nan fa"
Maryam ta fad'a tana hararar Sultanan,
"Ai ko baki ba kanki wahala ba ni daga ke har ita kallon tsaf nike muku wato ita Sultanan tunda ta cokalo zuciyar d'an mutane shine take neman tayi mishi wulakanci,
To duk ku gama munafuncin ku aini ko jiya da muka had'u dashi a wajen dinner na fad'a mishi cewa wallahi indai ya shirya k'arya wani saurareta ya wuce kawai kanshi tsaye ya koma wajen Baba Malam tunda ga yanda abubuwa suka kasance ya rasa Meenal to sai suyi mishi madadi da Sultanan," cewar Moon tana hararar Sultana,
Hayayyak'owa Sultanan tayi tana mai cewa,
"Allah ya tsareni wallahi nikam nafi k'arfin ayi madadi dani,
Shid'in wani tsamiyar biri dashi ne zai waniyi madadi dani,
Aini wallahi nafi k'arfin shi me ma zanyi dashi yana ji da isa kamar wani d'an Sarki, ke ni kaf Zaria ma fa banga mijin aure ba, ku barni kawai in koma Abuja ko Allah zaisa inyi gamo da katar da wani b'arkeken Alhajin dazai gina min gidan sama in shige abuna sai nayi sati masu aikina dake k'asa basuga kalar fuskata ba" ta k'arasa kalaman nata da k'arkato d'aurin kanta zuwa gaban goshi,
"Aiko dai wallahi an mata kinyi karya kice Bash bai burge ba, sai dai kawai kice kina so kina kaiwa kasuwa"
Meelat ce ta amsa musu yanzun,
"Wai bash ne yace yana son Sultanan?"
Meenal ta tambaya,
"Kwarai kuwa ke koh ai Sultanar mu bata wasa bace dole in namiji ya kalleta gaban shi ya fad'i bari kiji in baki labarin abinda ya faru ranar da aka d'aura auren ki da yamman yarinyar nan bata huta ba sai da ta cire number din shi a cikin wayar ki,
Video d'in zaman da akayi a falon Malam dana d'aurin auren ku duk ta kwasa ta tura ma Bash din bayan ya Sa'eed ya turo mata video din kamar yanda ta buk'ata,
Dan allah kuce yarinyar nan ba kashe d'an mutane taso yiba?"
"Ke Sultana meya kaiki inda ace da kika tura mishi bayan ya bud'e wani abu ya same shifa?"
Cacaca sukaci gaba da surutu kowa dai cewa yake Sultanar bata kyauta ba ita kuma ta had'e fuska tasha kunu abinta,
Meenal ce kad'ai bata tofa komai ba tana dai bin su da kallo ne kawai,
"Sai me ya faru kuma daga nan?" Moon ta tambaya,
"Yauwa to bayan ya gama kallon video din shine ya k'irata dan yaji ko waye ya turo mishi video din tunda ai shi dai bashi da number din ta, duk da yace min ya kwada number din a true caller Sunan Amina ne yayi appear a wajen amma bai tabbatar da cewa ita bace sai da ya k'ira,
Ita kuma bayan ta gama jan ajinta kafin ta d'auki wayar data d'auka sai tambayar shi tayi cewa congratulations kaga sakon dana turo maka?,
Ai dama nace maka an kasa ka toga tabbas nan ka gani basai na tsaya maka dogon zance ba,
Shi kuma sai yace mata oh kece Amina Sultana koh?,
Kwarai nice dai ashe ka gane ni,
Na taya yar uwar ki murna sosai ina kuma fatan Allah ya basu zaman lafiya ita da mijin ta, ke kuma ina miki albishir kamar yanda kika min dan kema ki shirya nan da kwana kad'an zaki zama Amarya mallakin wani kamar dai yanda itama a yau ta zama mallakin mijinta, yana gama fad'a mata haka sai kawai ya yanke wayar shi abinshi,
