Allah ya nufeki da yin magana kafin mutuwarki kya bada labarin zaluncin da kika aikata, duk da bana fatan Allah ya baki aron wannan damar, gwara ki tafi da tarin alhakin mutane ta yanda za ki ɗanɗani abinda kika shuka tun a ƙabari kafin ranar tsayuwa a gaban ubangiji, Azima insha'Allahu har mutuwarki babu me yafe miki abin da kika masa domin ke ɗin azzaluma ce".
tana gama faɗar haka ta bar bakin windon tana kuka.
hango tahowarta yasa Zaytuna fitowa daga mota tazo ta kama hannunta.
Hajiya Madina ta kalleta ta girgiza kai tace,"your excellency".
Mum ta ɗaga kai ta kalleta, sai Maama tasa tissue tana goge ma ta hawaye.
"don Allah ki daina zubar da hawayenki ga wacca bata kamaci a zubar ma ta da hawaye ba, duk da irin tsananin halin da take ciki, masu imani ake yiwa kuka ba azzalumai irin Azima ba".
sai kuma ta numfasa ta ƙara cewa,"in dai ina raye Allah har Azima ta mutu ba za ki ƙara zuwa inda take ba, balle ki dinga zubar da hawaye haka a banza, ba gwara ki tara mana hawayen ba idan abin farin ciki ya same mu ki yi".
"na daina ma daga yau, ba zan ƙara ɓarnatar da hawayena ba akanta".
"better!, ki godewa Allah da ya saka miki tun daga nan duniya".
da sauri Hajiya Ramla ta ɗago tana dubanta da mamaki.
Hajiya Madina tayi murmushin da ya tsaya a iyakar leɓenta sannan tace,"ban da masaniyar wanda yay miki asiri kika bar gida, but haka ɗaya nake jin zuciyata ta kasa aminta da Azima, zato zunubi ko da ya kasance gaskiya amma ni dai ita nake zargi, shiyasa ko kaɗan bana tausaya ma ta, wallah in har itace silar asirinki da na me babban suna da yardar ubangiji sai tayi mutuwar wulaƙanci".
tayi shiru tana rufe idonta na sakanni sannan ta buɗe, sai kuma ta juya topic ɗin da cewa,"yanzu me babban suna suka shigo, ba ki gansu ba gwanin sha'awa sunyi kyau sosai, sai naji kamar ni ɗaya nai sa'ar haihuwar ɗa me kyau da kuma dacen balarabiyar sirika".
Hajiya Ramla tayi murmushi. "ai ce nake ba za su zo ba, dan ɗan naki yayo halin kafiyarki".
"yanzun ma na faɗa musu sannu ce kawai ta kawo su, da zarar sunyi ma ta sannu ko ta amsa ko bata amsa ba suyi tasowarsu su tafi".
Hajiya Ramla ta girgiza kanta,"da ba ki ce musu haka ba ai".
"hakanne ma yasa na hanasu zuwa wurinki nace su wuce wurin Boɗejon kai tsaye, kana tausayin me tausayinka ne, haka kana mutunta me ganin mutuncinka".
ƙafafun Turaki suka shiga cikin parlon kafin na Babyn roba su bi bayansa, ya kama hannun Fillo da ke rakuɓe a bayansa suka shiga ciki.
su ka zauna da ga ɗan nesa inda Boɗejo tasa wata hadimarta tayi musu nuni, tun da akace ma ta su ne ta sunkuyar da kanta, har suka zauna kuma ko ɗago kai bata yi ta kalle su ba don bata tunanin iyayensa ma sun isheta kallo balle shi kansa da wata sillan karan matarsa.
Fillo ta kalleta taga tamkar bata san da shigowarsu ba, sai taji wani abu me kama da tsoro ya kamata, ta kalli Turaki suka haɗa ido, cikin bin umarnin da yay ma ta da ido ta buɗi baki ta ce,"Boɗejo ina yini, ya sauƙin jiki?, Allah ya ƙara miki lafiya yasa kaffara".
ta haɗe duka maganarta a lokaci ɗaya, dan ta san abu ne me kamar wuya Boɗejo ta amsa ma ta, ile kuwa kamar yanda tayi tsammanin uffan ba ta ce ma ta ba.
