kan titin dake da karancin abin hawa,
Tunda ta doso kofar gidan bakin ta ya gaza shiru har sai da ta furta abunda ke ranta "Na rantse da Allah dan dai ban iya azumin kaffara na wanda yayi kisan kaine, amma da take motar nan zanyi inje in haye kan wad'an can yan zaman kashe wandon"
"Kai Meenal yanzun tsakanin ki da Allah da babu wani hukunci akan wanda yayi kisan rai sai kije ki haye kan nasu?" Maryam dake bayan motar ta tambaya tana dariya.
"Mai zai hana harma sai na nemi shawarar wata a cikin ku"
Harara Meelat ke banka mata,
"amma wallahi baki da mutunci qawata wato ke tunda kinyi aure kin shige daga ciki ni bari ki kashe min nawa mijin tun kafin aure, "
"Eh ai dole kice haka tunda da saurayin ki ake zaman majalisar kullum, wai bazaki mishi wa'azi su dena zaman wajen ba"
Cewar Maryam
"Ina ruwan ki tunda dai ba'a kanku suke zaune ba ku shafa musu lafiya Alhamdulillah kowa ma yasan ba zaman banza sukeyi ba tunda dukan su babu wanda bashi da abunyi a cikin su"
"Dallah Maryam kyaleta ai bata son laifin su kwata²"
Cewar Meenal
"Naga alama kam.
Koda suk k'arasa kofar gidan babu b'ata lokaci aka bud'e musu gate suka shige,
gidan na nan a yanda yake sai ma abunda ya k'aru na gyare gyaren da ake mishi a koda yaushe.
"Ku shiga zan biyo ku a baya, ina son k'arema fuskar future husband d'ina kallo da kyaune, kun san kwana biyu baya gari"
Cewar Meelat
"Mayya kawai yar wahalar soyyaya"
Meenal ta fad'i hakan cike da jin haushi ta bude bayan motar ta cire ledar kayan fruits d'in data kawoma Hajiya na dubiya.
Ita dai Meelat bata kulata ba, Maryam ko jakarta kawai ta d'auka tayi gaba dan dama tun a school take ce musu tanajin fitsari,
Da sallama suka shiga falon na Hajjaju Masifaffiya, su biyu suka cimma ita da jikanta na hannun damanta zaune suna hirar yaushe gamo, domin dai shima a yanzun gaba d'aya baya samun damar zama a Zaria kamar da ,
saboda tsabar son kud'in shi yasa yau bashi nan gobe bashi can.
Sallamar nasu ne yasa shi dago kai yakai duban shi kofar shigowa domin dai wannan muryar aiko a magagin mutuwa ya jiyota yasan kunnuwan shi bazasu gaza gano mishi mai mallakin muryar ba,
ilai kuwa ita d'ince kamar yanda ya tsam mata yarinyar dake neman ta d'imauta mishi rayuwa dan gaba d'aya a watannin baya kamar wani mai shafar aljannu haka ya nemi komawa, ba damar yaga mace da jallabiya sai yarinyar nan ta fad'o mishi arai yana ta jimamin wani hali take ciki a gidan mijin nata amma ita jibita wallahi inba k'arya idanuwan shi suka mishi ba girma yaga ta k'ara babu alamun damuwa ko kad'an a tare da ita, shi yana nan kullum cikin jimami.
Da kyar ya iya kwato idanuwan shi daga kallon da yake binta dashi yana korar shed'an a zuciyar shi, dan gaba d'aya sai yake jin kamar ya dauwama yana kallon ta dan wani sanyi mai cike da nutsuwa ne yaji yana lullub'e shi.
Wata irin zazzafar ajiyar zuciya ya sauke wanda har saida sautin fitar ta yasa Hajiya maida duban ta gareshi,
"Kana lafiya? "
hajiya ta tambaya.