Ita kuma bata wani damu ba sai kawai taci gaba da harkokin ta, daga nan shi kuma sai ya taso rayuwarta a gaba da yawan kira da sak'o dan a daren da sakon ta na auren Meenal ya riske shi shi kuma ya yanke shawarar yin ma Meenal madadi da ita dan haka washe gari ya kirata, ya fad'a mata cewa sonta yake yi fa kuma daya ce ta shirya ma nata auren bada kowa yake nufi ba sai dashi,
Haka ta rufe ido ita kuma ta tsitsigale shi kamar dai yanda ta saba hakan kuma baisa ya gajiya ba haka yaci gaba da bibiyarta kuma ko jiya yaje wajen dinner ita Sultanar ce ta hanashi shiga nima acan na ganshi kuma duk shi ya bani labarin komai ni kuma nace mishi ya tura wajen Malam kawai karya b'ata lokaci,"
"Munasira wato shine take ta nokewa dan karmu sani mu tayata murna to wallahi nidai na bashi, ko ku baku goyi baya ba kuwa"
Meenal ta fad'a tana kaima Sultana duka,
Haka suka tasa Sultanar dayau bakin ta ya mutu murus gaba suna tsokana.
Da dare Hajiya na idar da sallan ishsha'i ko hijab bata cireba ta kama hanyar sashen su Meenal bata jira komai ba ta taso k'eyarta suka koma sashen Hajiyar,
AK ko tun barin shi sashen nasu da safe bai k'ara komawa ba dan ko abokan shi da zasuyi sallama da Meenal Sadeeq ne ya musu Jagora,
Da dare yayi koda ya shigo rashin ganin ta a falon k'asa bai d'aga mishi hankali ba sai dai ga mamakin shi a saman ma dai shiru ne duka d'akunan ya duba bata nan, hakan kuma bai sa ya wani damu kanshi ba sai ma bathroom daya shige yayi wanka yana fitowa yayi shirin bacci lokacin karfe 11 harta gota,
Dakin ta ya koma dan yasan zuwa yanzun duk inda ta shiga ya isa ace ta dawo ta nemi makwanci amma koda ya duba bata babu alamarta,
To ina take?
shida yayi tambayar shi ya ba kanshi amsa da cewa sashen Hajiya, dan haka can ya nufa amma koda ya isa wai har sun rufe k'ofa ta baya yabi Allah ya taimake shi basu kulle kofar kitchen ba dan yana turawa yaga ya bud'e,
Da kwarin gwuiwa ya shige ciki dan so yake ya ritsa yarinyar nan ta fad'a mishi dalilin ta na dawowa nan ta tare,
To data dawo nan tana nufin shi kad'ai zaici gaba da rayuwa acan ne?
Falon dund'um yake da duhu dan haka sai yayi amfani da torch light din wayar shi ya haska ya haura zuwa saman,
Kamar wani b'arawo haka ya dunga sand'a d'akin hajiya ya fara lek'awa ya hango ta nannad'e cikin bargo sai kwasar baccinta takeyi abunta,
Maida kofar yayi ya rufe ya k'arasa d'akin Meenal k'asa² yayi sallama a yayin shigar shi cikin d'akin yana binta da kallon mamaki, yayi zaton zai sameta tana bacci ne amma wai sai gata zaune a tsakiyar gado dangalgal sai wasu d'irka²n littafai irin nasu na likitanci dake gefen ta d'aya kuma yana rik'e a hannun ta tana karantawa rigar shimi singilat ne a jikinta da wani burmemen siket ne ko wando bai dai tantance ba,
Daure fuskar shi yayi tam a yayinda yake k'arasawa inda take karma taga damar shi tace zata raina shi,
Itama din kuma da kallo kawai take bin shi tun shigowar shi dan dama ita jikinta ya fad'a mata cewa wallahi sai ya biyota nan d'in musu ne kawai bata so tanayi da Hajiya shi yasa ta biyota suka taho tare,
Tun bai kai zaune ba ya jefo mata tambayar dake cikin bakin shi,
"Me kikeyi anan har k'arfe 11 na dare ya wuce baki koma sashen kiba?"
