d'age suke kuma suna da duhu sosai hakan yasa bai lura da ita ba har ya kunna motar masu gadin gate suka bud'e mishi ya fice.
"Alhamdulillah" ta furta a bayyane, dan hakan ma wani dama ne ta yanda zataje ta d'auki turare dama sauran abubuwan da take buk'ata kafin ya dawo,
Dan fa Allah ya sani bawai bata da kud'in da zata cire ta siya turaren bane, No tana dashi amma tsakani da Allah bazata iya cire makudan kud'i ta siya turaren da kud'inta ba duk da dai ba aikin wahala tayi ta samu kud'in ba hasali ma cuwa² irin na student kullum takeyi tana tara kud'ad'enta dan insha Allah in har zata siya handout ko wani abun da zata siya ko take buk'ata na fannin karatun ta tofa babu d'aga double take amsa a hannun iyayen ta, zata amsa a hannun Malam ta kuma amsa a hannun Baba Auta, Baba Adamu kai harda ma iyayen ta mata takan amsa a hannun su hakan kuma bazai sa tak'i amsa a hannun Sarki da wajen sauran yayyen ta ba dan haka maganar gaskiya bata talauci, amma tattala abinta takeyi dan so take ta kud'ance kafin ta gama makaranta ta samu aiki ta riga ta tara kud'in siyan ma Malam fili dan data fara aiki kud'in ginin zatayi tanadi, ita wallahi bata san haka ake samun kud'i da cuwa² in kana karatu ba sai da ta fara, to gadai kud'in a asusun banki amma fa ranar da sukaje kasuwa ta gwada tambayan kud'in turaren nan da sunan ta siya ma kanta wallahi da mai turaren ya kira kud'in juwa taji kamar yana neman ya d'auketa ya nana da k'asa, ashe tsadadden turarene take ma feshin ala tsine bisa rashin sani, to daga karshe dai dole turarukan cikin akwatin auren ta ta d'auko taci gaba da amfani dasu amma Sam ko kusa ko alama basu kama kafar waccen d'in ba, dan haka ta kuduri aniyar zata kwantar da kai indai AK zai cigaba da bata turaren dan lokacin data fad'ama Sarki sunan turaren wani daban mai sunan shi ya siyo mata amma kamshin su ba iri guda bane.
Barin duk abinda takeyi a cikin motar tayi ta fito, sai da ta wanke hannun ta sannan ta waige ta tabbata babu wanda ke ankare da ita sannan ta k'arasa bakin kofar inda suke ajiye key d'in ta duba, amma ga mamakin ta babu makullin a wajen, har ta fara tunanin juyawa dan jikin ta yayi sanyi da alama dai yau ba sa'a sai kuma ta karasa ta tab'a kofar wai ko Allah zai sa ya manta bai kulle ba,
Aiko tana murd'awa ta tura sai kofar ta bude,
Taji dadi matuk'a dan harda tsallen murna tayi tana jin jinama kanta,
Babu b'ata lokaci ta shige ciki sannan ta mai da kofar ta shige,
Bata tsaya wani kalle kalle a falon ba gudun b'ata lokaci kawai ta amfa cikin bedroom din dan gara ta d'auki abunda zata d'auka ta fice kafin wani cikin su Musty ya shigo ya ganta a d'akin tunda dai shi ya fice,
Kan mirror ta wuce kai tsaye kamar yanda tayi tsammani ga koh turaren nan har kwalba uku a ajiye,
D'aukar d'aya daga ciki tayi ta cire shi a kwalin shi ta mishi feshin huce haushi na kewar shi da tayi tsayin watanni tana sauke ajiyar zuciya cike da shauki,
"Kai gaskiya dai mutumin nan duk yanda akayi d'an Aljannah ne Allah kuwa, Allah dai ya k'ara arziki bari gobe tuwo zan kokarta in tuk'o in kawo mishi tukuicin turaren nan,"
Guda biyu ta d'auka tabar mishi guda d'aya can kuma kamar wacce akayi ma tuni sai ta shige cikin bathroom din shi, yau ma showel gel din ta d'auko harda wasu mayukan wanke kai dama duk wani abunda taga ya mata ta fito niki² kamar wacce tazo shopping, sai da ta zube kayan akan gadon shi da yau Allah yasa gadon a kimtse yake yaji gyara harya gaji ga d'akin sai kamshi yake zubawa, dibi dibi ta farayi tana neman leda sai dai kuma bata samu ledar ba duk binciken ta a d'akin, daga karshe dai ta yanke hukuncin cire gyalen data rufe jikinta dashi kasancewar yana da girma sai tayi rolling dashi ya rufe jikin nata da kyau, dan tana ganin hakan zaifi sauki in ya so in ta isa mota tasan bazata rasa ledar zubasu ba, ko bata samu bama ba laifi dan yanzun in tace ta barsu taje mota dubo leda tofa yana iya dawowa ya isketa. Dan haka zuciyar ta d'aya tunda dai tasan cewa daga ita sai itane a d'akin hankali kwance ta balle fin d'in data mak'ale gyalen dashi ta warware gyalen ta shimfide shi akan gadon ta fara zuba kayan akai tana gama wa ta daure shi da kyau gudun kar wani abu daga ciki ya fad'i.