"Yes yes yes am fine"
ya bata amsa yana mai sosa k'eyar shi da hannun shi na hagu,
Har ya yunk'ura da niyyar barin wajen kenan Meenal ta iso kujerar da yake zaune, kan hannun kujerar ta zauna ita kuma Maryam ta shige ciki dan sosai fitsarin da takeji ya matseta,
"Mai jama'a barka da war haka yaushe a gari?ashe ka dawo? Oh kar in manta...
Barka fa da arzik'i ashe wancan cingum d'in naka Nusaiba kuma lokaci yayi, gaskiya na maka murna ita kuma Allah ya bata zaman lafiya ya kuma sanya mata dangana yasa k'arshen wahalarta akan soyayya kenan, gaskiya dai na mata murna Wallahi gashi kuma ance mijin da aka bata d'in mai kud'i ne kuma sosai yake sonta,
Ni kuma nace oh Allah rashin sani yafi dare duhu dan Wallahi na tabbata da tasan tsarin da Allah ya mata na samun wannan mijin da bata tsaya b'ata shekarun nan tana dakon jiran ka amshi soyayyar taba, ups sorry fa Brother wannan dai ta samu tasha da kyar saura d'ayar guzuman itama ina fatan Allah ya bata lafiya ta warke daga halin makuwar da take ciki"
Tunda ta fara surutan ta bakin ta kawai yake kallo a zuciyar shi ko ayyana wa yake cewa, lallai ashe dai ba gaskiya bane da ake cewa in akama mutum aure yana hankali! To gashi dai yaga girman jikin ya k'aru amma fa hankalin har yanzun da saura,
"Ke wai sai yaushe zaki san kin girma ne? An miki auren ma amma har yanzun kin kasa hankali, dama munyi dake cewa zan aure tane? Ko mun tab'a zama dake nace miki akwai wacce nike so a cikin su? Tashi a wajen nan kafin in kifar dake mara kunya kawai"
Zaro ido tayi tana mai tashi daga kan hannun kujerar.
"Allah ya baka hakuri mai yayi zafi harda zaka kifar dani, tab aini yanzun mai kai hannun shi jikina tofa sai ya tabbatar ma kanshi da cewar ya shirya kwanan guardroom"
"Oh saboda kina auren soja koh? To tsaya ki gani in yaso idan na karya kin sai yazo ya d'aureni"
Ya fad'i hakan a yayin daya mike yakai mata cafka, aiko babu shiri ta kwasa sai bayan Hajiya.
"Wai takwara kinzo dubani ne ko kinzo tsokanar fad'a?"
"To Hajiya laifine dan na taya shi murnar auren macen daya nuna baya so bayan tsayin shekarun data d'auka tana nace mishi?aini gani nayi abun a taya shi murna ne, kuma wallahi in mutum baiyi hankali ba sai alhakin mata ya kama shi"
Mtsw yaja tsaki.
"Yarinya kiji da kanki Keda akama auren dole! "
"Eh irin auren dolen da aka min nima nike Addu'ar a d'auko wata y'ar daga kauye a had'aku, sai kaji yanda abun yake"
Juyawa yayi da niyyar barin falon dan yarinyar nan fa bazai zauna ta mai dashi mahaukaci ba,
"Taubashi na nace bah!
Nace turaren nan da kakan d'an ajiye min a d'aki kwana biyu na duba ban gani ba nace ko ka manta ne? "
"Kai"
ya fad'a da d'an karfi cike da mamakin k'arfin halin ta yana juyowa,
"Oh wato ga mai kud'in banza koh? Da mijin ki da komai sai in cigaba da siya miki turare kina fesawa saboda gani dan iskan da bai san zafin dukiyar shiba"
"Kai yayan mu dan Allah miye a cikin kyautar turare dai, naga su wadancan da suke zuwa maka kullum a kallah abincin nawa kake siya musu bayan ba wani lada zaka samu ba! Niko ai koba komai bayan ladan kyauta harda ma ladan zumunta zaka samu, nidai muje Allah ko gyaran d'aki ka sani yau zanyi maka shi da kyau indai zaka bani turaren"
"Hajiya kifa jama yarinyar nan kunne yasin ko a kofar d'akina na ganta sai na zane ta tom kar kice ban mata warning ba"
Banza dashi Hajiya tayi ganin hakan shi kuma yasa kai ya fice a d'akin....
