sani ba amma dai yanzun naga babu amfanin boyewa"
"Waye ya siyamin gidan to?"
Ta kara tambaya, ita kuma Hajiya ta amsa mata da cewa Sarki ne ya siya gidan kuma yace kar a fad'a miki amma ni nasan zaki rik'e wannan sirrin dan ko Moon bana so taji labari haka ma sauran mutanen gidan ku idan iyayen ki sun tambaya ki fad'a musu cewa kudin kayan ki dana siyar ne muka hada aka siya gidan dashi "
Duk da bayanin da Hajiyar tayi mata amma haka taso ta botse kan cewa ita ai tana da kudin ta kuma dasu zata siyama Malam din gidan, sai da suka hau sama suka sauko kafin Hajiya tace,
"Ki shirya Sa'eed zaizo ya maidake gida"
"Gida kuma Hajiya saboda me?"
"Saboda kin zama matar aure in kuma zakiyi zaman kine kawai basai munyi wahalar zuwa d'auko ki mu dawo dake nan din ba ai shike nan"
"Waima matar aure"ta fad'a tana tab'e baki dan bata d'auki maganar da mahimmanci ba,
Ficewa Hajiya tayi kuma itace da kanta taja kunnen Sultana akan koda wasa karta ta yarda zancen auren a gaban Meenal kuma koda Sa'eed din ya iso Hajiya da kanta tama Meenal din jagora suka fita ta kofar kitchen har suka bar gidan babu wanda ya lura da Meenal din,
*muje a gurguje*
Washe gari komai da Malam ya buk'ata tun daga kan lefe zuwa duk wani abun buk'ata haka su Hajiya suka shiryo suka kawo gidan Malam kaya bani da kaya ba abin ma dai kamar da gayya sukayi shi dan su nuna ma Malam cewa basu gaji tsiya ba na bakin hajiya,
Suma kuma gidan Malam din a ranar sukaje suka shirya ma Meenal sashen da aka ware mata a gidan Hajiyan matsayin inda zata zauna harka dai na arzik'i rab'a rab'a haka yake gudana tsakanin gidajen dan kowa baya son aga gazawar shi,
A ranar da Meenal ta koma gida ba k'aramin bori tayi ba,
Kenan dai ya tabbata ita kenan bata da gatan da za'aji ta bakinta aduk sanda zancen aurenta ya tashi, dan Allah yanzun hakan da suka aikata mata shi basai yayi zaton ko dama can an gaji da ita bane shi yasa kawai daga zuwa tambaya za'a wani ce an d'aura mata aure,
Haka dai tayi borin ta gaji babu wanda yabi ta kanta sai Fauxieyerh ce ta koma ban baki dan ita Sultana cewa tayi wai karyar iskanci Meenal din keyi,
Baki fa duk sun hallara yan nesa dana kusa sai harkar arziki kawai akeyi kai in kaga nima bazakace wai bikin da yazo babu shiri akeyi badan kowa ya saki jiki ana harkoki amma banda Meenal wacce ta d'auke ma kowa wuta ciki harda kawayen ta, suko basu wani damu ba dan sun san fushin ta bazai sauya komai ba,
*Ranar juma'a*
murmushin gefen baki yayi yana mai cigaba da kirar wayar sai dai har yanzun daga can gefen ita da yake aikama kiran bata dauki wayar ba,
Da alamun damuwa akan fuskar shi ya bude kofar motar da yake ciki ya zuro kafar shi daya waje daya tana ciki,
fita yayi daga gefen kira zuwa gefen tura sakonni yaci gaba da rubutu......
Abokan shi dake daura da motar da yake ciki a zaune ne suka karaso dukan su cikin shiga na Alfarma sunsha wanka har ba'a tantance kalolin turarukansu,daya daga cikin sune ya bude murfin motan ta gefen mai zaman banza sai dai duk da yaji sanda suka karaso da kuma surutun da suke mishi akai hakan baisa ya dago kai ya kalle suba har saida ya kammala rubuta sakon ya kuma turashi zuwa inda yake so in bata dauki kiraba ai dole zataga sako,
Fuskarshi cike da murmushin da yaki rabuwa da fuskar tashi tun daga ranar laraba zuwa yau daya kasance juma'a duk da cewa dama yakan dan saki fuskar ta shi sai dai sam baza'a sashi cikin mutane masu yawan fara'a ba,
amma yau kam kowa ya shaida yawan fara'ar tashi tana da nasaba da samun cikar burin zuciyar shi da yayi a wacce yake da tabbacin tarewar ta a d'akin shi yau dan hakan ne zai kara tabbatar da kasancewar su ma'aurata.
