ko ruwa bazata maka tayin shiba balle kasa rai da abinci mtsw ina ma amfanin rowa" Antyn tace sannan tasa kai ta wuce ciki ba tareda ta karabi ta kansu ba,
"Goben da ƙarfe nawa zakuzo? " ya tambaya, "Ya'ya in zamuzo zan kiraka"ta bashi amsa "ok to saida safen ku sai naji ki" ya fada sannan yasa kai ya wuce.
Falon ya rage saura su uku, kai ku tashi mu shiga ciki waccan ƴar rainin wayan bansan uwar me take a ɗakin daya hanata fitowa ba! Jagora ta musu zuwa ɗakin Meelat ɗin koda suka isa zaune suka sameta kan kujerar mirrow da waya a hannun ta, jin motsin bude kofar ne yasa tayi hanzarin ɗago kanta daga kallon wayar da take ta maida kallon nata zuwa bakin kofar, "ke wai wani salon wulakanci ne sabo kika samu kina jin motsin mu a falo kikaƙi fitowa kuma bawai bacci kike ba! ", cewar Meenat
"Ke dallah ai nasan dole zaki shigo bagashi yanzun kin karaso ba ta faɗa tana mikewa "Moon Aisha bismillan ku ku zauna mana please ku dena biyema wannan Autar Malam ɗin bari in kawo muku ruwa" ta karasa faɗa tana shirin barin ɗakin " ke in akwai meatpie ki ɗibomin zanje gida dashi" inji Meenat,
Bazan ɗibo ɗinba ai kila ni ƴar aikin kice kin ma rainan wayau! ta karasa faɗa tana hararar Meenat ɗin,
Haba abar kauna nice fa"Meenat ta faɗa tana marai raicewa Meelat bata ƙara bi ta kanta ba tasa kai ta wuce, kan mirrow inda Mealat tabar wayarta Meenat ta karasa ɗaukar wayar tayi sannan ta nemi waje a gefen gadon ta zauna tana cire naɗin gyalen dake kanta, call log ta fara dubawa idanuwan ta suka ci karo da wata special Number wacce itace number ta karshe da aka amsa kira daga gareta akallah kuma wanda ya kiraɗin yayi Magana da Meelat din na kusan mintuna 40,fita daga wajen tayi ta koma wajen ajiye saƙo anan ma taci karo da sakonni biyu dukan su kuma daga waccan number ɗin ne sai dai duka sakon ba wacce Meelat din ta bada reply akanta,
"Bebs ku matso ku gani yasin tarkon mu ya kama Zakara dan mu dai munfi karfin muyima kurciya tarko wallahi"
Cewar Meenat tana matsawa kusa dasu Moon sosai yanda zasuga abinda take son nuna musun,
"Dan Allah dai kice munyi sara akan gaba Sister? " cewar Moon, "ah kwarai kuwa to muɗin ai ba na wasa bane, "da fari dai bayan doguwar magana a waya ta kusan awa guda ga sakon nin da suka biyo baya "
dariya tayi sannan ta kara da cewa
" bari mu karanta sakon soyayya atoh da muna ganin wasu nayi yanzun muma yazo kanmu"
"Ke dallah kiyi ki karanta kina jamin rai na matsu inji me sakon ya ƙunsa" cewar Aisha cikin zakuwa, juyowa Meenat tayi tana hararar ta "ko kimin shiru ko inƙi karantawa wallahi tam" kara gyara zama dukan su su kayi ke in kika gansu zakice ko wani abu mai matukar mahimmanci zasu karanto a cikin sakon,
Ga abinda sakon farko ya kunsa:
Assalamu Alaikum Mai Kyau, Meelat akwai Matsala fa! dan ina zaton akwai abunda na rasa a jikina bayan rabuwar mu! Ki tayani nema idan kin ganshi ki adana min shi a wajen ki domin kece mafi dacewa da ajiyar shi dama,
Ki kasance cikin farin ciki daga yanzun har zuwa karshen numfashi.
