɗin kai ameen._
_*Ina mai bada hakuri sakamakon jina shiru da kukayi, to gani na dawo insha Allah zamu cigaba daga inda muka tsaya, Nagode.
*********/////////.
`````` Page 16
*Zuwa wannan lokacin sosai suka karayin suna kana kuma sukayi fice akan har kokin kasuwan cin su.
Sadeeq,
Yusuf,
Musty,
dukan su ukun sun Kama ayukanyi na gomnati duba da cewa dama su yaran masu (Kunbar susa; littafin Surayyahms) tun kafin su kammala nasu karatun daman iyayen su kan tanadar musu da guraban aiki a inda ya dace,
to su ma dai da yike yaran gaban goshin ne, Dan haka tuni nasu iyayen suma suka nuna bajinta su wajen samar musu da guraben aiyukan yi na garari,
sai dai sam Mai Gayya mai aiki ya nuna baya wani bukatar yin aiki a karkashin gobnati yafi muradin kasuwan cin shi dan ta hakan ne zai iya taimakawa al ummah kai tsaye ba tareda ya jira umarni daga na sama dashi ba.
Dan haka baiyi kasa a gwuiwa ba wajen Kara habbaka kasuwancin shi bayan kamfanin su da suka kaddamar Wanda yake na hadin gwuiwa tsakanin su hudun.
Mai Jama'a yana da Manya²n plaza daya gina a filin da Kakan shi na wajen uwa ya Mallaka mishi bayan Kasuwan cin da sukeyi na gwala²i wanda Ummi ke turo mishi su daga Saudiya, Sannan ga wasu daga cikin Kasuwan cin Dadyn shi wadanda shine yake kula musu dashi.
Hakan yasa ya zama busy sosai yau baya nan gobe baya can duk da cewa yana da mutane na amana wadanda suke kula mishi da wadansu abubuwan, duk da rashin samun lokacin hutun da yake fama dashi hakan bai hanashi Kara komawa makaranta ba yaci gaba da karatu shida Wase dan Musty da Sadeeq fir sukaki acewar su basuzo duniya dan bautar boko ba wanda sukayi Allah yasa mishi Albarkha su yanzun next agenda din su shine aure kuma,
Oho shidai bai damu dasu ba Dan shi idan har ya riga yasa kanshi yin abu tofa ko kanshi baya saurara har sai ya aiwatar, su basu san so yake ya maida kanshi busy ba dan komai ba kuwa har sai Dan saboda kwata² har yanzun bayajin lokaci yayi dazai kula wata diya balle akai batun aure, dan zuwa lokacin Ummi ta fara tuntubar shi akan batun auren dan yayyen shi maza biyu da yake bi sun fidda nasu matan har ma ana batun a hada auren nasu ayishi lokaci daya dan haka ta fara tuntubar shi taji ko zai yarda a hada da nashi ayi a lokaci daya.
Kuji wani neman magana irin na Ummi fa shi dan Allah yaushe har ya isa aure?
To yaji in ma sunce ya kai auren in sun mishi auren wazai kula da matar?
Dan shi dai lokacin kanshi ma ba samu yake ba balle ya kula da wata!
To in ma tace aure to shi fa har yanzun kaf cikin matan da suke rububin shi baiga ta aure ba, kai wama ya sani ko kilama har yanzun ba'a haifi matar tashi ba.
Oho su dai wadanda suka isa auren su sukaga zasu iya sai suje Suyi ta kaya amma shikam a rufa mishi asiri a shafa mishi lafiya.
Duk yanda Ummi takai gason ganin ta shawo kanshi hakan ya faskara dole ta hakura har zuwa lokacin da bikini su Mudassir da Saleem yayi suka baro Saudiya suka dawo aka sha biki dasu kafin suka koma,
Saleem yana aiki da NNPC ne a Lagos amma matar daya aura yar arewa ce jihar Kaduna shi kuma Mudassir Abuja yake aiki.
A gaskiya dai tako wani gefe Mai Jama'a ya kafu da kafafuwan shi Dan haka baya fadin komai sai Hamdala, domin arzikin dama akwai shi ko ba'a cigaba da nema ba an riga an tara sai kuma ya tadda inda akasan dadin shi ake kuma amfani dashi wajen daga marasa karfi Dan suma su dogara da kansu,
sau tari Hajiya kan mashi tsiya cewar bata san me zaiyi da kudiba kuma inba dai rijiya zai haka ya dunga zuba kudin ba Ina zai kaisu, shiko sai dai yayi dariya in kuma taci sa'a yakan bata da cewa,
"Hajiyata aiko sabida ke kadai dole in nemi kudi so kike wata rana ki tambayeni kudin siyan tikitin jirgin zuwa Saudi ziyara in nace babu kimin saki uku?