"Abakar ya akayi kun sallame sune?"ya tambayi wani abokin shi bayan ya gama shan kamshi,
"Eh kusan hakan Dan su abba sun wuce tun dazun nasa su hafees suyima sauran jagora gamai bukatar zuwa"
"ok" kawai ya iya fada yana mai kara duban wayan shi a zaton shi ko zai samu amsar sakon daya tura mata sai dai har yanzun dai ba wani sako daga wannan lambar,
"Da kyau Dr"
ya fada a bayyane yana mai fita daga cikin motan mika mishi hannu sauran abokan sukayi suna masu tayashi murna dafatan dorewar zaman lafiya da fatan samun zuria masu albarkha! shi kuma yana amsa musu da "ameen nagode" Abakar ne ya matso gefen shi hannu ya mika mishi
"congratulations once again my brother". . Thanks abuu nagode sannu da kokari allah yabar zumunci, ya fada yana mai runguman abakar din ta gefe.
(jar uba) aka fada daga gefe "
lallai kullu yaci amanar koko, wai gayun nan tun ban mutuba zasu fara wareni" karasowa yayi ya hada su duka biyun ya rungume haka suma sauran abokan su Yusuf Musty Sadeeq Faisal kamar da sauran su suka karaso suma suka rungume su abun dai gwanin burgewa.
"Kai! Kai!! Kai!!! Kai Dan allah ku cikani duk kun wani dakune ni kamar sabon jariri a hannun juya kar ku taramin gajiya tun daren baiyi ba ku cikani dallah"
Fashewa abokan sukayi da dariya baki daya,
" Ah to eh mana gaskiya kunsha dani nida ya dace in rungumi yar amaryata kawai wasu gaddawa daku kunzo kuna dakunata,gaskiya duk wanda ya k'ara rungume ni sai nayi mishi Allah ya isa"
sadeeq ne yakai mashi duka shi kuma saiya goce
"Eh lallai Mai Jama'a amma ba komai ai munyi mai wuyar tunda munyi tsayin daka har an daura amma zakaci ubanka wallahi ai daurawa akayi bata tareba. idan banje na zugata ba kacanza min suna, kai imba banda Allah yana sonka ba taya har zaka rigani yin aure nema?"
ya karashe fada yana rike haba irin abun ya kai mishi ko ina din nan,ba tareda yadamu da abun da sadeeq din yace ba ya kalli Abuu yana me cewa,.
"Wai kunsan yarinyar nan tunda gari ya waye nike kiran ta taki daukar min waya?kuma fa tun ranar laraba da tayi min rashin kunya bamu k'ara had'uwa ba ta gudu gidan su" ya karashe maganar yana mai girgiza kanshi dan abinda ta mishi fa ya bashi haushi,
Murmushi abakar yayi musty ne kuma yace " kai haba mai jama'a karka wani bata ranka shareta kawai ai duk wayon amarya ko taki ko taso dole dai sai ansha manta balle wannan amaryar da tazo a lokacin da ake cikin halin rabbana atinaa.....kai da kake cike da yunwanta, share kawai AK yau dai insha allah bamu ba baccin dare har sai mun kai amarya dakinta"
"ko a kafadane kuwa", wani daga cikin su ya karasa mish,
wani kuma daga cikin su yace "kaga koh zance wasan buya,
kin daukar waya,
dama duk wata dojewa ya kare yau dole kuturu yasha ladan aski" Haka dai sukaci gaba da sakin layi suma,
kun san mazama sun iya sakin layi wani lokacin kamar dai mu mata π
.