Turaki ya kama hannunta ya riƙe wanda yake jin yana rawa a jikinsa. ransa ya ɓaci sosai, daraja ɗaya Boɗejo zata ci haifar Baffa da tayi, ya rumtse idonsa ya buɗe, ya danne abin da yake ji yana taso masa a zuciya ya ce,"tsohuwa ashe ba kiji daɗi ba, na san ba komai bane sai kewata ko?, to ai gani na zo kuma naga sai wani ciccin magani kike yi, ko ba'a maraba da ganin nawa?".
ya faɗa cike da tsokana dake tsakaninsa da Kakar tasa.
ta ɗago tayi masa wani kallo me cike da ban haushi ta ce,"munafiki, mara mutunci, wanda ya kunyata ni akan kucakar ƴar aiki, wanda ya fifita mace akan bin umarnin mahaifinsa, kai har kana tunanin muryarka ma ina ƙaunar ji ne, ai tuni na sallamaka acikin jikokina, saboda haka ka bar bin wata hanyar shishshige min, ranar da Amaryarka ta koma ɗakinta wataƙila ma iya shiryawa in akwai rabon hakan".
yay murmushi me faɗi har da sauti yace,"ashe zamu shirya ɗin dai, yanzu dai ya jikin naki kin ji sauƙi ko ya?".
ta galla masa harara,"ina ruwanka da lafiyata, ka ga tun kamin raina yay mugun ɓaci tashi ka fita ka bar min waje, idan ba haka ba na ƙwala ihu yanzu na ƙalawa wannan ƴar banzar yarinyar sharrin da babu wanda zai iya ƙwatarta duk duniyar nan".
fuskar Turaki ta washe da murmushi ya ce,"yo ba tana da Allah ba, shi ai zai ƙwaceta, yanzu dai ban gaji da ganinki ba kya bari in gama kallonki tukunna sai ki kora ni, ke kawai daga yi miki kishiya duk sai bi ki zama fitinanniya, wannan kishin naki yayi yawa".
ta jijjiga kanta ba tare da tace da shi ƙala ba.
Fillo ta miƙe ta ɗauki manyan ledojin da suka shigo da su guda biyu, taje gaban Boɗejo ta tsuguna ta ajiye, muryarta ta fito very cool da cewa,"ga wannan ba yawa, Allah ya ƙara miki lafiya".
ta numfasa, ta ɗora hannunta akan ƙafar Boɗejo, cikin taushin murya tace,"don Allah kiyi haƙuri, Allah ya huci zuciyarki, da ni da shi duk bamu da laifi, zanen ƙaddarar mu ne ya zo a haka, tun kafin zuwanmu duniya ubangiji ya rubuta cewar zamu kasance a inuwa guda ɗaya, Allah ya rubuta hakan a lauhul mahfuz, dan haka ni ko shi ko wani babu wanda ya isa ya sauya abin da Allah ya rubuta zai faru, illa kawai mu roƙe shi ya juyar da abinda zuciyoyin mu basa so su zama alkhairi a gare mu, ya kuma saka mana haƙuri da dangana mu karɓi lamarin a yanda yazo mana".
tayi ƙoƙarin ɓoye kukan dake shirin ƙwace ma ta. "don Allah don Annabi kiyi haƙuri ki daina fushi da kowa, duk mun san munyi miki laifi, babu wanda yaƙi bin umarninki, babu wanda zai so abin da ba kya so, kawai dai babu yanda zamu yi da lamarin da Allah ya shirya dole zai faru ne. don Allah Boɗejo ki daina fushi da Maama da Mum, haka ki daina fushi da mijinmu".
ta ƙarashe maganar su na haɗa ido, sai Boɗejo taji wani abu da bata san menene shi ba ya tsarga ma ta akan Fillo, abu ɗaya ta sa ni kamar yarinyar tana da wani girma na kwarjini wanda ba zaka san da hakan ba zai ka kalli ƙwayar idanuwanta.
duk sai taji ta kasa yi ma ta cin mutuncin da tayi niyyar yi ma ta a duk ranar da tayi tozali da ita, alwashi ne da ta ɗauka, so tayi duk ranar da suka yi ido huɗu sai ta yiwa Fillo abin da zai sa ta bar gidan Turaki da ƙafafunta, tayi tafiyar da ba zata taɓa dawowa gare shi ba.
idanuwan Fillo suka manne akan mirrow ɗin da ke fuskantarta, murmushi ya suɓuce a saman leɓenta wanda ita kaɗai ta san tayi shi, hatta Turaki dake kallonta ba zai ce tayi ba.