*El~Mustapha*
Kallon² suka tsaya yi a tsakanin su bayan Meenat ta gama karanto musu saƙon, Bebs kun gane me sakon ke nufi kuwa? Meenat ɗin ta tambaya, tana mai kara maimaita karanta saƙon a karo na biyu,
Aisha ce ta mike ta fara rawa su kuma suna kallon ta suna murmushi saida ta gama rawar sannan ta dawo ta zauna, a dai² lokacin ne kuma Meelat ta shigo ɗakin hannun ta ɗauke da katon farantin data gero plates ɗin abinci ruwa dasu drink kan mirrow ta karasa ta ajiye shi sannan ta dawo tsakar ɗakin tana kallon su kamar yanda suma ɗin suke cigaba da kallon ta, "Nidai karku tambayeni komai yanzun ku bari har muyi sallah tukun sai in baku labari dan nasan wallahi harda jin gulma yasa kukazo"
ta faɗa tana hararar Meenat, Ke Baby inani Aminatu ina bacci banji ya aka kwana ba bayan nasan baiwar da Allah yama kawata nidai zoki taimaka ki shafamin labarin abinda ya faru karkisa inyi sallah ba cikin nutsuwa ba kinji dai yanzun nema ake kiran Sallah ɗin"
cewar Meenat, shareta Meelat ɗin tayi ta juya inda ta aje farantin data shigo dashi ta ɗauko ruwa da drink tazo ta ajiyema Moon da Aisha a gaban su " kusha ruwa ta faɗa sannan ta juya ta shige bayi batareda ta kara bi takan Meenat ba, "kutmelesi ke ni zakima iskanci kika shige kika barni, da kyau eh ba laifi yarinya to yasin ban barin gidan nan sai kin bani labari inba haka ba yanzun nan in maida mishi amsoshin sakon nin shi kin dai san halina tsaf bakya buƙatar karin bayani,"
"kin daɗe baki tura ɗinba" cewar Meelat tana shigewa makewayin, komawa tayi ta zauna "ke Aisha baki faɗa mana abunda kika fahimta ba" cewar Moon bayan ta cire goran drink ɗin da take sha a bakin ta,
"humm wallahi Ya Musty son Jamila yakeyi ku gane mana wai cewa fa yayi ya rasa wani abu a jikin shi, kuma wai inta gani ta adana, to na rantse zuciyar shi yake nufin ya rasa ta adana wato ta haɗa zuciyar shi da nata zuciyar wai shinan mai wayau bazai fito kai tsaye yace yana son ta ba"
"ke barshi dan Allah ai tunda aka fara haka duk taurin kanshi wata rana sai ya furta muje zuwa dai,
Kai ku tsaya nifa wallahi tsoro nikeji" cewar Moon, tsoron me? Suka haɗa baki wajen tambayan ta, gyara zama tayi sannan ta ɗaura da cewa "wai ku bakwajin tsoron a gida a gane kuna kula samari?
Ke wani saurayin muka kula? Meenal ta tambaya tana tsareta da ido, "shi Ya Musty ɗin mana!" Moon ta bata amsa, ke dallah ware wani munafikin ne zaije yakai labarin cewa Ya Musty nason Meelat a cikin mu? ta faɗa tana tsatsatsare su da ido, "ah² ni wallahi bazan faɗa ba",cewar Moon "to da dai yafi miki kuma ai wannan abun dukan mu zai amfana dan wallahi kuna ganin bikin nan in bakuyi wasa ba yan aiki zaku zama, kunaji dai ɗazun ake cewa wai wajen reception ba yara wai mune yaran suke nufi fa, amma kunga in muna da Ya Musty ai ba fashi sai munje dan kunsan wallahi indai Iliya ɗan Mai karfi ne ba bari zaiyi muje ba"
Ke wai waye Iliya ɗan mai karfin?" Meelat data ɗauro alwallah ta tambaya, Ya Abdul mana ta fada tana mikewa domin zuwa ɗauro alwallah itama, "kr wai wanda hajiya tasa aka kira mata dazun? Eh to ba laifi yaci sunan"ta karasa faɗa tana dariya,
Saida suka idar da sallah dukan su sannan sukayi zaman cin abincin da Meelat ta shigo musu dashi bayan sun zama ci Meenat ce ta janye farantin gefe, "ke kawata dan Allah ki bani labari meya faru a hanya ciniki ya faɗa kuwa?"
"Ai in ban baki labari ba na tabbata har mafarki sai kinyi yau to gyara zama kisha labari, amma dai kafin nan bani tuwon madara da ilokata sai inji daɗin baki labarin"
Mika hannu tayi ta ɗauko jakarta ilokar ta ciro ta mika mata gashi ni ban son jinini,
Abinda ya faru......
Bayan su Meenat sun wuce.