"Masha Allah" ta furta a yayin data gama kullewa ta juya da niyar d'auko hulan kanta daya fad'i a gefe a yayin da take warware gyalen, sai dai mai tana dagowa daga duken da tayi kamar almara kamar a mafarki idanuwan ta suka fad'a cikin na mutumin da bata san da wani suna zata kira shiba,
Aljani zatace ko kuma fatalwa, domin dai ai mai d'akin ta tabbata ya fita a gidan da mota, kuma sanda ta shigo ta tabbatar cewa babu kowa a cikin d'akin dan haka bata tsaya wata ² ba ta fasa ihu had'ada tsalle tsalle tana kiran aljanni,
"Waiyo Allah na shiga ukuna, dan Allah dan annabi aljani kayi hak'uri, Wallahi niba barauniya bace ba sata nazo yiba, wallahi niba barauniya bace, dan Allah kayi hak'uri, waiyo Allah Hajiya, Jamila Maryam Sadeeq Musty, dan Allah kuzo d'akin Mai Jama'a ku kawo min d'auki nayi gamo da mutanen boye,
K'alu innalillahi wa innah ilaihir raju'un, Allahu la'ilah ilah huwa innahu min sulaimana wa innahu........ A uuzubillahi mina shaidanir rajeem."
Sosai fa ta firgita dan Allah ya sani gaba daya ta riga ta sadakar cewa aljannun d'akin ne suka gaji da zuwa d'akin da takeyi tana sama da fad'i da kayan mai d'akin shine yasa suke shirin hukun tata,
Tafa tsorata matuk'a dan sosai take karkarwa addu'a kam yau babu kalar wacce batayi ba, tayi rantsuwar cewa ita ba barauniya bace yafi cikin tirela marasa adadi, alqawari koh tayi ta k'ara cewa daga yau ko hanyar d'akin bazata k'ara kallo ba balle tazo da sunan d'aukar turare.
Har kasa takai idanuwan ta a runtse tana fad'in dan Allah dan annabi aljani yayi hak'uri ya barta ta tafi, wallahi tayi alkawarin ta bari daga yau bata karawa,
🤣🤣🤣🤣😂
Abinda bata sani ba shine babu wani aljani mai d'akin da take zaton ya fice a gidan ne ya dawo domin dama fitar ba mai nisa bane ya fita da motar ne yaba wani yaron shi ita dan ya wanke mishi dan kwana kin nan da baya nan motar tayi kura, jiya kuma daya kira mechanic din shi yazo ya duba motocin gidan ya manta yace su wanke motocin gashi kuma yana da wajen zuwa anjima.