Boɗejo ta haɗe rai tana ɗauke hannun Fillo akan ƙafarta ta ce,"Malama ta shi ki bar kusa da ni, kuma ki ɗau tsiyarki, ki kai can ƙauye inda ake yunwa, amma ba nan inda aka fi ƙarfinsa ba".
Fillo ta marairaice murya ta ce,"tuba nake ranki ya daɗe, ina barin kusa da ke ne kawai idan har an dubi girman laifin da na aikata an yafe min ba, hakan kaɗai zai sa in sami sukuni da salama. Kaka bata fushi da jikokinta, ko da tayi hutu ne ta ɗauka saboda ta huta da rashin jinsu, ranki ya daɗe namu hutun ya isa haka a tausaya mana".
mamaki ya hana Boɗejo cewa komai, ƙaramar yarinya kamar wannan ta iya zaro zancen tsari irin haka, zancen da tana da tabbacin ba har zuciyarta take yi ba, tsabar kissa ne kawai.
"ka taso ka dawo nan".
muryar Fillon ta fito ta wuce kai tsaye zuwa cikin kunnuwan Turaki, ya rufe bakinsa da ya buɗe yana kallonta tun ɗazu, ta sakar masa wani kyakykyawan murmushi da ya sa shi tasowa babu shiri, sannan nata murmushin ya ƙaru a sanda ta kuma yin tozali da madubin.
ya zauna kusa da ita, ya kama hannunta guda yana murzawa, tare da kai hannu ya ɗauki apple dake cikin plate, ya gatsa sannan ya kai bakin Boɗejo ya ce,"Uwar gidana".
ta mangare hannun nasa, ta taso masa cikin masifa har sai da Fillo ta ƙanƙame shi saboda tsorata ba tare da ta san tayi hakan ba. shi kuma yay saurin kewayeta da hannunsa yana cewa da Boɗejo,"yi a hankali tsohuwa Baby bata son hayaniya".
sai ya ɗan narkar da murya yace,"kin ga kin tsorata min ita ko, haba don Allah Boɗejo wannan wanne irin fushi ne haka da ba'a hucewa, ce nake tun da har yarinyar nan ta riga ta tare shikenan komai ya wuce".
ya faɗa yana shafa bayan Fillo, ita kuwa tun da idonta ya ƙara ƙyallawa ya sauka akan mirror ɗin ɗazu sai ta ƙara shigewa jikinsa tana sakin makirin nishin firgici.
Boɗejo kuwa zazzaga masifa da zagege da baƙaƙen maganganu kawai take yi, tana ta zagin kafatanin ahalin Fillo, da Hajiya Madina, ran Turaki ya ɓaci sosai yay ƙasa da kansa, ya kasa ko da motsi ƙwaƙwƙwara.
tun shigowar su Turaki parlon Ilham ita ma ta shigo ta ɗayar ƙofar, ganinsu yasa tayi turus a wajen, tayi tsaye ba tare da sun san tana wurin ba, ji take yi kamar ta juya, amma sai taji ta ka sa ɗaga ko da ƙaramin yatsanta, jan ƙafarta ma take so tayi but shi ma ta kasa, ji take yi kamar an daskarar da ita ne a wurin.
kuma a lokacin da Fillo ta faɗa jikin Turaki sai ji tayi kaman an kunna gobarar wuta a ƙirjinta. duk sai taji ta rasa me yake yi ma ta daɗi acikin ranta, tun da ta baro gidansa bata ƙara ganinsa ba sai a yau, yau ɗin da take ganin kamar an sauya shi, ya ƙara kyau ya ƙara kumari, annurin fuskarsa ya fita daban da asalin yanda ta san shi.
sai taji masifar son shi da kishinsa ya ƙara bin sassan jikinta, yau shi ne gabanta da wata mace da ba ita ba, macen da ta san ta fita asali, kyau, nasaba, ilimi kai komai na rayuwa ta san ta fi Fillo.
a gaban idonta yake ririta ƙwailar da ta san bata da uban komai bacin kyau irin na ƴaƴan aljanu, har yake rungumeta a jikinsa alhalin ya san a cikin gidan su yake.
duk sai taji duniyar ta ƙara yi mata zafi, taji kaman ta samu wuƙa taje ta ɓurmawa Fillo, gwara ta kasheta kawai ko ta samu ta sami sauƙin raɗaɗin ciwon son Turaki da kishinsa da ke neman hallaka ta.