"To ba Hajiya bace taje ta taho dani"
"Ban gane cewa ta taho dake ba, ta taho dake kamar ya?"
"Oho nima ban sani ba ta dai ce anan zan zauna"
"Ke dallah ban son rainin wayau tashi ki wuce mu tafi"
"Ai dai kana gani karatu nikeyi kuma yanzun kawai sai in bika mu tafi Hajiya bata sani ba,"
"Kambala'i! Eh lallai bakya neman zaman lafiya yarinyar nan shin to wai ma waye mijin ni ko hajiya?"
Shiru tayi bata amsa shiba shi kuma sai yasa hannu yahau tattara takardun data jibge akan gadon yana mai dasu mazaunin su,
"Tunda anan kike son mu kwana yau ai shi kenan"ya fad'a a yayin da yakai zaune a gefen ta ita kuma sai ta matsa,
"Nidai ka tashi ka fita in ma anan sashen zaka kwana ai naga dai kana da naka d'akin a kasa ka sauka ka koma can nidai kar Hajiya taji motsin ka"
"Ke wai ya kike korona ne, miye in Hajiya taji motsina bafa kwartanci nazo yi ba wajen matata nazo,
Inma dai bacin an raina ni taya daga kaimin Matar jiya yau za'a wani d'aukota a dawo da ita nan,tunda kin zab'i zaman nan ai gani nima nazo"
"Wai anan kaima zaka kwana?"
"Kwarai kuwa tsorona kike jine? Naga dai tsakanina dake kuma ai babu wani abu da yayi saura me ya rage kuma bayan jiya babu abinda ya rage ban gani kuma na tab'a shi da hannun nan nawa ba"ya fad'a yana d'aga hannayen nashi,
"Nidai dan Allah ka tafi ai gobe da kaina zan koma can d'in"
"Ah ah ai kuma na fasa nima na shirya yin mak'otaka da Hajiya kinga ita tana can tana bacci mu kuma gamu anan zamuyi gabatar da bauta"matse mata waje yayi bayan ya sak'ala hannun shi ya rike kugunta ta gefe,
"To yane kin shirya?"
Muryar ta na karkarwa ta amsa mishi da cewa, "nidai gaskiya indai anan din zaka kwana to tsaya kaji, babu runguma kuma ba kiss bacci kazo yi ka kwanta ga waje nan kaga dai aini karatu nikeyi koh?"
"Ke wai ni zaki kafama wasu sharud'anki na banza? To bari in gani waye mai taurin kai a tsakanin mu biyun,"
K'arfi yasa ya maida ta zuwa baya shi kuma ya haye saman ruwan cikin ta yana kissing sassan jikinta yana kuma mata cakulkuli a lokaci d'aya,
Duk yanda taso ta rik'e dariyar ta gudun kar Hajiya ta jiyo su hakan ya gagara, babu shiri ta dunga kyalkyala dariya shima yana tayata,
"Waiyo Allah Yaya dan Allah ka bari kar kasa dariya na ya k'are"
"Oh Yaya ma kike cewa ko? Wato dai har yanzun ban kai matsayin da zaki sauya min suna zuwa mai dadi ba, to bazan bari ba yau sai kin kirani da daddad'an suna"
"To Kayi hakuri ka zab'a da kanka ni kuma zan kira ka dashi"
"Naki wayan kedai zaki zab'a da kanki" ya fad'a yana cigaba da aikata aikin daya sa kanshi,
"Honey"
"Ah ah ba dai honey ba"
"Sugar to"
"Sugar kuma ana zaune kalau tea zaki sha?"