Koda ya dawo gidan baiyi tunanin k'ara komawa wajen Hajiya ba, dan bai san dalilin da yasa a yan kwanakin nan ko tunowa yayi da yarinyar nan sautin zuciyar shi ke sauya bugu ba,
Dalilin hakan ne ya yanke hukuncin ya shigo ciki ko wani abun yayi wanda zai dauke mishi hankali, koda ya shigo Sam bai lura da takalman taba, har ya shigo cikin d'akin ya nemi kujera ya zauna yana yan k'ana nan tunane tunanen da bazai iya cewa ga katamai man abinda yake tunanin ba,
Tabbas yaji kamshin turare a d'akin ya k'aru ba kamar yanda ya fita yabar d'akin ba, amma ko kusa bauyi zaton wani ne ya shigo d'akin ba duba da cewa dama duk inda aka ajiye turare kamshi baya barin wajen ne yasa ya kauda tunanin daga karshe ma sai ya d'auki wayar shi ya shiga latse latse,
Babu jimawa ya fara jin motsi, sanin shi kad'ai ne a cikin d'akin yasa ya so ya share sai dai kuma yawan motsin daya k'ara karfine yasa shi dago kai ya maida duban shi inda motsin yake fitowa,
Da fari shima ya d'auka dai ko gizo ne yarinyar nan ta fara mishi, to inba ciwon hauka keson kama shiba taya zai dunga ganin ta a wurare daban daban, lallai in ya riketa zai buga mata warning in ma wani abun ta mishi gara ta karya dan shi ba wasa yakeyi da yara ba,
Sai dai kuma abun mamaki koda ya kulle ido ya bud'e ita din dai yaci gaba da gani ta jido abubuwa daga cikin bayin ta fito kamar wacce ta dawo daga shopping, sai dai da alama itama bata san da wanzuwar shi a d'akin ba hakan nema yasa yaci gaba da zuba mata ido dan yaga iya inda ruwan nata zai tsaya da gudu,
Kallon ta yake harzuwa sanda ta warware lullubin data rufe asirin jikin ta dashi wanda a wannan lokacin shima ji yayi kamar asirin dake cikin zuciyar shi take warware wa, yayi kokarin ganin ya raba kanshi da kallon abunda yasa ya haramta gareshi amma Ina bai samu wannan kwarin gwuiwar ba dan haka yaci gaba da k'are mata kallo har zuwa sanda ta duk'a da niyyar d'auko hulanta dake kasa, kasancewar a wannan lokacin ta fuskanci ainihin inda yike ga kuma dukawar da tayi hakan yaba wuyan rigar jikin ta damar zazzagowa hakan yasa daga inda yake zaune tsaf yake Ina hango lafiyayyun na shanun ta da suke nan kamar an d'auko an dasa mata su, I zuwa wannan lokacin kam ko kifta idanuwan shi daga kanta baya iyawa, hakan nema ya zama sanadin da tana d'agowa suka h'ada ido da ita,
Duk wannan iface iface da sambatun da takeyi tsaf yake jinta, ga abun dariya amma halin da yake ciki yasa bazai iyayi ba dan wani irin kullewa cikin shi yayi irin kullewar da bazai iya yaushe yayi irin shi ba yana daga zaunen nan tsabar azaba bai san sanda ya nemi kifewa yana dafe cikin nashi ba, ga azabar da yakeji da kuma ihun yarinyar nan data bud'e murya tana mishi hauka, ganin Infa baya taka mata burki bane tana iya fashe mishi dodon kunne hakan yasa shi cike da dauriyar daya aro ma kanshi ya d'ago kanshi yana korar shaidan a cikin zuciyar shi.
Wata irin tsawa ya daka mata wacce tasa ta komawa ta kankame jikin ta waje guda,
"Ki rufemin baki a wajen nan, ki kuma zo ki fita min a d'aki kafin in k'araso wajen nan wallahi zane ki zanyi ciki da wajen ki,
Kai wai ubanwa ma ya baki izinin shigowa d'akin nan ne iye?"
Ya tambaya cike da hargagi,
"Ba dake nike magana ba, uban waye yace ki shigomin d'akin iye, wato ashe rashin hankalin ki da nike gani ya wuce tunani na, zaki kama hanya ki shigo d'akin namiji kamar wani d'akin mijin ki dan iskanci har kin samu zarrar cike lullubi ba tareda tunanin cewa wani na iya shigowa ya sameki babu lullubin ba"
Ita dai Allah ya sani ta samu sa'idah ne kawai a sanda ta tabbatar da cewar ashe dai mai d'akin ne ba aljanin da tayi tsammani ba,
Jin yana ta b'abatu bata da niyyar tashi yasa shi Kara daka mata tsawa.
"Wallahi ³ idan na mike sai kinji ba dadi tashi ki fitar min a d'aki mara wayau kawai, kuma Allah yasa in kara ganin kin fito gidan ki bada dogon hijabi da kyakyawan shiga ba, tunda shi mijin naki ya zama sakaran namiji shi yasa ya sanya miki ido kina shigar da kikaga dama kina fita, shima sakarai dabai kishin iyalin shi, to ni nan zan gyara mishi zama wallahi"
Sif Sif Sif ta mike jiki ba kwari, dan tasan yanda ya rufe ido yana bala'in nan ba sauraren hakurin da zata bashi zaiyi ba,
Harta kai bakin kofa tana shirin ficewa ya kara daka mata tsawa da cewa.