tana ganin sun miƙe za su tafi zuciyarta ta yanke shawarar zuwa ta bangaje Fillo, ta hankaɗata daidai saitin in da idanuwanta ke hango ma ta garwashin wutar da aka ajiye wanda akewa Boɗejo gashin ƙafa da shi.
without second tought ta baro bakin ƙofar ta taho gadan gadan kamar wacca ake tunkuɗowa. idon Fillo ya ƙara sauka akanta ta cikin mudubin, kamar tasan abin da Ilham ɗin ke shirin yi, tana ganin ta kusa zuwa in da take, da gangan tai saurin wuntsilawa gefe zata faɗi aikuwa a kiɗime Turaki ya tarota yana faɗin Subhanallah.
"Fulani Nah yi a hankali, am sorry kinji, hankalina na kan wannan tsohuwar ne".
ta ɗage ƙafa tana cije fuska tace,"ka daina bani haƙuri ba kai ba ne".
sai ta dafa shoulders ɗinsa ta ɗago tana duban Ilham dake gefe ɗaya tana faman huci tace,"ina yini, ya mai jiki, Allah ya sawwaƙa ya tashi kafaɗunta. kiyi haƙuri ban san za ki wuce ba da ban tsaya a hanya ba".
Ilham taja dogon tsaki na baƙin ciki da takaici, ta bar wajen tana jin zuciyarta kamar zata ƙone.
Turaki ya bi bayanta da mugun kallo, ya dunƙule hannu yana ɗauke idonsa akanta.
"ita ta bige ki?". Fillo ta kalle shi tayi narai-narai da idanu kamar zata yi kuka ta ce,"don't bother your self, mu tafi kawai kaga ran Boɗejo a ɓace yake".
sai ya tallafota jikinsa ya juya ya fuskaci Boɗejo, muryarsa na shaida zallar ɓacin rai yace,"wurinki muka zo ba wajenta ba, a da nake da hurumi da ita amma a yanzu ban da wata alaƙa da ita, ki ja mata kunne karta ƙara gigin illata min Mata ko da kuwa bisa kuskure ne, dan ba zan ɗauka a hakan ba. ina da sauƙin kai but akan wannan jaririyar da ke jikina ina iya rufe ido na manta duk girman alaƙar dake tsakanina da ko wanene in ci zarafinsa, wannan jaririyar tafi min duk wani mutum a duniyar nan bayan mutum uku, domin ta sadaukar da ranta da lafiyarta akaina tun kafin ta san waye ni, ta cusa kanta a haɗarin da ko wanda yake sona ba zai iya ba, saboda haka nake mutuntata, nake martabata, nake darajtata fiye da ƙima, fiye da lissafi duk wani me tunani. zan ɓata da ko waye matuƙar ya nemi ya cutar min da jaririyata, if not zan manta da alaƙa in nuna the bad side of me, hakan kuma babu wanda zai yiwa daɗi".
a hasale Boɗejo tace,"to ai ka rufe mu da duka ni da ita shi ne kawai, mene wani gargaɗinka, gargaɗin banza da zai bi ta iska, ai rama ma ta kawai zaka yi, wato ga Ramla an taɓa ko Zaytuna dole ka nuna baka da mutumci".
ya rufe ido yana ƙara dunƙule hannunsa, Fillo ta riƙe shi ganin kamar yana ƙoƙarin aikata abin da ba zaiwa kowa daɗi ba.
ya buɗe ido yana kallon Boɗejo yana ta huci yace,"kamar yanda Baffa ba zai iya haɗaki da Mum ba, haka ma ni, amma ki sa ni, gwara a taɓa Zaytun akan a taɓa wannan, saboda haka me kiyayewa ya kiyaye, wanda ba zai iya kiyayewa ba kuma ya shiga sata gonar Muhammad Turaki".
yana gama faɗar hakan ya duƙa ya ɗauki Fillo suka fice, tana ta cewa ya sauketa amma yaƙi, hadimai da dakaran gidan sai kallonsu suke yi har suka shiga mota.