"To sweetie"
"Shima bai min ba" haka yasa ta ta dunga jero mishi sunaye amma duk wanda ta kira sai yace bai mishi ba ta canza wani,
"To dan Allah kai kana tayin abu kamar dai Baby"
"Wow what a nice name, kinga kenan daga yau na zama Babyn ki nidai hakan ya min"
"Ah ah nidai ban yarda ba gaskiya taya kawai k'aton ka dakai sai in wani kiraka baby kuma ka amsa"
Ihun dariyar sune ya tashi Hajiya daga bacci bayan ta farka ta d'an jima a kwance tana son ta tantance daga ina dariyar yake fitowa ko dai cikin bak'in da akayi ne wani ya kawo mata tsarabar aljanu masu dariya,
Jin dariyar yaki d'aukewa ne ta mik'e ta sauko daga gadonta tana karanta ayatul kursiyu a bayyane ta bud'e kofar d'akin ta fito,
Hasken wuta ta hango daga cikin d'akin meenal kuma daga nan takejin dariya dama k'ananan surutai,
"Wai yaron nan biyo yarinyar nan yayi ita kuma munafukan ta bud'e mishi kofa ya shigo suke min iya shege a cikin sashe?"
Kofar d'akin ta fara bugawa,
"Kai Abdul tattaro Matar ka kuzo ku barmin sashe bazaku hanani baccin dare ba wallahi,
Ke kuma badai ni zaki juya ma baya ina tausaya miki ke kuma bakyajin tausayin kanki ba?
Da kaina fa na kulle kofar falon nan saboda dama nasan tabbas zai biyo sahu wato shine ya kiraki kikaje kika bud'e mishi kofar ya shigo, to ku tattaro ku wuce can ku k'arata"
Shi dama ai da gayya ya aikata abunda yayi dan haka babu b'ata lokaci yama yar Matar shi d'aukar chak ya sauketa akan gadon,
"Ka gani ko shi yasa ai nace ka koma,
ka koma kai kuma kak'i tafiya gashi nan ai kaja ta ritsa mu"
Bai kulata ba sai da ya ciro Hijab yasa mata kafin ya k'ara mata daukar cak tana wutsul² da kai mishi duka akan ya sauketa yak'i sai ma gyara rikon ta da yayi ya bude kofar ita kuma sai ta cusa fuskarta a k'irjin shi saboda kunyar Hajiyar daya rufeta,
Duk surutan da hajiya keyi bai tanka taba har suka sauka k'asa ya bude kofar falon sai da ya fita kafin yace da Hajiya " Hajiya sai da safe kuma dan Allah goben nan dai in Allah ya kaimu a raye kar ayi saurin zuwa kawo mana breakfast da sassafe idan mun tashi zamu zo mu amsa"
Yana gama fadar hakan ya wuce abinshi yabar Hajiya naci gaba da sababi,
"Wani shegen ka ajiye dazai muku girki?
Ai kuma kunyi da y'a wallahi bacci kuma idan k'unso ku yini goma kunayi jarababbu kawai".
*UMMIEE CE*✍🏼
[10/18, 3:06 PM] Ummiee Zaria: ⚜️🔱👨👩👧👦 *DANGINA*👨👩👧👦🔱⚜️
*BOOK 2*
*INA MAI CIKE DA FARIN CIKI A YAU DA ALLAH YA BANI IKO NA GANIN NAKAI K'ARSHEN WANNAN LABARIN MAI SUNA A SAMA*
*NAGODA KWARAI GA MASOYA WAD'ANDA SUKAYI JIMIRIN BIBIYAR LABARIN TUN DAGA LITTAFI NA D'AYA HAR ZUWA YAU, KU SANI CEWA UMMIEE ZARIA NA KAUNAR KU KUMA NA YABA DAN HAKA NIKE MA KOWA FATAN ALKHAIRI,INA SONKU³ SAU A DADIN DA BAKI YA GAZA FURTAWA YAN GROUPS DINA FAMILY HOUSE DA DANGINA COMMENT SECTION DAMA SAURAN GROUPS NAGODE KWARAI INA FATAN ALLAH YA HAD'AMU A GABA CIKIN AMINCIN SA*
*BAYAN WASU KWANAKI*
Amarci sosai ake gurza tsakanin AK da Amaryar shi wanda tun Hajiya na yawan surutu in taga sunyi wani abun har dai yakai dan dole ita da kanta ta gaji ta shafama kanta lafiya ta kawo ido ta zuba musu,
kuma dan wulakanci basu tashi barbad'a ruwan rashin kunyar su ako ina sai sunzo sashen ta, tayi kora harta gaji amma sunk'i suyi zuciya su dena zuwa mata sashe, dan haka ta taso AK d'in a gaba da mita cewa yayi da jiki ya kammala gyaran gidan shi na Kaduna ya kwashi matar shi subar mata gida ita bazata iya gani ba dan kar suja mata makantar wuri,
shi kuma yace mata barin Zaria ba yanzun ba har sai sun bar mata d'an raino dan in suka bar gidan tun yanzun ciwon kewar su yana iya kamata.