"Dan Allah Hajiya ku mishi auren dole, shima yaji inda dad'i.......
Ummiee Zaria ✍🏼
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱👨👩👧👦 *DANGINA!* 👨👩👧👦🔱⚜️
*Free book ne ga masu buk'ata daga farko zaku iya magana dani kai tsaye* 08061358462
*Rubutawa*
*Ummiee~Zaria*✍🏼
Page 36.....
"Dan Allah Hajiya kuyi mishi auren dole shima yaji inda dad'i, ai ba iya mata kad'ai ake ma auren dole ba,
inba haka ba ni karamar yarinya dani haka nan fa kuka had'a kai saboda kun gaji da ganina kuka aurar dani sai shi k'aton tuzuru amma ba wanda ya matsa mishi yace sai yayi aure,
to gashi nan dai ai yan matan nashi sun fara watsewa tunda sun gaji da gafara sa basuga k'aho ba, Allah in bai wasa ba zuwa gaba a sanda zai buk'aci auren babu macen da zata saurare shi, badai dan yaga yana da kyau kuma yana da kud'i shi yasa yake wulak'anci ba"
Kyacci tayi tana hararar hanyar da yabi ya wuce.
"Ke Meenal wai me yasa ne ke in kinzo waje gaba d'aya bakya son kiga an zauna lafiya sai kin nemi wani zancen hankalin ki ke kwanciya ne? Kin dai san halin shi karkiga wai kina da aure in kika kureshi kin san jikin kine zai fad'a miki, kuma wama ya fad'a miki cewar irin su akewa auren dole? to yasin ko rantsuwa nayi nasan kaffara bazata hau kaina ba wannan in aka mishi auren dole tun a wajen taron d'aurin auren zai ma matar saki uku kwarara kuwa! "
Cewar Hajiya.
Turo baki Meenal tayi gaba sannan ta d'aura da cewa...
"aike Hajiya dama bakya tab'a ganin laifin shi komai yayi dai² ne in dai a wajen kine kamar shi kad'aine jikan ki mu kuma yan karere,
ni bama wannan ba mi kuka dafa a gidan nan dan Wallahi yunwa nikeji da safe ban samu nayi girki ba na fito koda naje makaranta kuma kame² kawai na dunga yi banci wani abincin kwarai ba,
wai Hajiya Jummai har yanzun bata dawo daga Kauru d'in bane? Lallai a gaisheta kawai taje kauye tayi zaman ta kamar wata wacce taje Abuja"
"Ke dai wallahi kin cika shegen surutu kamar aku, tunda kika shigo kike zuba uwa wata lalatacciyar famfo, ni na rasa Ina kikayo wannan mugun gadon na surutu wallahi, tunda kika shigo kike zuba tad'i kamar ana zuge zogale"
Zaro ido Meenal tayi cike da mamaki
"Hajiya wai nice mai shegen surutun? "
ta tambaya tana dariya.
"Lallai ma toni dan nayi surutu har a tsaya neman dalili ko tambayar wajen wa nayi gado bayan gaki!
Minene ya rage naki wanda banyi gado ba?
Kinga dai naci gadon sunan ki ni kad'ai a cikin *DANGI*.
Na kuma d'auko fuskar ki da hasken fatar ki,
surutu kuma ai bama sai na baki amsa ba, ga kuma farin jini masha Allah, yauwa Hajiya nace wai dan Allah su maza basa gane banbancin budurwa da kuma macen aure ne?"
Ta tambaya tana maida hankalin ta kacho kan a wajen Hajiyar dan da gaske so take taji amsa daga bakin ta,
Fitowar Maryam tana gaishe da Hajiyan ne ya d'an tsaida ta,
sai kuma ta maida idon ta kan Maryam d'in
"Besty wai kin san ko d'azun da safe da muka rabu daku sai da mutumin nan na shekaran jiya ya k'ara tsareni bayan a gaban ku shekaran jiyan na shaida mishi cewar ni matar aure ce!