Ina yini" Meelat ta gaishe shi, "lafiya lau kanwata amma dai kin san saura kada) n kisa zuciyata ta tsaya cak koh? Waigowa tayi taɗan saci kallon shi, "yes kalleni da kyau ba wasa nike miki ba Allah da kin tafi batareda kin min sallama ba ba abunda zai hana ni suma",
Kai Ya Musty suma kuma ana zaune kalau?
Waiyo Allah Momina kinji wata murya mai daɗin amoh dan Allah kara kiran suna na a bakin ki inji, ban taɓa jin daɗin sunan ba sai yau" hannu takai kan fuskarta ta rufe tana murmushi, "kai dan Allah amma dai wasa kakeyi koh", ki taimake ni ki dena rufe fuskar nan Allah dan bakiga yanda murmushin ki ya kara kawata fuskar bane Allah cutar dani zakiyi muddin kikaci gaba da rufemin ita dan ni banki in gangare gefen hanya in faka kawai dan inci gaba da kallon fuskar mai kyau ba.
"Ah ah nidai kar kayi haka kaga jirana akeyi a gida"
To yane an mata bani labari na samu shiga kuwa? dan kawance nike so mu kullah, kin san kowa yana son mu'amalah da abu mai kyau toya zaki iya kawance dani? "
Kai Ya Musty to ai ba'a kawance tsakanin Namiji da Mace, "
Ke mai kyau waya faɗa miki?
Nidai na sani ai"itama ta bashi amsa,
"To yanzun kina nufin ban samu karbuwa ba kenan? " ya fada da karyayyar murya,
Ah ah ni ai bance ba" ta bashi amsa batareda ta kalleshi ba, "to in haka ne na samu shiga kenan, to dafari dai domin abota tayi karko ina bukatar phone number ɗinki ta yanda zan samu damar kiranki aduk sanda naso jin muryar ki, bani wayar ki "
Ciro wayar tayi daga cikin jaka ta mika mishi bayan ya loda number din shi akan wayar nata sai da ya kira wayar sannan ya waigo gefen ta "da wani suna zan miki saving number ɗin? Ya tambaya,
Zanyi saving da kaina" ta bashi amsa "oh right nidai Mai Kyau zansa a nawa Kinga duk wanda ya dauki wayar yasan mai kyau ce ke kirana,
Bai barta ta sarara ba haka yasa karamar yarinya a gaba yana ta bulaleta da kalamai a tsanake a haka har suka iso kofar gidan su Meelat ɗin sannan ya sauketa, ko a kofar gidan nasu ya ɓata lokaci sosai kafin ya juya ya koma ita kuma ta shige gida,
To kunji abunda ya faru.......
"Kawata faɗamin wani abu kin kware mai ko ah ah? Meenat ta tambaya tana kallon Meelat ɗin, ke dallah can ai kema kin san ko giyar wake nasha bazanyi saurin kware mai ba, koba a bakin ku naji kuna faɗar yanda mata ke musu layi ba? Yanzun ni fisabillahi ina ni ina sa kaina a shiga uku dududu fa shekarun mu basu kai 15 ba har yanzun shi yasa na kasa bashi amsar saƙon nin shi, kin san dai gidan nan har yanzun kallon jaririya sukemin shi yasa na kosa ingama sakandire ko sa faramin kallon matashiyar budurwa, "
Yauwa yanzun dai bazaki bashi amsar saƙon shi ko ɗaya ba in yayi magana kuma kice baki fahimci abinda saƙon nashi ya kunsa ba, karki sake koda wasa yazo gidan nan da sunan zance wallahi inba so kike acicci mana uwa ba toh, kidai rike mana shi a waya kaɗai ya wadatar inya matsa yana san ganin ki sai kizo gidan mu in yazo sai ku gaisa fakat,
Aisha karanto mana ɗaya sakon muji shi kuma meya ƙunsa "ta faɗa tana mikama Aisha wayar Meelat ɗin.
Sai kuma sako na biyu shima ga abunda ya kunsa.....
****Gaskiyar yan magana da sukama wannan rana laƙabi da Jummu'at babbar rana, domin nima ayau naci alfarmarta daga cikin nasabarta nayi katarin samun abunda ya girgizamin zuciyata, wato haɗuwa dake da nayi ayau.
Ki karanta da murmushi domin hakan yana karama kyan ki kyau,
El~Mustapha
Huhuhuhu kunji wani salo dan Allah gaskiya Ya Musty na kawo wuta, dan littafi zan nema in dunga rubuta kalaman nan ina adana ma future husband, oh my future husband were are you sai nan da shekara nawa zamu haɗu ne? Kayi ta kulamin da kanka kafin haɗuwar mu,"
cewar Meenal tana murmusawa.