ɓangaren Ilham kuwa su na fita ta kalli Boɗejo tana nuna kanta ta ce,"ni yarinyar nan zata haɗawa sharri, ko fa taɓata fa banyi ba Boɗejo, amma ki ga irin maganganun da Hammah yake faɗa, to wallahi ko ban da niyyar komawa gidansa sai na koma, zata gane tayi da ni".
ta miƙe tana barin falon haɗe da yin ƙwafa me girma wacca ita ɗaya ta san ma'anarta.
a hanya Turaki ya tsaya ya sayi kaza da takeaway na mandi rice. tun da suka taho daga shi har Fillo babu wanda yay magana a motar har suka koma gida.
yana yin parking Fillo ta buɗe ƙofa ta fice tai tafiyarta, shi ma kuma ko da ya shiga part ɗin bai bi ta kanta ba ɗakinsa ya wuce, ya sakar ma kansa shower sannan ya kwanta akan gado ya runtse idonsa, tunaninsa guda ɗaya ne, Anya zai dawo da Ilham cikin gidan nan?.
ya daɗe kwance yana lissafi acikin kansa, kafin ya buɗe ido ya sauko akan gadon ya fita, ɗakin Fillo ya shiga, zaune ya ganta akan gado tayi shiru kanta jingina da gadon, ya tsaya yana kallonta kafin ya ƙarasa bakin gadon, yana zuwa ya ɗaukota ya fito da ita zuwa ɗakinsa.
*LULLUƁIN BIRI*
*©️Halima h.z*
*54*
akan kujera ya zaunar da ita, idanuwan Fillo suka manne akan hannun Turaki da suke cikin plate ɗin abincin da yayo takeaway, abincin da ta san ya siya ne saboda ita, ba don shi yaci ba.
ya ɗebo ya kai bakinta, har yanzu ɓacin ran da ke saman fuskarsa bai gushe ba, idanuwansu ya sarƙe ana juna, ta kaudar da hannun nasa da ke nufar bakinta.
"ban ji daɗin yanda ka yiwa Boɗejo ba".
ya rufe idonsa bai ce komai ba.
"don Allah kar ka ƙara, ko babu komai ita ce fa ta haifi Baffa, tana da girman da bai kamaci ai faɗa ma ta kowacce irin magana ba saboda ɓacin rai".
still idonsa na rufe ya ce,"ba don hukuncin ubangiji ba, sannan ba don ke da taimakonki ba, da yanzu bana raye, ko kuma da ban kawo yanzu da lafiyar da zan yi tafiya ba, da yanzu wataƙila ina kwance marabata da matacce numfashi kawai, kuma wataƙila da har yanzu ban ga mahaifiyata ba. saboda haka girmanki da nake gani yafi gaban tunani, kina da girman da ba zan iya ganin an ci mutunciki na ƙyale ba".
ta buɗe baki zata yi magana ya ɗora yatsansa a leɓenta,"shhhh bana son magana, ki ci abinci".
ta kalli abincin ta ce,"bana ci".
"saboda me?".
"saboda kaima ba zaka ci ba, me yasa zaka tsaya siyan abinci bayan na iya dafawa, and beside da ka siyo bafa ci zaka yi ba, so kake ka kwana da yunwa?, ban iya rashin adalci ba kuma ba zan fara ba daga yau, Ummi ta jaddada min sau babu adadi cewar kar na taɓa barinka da yunwa".
kafin yay magana ta miƙe, ta kamo nasa hannun shi ma ya miƙe.
"muje kitchen na dafa mana abin da zamu ci".
ya dakatar da ita,"kin gaji ba za ki iya girki ba, kuma kinga akwai ciwo a ƙafarki".
"ni ban gaji ba". ta faɗa tana saƙalo hannunta guda a wuyansa sannan ta ƙara cewa,"idan ƙafan na ciwo ai sai ka ɗauke ni".
murmushi yay tare da ɗaukarta su ka fita a ɗakin, su na saukowa downstairs kitchen ya nufa, sai da suka shiga ya ajiyeta, ya kama ƙugu yana cewa,"zan ga yanda ake aiki da gurguwar ƙafa".
tayi murmushi me sauti tare da jan gemunsa ta ce,"to ai da ka ɗauko ni na warke".
ya buɗe ido yana kallonta,"ƙatoto da ni kika yiwa wayo?".
ita ma ta kama nata ƙugun ta ɗaga kai sama ta juya idanu, sannan ta ce,"me zamu ci?".
