ya iskeni ita kuma tana makaranta bata kuma dawo da wuri ba, ya mukaji da k'arin hakuri ya mai jegon kuma? Tana dai lafiya koh"
"Hakuri sai mai aiki mai jego kuma Alhamdulillah suna lafiya su duka ita da Babyn ku shigo daga ciki"
Bayan ta suka bi zuwa cikin Sashen dake cike shima da matan tun daga kan yan uwan Aunty Murja Maman Raheenat d'in zuwa kan sirikan gidan Malam din su Aunty Billy matar ya Sa'eed Matar Farooq Yayan Meenal d'in dama sauran Matan yayyen Meenal din da wasu daga cikin yaran Malam mata suma,
A tsai-tsaye suka gaisa da mutanen falon hajiya bata yarda ta zauna ba sai fad'i take a nuna mata inda zatayi Sallah,
D'aya daga cikin d'akuna ukun dake falon Innar yara taja Hajiya, dan lokacin Mommy Hauwa tana Sallah itama,
D'aya bayan d'aya Meenal ta gaishe da yan uwanta mata dama matan yayyen nata suka ma juna gaisuwar rashin,
"Mai jegon tana ina?"
Meenal ke tambayar su,
Farida matar Farouq ne ta amsa mata da cewa,
"Tana cikin wancan d'akin"ta karashe da nuna mata d'akin da take nufi d'in,
Mikewa Meenal tayi zuwa d'akin babu mutane sosai a ciki daga Mommy Hauwa sai Matar malam na biyu Dije dake rik'e da jariri ita kuma Mommy Sallah takeyi,
Karasawa inda Dijen ke zaune tayi bayan tayi Sallama dijen ta amsa,sai da takai zaune a gefen gadon dijen ke tambayar ta " yanzun kuka iso", ita kuma ta amsa mata da,
"Eh" tana amsar yaron, dan kyakyawa abunshi sai saiyi yakeyi kamar zai bud'e ido sai kuma ya koma ya rufe,
Tausayin shine ya kamata har idon ta ya cika da kwalla,
Gaisawa sukayi da Dijen tayi mata gaisuwa kafin ta tambayeta uwar yaron,
"Tana cikin makewayi" cewar Dijen,
Yaron na rik'e a hannun ta har Mommy ta shafa add'o'in da takeyi bayan ta idar da Sallah,
Sabon gaisuwa sukayi itama Meenal d'in tayi mata gaisuwa,
"Ina ita Hajiyar take na ganki ke d'aya?"
Momy ta tambaya,
"Tana tareda Innan mu a wancan d'akin dake kusa da wannan"
Mik'ewa Mommy tayi ta fice daga d'akin bayan ta nad'e daddumar da tayi sallan ita kuma Meenal taci gaba da zama yaron rik'e a hannun ta tanaci gaba da kallon shi,
Jin motsin bud'e kofar toilet din da Raheenat tayi ne yasata d'ago kanta da sauri sai kuma ta mik'e da sauri ta d'aura ma Dije yaron akan cinyanta ita kuma da hanzari ta k'arasa wajen Raheenat din suka rungume juna Raheenat din kuma sai ta fashe da kuka saboda ganin Meenal din,
Mai makon Meenal din tayi aikin rarrashi ah'ah sai itama ta biye mata sukaci gaba dayin kukan,
"Amma dai kun san wannan ba abun kwarai kukeyi ba koh, ke dama Meenal zuwa kikayi dan ki sata kuka ne kome, ke kuma Raheenat tun safe fa kike kukan nan amma ace mutum ko gajiya da kukan bayayi, ai ko dad'ewar da kikayi a cikin bayin nasan zuwa kikayi kikasha kukan shi kafin kika fito, fisabilillahi in kuka na dawo da matacce ai duban nin mutane ne zasu dawo duniya bayan sun mutu suci gaba da rayuwa kuma, ki saketa tazo ta zauna taba yaron nan Mama tun bai fara kuka ba, bawan Allah dan ma ta same shi mai hakuri tunda ya fad'o sau biyu kawai fa kika bashi abincin shi"
Sababin da Dije keyi shi yasa Meenal ta sake Raheenat din bawai dan taso ba, tana share mata hawayen ta da sukak'i tsayawa, kafin ta kamo hannun ta ta zaunar da ita a gefen gadon itama ta zauna,
"ya kikeji a jikin ki akwai inda yake miki ciwo ta ciki ko ta waje?" Meenal ta tambaya,
Girgiza mata kai Raheenat din tayi alamun ah ah,
"Babu inda yake miki ciwo?"