"Shi wancan kullin kayan naki wani shegen ne kika barma zaki zo ki d'auka ki fitar min dashi daga d'aki ko sai nazo na had'a kanki da bango? "
Baya baya ta dawo jiki duk ba lakka, tasan cewa AK jarababbene amma batayi zaton ya iya masifa haka ba,
Haka dai ta dauki kayan harta kai tsakiyar falon taji ya kira sunan ta,
Wanda hakan yasa dole ta tsaya cak ba tareda ta iya amsawa ba,
"Wallahi in na k'ara ganin kafar ki a gidan nan nan kusa sai na zane ki, kuma zansa a samin ido akan ki ki tabbatar bakya zuwa ko Ina daga Makaranta sai gida, inba haka ba ni zan biyoki har gidan naki in gyara miki zama tunda shi mijin naki naga alamar dan kwali ya kamata ya koma d'aurawa ba hula ba"
Sif Sif ta fice daga falon,
Duk magan ganun daya gaya mata bataji zafin suba sai da ta fito, aiko a bakin kofar ta tsaya ta bare baki tana kuka, yana daga ciki kuma yana jinta dan shima fa kanshi da ace yana da hali ihun zaiyi ta kwararawa wallahi,
Muguwar yarinya kawai, inda yasan tana d'akin ai koda wasa bazai shigo ba, ita bata san yana kauce mata bane saboda gudun take iyakoki...........
*Babu editing atoh* inda kukaga kuskure ku wuce shi kawai kuje gaba
*Ummiee Zaria*✍🏼✍🏼✍🏼
[8/7, 11:53 PM] Zainabusmanummiee584: ⚜️🔱👨👩👧👦 *DANGINA!*👨👩👧👦🔱⚜️
*Free book ga masu buk'ata daga farko zaku iya magana dani kai tsaye* 08061358462
*Rubutawa*
*Ummiee Zaria*✍🏼
'''''Page 37.
Alhamdulillah rayuwa fa yana ta tafiya, karatun su Meenal yayi nisa sosai domin yanzun haka dai shekara 1 kachal yayi saura su kammala wanda hakan ne zai basu daman amsa sunan likitoci kai tsaye ba tareda shamaki ba,
a kuma wannan lokacin ne aka tsaida ranar auren Meelat da Musty duk da dai ita Meelat taso yayi hak'uri har sanda zata kammala karatun ta amma ya nuna mata gara ayi a wuce wajen kawai,
Maryam dai kam duk yanda Sadeeq ya so akan ta yarda shima ayi nasu bikin kafin ta kammala, k'iyawa tayi a cewarta bazata iya had'a hidimar karatun ta dana aure ba, dan haka badan yaso ba haka nan dai ya hak'ura dan yasha fama sosai kafin ta amshi tayin soyayyar shi,
A gefen uban gayyar shiko dai D'an mai karfi har yanzun dai babu wata tsayayya, domin ta gefen shi tsakanin shi da mata babu wani abunda ya canza, dan harta da su Meelat da suke matsayin yan matan manyan abokan shi ba wani sake musu fuska yake yiba,
Kwata kwatama yanzun halayyar shi k'ara juyewa yayi ya zamana ko yana gari ma ba kasafai zaka ganshi a majalisar shi ba, matan da ke zuwa wajen kuma domin shi tuni ya warware musu zaren rashin mutuncin shi tass ya musu hauka akan duk ma yarinyar data k'ara kallon su da suffa ta burgewa harta rayama zuciyarta cewa tana son shi to wallahi ta kuka da kanta,
Hafsa ko bata shafama kanta lafiya ba har sai sai wata rana data cika mishi ciki, a lokacin yayi tafiya kusan na wata uku baya gari sabon shine muddin yayi tafiya zuwa wata k'asar ko ka kirashi a waya ba lallai ya d'auka ba zaifi sauki ma in ace sako ka ajiye mishi ba kirar waya ba, to a wannan tafiyar nashi haka yarinyar nan ta taso mishi rayuwa a gaba domin a kallah kullum sai ta mishi kira sama da hamsin amma tsabar wulakanci mutumin nan ko sau d'aya bai amsa kiran ba, kuma bai kirata yaji dalilin kiran ba.