"duk abin da aka girka da waɗannan siraran hannun zan ci".
ta dafa kafaɗarsa ta ce,"ummm Maama ta taɓa cewa kana son soyayyan indomie, so yau zan ci abin da kake so ni kuma bana sonsa, but na san daga yau zan fara so, in dafa ko?".
ya ɗaga ma ta gira yana jin wani daɗi a zuciyarsa, ta wuce ta ɗora tukunya a gas, ya bi ta yana faɗin zai tayata, ta dakatar da shi,"no ba yanzu ba, zaka fara girki but not today not now, but one day. for now just sit and watch".
kujeran dining ɗin dake kitchen ya ɗauko ya zauna gefe daga in da cooker gas yake, kafin ta gama yankan albasa idonsa duk ya cika da ruwan hawaye saboda yajin albasar, tuni kuma suka zubo, sai ƙyafta idanu yake, Fillo duk na kallonsa tana ƴar dariya, tace,"me aka maka kake kuka?".
ta tambaya tana dariya ƙasa-ƙasa.
"ni kike yiwa dariya?".
ya miƙe zai bar kitchen ɗin ta maido shi ya zauna tana faɗin,"sorry, idan ka fita ina jin tsoro".
ya ƙanƙace idanu yana kallonta cikin tarin ruwan da ya cika idonsa,"Fulani Nah idona yaji".
"ni dai ka zauna haka, ina gama yankawa zai daina ai". ta faɗa tana narkar da murya, haka ya zauna babu yacca ya so, har sai da ta gama yankan albasa tukunna ta wanke masa fuska a sink.
wayarsa tayi ringing yana dubawa yaga Sameer ne, yay picking Sameer na faɗa masa ga shi ya kawo masa ticket ɗin.
ya kalli Fillo ya ce,"Fulani Nah zan amso saƙo wajen Sameer".
tayi shiru kamar bata ji shi ba har sai da ya ƙara kiran sunanta.
ta ɗan ɓata rai ta ce masa,"to ya shigo parlo ya jiraka mana, idan mun kammala sai mu same shi, ni ba zan iya jira idan ka fita ba, kafin ka dawo dodon kitchen ɗin ya cinye ni".
yay murmushi yana girgiza kansa,"my drama queen". sannan yace da Sameer ya shigo ya jira shi a parlo ga shi nan fitowa.
wucewar minti goma ta kammala suyar indomie ɗin, sannan ta haɗa pineapple juice, tana sane take ta delay dan ita bata cika son Sameer ba, musamman ma idan tana tuna ƙullin da suka dinƙa yi akan su kashe Turaki.
"na gaji ka zo ka wanke min hannu".
ta faɗa a sanda ta nufa sink ta tsaya. ya taso ya tsaya ta bayanta, ya kama hannayen da suka shige cikin nasa, ya zuba morning fresh ya wanke ma ta.
ta ɗauka abincin da tasa a plate shi kuma ta ba shi jug da cup ya riƙe suka fita, Sameer yana zaune yana jan tsaki kaɗan kaɗan saboda ya fara gajiya, ta ajiye plate ɗin akan table tana gaida shi, ya bawa Turaki ticket ɗin yana faɗa masa ba'a samu flight ɗin 8 ba kamar yanda ya ce, sai na 9 aka samu.
kaɗan Sameer yaci indomie ɗin, shi ma saboda Fillo ta takura ne, bayan tafiyarsa suka koma kitchen suka ɗauki na su sannan su ka wuce upstairs.
kamar yanda ya zamar musu jiki yanzu, kuma kowannen su ya saba da hakan, ba wanda ke iya cin abinci shi ɗaya, sai dai su yi feeding junansu, yanzu ma tare suka ci abinci.
su na ci Turaki na zuba santi, ita kuma sai taji tamkar bata taɓa ƙin cin indomie da ƙwai ba saboda yacca take enjoying feeding ɗin nasa.
bayan sun gama ci Fillo ta fita a ɗakin ta wuce nata, shi ma toilet ya shiga bayan fitarta, yay wanka sannan yay alawala ya fito ya wuce masallaci, bai dawo gidan ba sai da akayi sallar isha'i.
ɗakinsa ya wuce direct, shigarsa ya tarar bata nan hakan yasa ya fita ya koma nata ɗakin, nan ɗin ma bata nan, ya murɗa handle ɗin toilet nan ma bata ciki, sai yaji faɗuwar gaba ta kama shi, cikin sauri ya fito sai gata tana hayowa upstairs ɗin.
doguwar ajiyar ya sauke, ya harɗe hannayensa a ƙirji, idonsa akanta yana duban wata riga da take ninkewa.