"Babu kirjina ne kawai yake d'anyi min zafi kad'an kad'an"
"Sannu kiyi hakuri kinji, amma kinci abinci?"
"Meenal ban iyacin komai baki na ba dad'i ko yunwa ma banaji"
"Kuma dai kin san bazai yuwu ki rayu da yunwa ba, Mama Dije ki had'o mata tea da abinci taci yanzun dan Allah inta gama sai tasha magani ta kwanta"
To Dijen ta amsa dashi tana mik'ewa ta fice daga d'akin ita kuma Meenal ta zauna taci gaba daba Raheenat din baki wacce keba yaron Nono har ya koma bacci,
Bata tashi ba sai da Dijen ta dawo da abincin kamar yanda Meenal ta buk'ata sannan ta amshi yaron ta kwantar,
Sai da Raheenat ta shanye tea din ta faracin abincin kafin Meenal ta shiga toilet tayi fitsari kana kuma ta d'auro alwallah ta fito ta tada Sallah bayan ta idar bata tashi ba har saida ta gabatar da sallar ishsha'i Hajiya ma kuma ta shigo tayi ma Raheenat d'in gaisuwa,
AK ma ya shigo har cikin Sashen na Raheenat din yayi gaisuwa tareda su ya Sa'eed da Farouq da suka had'u bayan sun fito daga masallaci.
*UMMIEE ZARIA*โ๐ผ
[8/29, 10:40 PM] Ummiee Zaria: โ๏ธ๐ฑ๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆ *DANGINA*๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆ๐ฑโ๏ธ
*BOOK 2*
*PAGE 15*
Tunda suka shiga cikin falon yake ware ido yaga ta inda zai gano Meenal ko Hajiya sai dai dukan su babu wacce ta fito falon ya daiyi ma mutanen falon gaisuwa Mommy Hauwa ma dake d'aya d'akin da Hajiya take ta fito sun gaisa itama ya mata gaisuwa Raheenat d'in ma ta fito sun gaisa,
Bayan sun fito daga sashen na Raheenat gefe suka koma k'arkashin canopy d'in dake harabar gidan suna ci gaba da hira dan tunda aka idar da ishsha'i yan zaman gaisuwan suka watse sai ya zamana saura yan gidan kawai,
D'aya bayan d'aya matan su Ya Sa'eed suka dunga fitowa sunayin sallama da mazajen su, sai yayi yunk'uri kamar yace su taimaka su kira mishi Meenal sai kuma ya k'asa suna zaune a harabar gidan har karfe 10 na dare ya gota su Ya Sa'eed suka fara haramar komawa masaukin su, dan haka tare suka fito daga cikin gidan dasu Ya Sa'eed d'in sai dai su suna fitowa sukayi Sallama dashi suka shiga motocin su suka wuce masaukin su duk da ya musu tayin zuwa can gidan shi amma suka nuna mishi a'ah karya damu,
Bayan wucewar su shima cikin motar shi ya koma ya kwantar da kujerar motar ya kunna ac sannan ya sanya karatun qur'ani a radio din motar yana bi da sauti mara amo,
Lokaci bayan lokaci yake duba wayar shi a zaton shi wai ko hajiya zata tab'o shi suyi haramar wucewa suma tunda dare ya farayi sai dai kuma shiru,
Sai ya d'auki wayar da niyyar ya kirata kuma sai ya fasa,
Can dai daya kasa sukuni ganin ana neman k'arfe 11 sai kawai ya maze ya lalubo number d'in nata ya doka mata kira,
D'in din din wayar taci gaba da k'ara sai dai kuma harta yanke ba'a d'aga kiran ba, bai gajiya ba haka yaci gaba da danna mata kira ba k'ak'kautawa amma sai da ya mata kira 6 babu wanda ta d'auka,