Haka suka shantake suka dunga tsara yanda suma zasuyi shagalin bikin Anty binta ba tareda sun takura kansu ba, a haka har lokaci ya fara ja basu ankara ba, Hajiya Kausar ne jin shiru² basu fito ba yasata lekowa taga mai sukeyi.
Meenal halan dai yau kwana zakiyi a gidan nan Malam baya gari ne hala?
Cewar Anty,
La'ilaha Illallah Muhammadur Rasoulullah (s,a,w) Meenat ta faɗa tana wantsalowa daga kan gadon da take kwance, tsakani da Allah itafa ta manta da cewa ba'a gidan su take ba hira tayi daɗi ta manta cewar Malam tabbas zai neme ta, rarumar jakarta tayi ta lalubo wayarta 2 missed call ta gani daga Malam sai 3 missed call na Ya Sa'ad 1 missed call na Momin ta, kai ku tashi mu wuce gida wallahi Malam ya kira take faɗa a firgice, murumshi Anty tayi tana rufe kofar ɗakin take faɗin ai "dama nasan kuna nan kuna shuririta kin manta zakuje gida to kuzo ku wuce dai dare yayi kema bisu ku barni in sarara, ke Meenat karki Manta da kayan nan gasu nan a falo" daga haka ta koma ɗakin ta,
Moon ne tace "Meelat ga tsarabar ki kiyi hakuri ba yawa" cike da murna ta karɓa tana godiya, muma Anty ma tace in biku muje can gidan in kwana bari in dauki kayana" karamar jaka ta dauko ta zuba duk wani abunda tasan zata bukata a ciki Aisha ce ta ɗaukar mata jakar ita kuma ta ɗauki farantin data kawo musu abinci sannan suka fita daga dakin kitchen ta wuce su kuma Meenat ta musu jagora zuwa ɗakin Anty bayan Antyn ta musu izinin shiga, "Anty zamu wuce saida safe" to ƴaƴan Albarkha sannun ku angode da zumunci Allah yayi Albarkha ke Ƴar gidan Malam baƙi kukayi ne hala? "
Antyn ta tambaya "eh yaran yayyen Momi ne da sukazo yau" ah masha Allah to sannun ku kunji nagode kwarai Allah ya kara haɗa kanku"
Ameen suka amsa mata dashi, Meelat ne ta shigo ɗakin hannun ta dauke da ledar tsarabar da suka kawo mata zazzage kayan tayi kusa da inda Antyn ke zaune cike da jindaɗi tace "Anty kinga tsarabar da suka kawo min, kuma fa yau muka san juna dasu",
Kai Masha Allah sannun ku da ɗawainiya kunji angode,
Meenat ce ta rike ƙugu tana hararar Meelat ɗin "ke wai wannan godiyar da kike tun ɗazun na miye? nifa bana son haka duk kinsa naji wani iri, to nima ku tayani godiya aina faɗa muku kayan ɗazun Anty ce ta siya mana koh? ta karasa faɗa tana kallon su Moon, su kuma kamar wasu masu jiran umarni suka haɗa baki wajen cewa "angode Anty ubangiji Allah ya kara arziki" Ameen,
Sai da Anty ta rako su har bakin gate bayan ta sa Meelat ta ɗauki kayan da zasu kaima Momi Hauwa sannan ta koma cikin gida.
Sai bayan sun fito sannan tabi bayan kiran Ya Sa'ad, "ina kika ajiye wayar ne? " ya tambaya bayan ya ɗauka, sallah nikeyi Ƴa'ya ta bashi amsa tana istigfari a cikin zuciya na ƙaryar data sharara mishi "ok to ya maganar kazar a siyo ko kin koshi?"
Kai ya'yan mu bafa ni kaɗai nasa raiba harda su Aisha ma sunsa rai ga kuma Jamilata itama yau a gidan mu zata kwana dan Allah ka siyo mana kaga sai ya tayamu hira wallahi Allah ne kaɗai yasan ladar da zaka samu in kai wannan taimakon yau kaji Angon Anty Billy" bata kara sauraran jin me zaice ba ta yanke wayar a dai² kofar wani shago dake cikin layin nasu ta hango shi zaune gefen shi dama da hagu waɗansu irin ɗika ɗikan karnuka ne sunci sun koshi gwanin firgitarwa gamai kallon su gefe guda kuma yaran shine suke dafa shayi a cikin irin kananun butocin nan na buzaye,
Meenal ga ɗan gidan kinan fa, cewar Meelat data matso kusa da ita, "yaushe ya dawo kuma ni Amina? " oho in kin matsa kusa kya tambaye shi.