Acan unguwar malamai ko maganar gidan Malam da Meenal ta bashi ko ana watse bikin Meenal d'in yaran gidan mazan su da mata kowa ya bada nashi gudun mawar wajen sanyama gidan kayan furniture da sauran su ana kammala gyaran gidan kuwa suka shirya walima gangariya Malam yanaji yana gani dai haka shida iyalan shi suka koma sabon gida aka bar Baba Adamu da Baba Auta a family house suda sauran ahalin,
Soyayya tsakanin Bash sa Sultana kuwa abu dai kamar wasa tun tana basar dashi tana nuna ita batayi har dai da taimakon su Meelat, Maryam, Moon da ita kanta Meenal din wanda suka tayashi yak'in neman zab'e a fadar Sultanar daga k'arshe dai sunci nasara ta amsa sai gashi a hankali abubuwa sun kankama dan koda Bash ya k'ara tura iyayen shi wajen Malam a karo na biyu Malam bai b'ata musu lokaci ba a gaban iyayen nashi ya kira Sultanan ya zaunar ya kuma tambaye ta shin ko tana son Bash d'in? kuma da yardar ta ya turo a nema mishi auren ta?"
Bata tsaya ba sharia wahala ba itama ta amsa da cewa eh, bayan ya sallameta tabar falon mahaifin ta ya kira ya mishi bayanin halin da ake ciki kuma yarinya ta amsa cewa eh tana so dan haka yana so a basu dama suje can Abuja su nemo auren ta,
Alhaji Mahmoud yaso ace Malam ya zartar da komai amma sai Malam din ya zame akan gara dai ya basu ranar da zasu je shi sai yayi ma iyayen bash din jagora,
To dai da yike magana ne na manya babu wani kolo² ya basu ranar da zasuje dan haka iyayen Bash suka bar gidan Malam cike da farin ciki *wannan kenan*,
Itama Maryam a gefen ta ana gama bikin su AK Sadeeq ya sata a gaba da cewa shima fa a yanzun ya fasa wani jira har saita kammala karatun,
Tunda dai yan watan ni ne suka rage musu kawai tayi hak'uri ta k'arasa a cikin d'akin ta itama kamar dai sauran kawayen ta,
Taso ta bujire sai dai da wuri ya taka mata burki wajen kai maganar gaban manya babu b'ata lokaci kuma aka sa bikinsu sati d'aya tsakanin su da nasu Moon ita kuma Sultana bayan zuwan su Malam Abuja wata d'aya kachal akasa nata bikin dan haka nasu Sultanan za'a farayi kafin nasu Moon da Maryam d'in,
AK tuni ya koma KD yaci gaba da gudanar da abubuwan shi sai dai yanzun a maimakon weak ends da yake dawowa zaria sai ya mai dashi duk bayan kwana d'aya ko biyu, wani lokacin ma bazai fad'a mata cewa yana hanyar zuwa ba sai dai kawai ta ganshi kwatsam duk da bako yaushe yake tareda ita ba hakan bai rage komai na daga kauna da kulawar da suke ba junan suba.