Ajiyar zuciya ya sauke mai zafi,
To me ya samu Hajiya haka kardai ace hartayi bacci ne ta barshi a kofar gidan mutane ya dakon fitowar su,
Yau rana ta farko da yayi abunda bai tab'ayi ba,
Number d'in Meenal wacce ya dad'e da adanata a cikin wayar shi ya lalubo, ya dad'e yana k'arewa number d'in kallo wacce yayi saving dinta da emoji mai shape d'in ๐ heart,
Ya dad'e yana jayayya tsakanin shi da zuciyar shi, wannan tana fad'i mishi cewa ya kirata kawai dan wannan shine damar da yake dashi na samun kusanci a tsakanin su, yayin da wata zuciyar kuma take ce mishi yayi hak'uri kawai ya wuce ya tafi tunda dare dai ya riga yayi in yaso ai gobe ma rana ce, sai yasan yanda duk zaiyi goben dan yaga sun koma can gidan nashi da kwana,
Sai dai kuma a kokarin shi na fita daga kan number d'in nata kuma kawai sai yayi dialing number din ba tareda ya luraba har saida kara d'in d'in d'in da wayar take alamun cewa kiran yaje kan nata wayar ne ya ankarar dashi,
Da azama har wayar na neman kub'ucewa daga hannun shi yayi saurin yanke wayar yana sauke ajiyar zuciya kamar wani wanda ya had'u da abun tsoro, bai gama dai daita kanshi ba wayar nashi ta fara k'ara, k'ur yama wayar domin kuwa Meenal d'ince ta biyo bayan nashi kiran,
Kamar bazaiyi picking kiran ba sai kuma can dai kiran na gabda katsewa ya runtse idanuwan shi ya amsa kiran nata ba tareda yakai wayar kan kunnen shiba sai kawai ya sata a speaker,
"Assalamu Alaikum"
Tayi sallama daga gefen ta bayan ya d'auki wayar,
"Ameen Alaikum Salam, baku gama bane wai dare yana yifa kice ma Hajiya ku nike jira ina waje a inda mukayi parking d'azun"
Yana gama fada mata hakan yayi saurin yanke kiran ba tareda ya tsaya sauraren amsar da zata bashi ba, dan Allah ya sani bazaiso yaji cewar bazasu bishi zuwa nashi gidan daga bakin taba,
Ita ko ata gefen ta bayan ta idar da Sallah Maryam da Meelat ta kira a waya ta had'asu da Raheenat sukayi mata gaisuwa,
Ta dad'e zaune tare da Raheenat d'in a cikin d'akin dan ko lokacin dasu AK d'in suka shigo sashen tana jin shigowar su bata daiji fita zuwa falon bane shi yasa kawai tayi zaman ta bayan fitan su kuma cika d'akin da suken yayi da yayyin su mata nan kuma sabon hira ya b'arke akan mutuwar auren ta, da yike yawancin su tun bayan mutuwar auren nata basu had'u ba,
Kun san mu mata ba gidan mutuwa ba yasin ko cikin mak'abarta ne sai dai in hirar bata zoba amma sai anyi,
To hirar mutuwar auren Meenal d'in shi ya rage jimamin mutuwar da suke ciki aka cigaba da tattauna batun ko wacce a cikin su na tofa albarkacin bakinta daga masu ganin laifin Sarki sai masu ganin laifin Teemah,
Itafa gaba d'aya ma wallahi ta manta da batun cewa wai zasuje gidan AK dan tunda suka iso ita da Hajiyan kowa nashi sabgar kawai yakeyi,