No!
No!!
No!!!
Hajiya ta kudi fa abin nema ne kedai kawai kiyita min addu'a Allah yayi ta bamu masu albarkha, Dan su kudi dadine dasu kobaka nema dan kanka ba Ka nema Dan mabukata.
Daga karshe dai Hajiya ta samu ta shawo kanshi da kyar da sidin goshi ya dawo gidan ta da zama bayan kammala degree din shi na biyu wanda hakan ne yayi dalilin dawowar shi Tudun Wada gaba daya da zama duk da cewar harkokin Kasuwan cin shi sunfi yawa a kudu duk inda yaje ya dawo dai gidan Hajiya ne masaukin shi, Yusif da Sadeeq zaman su yafi yawa a Abuja sai dai duk ranar Friday suke dawowa Zaria su koma Abuja on Friday Domin dukan su can suke aiki sai Musty shi kuma nashi Aikin a Kaduna yake yin shi dan haka duk ranar aikI zuwa yakeyi yana dawowa danshi ke kula musu da Kasuwan cin su na cikin gari,
A kullum shakuwa da kaunar junan su karuwa yakeyi domin komai daya daga cikin su zaiyi sai da shawarar sauran,
Bazamuce basa samun sabani kai tsaye ba,
sai dai suna da matukar fahimtan junan da koda sun samu sabani basa bari yayi tasirin da zaisa suyi fushi da juna duk da sau tari ma dai Ak ne yake shigar musu hanci da kudun kune wani lokacin a wani wajen can za'a bato mishi rai in bai samu ya sauke a can ba to Wallahi sai ya dawo wajen su da gangan zai janyo wani abun da zai sa dukan su ransu ya baci a banza sabida tsabar mugunta, inko aka fara musu dashi tofa ko abu farine zai kife kaine yace jane sai dai kai mai musun Ka gaji ka barshi, inko a cikin abokan su ne wani ya bata mishi rai rana guda zai ware yace yasa musu wasan kwallo to Insha Allah ko a cikin filin zai kirkiri wani mugunta da zaima wanda ya bata mishi ran ta yanda in ya kaishi injury sai yayi jinyar jikin shi, Wallahi AK bakin mugune duk wani hanyar mugunta a ruwan sanyi ya santa ta yanda zaiyi Abu da gayya amma babu wanda zaiyi zaton da gangan yayi saboda tsabar iya kisan mummuke sai dai kaji Ana cewa Wallahi tsautsayi yasa yau wane kaza yaji targade koya goce a filin ball,
Dan shi gani yake zuwa yanzun ai yafi karfin ya tube riga dan yin dambe da wani No a ruwan sanyi zai maka muguntar da zakayi sati ko fiye da haka baka iya fita yawo ba.
Komawar shi tudun wada yasa majalisar shi ta koma can dalilin da yayi ginin fadar shi kenan Domin ko sunan ya gama makaranta ne kawai amma koda yaushe yana tarene da daliban makaranta ta yanda in har ya samu lokaci yakanje ya musu lecture jefi².
Har yanzun kuma Hafsa bata hakura tayi aure ba,
kullum cikin binshi take a kokarin ta na ganin ta fahimtar dashi cewa itafa shi take jira, amma kullum amsar shi a gareta shine.
Shifa ba yanzun zaiyi aure ba.
To itadai ta daura ma kanta dakon wahala Dan kuwa dai bawai masoyan ta rasa ba, amma dai ta yarda zuciyar kare ya dauka,
Haka Nusaiba itama take fama, su biyun nan dai da kowa yasan yanda suka mato akan AK tofa kullum cikin dambace wa suke a duk inda suka yi kacibis kamar dai yanda suka dambatu ranar a kofar gidan Hajiya abun haushin kuma shi dai har yanzun babu wacce yake ma kallon mace a cikin su,
Duk yanda AK keda kyakyawar alaqa tsakanin shi da mutanen waje tofa kar kuce ya banbance matsayin yan matan family din su da sauran yan matan dake mishi naci a waje ne, dan suma basu tsiraba domin duk yanda yake dason yara tofa da zarar diya mace ta dan fara tasawa shike nan kuma tsakanin shi da ita tosai dai kuma in tayi laifi ya zane mata jiki dan sosai yake daure musu fuska a ganin shi suma idan ya sake musu da yawa ba mamaki cikin su a samu mai tsaurin idon da zatace sonshi take dan yasan dai koda ganganci baza'a danganta shi da wata diya da sunan auren zumunci ba.