Basu bar harabar masallacin ba sai da yawancin jama'a suka watse sannan suma suka shiga cikin nasu motocin suka dauki hanya a tsanake kuma a jere suke tafe gwanin burgewa ba tareda wani ya wuce wani ba, tun daga tudun wada har zuwa GRA gidan Sadeeq . """"""
""""Meenal kuma a gefeta gaba daya ta kasa masalta yanayin da zatace ta tsinci kaita a ciki yau juma'a da take da tabbacin cewa yau za'a mik'ata d'akin ta dan yanda taga ana ta shirye alamun sun nuna mata hakan,
a kasan zuciyarta ta sani bata bakin ciki ko kadan amma a gefe guda kuma cike take da fargaban auren nan da yazo babu shiri dan haka tun safe take gujema idanuwan mutane badan komai ba sai dan yanda abokan wasan su suke neman saki ta gaba da tsokana dan haka ta gudu can gefen Baba Malam dan nan ne bashi da cin koso bata baro can d'inba sai da aka taso daga masallacin juma'a saboda bak'in da tasan zasu cika sashen dan haka sai ta fice ta lallab'a ta dawo sashen su ta shige d'akin Baba Auta.
Kwance take a kan gado tunani ne kawai ya cika mata kai sai faman mulmula take daga farkon gado zuwa karashen shi kamar mai nakuda ko kuma ciwon mara,
a dai dai lokacin da hayaniyar mutane ya karu saboda walimar da ake gudanar wa na mata anan cikin gidan haka itama zuciyarta taci gaba da gudu bata kara sarewa ba har sai sanda kunnuwanta suka jiyomata shelan da malaman keyi cewa a fito da Amare Bata karasa jin karshen zancen ba tafashe da matsanan cin kuka tana mai ambatar innalillahi wa'ainnah ilaihir'raju'un........ Haka naci gaba da maimaitawa tun ina kukan da karfi harya zamana hawaye ne ke fita ba muryar ihu,
Ita Allah ya sani ba'a yanda ta tsara abubuwa suke zuwa mata ba, ita shikenan bata da halin da zata more nata rayuwar shi kenan kullum sai aureta yayi ta zuwa mata a hagun ce babu wanda yake damuwa da ra'ayi ko abinda take muradi, "Allah sarki su Meelat sudai sunji dadi wallahi komai nasu a tsare ba irin naga da yake zuwa da arangizo ba".
Ta fada tana mai cigaba da zubda hawaye "me yasa komai nawa baya zuwa a yanda nike son shi? alhamdulillah allah nagode maka daka tsaramin kalar tawa rayuwar a haka,ya allah ka sanyama wannan aure albarkha kasa ya zamto aure na karshe da zanyi a doron kasa, Allah ka bani ikon yima mijina biyayya a zaman da zamuyi ameen ya rabbi" ta fada tana goge hawayen idonta.
Pillow din dake gefenta ta rungume hakika ranar yau tamata zuwan bazatan da batayi tsammani ba haba dan Allah an daura aure babu shiri ai ya dace ace ita kuma a bata damar shiryawa da kyau kafin asa ranar tarewa,
Amma kowa ya azalzala kamar dai dama duk sun gaji da ita, in kayi magana ace kayi hakuri kayi biyayya,
"wato ni Abdul zai munafunta bayan na nuna mishi a'ah shine ya zagaye yaje ya koma ta sama ya nemi aurena ba tareda sanina ba a matsayina na bazawarar dake da yancin zabarma kanta miji shine harda zuwa gabana yana ma yan uwana mugayen addu'a wato tunda shi yasan abinda ya taka wato,hakika kullu yaci amanar koko"
ta fada ina tura baki
"nidai kamar mara gata duk lokacin aurena ba wanda yake damuwa dason jin ra'ayi na,duk yanda suka yanka hakan zanbi.
anyi na farko ba'a bani zabina ba duk da na nuna bana so,shine na biyun ma gashi a haka akayi shi,e mana to bashi gashi ba yanzun din ma bata canza zani ba,shi kenan nidai a kullum bani da zabi kenan? Amma ai ba laifin kowa bane laifin Mai Jama'a ne tunda yaje kai tsaye ya nemi aurena bayan na sanar dashi cewa ban shiryama wani aure yanzun ba,wato ma ni aka hade ma kai a gidan nan aka mai dani kamar wata bare wai daurin aurena ne akayi da yamma kawai dan sun mai dani zawarar da gaske,wai ace harda Sultana duk shegen gulma da tsegumin ta wannan karon ta kasa kwaso gulmar ni ta fad'amin saima aka hada baki aka karamin auren dole! Ita da take kawata ta amana da ita aka shirya aka kara gabatar da komai suka rufe ".