Wallahi kawai Ina tafiya sai gashi nidai karfin haline kawai yasa dana ganshi ban zura da gudu ba to nasan koma na gudun aikin banza ne dan tsalle daya ne zai kamo ni,
Sai fa da na duk'a har kasa na dunga had'ashi da Allah akan ya rufa min asiri ni matar aure ce amma d'an iskan mutumin nan wai fa cewa yayi ai dama mu mata in bama son alaqa da mutum haka muke cewa bayan yasan cewa ni ba matar aure bane kawai kora da hali nike mishi,
Kin san me yasa ban d'ud'dura ma uwatai zagi a lokacin ba? Wallahi tsoro nikeji dan kamar an hana mutane bin hanyar ba kowa dagani sai shi kin san ko yasin ko yankani zaiyi yana iya gama fed'ewa wani bai biyo ba balle ya ceceni"
Dariya kawai Maryam keyi dan sosai alamun Meenal ya nuna ta tsorata.
"Dallah ke banzane wallahi Ina miki magana serious kina neman mai dani wata tababb'iya, nifa tsoro nike kar wani abunda zai shafi karatuna ya gifta kin san in da lokacin baya ne wallahi shida kafafun shi zai gudu"
Amsa Maryam d'in ta bata da cewa..
"Ai na fad'a miki ki nemi dogayen hijabai masu rufewa har suna jan k'asa ki kuma had'a da niqab amma kinkiji ba dole su biki ba tunda yan matan ma ai suna sa irin hijjaban da kike sawa, amma dai shima d'in dan iskane tunda ai mun fad'a mishi ke matar aure ce ya kamata ya yarda, in ya k'ara tareki wallahi k'arar shi zamu kai"
Juyawa tayi wajen Hajiya bayan ta gama hararar Maryam d'in dake magana tana dariya,
dan tafa bata haushi da gaske,
"Bari in debo abinci inzo ki bani amsa kinji Hajjaju, Allah kuwa Hajiya in kikayi ciwo lafiya kike k'arawa masifar duk sai mu nemeta mu rasa itama ciwo ya korata!"
"Eh amma ai a lissafin da kika gama d'azun banji kinsa harda masifar ba, kuma Kitchen d'in nan inba wani sabon girkin zaki d'aura ba tofa ba lallai ki samu abunda kike so ba dan tuwo mukayi kin san shi yafi ta'amali da abunci mai nauyi, Jummai kuma kin san taje zaman jegon jikarta ne data haihu nasan da bazaki rasa abunda zakici a can wajen taba, Larai kuma na aiketa kasuwa"
"Tuwo kuma" ta fad'a tana b'ata fuska jin an kira makiyin ta,
" kai innalillahi wai shi mutumin nan da zarar yana gari dole ne cimar gidan nan ya canza ne? Haba dan Allah shi kenan dan shi yana son tuwo kuma sai ku wani dunga biye mishi, ni wallahi in nice matar shi dole ma ya sauke ma kanshi wannan tsurfan atoh kullum tuwo, kullum tuwo kamar a prison"
"Wannan kuma ke kika jiyo in yunwan kikeji da gaske sai ki fita ki siyo anan wajen matar can mai bleaching dan suma dai girkin nasu babu laifi, inaga hakan zaifi miki sauk'i"
Hajiya ta k'arasa fad'a tana kauda kai gefe,
Yaraf Meenal ta dawo ta zauna a kujerar data tashi,
"Wallahi yunwa nikeji!" Ta fad'i hakan tana b'ata fuska da matse cikin ta daya k'ara lafewa saboda bai samu abu mai nauyi ya d'auka ba.
"Bari in fita sai in amso mana, me kike so?" Maryam ta tambaya a yayin da ta mik'e dan zuwa Restaurant d'in dake kofar gidan kamar yanda Hajiya ta basu shawara.