Bata tashi tunawa ba sai da ta kira, koda ya kirata tana cikin yan uwanta suna hira ita kuma dama bata tab'a saving number din shiba shi yasa koda ya kirata bata san shi bane ganin dai cewa kiran ya katse shi yasa ta biyo bayan kiran dan taji ko waye kuma duk hirar da sukeyi ita bata san dare yayi sosai har haka ba,
Koda ya gama rattafa mata abunda zai fad'a ya yanke wayar, bata wani damu ba sukaci gaba da hirar su ita da yan uwanta, dan rabon da su had'u a waje d'aya irin hakan gaskiya an dad'e tunda ko biki sukeyi a gida duk wacce tazo d'akin uwarta take sauka sai dai a had'u a tsakar gida amma yau gasu kusan su duka dan ma wasu basu samu isowa ba sai gobe wad'anda suke kusan ne dai yau suka samu isowa,
Ita ko Hajiya a gefen ta tun bayan data idar da Sallah ta fito daga d'akin suka k'ara sabon gaisuwa da mutanen dake sashen har zuwa sanda Mommy Hauwa da Innar yara suka mata jagora suka shiga sashen sauran matan gidan suma suka musu gaisuwa bayan sun dawo kuma cikin d'akin da aka sauke tan ta koma aka gabatar mata da abinci taci,
Duk abunda akeyi tana ta lura dan ta kirga d'akunan dake cikin sashen d'akuna ukune a kalla kuma mutanen dake cikin sashen mata wad'anda tasan kwana zasuyi kun kusa ashirin ko fin hakan ma banda yaran su, to idan dare yayi wani irin kwanciya za'ayi har aji dad'in bacci shi take ta lissafi,
Sai dai bazatayi saurin bada kaiba tunda ita ba yarinya bace ta gane cewa shima daya gayyace sun zuwa gidan shi yana da nashi dalilin dan haka shiru zatayi tukun, duk zaman da takeyi lokaci lokaci take kallon agogo taga ko zai kirata, kuma itama koda ya biyo ayari suka shigo falon tsaf taji shigowar nashi kuma bayan Jidda ta shiga wajen tama ta k'ara jaddada mata cewa AK ya shigo ya musu gaisuwa dan ita Jiddan ma bata san cewa shine ya kawo suba tayi zaton ko da motar Meenal sukazo har sai da Hajiyar ta sheda mata cewa ai shine ya kawo su tukun,
Ganin cewa Meenal bata neme ta shi yasa ta share batun duk da dai ta yanke cewa idan 11 tayi taga bai kiraba kuma Meenal bata tada maganar ba ita zata kira shi dan gaskiya tasan in tace ta kwana a gidan bazata sake ba, in yaso ita sai ta bishi Meenal din ta zauna tunda ita zata sake a cikin yan uwan ta,
Sai gashi tun sha d'ayan bata buga ba da yaji shiru shi ya kirata, kuma duk kiran da yake mata tana kallo tsaf sai dai kuma itama sai ta wana shi kafin,
Haka yaci gaba da zama a cikin motar yana duba lokaci daga kan minti d'aya sai gashi anci kusan mintuna 15 ba Hajiya ba Meenal,
kamar ya tada motar yayi tafiyar shi dan yasan da gangan yarinyar nan ta shanya shi sai kuma dai ya daure ya k'ara ba zuciyar shi hak'uri ya danna ma number din nata kira a karo na biyu,
Wayar bata dad'e tana k'ara ba ta d'auka,
"Bakiga Hajiyan bane wai ko ya akayi ne kun shanyani a waje sai jira nikeyi duk mutane sun gama watsewa ko baku san dare yayi bane?"