Kalmar auren dolen data furta ne yakara dawo mata yama tsaye a zuciya,
"Shin da gaske auren dole akamin?
Ko auren gata? "
Ta tambayi kanta,
a matsayita na bazawarar da tayi zaman aure na tsayin shekara 6 iyayenta suka kara wanke saurayi dal suka auramata,
saurayin daya kasance saurayin da bashi da tamka a fadar zuciyarta a wannan lokacin,taya zata kira hakan auren dole murmushine ya subuce mata "lallai ni mai sa'ace,to wai ma kukan me nike????? Ba amsa .............
Tana cikin wannan hirar tsakaninta da zuciyarta ta jiyo karar wayarta dake ajiye a gefenta,
mika hannunta tayi ta dauko wayar saidai kallo guda ta ma number din dake yawo akan wayar ne ya kayar mata da gaba,
" shike nan ni Aminatu ta faru ta kare iko da nuna isa kuma tsakanina da mutumin nan ai sai ta Allah maye kawai ka kira har ka gaji baza'a d'auki wayar ba" number din ba suna domin ban ajeta akan wayar ba har yanzun amma ko ciwon mutuwa takeyi kallo guda zata mata ta shaidata,
" Abdul Khareem" ta fada a bayyane tna mai murguda baki
"baza'a dauki wayar ba wato burinka ya cika bari ka kirani" ta fada tana mai kife wayar,ganin ba gajiya zaiyi da kiraba hakan yasa ta cire karar wayar gaba daya yanda koya kira bazata dame ta da karaba,inya gaji ai dole ya hakura da kira shima dauko wayar tayi da niyar in kasheta gaba daya sai gashi kamar mai hasashe tna daukar wayar sako na shigowa cikinta,ko bata budeba tasan dan anacen ne dan babu number din kowa akan wayar sai tashi,
dan tun jiya da Sultana ta amshi nata wayar da sunan zata kira bash tayi mishi albishir har yanzun bata dawo mata dashi ba data matsa da tambaya ma cewa Sultanar tayi wai ita dai ta manta inda ta ajiye wayar wallahi, sai da safen yau ne ta kawo mata wannan sabuwa ce kuma babu komai a kanta.
Tun kiran farko daya shigo wayar taga number din shi yasin tasan shine yasa aka dauke mashi nata wayan, Ba tareda ta karanta sakon ba na kashe wayar baki daya ta koma taci gaba da kwanciya,.
"Hummmm dan samari duk ka gama rawar jikin ka ai bazakusan nasara ya shuka tsiya ba sai zashi ganin gida,ba kana murnar kai angoba aiko ban tarewa yau boyewa zanyi inda babu mai ganina" murmushin mugunta tayi a bayyane tace "shawara mai kyau" harda tsallen jin dadi saida tayi daga kwancen da take
"yo ni hauka nike in tare yau lallai idan na tare yau tabbas gobe a gadon asibity za'azo aci gaba da ganin amaryaπ’ mugu kawai mai shan bakin Mata"
Ita kadai a daki Yayin da acan cikin gida mata ke cigaba da gudanar da biki babu kama hannun yaro domin dai ita d'ayar amaryar wato Fauxieyerh babu abinda yasha mata kai ta sake abinta tana walwala bata takura rayuwarta ba, bayan an gama walimar da aka nemi Meenal aka rasa can ta kofar baya wajen sashen su ya sa'eed masu kidin kwarya sukaja da'ira suma dai sai faman ihun kiran amarya meenal suke amma babu amarya meenal taki fitowa sai iyayen amaryar ne da su Sultana suketa kara'i domin ranar yau ba bakin ciki domin ko bakama Meenal kara kataka ba kayi Fauxieyerh ustaziyar gidan malam wacce da kyar ta yarda ta fito filin sai dai kamar soja haka ta zamar musu ko dan rausayar nan babu.