Ganin bazai dauki kiran bane yasa taje gidan Hajiya ta tasa ta a gaba da kuka aka cewa ta rufa mata asiri tasa baki AK ya fito suyi aure domin a lokacin itama a gefen ta sosai abubuwa suka kwab'e mata,
Domin dai d'aya daga cikin tsoffin samarin da suka dad'e suna mata hidimane, wanda shi dai yaji ya gani yana sonta kuma auren ta yake son yi, dan dai itama d'in bata rasa komai ba tana da kyanta ga kuma diri irin na manyan mata data mallaka, toshi dai ganin shekara da shekaru yana mata hidima amma kullum yayi mata maganar aure sai ta zame bayan tun tana karatu yake naci a kanta harta gama tuni tana aikin ta kuma yayi bincike ya gano cewar shegen yaron da tanace ma so akan shi kwata kwata babu mata a gaban shi balle kuma ita da kusan tare suka taso,
A yanda yake son ta inda ace shi wanda take so d'in yana sonta tofa babu shakka zai hak'urane ya barta ta aure shi, amma binciken da yayi akan yaron ya tabbatar yaron bazai aure taba, tunda ko shi ba auren ta zaiyi ba ai gara shi yayi duk yanda zaiyi ya aureta yakai d'aki ya adana dan sonta yake da gasken gaske.
Bai tsaya jiran jin ta bakinta ba koh ya tura iyayen shi wajen nata iyayen kafin ta an kara har sun kalmashe bakin zaren,
Tayi hauka sosai cewar tana da wanda take so, jin wannan kalmar a bakin ta ba bak'on abu bane domin dai kaf ahalin ta sun san yanda take hauka akan AK dan inhar kana son kayi shiri da Hafsat tofa sai ka nuna kana son AK anan ne zakaci moriyarta,
Dama suka bata akan cewar tunda bata son Anas d'in da ya fito neman auren ta tofa sun bata wata uku ta fad'a ma AK d'in ya fito, in kuma hakan bai faruba tofa ta sani su kuma nan da wata Biyar suka yanke ranar bikin ta,
Su kuma sunyi hakan ne dan su bata dama kartaga kamar sunyi son kai sun aurar da ita ga wanda bashi take so ba, domin dai sun san tunda wad'ancan shekarun suka shud'e AK bai so tan dahar zai nemi auren ta ba, tofa wata uku bazai canza komai ba,
Dalilin hakan duk tabi ta tashi hankalin ta ta tayar ma wadanda ke tareda ita da nasu hankalin,
Domin dai tayi iya bakin kokarinta akan yanda zatayi magana dashi ta fad'a mishi halin da take ciki amma hakan ya gagara kira kan kira har bata san sau adadin kiran data mishi ba amma yaki amsa wayar ta,
Tabi dukkanin abokan shi dan su h'adasu amma shi kuma mugun dukan su ya musu warning akan koda wasa karsu yarda su kira shi a sanda suke tare da ita,
Tofa ganin bata dace a ta fannin su bane hakan yasa ta yanke hukuncin tunkarar Hajiya tasan AK yana ganin girman ta sosai kila in hajiya tasa baki zai yarda ya aureta,
Ita ta yarda zata zauna dashi duk da baya son ta tasan soyayyar da take mishi zai wadace su.
Taje gaban Hajiya tayi kuka tayi roko wanda har saida Hajiya ta tausaya mata, ta kuma bata shawara akan taje tayi ta addu'a in auren ta da AK alkhairi ne allah ya tabbatar,
Taji sanyi sosai a yanda hajiya ta zaunar da ita ta mata nasiha ta kuma ce mata zatayi magana da AK din,
Bata bar gidan ba sai da taba masu gadin gidan sallahun cewa in ya dawo su kirata, ta basu number d'inta sannan ta musu alkhairi kamar yanda ta saba duk zuwan da zatayi gida.
Sai dai kuma dawowan na AK bai zamo mata alkhairi ba domin a sanda labarin dawowar nashi ya riske ta batayi k'asa a gwuiwa ba ta d'auko mota ta taho,
Koda ta iso ta iske shi a cikin jama'ar shi na majalisa suna ta hirar su ta yau da kullum,
Zumud'i da murnar dawowar shi yasa kashi hamsin cikin d'ari na tashin hankalin da take ciki ya kwaranye, domin AK fa namijin gaskene burin ko wacce mace,
Tunda ta shigo unguwar ya na hango motar ta ya b'ata fuska, kafin ta k'araso wajen kuwa bayan tayi parking a gefe ya tashi tsam a majalisar ya wuce cikin fadar shi, taji dad'in hakan sosai domin koba komai zata so dama su tattauna abunda ya kawota wajen shin a sirrance, bata bi ta kan yan wajen ba ta take mishi baya.