wannan dalilin yasa suma suke tsoron shi suke kaf² da alamarin shi, duk da zamu iya cewa kaf cikin yaran family din maza babu mai kyauta da kyautatawa kannen shi kamar shi, domin duk abunda Ka nema a wajen shi ba zaka rasa ba,
sau da yawa ma yaran basu fiya tunkarar iyayen su da wani bukata ba sai Ya Ak yana da kyakyawar alaqa da kannen shi harda ma yayyen sai dai rashin daukar raini.
Saukin abun ma da kusan dukan su ba gari daya suke ba kowa yana inda yake amma hakan bai taba hadasu zumunci domin duk hutu Zaria sukeyin shi wani lokacin koba hutuma sukan zoma hajiya weakened.
*bari mu takaita bayani akan Mai Jama'a anan dan tafiyar mu da nisa kuma har yanzun bamuyi komai ba tukun*
Gaskiya in bakwayin comment ku sani posting zai koma sai yanda hali yayi😒.
Share Please
#Ummiee~Zaria
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱 FAMILY HOUSE ⚜️🔱
~{{ȶֆɨռȶֆɨʏǟ ʍǟƊǟʊʀɨռӄɨ Ɗǟʏǟ}}~
*©®UZ-2023.*
*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne ga gidaje biyu masu albarka,BENEFICIAL WRITERS ASSO,tare da gidanmu na gado abun alfahari FAMILY HOUSE,Allah ya ƙara haɗin kai ameen._
*Ga masu tambayar littafin daga farko zaku iya tuntuɓata kai tsaye da wannan number ɗin 08061358462,*
Karku manta littafina kyauta ne banyi shi dan in siyar ba dan haka karkuji ɗar kuba duk wanda kuke so.
Free book ne yan bati a dage da karatu a daure a dunga comment atoh.
```Page 17
*Mu koma gefen su Ameenatu*
Idan mai karu bai manta ba a page 14 mun tsaya a inda Ameenatu ke cewa.
"Daga can kuma gidan su Besty zamu nufa, dan haka zuwa gidan su Besty cancel ba wannan maganar a yanzun,
Daga nan muna gama siyan awarar Tudun Wada zamu koma dan gara muje muyi hakuri da halin Hajiya damu koma Sarki ya hadamu kwana daki guda da karnukan shi dan Wallahi bani ba kwanan cell nikam"
*Hajiya gamu nan tafe gareki*
ta fadi hakan a yayin da ta damki hannun Meelat sukaci gaba da tafiya zuwa inda su Moon suke,
Can suka hango su gaban kaskon mai awarar dake ta aikin suya awarar tana sallamar masu siya.
"Kun siya awarar ne? " Meelat ta tambaya a yayin da suka karasa wajen.
"Wanda ta kwashe bai kai na kudin muba dan koda muka zo akwai layi saida ta sallami na gaban mu tukun na, amma inta kwashe wannan kaskon zai ishemu"
Aisha ta bata amsa,
Tsugunno Meelat da Meenat sukayi a gaban kaskon duk kuwa da Cewar akwai tebiri na zama da aka tanadar ga masu siyan awarar musamman masu bukatar ci a wajen.
Hannu ta mika cikin karamin kwandon da take zuba awarar inta kwaso shi daga mai dan ya tsane ta dauki guda biyu sannan ta dan gwali yaji ako wannen su,
Mikama Meelat daya daga cikin awarar tayi sannan ta cusa dayar itama a baki duk da yankar awarar suna da girma ba laifi ba tareda damuwar cewa akwai Abu a cikin bakin taba ta mike dan karasawa kan bencin dasu Moon ke zaune tana mai cewa,
"Ke Moon ..... Tudunnn wada faa...... zamuu... wucce daga nan dan an yanka ta tashi"
Haka maganar ke fita a har harde dan tana magana ne tana kuma taunar awarar dake cikin bakin nata.