A can gidan Hajiya ko shiri sukeyi sosai na tarbar amarya gida ya cika dam da gayyar yan uwa da abokanan arziki bakin Hajiya yau dai yak'i rufuwa,
gefe guda kuma yan mata da samarin gidan ne suka shirya nasu shagalin suma sun rantse cewa baza'a barsu a baya ba dan haka suka ware gefe guda a harabar gidan suka kira masu decorations suka shirya musu shi ganin burgewa a cewar su tunda ya Abdul yace babu casu to sun san bazai hana na cikin gida ba,suma dai sun shirya sun kuma dau wanka duk wanda ka gani sai dai kace masha allah sai zabgaga kamshi sukeyi sunfa wanku,.
~~~~, Su kuma angwaye bayan sun baro gidan Sadeeq sun dawo tudun wada tun daga junction din gidan Hajiya zuwa fadar mai jama'a tarin motocin da suka gani faffake ya shaida musu cewa lallai jama'ar mai jama'a sun taru dan ko ina Abubuwan hawane fake Kama daga mashin keke napep mota da kuma wasu mutanen a waje,musty dayafi sauran bakine ya gaza shiru saida ya tanka "kai AK anya kakanka bai jika maka hatimi kasha a lokacin da yake raye ba kuwa?"
Ya fada tana mai kara bin motocin dake fake da kallo
"lallai halin mutum jarinsa my brother please say Alhamdulillah".. dariya sauran sukayi suna masu mai maita kalmar alhamdulillah di gangarewa yayi ta wani gefen daban ya fito ta saitin masallacin,duk da cewa an kammala liyafar cin abincin amma har yanzun dai akwai jama'a sosai a gidan bai shiga masallacin ba saida ya nufi gefen da motocin shi ke fake sannan yayi amfani da key ya bude motar ya zuba wayoyin shi hula da babbar rigar shi,kulle motar yayi suka karasa cikin masallacin shida su sadeeq da suka idar da alwallah yanzun,. Bayan an idar da sallah da yawa daga cikin abokan shi motocin su suka shige domin komawa unguwan unguwar malamai gaisuwar sirikai daga can kuma idan sun d'auko amarya wajen dinner za'a rΓ nkaya dan gogan yace ba uban da zaisa matar shi tayi dare a wajen wata uwa dinner dan ma maita ne yasa suka dage cewa sai anyi badan shi yaso ba,
sai da yaga da yawa daga cikin su sun wuce tukun shima dasu sadeeq suka shiga cikin nasu motocin suka takema sauran baya,tarin messages din dake wayar ya fara bi bayan ya bude data domin bama sauran sakonnin social media damar sauka suma,
da yawa daga cikin sakonnin na fatan alkhairi ne da taya murnar samun karuwar aure wasu daga ciki kuma na ban hakuri ne daga wadanda basu samu zuwa ba duba da yanda bikin yazo babu shiri,
*******"*******
A gefen hafees kuma bayan sun isa saida suka gabatar da sallah la'asar sannan suka shiga cikin gidan kamar yanda suka tsammata dam gidan yake da jama'a a hakan yaci gaba da kukku tsawa cikin mutanen duk inda yake tunani zaiga Aminatu ya dubafa bai gantaba,dan har maryam ya gani da sauran kawayen su amma wai suma basu san ina ta shigeba tun kafin daurin aure,dakyar ya samu ya gano Aunty Hassana maman Abiey can cikin filin rawa suna cashewa acewar su ko amaryar bata fitoba bazasu fasa abunda suka shirya ba.
*Ummiee ce*
[10/10, 11:24 PM] Ummiee Zaria: βοΈπ±π¨βπ©βπ§βπ¦ *DANGINA*π¨βπ©βπ§βπ¦π±βοΈ
*BOOK 2*
*PAGE 47*
Mom Abiey dan Allah ina Meenal take?