"ina kika je?".
"yaushe ka dawo?".
ya fizgota jikinsa,"answer me first".
"kayan da zan bayar na ɗauƙa na kaiwa su Sakina".
"su waye hakan?".
"ƴan aiki mana".
"me yasa ba ki faɗa min ba?".
"to ai masallaci ka tafi".
ya mintsini gefen cikinta da faɗin,"kuma daga kai musu kaya sai kika zauna hira".
"ummm ina son hira da su sosai, da yake ƴan ƙauyen su Yami ne, ina son ƙauyen na su yana da daɗi shiyasa idan naji su na hira sai nayi ta tambayarsu wuraren da na sa ni".
ya karɓi rigar hannun na ta,"ita wannan ɗin ya ba ki ba su ba?".
"tayi musu kaɗan, waɗancan ɗin ma duk sai an buɗa musu".
murmushinsa me sauti ya fito, yaja hancinta yana cewa,"ke ma kin kusa yin ƙiba ai".
ya riƙe hannunta su ka wuce room ɗinsa, toilet su ka wuce ta wanke masa gashin kansa da yace yana yi masa ƙaiƙayi.
su ka fito tana tsane masa kan da towel, ya zauna kan stool tana cakuɗa yatsunta acikin gashin tana sosa masa bayan ta shafa wani oil.
ta cikin madubi da take kallonsa ta ce,"bacci?". ta tambaya ganin yanda idanuwansa suka sauya yana faman lumshe su.
ya girgiza ma ta kai yana ƙara luma hannunta cikin sumar.
"to ni idan ma baccin ne ka kore shi, ka fa ce zaka ban labari yau me daɗi".
ya miƙe daga kan stool ɗin yana juyowa ya fuskanceta, numfashinsa ya shiga busawa akan furskarta.
cikin kasalar da yake jin tana neman lulluɓe shi gaba ɗaya ya ɗaga hijab ɗin dake jikinta ya cire, ya dinƙa kallonta musamman breast ɗinta da suka bayyana sosai a cikin sleeping dress ɗin.
sai duk taji nauyi da kunya sun kamata, ta taka zata bar wajen ya janyota, ya ɗaura kanta a ƙirjinsa ya zagayeta da duka hannayensa, yana jin wani abu na fizgarsa akanta.
Fillo ta rufe ido ta buɗa hanci tana shaƙar daɗin ƙamshin jikinsa. taji ya warware gashinta da tayi parking, kafin a hankali taji ya kira sunanta da amon sautin da ya zama kamar ba nasa ba.
"Fulani Nah".
ta ce "ummm".
ya nutsa yatsunsa cikin gashin kanta yana barbaza shi a fuskarta tare da kissing forehead ɗinta, sannan cikin taushin muryarsa yace,"I always want you very close to me Fulani Nah".
maganar ta shiga jikinta sosai, tayi shiru tare da ƙara lafewa a ƙirjinsa, tare da zura hannu cikin rigarsa ta kama wasa da gashin ƙirjinsa, tana jin yacca bugun zuciyarsa ke
All Chapters
Chapter 1
Chapter 2
Chapter 3
Chapter 4
Chapter 5
Chapter 6
Chapter 7
Chapter 8
Chapter 9
Chapter 10
Chapter 11
Chapter 12
Chapter 13
Chapter 14
Chapter 15
Chapter 16
Chapter 17
Chapter 18
Chapter 19
Chapter 20
Chapter 21
Chapter 22
Chapter 23
Chapter 24
Chapter 25
Chapter 26
Chapter 27
Chapter 28
Chapter 29
Chapter 30
Chapter 31
Chapter 32
Chapter 33
Chapter 34
Chapter 35
Chapter 36
Chapter 37
Chapter 38
Chapter 39
Chapter 40
Chapter 41
Chapter 42
Chapter 43
Chapter 44
Chapter 45
Chapter 46
Chapter 47
Chapter 48
Chapter 49
Chapter 50
Chapter 51
Chapter 52
Chapter 53
Chapter 54
Chapter 55
Chapter 56
Chapter 57
Chapter 58
Chapter 59
Chapter 60
Chapter 61
Chapter 62
Chapter 63
Chapter 64
Chapter 65
Chapter 66
Chapter 67
Chapter 68
Chapter 69
Chapter 70
Chapter 71
Chapter 72
Chapter 73
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 61 Chapter of 73