"Ke dai wallahi kalar ki daban ne Meenal to sai kace wani dole sai kinyi maganar kin cusa awara a baki kina magana kamar wacce aka shake ni ban ma fahimci abinda kikace da kyauba, naji kamar kince Tudun Wada komai ma ohon miki dai"
Aisha ke cewa tana hararar Meenal din,
Bata amsata ba sai bayan data gama hadiyar awarar tukun ta bata amsa da cewa,
"Eh cewa nayi Tudun wada zamu wuce daga nan"
Ba tareda Moon ta bari takai karshen maganar ba ta katseta da cewa "yin me kuma a gidan Hajiya? Kin sani sarai cewa tsohuwar nan da zarar Ka rabi inda take saita kirkiro wani abunda zatayi wanda ran mutum zai baci a banza ya su Aunty Sas su kuma suyi tasa mutane yin wadansu unnecessary ayuka, ni bazan hanaki zuwa ba inkin tashi amma nidai bada niba,
Kuma bari kiji inma tsoro ne yasa zaki gudu can to wallahi Ina fada miki gara miki gidan Malam koba komai nasan komai kika taro zaiyi tsaye wajen kareki dan in har gidan Hajiya ne to Ina miki albishir da cewa kowaye zai tsaya miki Ya AK bazaiji kunya ko nauyin rugurguza kasusuwan jikin ki a gaban su Baba Usman ba"
Moon takai karshen jawabin ta tana mai mikewa tsaye,
"Mai awara ki kwashe mana sauran haka ni bana son wanda ya soyu sosai kuma yajin a Leda zaki kulla mana kuma karki mana kauron yaji dan yau dai mu muka siye miki awarar shima Albasa da kabejin daban² zaki kullasu karki hada su waje daya"
Da "to" mai awarar ta amsa tana ci gaba da kirga musu awarar dan yau dai kam ita tafito a sa'a awarar dubu da dari biyar suka siyafa ko Ina zasu kaita oho, bata yi nawa wajen hade musu komai a cikin Leda ba Sannan ta mika ma Moon.
Bayan tashin Moon ko Aisha ne ta fuskanci Meenat tana mai cewa.
"Kin san Allah Sister komai zai faru gara ayishi anan muddin muka kwasa jiki zuwa gidan can tofa yau sunan mu sorry dama ace Dan Mai Karfi baya nan ne da sauki amma wallahi a yanzun kam gidan nan baya ziyuwa ke dan baki taba shiga komar Ya AK bane shi yasa har kike mararin zuwa can a yayin da kika tono kura to ki sani in tsoron ki kare can in kika je hannun mayun wacin zaki zaki afka, Meelat tashi mu tafi"
Ta fada tana sauke ajiyar zuciya.
Cigaba da tafiya sukayi batareda daya cikin su ta Kara tankawa ba har saida suka danyi nisa kadan daga wajen mai awarar,
Moon ce ta jefo tambaya kai tsaye jin babu wacce tace wani abu cikin su.
"Baku bamu labarin abunda ya faru a station din bayan kun kai yaron ba? Ko kuma su police din haka nan suka amshe shi ba tareda sun bincike juba? "
Gama tambayar nata keda wuya taja ta tsaya tana mai karema su biyun kallo,
Kauda kai Meenal tayi batare da ta bata amsa ba, Meelat ce tayi karfin halin zayyana musu yanda abun ya faru harda ma haduwar su da kwaro yayin fitowar su a station din.
Hummm kawai Moon ta iya cewa kafin wata cikin su ta samu zarafin magana wayar Aisha dake rike a hannun ta ya fara ringing ba kowa ke Kira ba sai Momy Hauwa,
"Wake kiran ki? "
Meenal ta tambaya.