Nasan bazaki rasa sanin inda take ba, wallahi ina zaman zamana ya AK ya tasoni wai in kawo mata waya zaiyi magana da ita kinsan kuma ban isa ince mishi ban ganta ba raina ya b'aci a banza kuma nima yau bazan so in b'ata mishi raiba",
Dariya tayi "kai koh Hafees ai yau dai duk fadan mai jama'a dole ya daga kafa ko ka manta yau din babbar rana ce a gareshi?"
"Nidai taimaka ki kaini wajen ta in sauke wannan nauyin in huta,"
"Muje" tace dashi a yayin da tayi gaba shi kuma ya take mata baya,
Can sashen baba Auta suka wuce domin nan ne kad'ai inda yake da k'arancin cikowar mutane cikin falon suka shiga babu kowa a ciki domin tun bayan da su Baban suka dawo daga sallar juma'a suka shigo cikin gidan abinci kawai sukaci anan falon sai suka koma harabar gidan inda aka kafa rumfuna sukaci gaba da zama suna ganawa da nasu bak'in,
Dan haka sai nan din ya kasance shiru cikin jerin dakunan dake jere na k'arshe Mom Abiey ta kwan kwasa kafin ta bude kofar ta shiga da sallama shi kuma Hafees yana tsaye ta bakin kofa bai shiga cikin d'akin ba,
zaune ta iske ta a bakin gado dan tun bayan data fito daga wanka ta shafa mai take zaune a wajen tana tunanin yanda zatasa kaya ta shiga cikin gidan dan tasan da zarar ta shiga tofa ta shigesu a hannun abokan wasa dan tun jiya basu barta ta sarara ba dalilin sune ma yasa ta dawo nan d'in ta b'oyema ganin su,
ace warsu wai sun bada gari dan sunga alamar karfin jinin su itda Mai Jama'a duk wanda ya tsaya masu a hanya tofa kiyama zai zarce kobabu shiri dan haka sukam sun bada gari dan sunga alamar gara subi yarima susha kid'a dan wanda ya iya zuwa d'aya ya watsar da mazaje har 4 a rana d'aya tofa duk wanda yace zai shiga gaban shi yasan aradu ya tara,
kai gaskiya dai babu irin sharrin da basu mata ba wai ashe tsohon tuzurun dama duk wannan lokacin ita ya tsaya jira shi yasa yaki aure waya sani ma ko dama rabon a jikin shi yake dan haka nema auren ta da Sarki yazo a haka,
Ita kuma data gaji da iya shegen da suke mata sai tace musu "ai mazama ana musu auren dole mai yasa shima basu duba ko a dangi sun hadashi da wata ba? ko tsoron shi sukeji ne?"
kuma ta fada musu sudaiyi a hankali dan ita mutum ko shishshigi yafiye yima abinda take so bazai taba ci gaba ba balle kuma har yace zai so abinta take so sai dai kwabar shi tayi ta ruwa,
shi yasa wasu ma da suka kai hajar su kasuwa ko kallo basu samu ba balle a fara tunanin ta ina ciniki zai fada,hakan da tace musu kuma da wata karamar mara kunya takeyi a wajen dan wata yar balaja'u ce cikin yan uwan Maman AK da sukazo daga maiduguri inba gulma ba kinzo ma uwar ango biki ai sai ki tsaya a inda take koh?
Maye na wani kwaso jiki ki taho gidan su Amarya to ashe wai ita Ramlat din son AK takeyi shi kuma gogan kun dai san hali dan saboda itama gaba d'aya ya dauke kafa zuwa wajen kakan nin shi na gefen uwa,
To da labarin auren yaje musu dai ance wai harda suma tayi shine fa tun zuwan su ta kwaso jiki wai ita wajen Amarya zata sauka a cikin zuciyar ta kuma to take ta zauna da Meenal din dan taga uban miye ta fita da har shi AK ya zab'i Meenal din ya barta, ita kuma Aisha wacce suka zo gidan Malam din tareda Ramlat din itace
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 84 Chapter of 92