***
Bayan wani lokaci da bikin su Meenal hutun yan makaranta ya k'are dan haka bak'in gidan Hajiya suka fara haramar komawa gidajen su akan sai bikin Moon kuma idan Allah yakai rai zasu dawo,
Dan haka ana gobe zasu tafi suna zaune a falon Hajiya suna hirar dare Hajiya ta kawo nata batun da cewa,
"To dai gashi naga sai shirin barin gari gobe kukeyi amma kaf cikin ku har yanzun banga wanda ya dunk'ulo yan kud'ad'en shi yace min Hajiya ga wannan gudunmawa naba,"
"Gudun mawar me kuma Hajiya? Akwai wani sha'anin da za'ayi ne bamu da labari?"
Baba Usman ya tambaya
Amsa mishi tayi da cewa,
"Sha'ani kai !
inace nan har akaci aka sid'e bikin d'anku babu wanda a cikin ku hankalin shi ya bashi cewa bari ya bani gudun mawa zan aurar da jikata ah ah ko koh dan kuma kuna aurar da d'a,
shi kenan ni kuma bazaku bani nawa gudun mawar na auren jikata ba,
In takamar ku shine kun ba uwarta gudun mawa naga dai uwarta daban ni kaka marigiya daban,
Kuna ganin dai yanda suka bugi k'irji suka gyarama yarinyar nan takwarata sashenta komai acan acan wallahi babu ne kawai basu siyo sun kawo ba,
To yanzun kuma dashi naku d'an ya kammala ginin gidan shi so kuke in saka ido su iyayen nata ne zasu k'ara zuba mata kaya a cikin wancan gidan shima?"
"Hajiya nifa na riga nayi oder d'in komai da za'asa a cikin gidan ban fad'a miki bane dama naso sai komai ya kammala sai in kaiki ki duba abubuwan da babu sai a k'arasa kafin mu tare acan..... "Cewar Ak
Katseshi Hajiya tayi da cewa,
"Kai dallah can matsa bani waje ina magana da iyayen ka kana samun baki ko kaji na kira sunan ka a zance nane?,
In kayi hakuri ai dana gama dasu kanka zan dawo ko ce maka akayi na manta da kaine?
Da kake zancen sa kaya a gida kuma Allah ya kyauta jikata ta dogara da kayan da miji ya siya salon wata rana kai ko yan uwanka kuyi mata gori ah ah wallahi,"
"Haba Hajiya waye zai mata gori kuma?"AK ya tambaya yana b'ata rai,
"To bari kaji in ma siya zakayi sai dai ka tabbatar da cewa da sunan ta ka siya,
kayan nata ne halak malak ta yanda ko yau ka fad'i ka mutu babu mai sanya su cikin sahun kayan gado atoh namiji kuma da gadara ko koh salon in yan uwanka suka san cewa kaine ka siya su dunga zuwa gidan suna mata abubuwa isa²? halin dangin miji kuma ni wanne ne za'a layance min ni Aminatu"
Umma ne ta amshi zancen da cewa,
"Hajiya ai ba laifi bane idan yace zaisa kayan daya siya a gidan tunda ai koda ace aure bai had'asu ba shid'in ai yana da halin da zai d'auke ma iyayen shi kayan d'akin k'annen shi mata kuma ita Meenal din ai bata da banbanci da kannen shi tunda dai Jidda ce ta haifeta kamar dai sauran jikokin gidan"
Katseta Hajiya tayi da cewa,
"Shi yasa ma nima yanzun a gaban ku na shaida mishi cewa zai zuba kayan ne da sharad'in cewa kayan mallakar meenal ne ba nashi ba,
Yo nawa akayi da zarar k'addarar da ba'a fata ta gifta tsakanin miji da mata sai gori ya tashi, ko kuma in mijin ya mutu yan uwa sai suzo suyi bake² suna kurin cewa ai nasu ne ya siya kayan ba daga gidan su ita matar ta kawo ba,