"Ke ni komai ma ki amso min amma banda tuwo "
"To"
ta amsa mata dashi tasa kai da niyyar barin falon.
"Ki shiga kitchen ki d'auko kulan da zaki zubo abincin a ciki mana koh!"
Cewar Hajiya
"Ki barshi kawai Hajiya zan amso a takeaway"
Bayan fitar Maryam kacokam Hajiya ta mai da hankalin ta kan Meenal,
"Dawo nan muyi magana" ta fad'a cike da bada umarni tana mata nuni da gefen kujerar da take zaune,
Babu musu koh ta tashi ta koma wajen.
"Hajiya ya jikin naki? Koda yake naga kin warware tunda mijin ki ya dawo"
Murmushi Hajiya tayi, "jiki Alhamdulillah kam naji sauk'i sosai fa, shi kuma adawa kike da dawowan nashi ko meya faru?
dan na dad'e da sanin sosai kike kishi dashi, tsakanina da Abdul Khareem ko mai shiga tsakani sai ya shirya gara ma kiyi ta kanki,
ya kike kema da naki ciwon marar koda yake yanzun kam banji kina yawan kuka dashi ba! D alama ya dai tafi kenan?"
"Bai tafi bafa amma dai ya rage sosai ba kamar da can baya ba"
"To ya mai gidan naki dama wajen ita kishiyar naki duk dai kowa lafiya koh?"
"Shi dai nasan Lafiya lau yake dan d'azun ma dana kira shi nace mishi zanzo duba ki banji wani alamun ciwo a tare dashi ba dan shima ya shigo garin jiya da dare"
"To shi kuma haka akeyi? Kalar nashi rayuwar kenan da bazai zo ya duba kakar matar shiba? Ko baki fad'a mishi bani da lafiya ba ai yaci ace yazo ya dubani, Rabon shi da gidan nan fa tun ana saura kwana biyu auren ku!,
Shin wai ma wani irin zama kukeyi ke da shi ne takwara? ,
ya kamata ace zuwa yanzun dai kema ki fara laulayin nan da mata keyi in sun d'auki ciki,
amma shiru nikeji har yanzun ba labari ga k'annin ki ma da ake zaton cewa basu isa auren ba duk sun haihu,
Kodai akwai wani abu a k'asane wanda bamu da masaniya akan shi?"
Shiru Meenal tayi ba amsa, to jama'a fisabilillahi wani amsa zata bata, ah ah wallah ita kam ba'ajin mutuwar Sarki a bakin ta.
"Shirun nan naki shike k'ara tabbatar min da cewa har yanzun dai baki amshi auren ba kenan?"
Da sauri ta amsa Hajiya da cewa...
"Ah ah Hajiya ni wallahi ba laifina bane, kuma da ban amshi auren ba ai bazanyi ta zama har yanzun a gidan ba shekara biyu fa da watanni yanzun.... "
Katseta Hajiya tayi da cewa
"Kenan laifin shine tunda kince ba naki ba?"
Shiru tayi bata cema Hajiyar komai ba,
"Wai shin yama tab'a neman ki a shimfid'a kuwa?"
Innalillahi jama'a wannan wani irin magana ne,
Wani irin kunya ne ya sauko daga sama ya lullubeta kai Hajiya miye kuma na zakule zakule fisabilillahi.
"Ina magana dake kina wani duddukar min da kai uwa kwarton da aka ritsa a d'akin sabuwar amaryar da ango bai kwana da ita ba,
Nace kun tab'a had'a shimfid'a tun bayan auren ko a'a? In kuma so kike in fito miki a mutum ta yanda zaki gane to!
Ina magana ne akan kwanciyar aure tsakanin miji da mata nasan kin san wannan, shi mijin naki ya tab'a neman ki kun raya sunnar ma'aiki ko a'ah? Dan ya kamata in sani.
Ina tambaya ne saboda insan ta inda zan kamo bakin zaren, kinga in ma bashi da lafiya ne mu sani dan mu d'auki mataki, koda yake Ina mara lafiya zai haife yara har Biyar,
Shin ko kuma dai kece kikayi wani siddabarun dazai hanaki d'aukar cikin dan karki haihu tun yanzun?"