"Umm nifa bazan bika ba anan zan kwana sai dai ko ita Hajiyar ne zata bika,"
"Oh kenan ma d'an iska kika maida ni tun dazun dana kiraki ma baki fad'ama Hajiyan sakon ba,"
Mtwss yaja tsaki mai tsayi bayan ya yanke wayar dan ranshi fa ya fara baci yanzun kam,
A bayyana ya furta,
"Kunga abinda nike ta gudu tun tuni kenan koh, Soyayya da kana nan yara, to ita wannan ma tun ban furta mata cewa ina son ta d'in ba tasan ta shanya ni a waje kamar wani dan iska anya yarinyar nan duk ranar data gane ina sonta ba sai ta mai dani sakarai ba kuwa?, ina ma amfanin haka gaskiya soyayya bata min adalci ba miye haka mutum duk yabi ya susuce,"
Hannu shi ya d'aura a saman kai ya yamutsa gashin kan nashi yana fesar da huci mai zafi,
"Wai yarinyar nan nufin ta duk zaman da nayi a wajen nan zai tashi a banza ne? Lallai ma naki wasa ne Wallahi baki isa ba, Allah yasa nima ina da gata a cikin gidan bari ma ki gani"
Ya fad'a yana d'aukar wayar shi ya lalubo number din Mommy Hauwa,
Babu b'ata lokaci ko ta dauki wayar da sallama,
"Aunty nace dan Allah kiyi ma su Hajiya magana su fito haka nan mu wuce dare yayi, na kira number din Hajiyar bata d'auka ba ban sani ba ko tabar wayar nata a cikin jaka ne kin san halinta kilama ta manta dani ne"
Ya d'aura da cewa bayan ya amsa Sallamar na Mommy Hauwa,
"Ayya kayi hakuri bayi in mata magana zasu fito yanzun babu mamaki kam in akace maka Hajiya manta tayi"
Ta fad'i hakan tana kallon Hajiyar,
Shi kuma daga can gefen yanke wayar shi yayi hankali kwance dan yana da tabbacin cewa wannan aikin kuma ya kammala ba Hajiya ba har ita d'ayar mara kunyar saita fito, dan haka sai yama kawai ya tada kujerun motar daya kwantar ya gyara parking din motar zuwa dai dai bakin gate din gidan ta yanda suna fitowa shiga kawai zasuyi,
Maida kallon ta wajen Hajiya Mommy Hauwa tayi bayan ta gama magana dashi,
"Hajiya ina kika ajiye wayar ki hala?"
"Me ya faru kike tambayar wayata?"
Hajiya ma ta tambaya kamar bata san akan me zatayi magana ba bayan taji komai na kiran da AK din yama Jiddan,
"Mai Jama'a ne ya kirani yanzun ashe tun tuni yana kofar gida yana jiran fitowar ku, ai dai ya kyauta wallahi da bai wuce ba, dan dama ina ta tunanin yanda za'ayi bacci a sashen nan yau, gashi har daren ma yayi, yace ya kiraki ba'a d'auka ba shine ya kirani ai gara kuje can d'in zakifi sakewa ma, ai dama kayan ku yana cikin motar koh naga baku shigo nan dashi ba?"