Ganin suna kara matsawa inda suke yasa karnukan fara haushi, wani irin haushi suke mai bada tsoro, tsukuikuye juna sukayi tsabar tsoro, suko samarin dake gefe me zasuyi ba dariya ba,
"Shutup" ya daka ma karnukan tsawa sai gasu duk sunyi kwance sunyi shiru sun natsu, ku kuma miye na dariya anan" ya faɗa yana kallon samarin fuska ɗaure, ayi hakuri Sarki" suka haɗa baki wajen faɗa,
Daga ina kuke da daren nan? Ya tambaya babu alamun fara'a a fuskar shi, Meelat ce ta iya bashi amsa da cewa "daga gidan mu muke".
Kuma sai baku iya gaisuwa ba koh? Ya tambaya "mun iya" suka haɗa baki wajen faɗa kamar wasu gaulaye,
"oho to ina wunin ku"
Kayi hakuri Ya'ya Sufyaan ina wuni ka dawo lafiya ya aiki barka da zuwa" haka suka dunga jero gaisuwa domin duk sun riga sun gama ruɗewa, "lafiya lau" ya amsa musu dashi a takaice yana kauda kai.
"Kuzo ku wuce kai kwaro zoka rakasu, yace cikin wata irin buɗaɗɗiyar muryar shi da sam bata rikuwa duk sanda yaso ya rageta da niyyar yayi magana a tsanake baya iyawa dan muryar nashi tana da amo sosai da zarar yay magana harna nesa dashi sai yaji.
Huhuhu gafa Sarki ya bayyana🤕
ina fatan kun shirya tsaf dan yanzun zamu shiga cikin labarin kaain da naain.
#Share and Comment
#Ummiee~Zaria
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱 FAMILY HOUSE ⚜️🔱
~{{ȶֆɨռȶֆɨʏǟ ʍǟƊǟʊʀɨռӄɨ Ɗǟʏǟ}}~
*©®UZ-2023.*
*👨👩👧👦DANGINA!👨👩👧👦*
_{{ℳℽ ℱᗅℳⅈℒℽ}}_
ⱤɄ฿Ʉ₮₳₩₳.
*ZAINAB USMAN*
_{Uɱɱιҽҽ~Zαɾια}_
*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*
*₲₳฿₳₮₳Ɽ₩₳*
_Yabo da godiya da'iman wa abadan na Allah ne. Salati da sallama sune na ɗan gatan Allah fiyayyen halitta Annabi Muhammad (s.a.w),tare da iyalansa da sahabban sa baki ɗaya._
*₴₳Đ₳Ʉ₭₳Ɽ₩₳*
_Gaba ɗaya kacokan ɗin labarin nan sadaukarwa ne gareku ababen alfaharina._
*JAMILA MUSA* {{Meelat Musa}}
*HAUWA MUH'D USMAN*
{{Real Smasher}}
*H UMAR*
{{Admin Beneficial}}
&
*SAJIDA* {{🇳🇪 NIGER}}
*₮Ʉ₭Ʉł₵ł*
_Wannan shafin tukuici ne ga gidaje biyu masu albarka,BENEFICIAL WRITERS ASSO,tare da gidanmu na gado abun alfahari FAMILY HOUSE,Allah ya ƙara haɗin kai ameen._
_Bazan taɓa mantawa da ku ba aminan ƙwarai,ina kuma alfahari da kasancewa ta cikinku,ko ban kira suna ba kun san kanku,mutanen Family House. Na gode³ ƙwarai da ƙarfin gwuiwar da kuka bani,wajen rubutun littafin *DANGINA* ubangiji ya biya da aljannah._
```Page 10
#No editing
"Angama Sarki" wanda ya kira da sunan kwaro ya amsa dashi yana tasowa shima ɗin saurayine cikakke yana sanye da plain ɗin white shirt sai gajeren wandon sojoji a jikin shi, "muje ko yan mata" ya faɗa yana mai nuna musu hanya, haka sukaci gaba da tafiya har saida suka kusa isa gidan Malam sannan ya buɗe baki yace "ku dunga kiyaye fita gida da dare fa tunda sarki ya dawo kunsan zai dunga sakin karnukan shi, yauma kunyi sa'a ne da kunkai karfe 9 da kun zama nama" ya faɗa fuskar shi ba fara'a sam, waiyo Allah kinji ko Meenat wallahi dama nasha faɗa miki karnukan nan da wuya inba naman mutane ake basu suna ciba, yanzun shikenan yaufa da sun cinyemu" Meelat take faɗa a tsorace dan ita dama shegen tsoro gareta abu kankani ke firgita ta, shiko ya faɗa musu hakan ne dan su kiyaye fitan dare.