Ta karashe tambayar tana tsatsare Meenal d'in da idanuwan ta.
"Ni wallahi banyi komai dan kar inyi ciki ba, to bama sai an kwanta da miji bane akeyin cikin ni kuma ai har yanzun bamu tab'a kwana d'aki daya ba, haka ma fa kwanaki Uwar gida tazo tana tambayan wai in Ina shan wani abune dan Allah in dena karya bani matsala zuwa gaba, bayan ni bana shan komai, maganin ciwon marana mafa yanzun bana shan shi kuma tunda ciwon ya ragu"
"Iyee.. "
Hajiya ta furta da k'arfi cike da mamaki tana dafe k'irjinta da duka hannayen ta,
Kafin ta koma salati da sallallami tana tafa hannuwa,
"La'ilah ha illah lahu muhammadur Rasoulullahi Sallallahu Alaihi Wasallam, oh ni Ameenatu yan ninaga abunda yafi zare tsayi, Innalillahi wa'innah ilairir raju'un, "
Hannun ta ta maida kan habarta ta tallafe cike da jimami, can kuma tace,
"Anya kuwa jama'ah? Ah wallah babu lafiya a wannan harka, um umm aure shekara biyu da watan ni babu ci gaba, wani irin rashin rabone wannan a wanke maka karamar yarinya mai jini a jika a kaimaka amma ace miji ya zuba mata ido tsayin lokaci babu abunda ya shiga tsakani"
Sai kuma ta koma kan Meenal.
"Ke takwara kiji tsoron Allah ki fad'amin gaskiya, karki sa in fara tsine mishi alhalin bashi da alhaki!
Ya'ya za'a daura miki aura miki shekara biyu da yan watanni kina zaune a gidan mijin nan kuma duk bayan lokaci yana zuwa kuyi rayuwa a gida d'aya harna tsayin kwanakin dazai d'auka kafin ya koma ace babu wani abunda ya gifta a tsakanin ku. Anya kuwa fad'amin gaskiya dai hala tsoro kikeji shi yasa in ya nemeki bakya yarda? "
Ta tambaya tana tsatstsare ta da idanuwan ta,
"Wallahi Allah kuwa Hajiya ni bai tab'a nema naba balle ink'i yarda dashi, abinda ko d'akin shima baya barifa Ina shiga, kuma kullum in yazo in zan dafa abinci harda shi nikeyi kuma harma d'akin shi nike gyara mishi amma ko Ina ciki bazai shiga ba har sai na fita"
"Turk'ashi, lallai to indai haka ne akwai matsala kenan, dawa kuka tab'a yin irin hirar nan?"
"Ba kowa! Ni ban tab'a fad'ama kowa ba"
"Madallah dan ko yanzun ma shiru zakici gaba dayi da bakin ki, kin san dai kuma nace miki ki dage dayin azkar kullum safe da maraice koh?"
"Kullum ina yi ai Hajiya"
"To Allah ya k'ara tsarewa"
Rufe bakin Hajiya yayi dai² da dawowar Maryam wacce suka shigo tareda Meelat sa kuma Musty da Sadeeq na take musu baya.