"Momy Hauwa"
Aishan ta bata amsa,
"Dauka kiji me zata ce"
Meenal din ta bata umarni,
"Assalamu Alaikum Momy"
Acan gefen kuma bayan Momy ta amsane ta daura da cewa "Kuna Ina ne wai harna dawo tun dazun banga kun dawo ba, badai kuma daga gidan mashkur din wani wajen daban Meenal taja ku zuwa ba dan ga Maryam nan tazo tun dazun wai take kiran wayoyin su bata samu nima kuma na gwada kira baije ba, ku dawo gida haka yawon ya isa"
"To" Aisha ta amsa dashi tana mai yanke wayar,
"Momy tace mu koma gida dan Maryam tana gidan tun dazun ta Kira wayar ku duba bata samu ba, kuma da alama dai babu abinda yake faruwa a gidan,
Ina nufin banji alamun bacin rai a muryan Momyn ba dan nasan da abinda ya faru yakai gidan to tabbas dole ranta zai baci,
Dan haka muje gidan kawai ai dama hausawa sunce in zakasha giya kasha ta dubu,
Kuma da kuka kashe wayoyi taya zaku san abinda ke faruwa"
Jiyawa tayi ta kalli Meenal sannan ta daura da cewa ni ai nayi zaton cewa gwaskiya bata tsoron kowa Ashe dai akuyace da fatar kura"
Ta karasa fadan hakan cikin dariya,
"Wai ma hijira zuwa gidan Hajiya turkashi lallai Babyn nan har yanzun labarin Mai Jama'a kawai kikeji, kin dauki dan mutane kin kaima police da sunan tsuntuwa sannan dan wani ya ganki shine kike zaton neman tsira a gidan mai shara'a!
Lallai wanna shine ganganci Marin mace da magariba,
Toya yanzun kin shirya komawa gidan ne ko har yanzun kina kan bakanki na tafiya Tudun wadan?
Dan in sani kinga sai in diba miki awarar ki kiyi guzurin tafiya ala bashshi in kinje jiki ya miki tsami sai muzo mu dunga miki tuwon kasa"
Dariya su ukun suka sa
Itako gwaskiyar dogon tsaki taja,
"Kuzo mu wuce gida kar awarar nan ta huce"
Ta fadi hakan a sa'ilin da ta ciro wayarta daga cikin jakarta ta kunna,
Meelat ce tace
"Meenal bai kamata mu wuce ba tareda sanin halin da yaron nan yake ciki bafa,
Duk da nasan bazai yuwu mu koma station dinba amma nidai bazan so mu tafi mu barshi a can ba Ina ganin zaifi dacewa ko wani ne mu wakilta ya leka mana station din kinji"
Ta karasa fada cikin sanyin jiki.
"To ya kike ganin za'ayi? "
Meenal din ta tambaya,
"Mu shiga gidan su Sakina in tana nan sai mu wakilta ta taje ta dubo kin san Yayan ta Lawal police ne kamar ma anan ganuwa yake aiki dan haka nasan shiga cikin station din bazai bata wahala ba kuma suma police din bazasu zargeta ba.
"To mu karasa gidan Allah yasa tana nan" Cesar Meenat.
Da yike gidan baida tazara mai tsayi da inda suke nan da nan suka Samu isa gidan,
sun kumayi sa'a sun isketa basu bata lokaci ba dan ko zama basuyi ba da yike ma Allah ya taimake su mutanen gidan basa nan ita ma Sakinar tace musu bata dade da dawowa ba wai sunje kwarbai biki ne, babu bata lokaci suka zaiyane mata kaf din abinda ya faru da kuma abinda suke bukatar tayi musu na zuwa station din danta binciko musu halin da ake ciki,
To da yike dai dama ita dasu din duk zamu ne ta tadda muje mu ba tareda wani nazari ba amsa bukatar su dan haka suka kara rankaya wa zuwa station din........
Kar a manta a dunga sharing please 🤍
#Ameenatu. 🧕🏻
#Team Sarki. 🤴🏼
#Team Mai Jama'a. 🤵🏻
#Sheikh Naseer.👨🏻💻
#Ummiee~Zaria
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱 FAMILY HOUSE ⚜️🔱
~{{ȶֆɨռȶֆɨʏǟ ʍǟƊǟʊʀɨռӄɨ Ɗǟʏǟ}}~
*©®UZ-2023.*
*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne ga gidaje biyu masu albarka,BENEFICIAL WRITERS ASSO,tare da gidanmu na gado abun alfahari FAMILY HOUSE,Allah ya ƙara haɗin kai ameen._
*Ga masu tambayar littafin daga farko zaku iya tuntuɓata kai tsaye da wannan number ɗin 08061358462,*
Karku manta littafina kyauta ne banyi shi dan in siyar ba dan haka karkuji ɗar kuba duk wanda kuke so.
Free book ne yan bati a dage da karatu a daure a dunga comment atoh.
```Page 18
******* A cikin wani lungu da yake nan daura da gidan su Sakina kafin a karasa ga police station din Meenat! Meela!! da Aisha suka labe yayin da Sakina da Moon suka karasa cikin station din,
Batareda da ko dar ba kai tsaye suka shige station din domin dama ita Sakina ta saba da police din wajen saboda Yayan
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 92