"Ke barshi kawai ai dare kuma ya riga yayi kirashi kice nace yaje kawai saida safe zamuyi kwanan mu anan, ai dama ba munzo jin dadi bane"
"Ah ah Hajiya dan Allah kuje kawai tunda har Allah yasa bai tafi ba koni ai dan dai kar aga mun kwasa duka mun tafine da nima binku zanyi can din, bari in kira Meenal itama tunda ta iso suna can sun kule d'aki sai hira suke kamar ba'a gidan mutuwa suke ba, "
Jidda bata fito a d'akin ba sai da ta taso Hajiya a gaba suka fito a d'akin a falon suka had'u da Meenal wacce sai yanzun ne ta fito da niyyar zuwa ta isarma Hajiya sakon AK din,
"Yauwa gara da kika fitoma muje Kunbar min d'a acan waje yana jiran ku ga dare yayi"
Cewar Mommy Hauwa,
"Mommy nifa anan zan kwana ai na fad'a mishi sai dai Hajiya ta bishi"
"Ke dallah can ban son maganar banza, ita Hajiyar ce zata tafi can din ita d'aya ina ce tare kukazo dukan ku, wuce ki d'auko Jakar ki ki fito ku wuce dare na k'arayi"
Badan Meenal taso ba haka ta koma d'akin ta d'auko jakarta ranta a b'ace, lek'awa d'akin itama Hajiya tayi dan yin Sallama da mutanen cikin,
Sai da suka rakasu Hajiyar har bakin motar AK din dake kofar gidan, gidan baya Hajiya ta zauna kamar lokacin da sukazo, Meenal ma gidan bayan ta bud'e zata shiga Mommy Hauwa ce ta hanata da cewa,
"Shi din driver din gidan ku ne da kema zaki koma baya ki kame ku barshi da tuk'aku? Dallah koma baya keda baki san abun arziki ba"
Simi simi ta wuce ta bud'e gaban motan ta shiga ran nan nata a bace, sallama suka musu suka juya cikin gidan shi kuma yaja motar suka bar kofar gidan ranshi fess duk da yana ganin yanda Meenal d'in ke ta faman b'ata rai baibi ta kanta ba tuk'i kawai yaci gaba d'ayi,
Kamar yanda yayi alqawari sai da ya koma ta chawai ya siya musu chips din da Meenal tace tana so da kazar sannan sukaci gaba da tafiya, shida zai d'auke hanya zuwa malali kawai sai ya mik'e zuwa unguwan Sarki koda ya isa inda suke siyar da ice cream din bai tayama Meenal shiga wajen ba fakawa yayi yaje ya siyo musu ya dawo motar ya k'ara bata wuta suka koma daga baya zuwa Malalin,
Sai da yayi ta yawo dasu akan tituna kafin ya d'auke hanyar gidan shi, daga Hajiya har Meenal dai babu wacce ta tanka mishi a cikin su dan ita Hajiya dama tunda ta shigo wayar take amsa wayar Baba Usman dan haka bata damu da sanin ina yake kaisu ba sai dai in taga ya tsaya ta d'ago taga inda suke taci gaba da wayarta,
Ita ko Meenal duk da cewa a cikin zuciyar ta taji dadin yanda ya cika mata alkawarin daya dauka taji dadi amma sai ta fuske abunta taci gaba da hura hanci duk da dai daurewa kawai take amma wallahi ta matsu su isa gidan nashi kafin ta bada kanta sakamakon kanshin chips dana kazar da suka mamaye cikin motar basar wa kawai takeyi amma da lafiya lau ne tabbas da tun a cikin motar zata fara aikasu zuwa masaukin su,
"Bieeee" din daya danna ne ya dawo da hankalin ta kan kofar gidan da yake tsaye saboda tunda suka shigo cikin layin take faman bin gidajen layin da suka shigo din da kallo, gidaje a tsare lafiyayyu wanda kai bawa ko baka tambaya idanuwan ka ne zasu shaida maka cewa unguwan bana yaku bayi bane, dan gidajen sun jeru ne wannan yana wane wannan dan kyau,
Waigawa tayi dan ganin ko Hajiya ta lura da abunda ita take kallo sai taga Hajiya ko a jikin ta hirar ta kawai takeyi,
Sulalawa da motar yayi zuwa cikin gidan bayan an bud'e mishi gate d'in,
Tun kafin ya faka take faman k'arewa gidan kallo,
Hajiya dake bayan motar ita ta fara fita ba tareda ta jira ya bud'e mata kofa ba wannan karan,
Mutuniyar ko sai da ta kwamuso ledar kaji dana chips din ta kafin ta fito daga cikin motar.
[8/30, 3:18 PM] zainabusmanummiee584: ๐ฑโ๏ธ๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆ *DANGINA*๐จโ๐ฉโ๐งโ๐ฆโ๏ธ๐ฑ
*BOOK 2*
*PAGE 16.*
Shiko AK bayan ya faka motar baya ya koma zuwa wajen mai gadin dake bakin gate ya na ta kokarin kullewa,
"Assalamu Alaikum Malam Mansoor barkan mu dare fa ya gida?"