Suna shigowa Hajiya ta mike zumbur,
"Yau ni naga jaraba nifa likita na cewa yayi in dunga samun isashen hutu in raba kaina da hayaniya, amma shine fisabilillahi kuka kwaso jiki wato kuga zakarun da suka biyo kaji, su suna a gaba ku kuna take musu baya, to ga falon nan dan bazan zauna ku sakamin ciwon kai ba wallahi, dan yanzun in nace ku fitar min a falo sai kuce nayi rashin kirki na koreku, to ni dai so nike in gama da kowa lafiya atoh,
Ke takwara in kingama cin abincin ki duba cikin freezer akwai kajin da mai gida ya kawo ki taimakeni ki cire biyu a ciki kimin dambun kaza kafin ki wuce"
"Babu wani dambun da zan miki tafiya zamuyi tunda kin koremu"
"Ah ah fa kiji tsoron kwanciyar ki a kabari kar kimin sharri Allah ya gani ba Koran ku nayi ba, in kuma kinfi son kullum inyi ta fama da ciwo ai sai in dawo in zauna, dama mai yayi saura ai tsufa tuni ya dad'e da buga min kofa wadanda basu kaini bama suka mutu balle kuma ni da dama kullum cikin istigfari nike Ina fatan cikawa da imani, ki dai taimaki tsufana kimin dambun nan dan jiya har mafarkin shi saida nayi,"
Mai da dubanta kan Meelat tayi,
"Sannu Jamila tare kuke ashe? Hala wannan mai d'aga karfen ne ya tsareki a waje ya hanaki shigowa ki dubani tun d'azun? To kiji dai da kyau karki wani ce aure sai kin gama makaranta in dai da gaske yakeyi gara ki bashi dama ya tura ki shige d'akin ki kema hankalin ki ya kwanta, Allah dai ya rufama Yusufu Wase asiri shi uwar shi ta nema mishi mata da yike d'an mutunci ne haka ya amsheta hannu hurhud'u su kuma suna nan har yanzun sun kasa zab'ar wacce ta dace,
To ku kuma ai mun gaisa daku d'azun koh?"
Ta tambaya tana kallon su Sadeeq.
Basu amsa mata ba sai ma wajen zama da suka nema, to Hajiya cefa waye zai fad'a musu halinta ai su sai dai suba wani labari,
Maida budanta tayi kan Maryam,
"Maryam wannan ledar da qawarki ta kawo ban dai san ko miye a ciki ba tunda bata gabatar min dashi ba ki shigar min dashi ciki"
"To Hajiya ai har dambun ma sai in miki"
Taba Hajiya amsa,
Sadeeq ne ya katseta da cewa...
"Muje kitchen din to in tayaki aikin"
Hajiya bata k'ara kulasu ba tayi hayewar ta sama abinta.
"Bestyn mu ashe ana ganin ku? Aida cewa zanyi ko Soja ya hanaki yawon ziyara ne?"
Musty ya tambaya yana kallon Meenal.
"Kai Babana taya zai hanani ziyara kawai dai kune da bakwa zama sosai yanzun shi yasa mukan dad'e bamu had'uba kuma ai Ina cema qawata ta gaishe ka"
"Gaskiya ne kam dan tasha fad'amin,"
"Ba kullum kana zuwa tad'iba amma ko sau d'aya baka tab'a neman Indan nike ba, dukan kuma"
Ta fad'i hakan tana b'ata rai alamun abunda sukayin ya k'ona mata rai,
"Tofa kai Sadeeq kaji wani batu, to ke yanzun fisabilillahi Ina kika tab'a ganin yayye sun kama zarya zuwa gidan kanwar su balle kuma ni uba guda? To amma dai tunda kinyi korafi zamu gyara insha Allah zamu zo wata rana,
Ganin Maryam ta d'auki abincin ta tayi hanyar kitchen shi kuma Sadeeq ya take mata bayane yasa ita ma ta mike ta da'auki wayarta da nata ledan takeaway d'in ta fice daga falon, tabar Meelat da Musty a falon.
Kai tsaye wajen da ta faka motar ta ta wuce ta bu'de gidan gaba ta shiga kunna motar tayi sai ta d'an kwantar da kujeran ta kunna ac da radio din motan ta rage volume, ledan abincin ta bu'de ta faraci hankali kwance, tana cikin motar a zaune taji motsin alamar ana shirin fita da motar dake gefen ta wacce ta tabbatar da motar na AK ne dan kaf gidan shike iya cire manyan kud'ade wajen siyan manyan motoci kamar wanda bai san zafin naira ba,
Ilai kuwa shi din ne a ciki kasancewar motar da take ciki gilasanta a
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 32 Chapter of 92