Kuma ni koma dai menene bazai hanani amsar kudin gudun mawa a hannun kuba garama ku had'a ku bani tun yanzun basai zuwa gaba idan wasu hidimomin sun taso ku fara min kame² ba ni ban yanke ko nawa nike buk'ata ba balle kuce na tsanan ta kar kuma mutum ya fara nufo ni da wasu yan kud'ad'en da basu fi k'arfin in dunkula inyi kyautar su tashi d'aya ba"
Yanda Hajiya ta kafe dole sai da kowa ya sauke mata nashi gudun mawar mai nauyi in ma baka da cash zatace kayi mata transfer,
Wadanda kuma sukace sai sun koma zasu tura mata tasa an rubuta mata sunan su a cikin yan bashi,
Bayan tafiyar mutanen gidan kuma tabi AK har can Kadunan inda suka tafi tareda Hassana suka duba sauran abubuwan da gidan ke buk'ata aka siyo akasa, sai dai koda AK ya tambayeta akan yaushe Meenal zata tare anan din sai cewa tayi wani tarewa kuma ai hak'uri kawai zaiyi daga nan har zuwa lokacin bikin Moon zuwa lokacin itama Meenal ta gama jigilar zuwa makarantar da takeyi in yaso sai ta dawo gaba d'aya.
Haka rayuwa yaci gaba da gudu babu k'ak'kautawa,
Raheenat ta gama wanka tuni dan haka Malam yace ta dawo gida tunda dai ai ba zaman takaba zatayi ba, dan haka ya tura aka d'aukota ita da kayanta tana kuka mutanen gidan nayi haka suka rabu tunda mai rabawa ya raba,
Bayan komawar ta Zaria
a lokacin ne shi kuma kanin mijin ta ya bijiro da batun cewa yana son Malam ya bashi auren ta saboda ta koma taci gaba da kula da d'an data Haifa dama sauran da suke wajen shi a Abuja,
Malam baik'i ba sai dai ya nemi jin ta bakin Raheenat d'in a zaton kowa sun d'auka zatayi murna da hakan kodan saboda rik'on yaranta sai dai ita kuma ta buga k'asa akan cewa bata auren shi,
Kuma yarama da ake magana ai tun kafin uban su ya mutu ya kwashe su ya basu shida matar shi tana musu fatan Allah ya tayasu rik'o,
Dan kowa yaga yaran yasan basu rasa komai a wajen suba dan dashi da matar shi sun rik'esu kamar sune asalin iyayen su ba Raheenat da marigayi ba,
sai yanzun dan k'asa ya rufe idon mijin ta shine shi k'anin shi zai lallab'o yace wani wai zai maye mata gurbin yayan shi saboda yaran ta,
To inda ace kuma itace ta mutun ba mijin bafa?dole dai ai a gefen uba yaran zasu rayu
Haka dai akayi ta cakalkala zance dan dole dai kowa ya shafama kanshi lafiya bayan abubuwan sun lafa ne kuma Ya Abakar tsohon saurayin Raheenat d'in ya yunk'uro ya fara nuna kulawan shi a kanta da d'an da take goyo duk da cewa bawai ya fito mata fili akan yana son maida Soyayyar su na baya ne sai dai duk mai hankali in ya kalli abun yasan me ake nufi,
shima dai tun bayan daya rabu da Raheenat din a wancan shekarun k'asar ya bari yaje yana cigaba da k'aratu bai dad'e sosai da dawowa ba kuma tunda ya dawo ake mishi zancen aure amma bai maida hankali ba can Abuja yake zaune a yanzun haka yana aikine da central bank,
To dai zamu iya cewa tsohuwar soyayyar da aka binne ce ake kokarin tono ta domin shi dai bayan da yaga cewa boye boye bayayi dole ya fito
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 90 Chapter of 92