Ya fad'a yana mai dafo kafad'ar Mansoor d'in bayan ya bashi hannu sunyi musabaha irinta maza,
"Alhamdulillah Ranka ya dad'e barka da dawowa, ai ina ta zuba ido tun bayan da muka gama waya da kai sai kuma naji shiru, wallahi kaga yanzun hakan ina batun in kiraka a wayane inji ko dai ka fasa dawowa yau d'in ne sai kuma gaku, to barkan ku da isowa fa dafatan an baro mutanen gidan lafiya ya hanya kuma? "
"Alhamdulillah ai mun ma shigo garin tun d'azun wallahi dan a cikin Unguwan Dosa ma muka gabatar da sallan Magriba da yike rasuwa akayi mana a can d'in, mu k'arasa ku gaisa da Hajiya tare muke dasu anan zasu dunga kwana kafin su tafi"
Ba tareda ya saki hannun Mansoor din ba sukaci gaba da tafiya har suka isa bakin kofar dasu Hajiya ke tsaye suna jiran ya k'arasa ya bud'e musu kofar,ita dai Meenal tunda ta fito daga cikin motar take ci gaba da bin gidan da kallo, ba wani wargajeje bane wajen girma sai dai kuma gaskiya ya tsaru dan sosai ya d'auki hankalin ta sai faman kalle kalle take duk kuwa da cewa dare ne amma kana iya ganin komai da aka kawata gidan dashi a zahiri sakamakon kwayayen wutar lantarkin da suka haska gidan,
Har k'asa Mansoor din ya duk'a ya gaishe da Hajiya ta kuwa amsa mishi cike da kulawa, Meenal dai bata jira ya gaisheta ba ita ta fara gaidashi dan ko babu komai ya girme mata nesa ba kusa ba,
AK ne ya bud'e kofar suka shige ciki shi kuma mai gadin ya musu sai da safe ya koma,
A falon gidan dukan su suka zauna,
"Wash Allah na gaji wallahi" cewar Meenal a yayinda takai kwance,
"Ai zaki gaji kam daga dawowa makaranta baki ko huta ba mun kamo hanya sannu ki samu kiyi wanka da ruwa masu dumi kafin kiyi bacci sai kiga kin warware koda gari zai waye bazakiji gajiyar a tare dake ba"
Cewar Hajiya,
"Hajiya d'an wannan tafiyar ne har kike cewa sai tayi wani wanka da ruwan zafi?
Nida na d'auko hanya mai nisa na taho abinci ma a daddafe aka bani shi naci ga kuma shanyani da kukayi a kofar gidan mutane bayan na tuk'o ku daga Zaria zuwa Kaduna ko sannu baki min ba, ai dama na lura wallahi tunda yarinyar nan ta koma wajen ki kika dena tunawa ma kina dani, ni kuma na kasa zuciya in gyale ku keda itan nima in koma inda za'aji dani! "
Ya k'arasa fad'a rannan a had'e shi a dole an mishi ba dai dai ba,
Dariya Meenal ta fashe mishi dashi harda kyakyatawa tana nuna shi da yatsa,
"Kai amma wallahi Allah taubashi kana da abun ban dariya, to wai dama kishi kakeyi dani ashe ban sani ba"
Juyawa gefen da Hajiya take tayi tana ci gaba da dariyar nata take cewa,
"Hajiya to ga autan kinan fa yana kishi dani dan Allah shima kice mishi inyaje bacci yayi wanka da ruwan zafi saboda kar gobe ya kasa zuwa masallaci sallan asuba saboda tsabar gajiya, kujimin fa Babban shi dashi wai yana kishi dani, to ma ce maka akayi dama
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Chapter 74
Chapter 75
Chapter 76
Chapter 77
Chapter 78
Chapter 79
Chapter 80
Chapter 81
Chapter 82
Chapter 83
Chapter 84
Chapter 85
Chapter 86
Chapter 87
Chapter 88
Chapter 89
Chapter 90
Chapter 91
Chapter 92
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 54 Chapter of 92