Gab da kofar gidan ya dakata "na kawo ku gida koh? " eh Malam mun gode, cewar Meenat "to ku karasa ina hangen ku daga nan"
ai gudu² sauri² suka wuce shi kuma bai wuce ba har saida yaga shigar su cikin gidan sannan ya juya.
Dukan su kamar waɗanda sukayi gudu haka suka dunga sauke ajiyar zuciya bamai iyama wani magana a cikin su har suka ƙarasa cikin farfajiyar gidan, karar da wayar Meenat dake cikin jakarta tayi ne ya sanya Meenat ɗin kallon parking lot ɗin gidan aiko sai idonta ya sauka akan motar Momi Hauwa, "waiyo Momi ta dawo tun ɗazun kenan " ta faɗa a baiyane "ku ƙarasa ciki please zanje in duba Baba Malam ko zakuje? Ta tambaya "No kije zamu shiga da safe Insha Allah ",
Ok to ga wayata Meelat in Ƴa'Sa'ad ya kira ki ɗauka kuce ma Momi na shiga wajen Baba" ta faɗa tana mikama Meelat ɗin wayar da jakarta su sukayi gaba ita kuma ta juya akalarta zuwa sashen Malam dan tasan yanzun yana gabda tashin magidan tan da suke karatun dare a wajen shi, kamar ta shige ciki wajen matan shi sai kuma dai ta wuce falon shi kai tsaye, kamar yanda ta zata ɗin haka ta tarar ba kowa a falon dan haka guri ta samu ta zauna hango kulolin abincin da aka jera mishi a gefe ya sanyata mikewa ta karasa inda suke saida ta buɗe ko wacce kula taga abinda aka shirya mishi kamar yanda ta saba duk sanda ta shigo bata tarda shi ba takan ɗibi abincin iya wanda zata iya cinyewa taci, in kuma ta sameshi to tare suke cin abincin ko kuma in bataci ba zaici yabar mata saura dan yasan dai inhar lafiya lau take ba shakka sai tazo tayashi hirar dare, da zarar bai gantaba shima hankalin shi baya kwanciya yasan ba kalau take ba, dan haka ta ɗibi abinda take muradi duk da tana da koshi ta koma kan kujerar data tashi taci gaba da cin abincin ta hankali a kwance tana yi tana kallon Agogo, zuwa can ta fara jin mitsi da gyarar muryar Malam ɗin da yake nan kamar ƙa'idah domin inhar yazo waje kafin sallama sai yayi gyaran murya, plate din abincin ta ajiye a gefe sannan ta mike tsaye domin nuna girma mawa, da sallama ɗauke a bakin shi ya shigo fuskar shi cike da annuri, karasawa inda yake tayi tana amsa sallamar da yayi,
"Uwata idon ki kenan? " ya faɗa a yayin da take amsar littafan dake ɗauke a hannun shi, juyawa tayi tana rufe fuska da littafan alamun jin kunya, "to aini har saura kaɗan in bada cigiya naji shiru² banji ɗuriyar ki ba, harna fara cewa to ko Hajiya Amina tayimin garkuwa dake ne so take in kai mata ƴan kuɗaɗe kafin ta sakomin ke? ",
Baba ai mun dawo tun ɗazun mun shiga gidan su Jameelata ne mun karɓoma Momi saƙo yanzun ma saida Ƴa sufyaan yasa wani ya rakomu kofar gida, ni ban san ya dawo ba ai da bamu daɗe a gidan ba" ta karasa faɗa tana tura baki,
"Too haka akayi? To lallai Malam Sufyan ya kyauta tunda yasa aka rakomin uwata gida Allah dai ya saka mishi da alkhairi dan nima dai hankalina bai kwanta ba dan nasan karfe 9 ake sakin karnukan gashi banga uwata ta dawo ba, to barka tunda
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 8 Chapter of 92