"Kiran me kikayi ta min ne da kullum sai kin kirani sama da sau ashirin bayan kin san na tsani yawan kira? "
Ya tambaya ba tareda ya nemi guri ya zauna ba,
"Ka zauna please Abdul!"
Ta fad'a cike da marairaice wa a tsammanin ta ko hakan zaisa ya taimaka ya saurare ta.
Kujerar shi yaje ya zauna kamar yanda ta buk'ata,
"Ina jinki! Meke faruwa? "
Bata iya zama akan kujera kamar yanda ya zauna ba sai ma k'arasawa kusa dashi da tayi ta zauna a kasa tana fuskantar shi wato dai zama irin na d'alibi a gaban Malami,
Kaf halin da take ciki na auren ta da ake shiryawa da damar da iyayen ta suka bata akan shi ta zayyano mishi,
Daga karshe ta k'are da rokon cewa ya rufa mata asiri ya aureta ita wallahi ko baya sonta yaji ta gani zata iya zama dashi a hakan yardar shi kawai take nema,
"AK ka dubi girman Allah da kaunar da nike maka ka taimaka ka aure ni, wallahi Ina son ka son da na tabbatar ma kaina cewar idan na rasaka tabbas zan iya rasa lafiya ta"
Duk kalaman bakin ta saida tayi kokarin amfani dasu dan ganin ta shawo kan AK amma a banza, daga karshe dai tun sunayin zancen a sirri sai da abu ya fito fili domin kuka sosai tasa mishi tana rokon shi Allah annabi ya ji tausayin ta ya aureta amma gayen nan saboda bak'ar zuciya ko a jikin shi, yadai fad'a mata cewar aishi dama tuntuni yace mata taba samarin ta dama tayi auren ta itace tak'i domin shi dai dama bai tab'a kallon ta ta fuskar soba balle akai batun aure,
A takaice dai abubuwa gaba d'aya basuyi dad'i ba dan fitowa tayi ta dunga rokon jama'ar dake majalisan akan susa baki ya yarda ya aureta, shi kuma hakan ne ya tunzura shi harda cire belt yana neman zane mata jiki, dakyar da ban baki aka cusata a mota wani daga cikin su yaja motar suka bar unguwar da ita, tun daga ranar kuma yasa kafar cin uban duk yan matan dake zuwa majalisar indai yana nan, hakan ne kuma yasa ya kara maida kanshi busy sosai domin duk ragamar kasuwancin su a hannun shi yake hakan kuma bai hana shi karatun da yakeyi wanda kullum Hajiya take mita akai ba, a cewarta kwalayen da yake tarawa indai ba tikitin ketare sirad'i bane tofa ya rufama kanshi asiri ya bar karatun nan haka dan in karatu fa yayi yawa yana tab'a kwalwar mutu, shidai ko tana surutun ta baya kulata dan yanzun ya maida azumi kamar sallar farillah, hajiya tasha tsare shi da tambayar cewa ko kisan kai yayi ne bata da labari akan yawan azumin da yakeyi, wanda shi kuma yana azumin ne saboda ya rage ma kanshi bala'in da yake jin yana kara kusanto shi a kullum, daga karshe dai har sai da aka kai matakin da ko Zaria bai son zuwa dan daya rufe idanuwa wasu hotuna ke haska kansu a cikin idon nashi, memory d'in da kullum yake fatan Allah ya goge mishi su a cikin zuciyar shi dan zaman su a rayuwar shi gani yake bala'ine kawai dan ko kusa bazai kusan ta hakan da alkhairi ba.
****
Kasancewar aski in yazo gaban goshi dama akace yafi zafi hakan yasa kwata² yanzun Meenal bata da lokacin kanta balle na zaman gida dan hatta da baccin ta a yanzun ya zama ragagge ko islamiya ma tuni ta sallama shi duk da yanda take son karatun nata kuwa, sai dai takanyi kokari once in a while taje wajen Malam suna hira suna d'an duba wasu littafan dan wani zubin hatta da weakened bata samun lokacin kanta sai na karatun data sa gaba kawai domin kowa dai yasan yanayin karatun likita ba karatu ne da zakace zakayi mishi sakwa² ba,
Tuni kuma batun rashin haihuwarta yayi tambari a dangi tun wasu nayi a bayan fage har aka kai matakin da
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 33 Chapter of 92